Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yaje ya barwa Lahab Nnenna abinka da kasar turawa babu gulma babu sa Ido dakinsa Lahab ya wuce da ita har lokacin bai yarda sun had'a Ido ba tana Zama ya kawo Mata abinci,kafun ya Shiga yayi wanka ya sauya Kaya cikin t-shirt Mai kyau da wando dogo roba sai p-cap ya daura akan gashin kansa ya Yama wata arniyar aski, haraman fita yayi da sauri ta Mike ba tare da tayi magana ba kallonta yayi suka had'a ido,yayi saurin kauda nasa Yana magana cikin eiiieiiina yace"ya dai"?


"Zan bika"d'an zaro Ido yayi yace"muje Ina"Inda zaka"shuru yayi sai Kuma yace toh shirya muje mikewa tayi tayi wanka fita yayi a dakin ya zauna a kujera a kofar dakin Yana jiranta,wando tasa pencil Baki sai ta dau riga ta sanya ta kawo jacket ta d'aura akai gashinta ta daure ta sanya socks da boot nata,ta daura agogon hannnu ta daura, fitowa tayi a dakin wannan karon ma again Suka Kara had'a Ido dashi,kallonta yayi wannan Karo sosai sai itace ta kauda tata fuskar mikewa yayi ya koma cikin dakin sai gashi da veil medium baki matsowa yayi kusa da ita har Suna had'a numfashi da yake tana da tsaho tsakanin su babu nisa sosai amma dai yadan fita sosai,Yana kakkauda fuska yafa Mata yayi akai yayi rounded nasa a fuskarta ya gyara Mata tayi kyau kafun ya juya ya Soma tafiya binsa ta Soma a hankali a baya.





Motar wani abokin aikin su Lahab ya karba Suka wuce hotel insu Ade, daukar da sukayi daga nan Suka fita cikin gari sosai Suka ringa yawo a hankali-hankali Lahab da Nnenna suka dan sake jiki da juna har waya Lahab ya baiwa Ade yayita d'aukar su hoto da vedio duk Inda sukaje,sunje har cikin kankara, Suna ta hotona su kayi ciya ciye gashi Lahab ya Fara Zama popular yanzun suk Inda ya Shiga sai kaga ana Kiran sunan sa wasu su basa memo Koh wani Abu ya musu sign,Basu Suka dawo ba sai dare.



Daman sun riga sunyi dinner a waje Suna isowa wanka sukayi dukansu Suka sanya kayan bacci da yake daki d'aya ne babu yanda ya iya haka ya hau gadon ya kwanta itama kwanciyar tayi Suka bar space Mai yawa a tsakanin su a hankali bacci ya dauke Lahab,da misalin karfe 1 Lahab ya farka tare da dan juyawa zai gyara kwanciyar sa sai Kuma ya dan bude idanunsa da kyau ganin wajen Kamar ba mutum hannu yasa ya taba wajen kwanciyar ta Nan ma babu Nnenna,mikewa yayi zaune ya kunna hasken dakin.




Zaune take a kasan tiles ta tasa laidan da suka ci abinci Suka rage tun kafun su fita, ta lasheshi tass harda drinks in kana ta zauna tayi tagumi gabaki d'aya daga ka ganta kaga Wance take cikin damuwa hannu yaga tasa ta share hawaye da Suka saukomata a kumatun mikewa yayi a hankali ya sauka a gadon har lokacin bata San ya farka ba a hankali ya Soma taka kafafunsa a tiles in Yana nufar Inda take da Sauri yaga ta juya Suna had'a Ido ta Mike tsaye cikin kunya tana tattara kwalaye da laidodin abincin zata bar wajen,hannu yasa ya kamo nata Yana kallon ta sosai kana yace.........................



*Banyi Alkawarin na dare ba Amma Inna samu lokaci zanyi*

*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*




Wai menene haka don Allah meyake damunki"?girgiza Kai tayi tana kokarin kaucewa zata aje laidodin sake Mata hannu yayi ya kwace laidan yaja hannunta ya Kamota Zama yayi da ita a bakin gadon shima ya zauna kana yace"Wai meke faruwa ne na ganki cikin damuwa Kuma kincemin babu kome"?matsa Mata yayi lalle saita fada Masa meke damunta kuka ta fashe dashi sosai cikin Sauri ya rungumeta gam a jikinsa ya koma baya-baya ya kwanta da ita a jikinsa,Yan@ kwance a dollof ita tana kwance a kansa,hannu yasa ya kashe wutan.




Labiba"ya Kira sunan ta a hankali kin amsawa tayi har lokacin hawaye bai tsaya a fuskarta ba,a hankali ya manna bakinsa a kumatunta hawayen Nata yake lashewa,lumshe Ido tayi tana d'an sake jikinta a nasa sosai ya lashe hawayen tas Kuma hawayen ya daina zuba,dan Jan lips nasa yayi a fuskarta har zuba gefen lip's nata sannan ya tsaya Yana bin fuskar da kallo,idanunta a lumshe suke jira kawai take taji saukan lips nata a nasa amma taji ya tsaya cak,dan bude idanunta tayi sai Kuma da Sauri ta kauda nata saboda tsayuwa da yayi kawai Yana kallon ta,"kin koshi da abincin Koh a kawo Miki wani"?girgiza Kai kawai tayi batace kome ba,sakin murmushi yayi a hankali ya zamar da ita a jikinsa ya kwantar tare da gyara Mata rufuwa shima ya rufu tare da kamo hannunta ya rike Yana bin fuskarta da kallo kawai.




A hankali ta matso kusa dashi tare da manna jikinta a nasa,waro Ido yayi da mamaki sai Kuma yasa hannu ya dagata jabal ya daura a kansa,lip's nata ya Kama amma bai tsotsa ba kawai mannawa yayi da nata,dan Jimm tayi sai Kuma ta Kama lips nasa na kasa cikin sanyi ta tsotsa,Kama nata yayi Suka hau bawa juna hot kissing sosai salon wasan ya chanja duk wani kunya kunya gabaki dayansu ajesa sukayi a gefe sosai Lahab ke sarrafa matarsa yayinda ita Kuma ke basa goyon Baya dari bisa dari,lokacin da kome ya kankama Lahab yasha mamaki matuka Kuma ya rude don dadin da yaji na yau ya d'ara na Ranan dadin da yaji sosai.




Lokacin da nutsuwar sa ta samu kokarin tashi yake a kanta da Sauri tasa hannu ta Kama waist nasa gam,Wanda hakan ya fahimtar dashi cewa itama tana bukatar nutsuwarta duk da akwai mutuwar jiki da gajiya a jikinsa hakan baisa sa kasa tallafawa matarsa ba sosai ya tallafeta har ta samu natsuwa,mikewa yayi a hankali ya d'auki towel NASA wanka yaje yayi kana ya fito mikewa tayi itama ta shiga toilet in kafun ta dawo Harya chanja zanin gadon ya kwanta,tana fitowa Zama tayi daga ita sai towel,shuru shuru yaji Bata hau Kan bed in ba kallonta yayi kana yace"lafiya bazaki kwanta ba kinsan karfe nawa yanzun"?shuru ta Masa Bata hauro Kan gadon ba,shima Bai Kara magana ba ya gyara kwanciyar sa so yake ya samu bacci kafun asuba don gobe Suna da training da sassafe,amma kasa baccin yayi ya sauka akan gadon d'aukarta yayi gabaki dayanta yazo ya kwantar akan gadon ba tare da ya damu da towel in jikinta ba ya lulluba Mata blanket.



************
tashi tayi ta zauna again Wanda hakan ya saka sa sake tashi agogo ya gani kusan 2:30 na dare tsaki kawai yayi yace"Wai don Allah wannan ai d'aukar alhakine ya Zaki kasa bacci ki hanani nima"?a fusace tace"toh ninace maka karka kwanta ne"toh Taya Zan kwanta kina zaune"a hankali tace"yunwa nakeji"wani kallo ya Mata sai Kuma ya tashi tsaye hannu yasa ya taba jikinta Jin sanyi babu zafi yasa sa komawa ya kwanta abinsa Bai Kara magana ba ya barta a zaune bacci barawo yayi awun gaba dashi.






da asuba Lahab daya farka da mamaki Nnenna ya gani d'aure da towel Kamar yanda ya kwanta ya Barta idanunta biyu da mugun mamaki yake tambayar ta Wai Bata kwanta ba?kin amsa Masa tayi yasa hannu zai tabata kawai ta turesa Saida ya koma Kan katifa ya kwanta,bata Kara magana ba shima gyada Kai yayi irin lallai innan ma, ya mike Alwala yayi yazo yayi sallah duk tana zaune,Kaya ya chanja ya fita waje da asuban amma shuru babu kowa shaguna duk a rurrufe dakin wani makwancin sa ya shiga yadau fresh milk guda biyu ya kawo Mata kin karba tayi Wai tayi fushi daker ya samu ta karba tana Sha Koh aje goran batayi ba ta Soma amai Kamar zata amayar da hanjin cikinta sosai tayi aman lokaci d'aya wani irin zazzafi ya rufeta,daukarta yayi ya Kai toilet tare da wawwanke Mata jikinta ya fito da ita, Kaya ya sanya Mata ya kwantar da ita akan gado kafun yazo ya gyara wajen da ta batan.




Wanka yayi da misalin karfe 6 zuwa lokacin wani irin bacci yayi gaba da ita so yake suje asibiti Kar ciwon yayi tsananin amma ganin tana bacci tunda bata samu na daren jiya ba sai yayi tunanin bari ya barta sai ya dawo,kayan ball yasa wando da riga sai takalmi ya fita a dakin, direct training ya wuce basu Suka bar wajen ba sai kusan 9 na safe daga wajen wajen Saida abinci ya wuce kaza yasai musu sai kayan ciye ciye na laida Incase kada ta bukace Abu lokacin da bazai samu ba shiyasa ya sama Mata irin su cake su pizza duk ya sassaya sosai ya Mata sayayya.





Lokacin da ya dawo ya samu ta farka zaune take gabaki d'aya ta jirkita ganinsa da laida Koh barin ya ajiye batayi ba ta kwace tare da budewa cake Inda ta gani a ciki shita warware da Sauri ta Soma ci ci bana Wasa tama cake in ba,shidai Lahab idone nasa ba bakin magana amma yasan tabbas Bata da lafiya wallahi irin wannan haukan cin Kamar Wanda ta shekara da yunwa,Kamar d'azun da asuba tana gama ci sai amai,ganin haka yasa Lahab cewa ta tashi su tafi asibiti amma kai da fata Nnenna tace ita lafiyarta klau babu Inda zata,taba jikinta yayi yaji babu zafi Kamar d'azun, tambayar ta abinda zataci yayi tace apply,mikewa yayi yaje ya jido apply kwali guda fresh dasu yazo ya jera Mata a daki Aiko shikenan Nnenna ta samu abinci Bata da aiki saicin apply tunda kome taci amai yake sata Amma Banda shi.





Lahab yaga ikon Allah gabaki d'aya Nnenna ta sauya ta Zama mabukaciya don tun tana kunyarsa tana jiran shiya Fara tabata Harya kasance ita ke nuna tana sonsa a aikace ba'a bayyane ba,shima Yana iya bakin kokarinsa wajen sauke nauyin da Allah ya daura Masa akanta Koh da kuwa baya mood,ga cin apply ga fad'a fushi da mita duk yanzun Nnenna ta koya cikin satin da sukayi harta chanja Sosa ga yawan zazzabin asuba da kuma yamma, sai yace su tafi asibiti tace bazata ba suyita fada Harya hakura ya kyaleta.




Sun samu nasara sosai Lahab Yayi bajinta a wasan da suka buga yasha musu sosai,hakan yasa sa daukaka sosai,sun koma gidan su,sannan team nasu sun basa kudi sama da million biyu cikin abinda Suka samu saboda bajintarsa cikin kudin ya baiwa Ade have million sannan ya turawa Rahab 300k ya baiwa uzaifa 200k tunda Sunsan Inda kudin ya fito lokacin da ya tura musu basuki amsa ba account ya Kai Nnenna ta bude ya zuba Mata kudin da shayibu ya basa nata kana ya Kara Mata 100k a ciki,Lahab a sannu sannu ya Fara Zama sannan ne a fagen kwallon kafa don sosai ya iya buga wasa hakan yaja Masa farin jini da daukaka har yasa wasu team Fara daukar sa haya Yana buga musu Wasa ba tare da sun damu da kankantar sa ba kudi kuwa sosai ya Soma damkarsu sosai Kuma Alhamdulilah Lahab mutum ne da baida gyashi kome ya samu sai ya tsamma Rahab dake India da uzaifa haka zalika zaisa wa Nnenna a account nata duk da Bata cin Koh sisi haka zalika Adewale don yanzun tuni Suka bar gidan da suke lahab ya Kama musu gida Mai zafi wadacece Suka koma ciki don wani sa'in sai afi wata Ade Bai hadu da Nnenna ba waje d'aya sai in ya shigo part nasu Lahab ga moto Lahab ya saya ya saima Ade duka rayuwa tayi Dadi bana Wasa ba tuni papan Ade yayi sanyi lokacin da ya kawowa Ade ziyara yaga yanda Allah ya daukaka Lahab Kuma Yana taimakon dansa har dawainiyar makarantan Ade yanzun Lahab keyi,Amma tuni ya manta da zancen wani Nabeel don tunda yazo kasan Bai taba kiransa ba saidai in Suna waya da Ade in Yana gun shine inya tambaye shi sai Ade yace gashinan su gaisa.





Lahab sun koma makaranta tuni har semester yayi nisa yaso yasa Nnenna a makaranta Amma babu Hali tunda Bata da shaid'an takardun Gama secondary,ga rigimar da take fama da ita nata na masifa ga yawan ciye ciyen kayan fruit don yanzun tabar apply ta koma kankana da mangoro Koh Kuma abarba.




Lokacin da labarin Lahab ya Fara zaga katsa tuni Yan nageria Suka Soma Jin labarin sa wani Dan naija best footballer Kuma very young a turai gashi da farin jini bana Wasa ba duk channel na sport ba'a rasa nasa a ciki,lokacin da labari ya Fara riskan Mami tunda ba kallon kwallon take ba sai Yan uwa ke kiranta Suna cewa sunga Lahab na ball a TV koransa tayi tana Masa fada akan an turasa karatu yaje ya Kama abinda bazai amfane saba Bata yarda ba,Aiko waya yayiwa Abbu ya sanar dashi dare da Masa Alkawarin insha Allah zai kammala karatunshi tare da sakamako Mai kyau daker dai Abbu ya sauko ya baiwa Mami hakuri ya cigaba da Wasa tunda sunga kokarin da yayi a karatu.






tun safe Lahab ya fita Bai dawo ba saboda Wasa da suke bugawa Mai zafin gaske bashi ya dawo gida ba sai kusan 2 na dare,shigowa falon yayi ba tare da ya kunna wutan ba ya wuce sait nasu bude dakin su yayi ya shiga da sallama,dan waro Ido yayi ganin wutar dakin a kunne ga Kuma Nnenna kwance a bargo"Kai amma yarinyar Nan bakiji taya Zaki kwanta da wuta a kunne"kashe wutan yayi ya zaro tafkeken wayarsa dake bag dake bayansa ya kunna hasken waya aje bag in yayi yadau towel ya nufi toilet wanka yayi kana ya fito,daure da towel in kayan bacci yasa ya fita a dakin kitchen ya wuce ya tare coffee nasa Mai zafi ya zauna a dinning dake cikin kitchen in ya Soma Sha Saida yasha Rabin cup kafun ya mike.




d'akin ya shiga tare da matsowa kusa da gadon hannun sa yasa ya warware blanket Inda ta lulluba zai kwanta da Sauri ya sake blanket in, saboda turirin da yaji ya fito daga cikinsa har yanajin wucin numfashinta Mai zafi Ashe idanunta biyu sai rawan d'ari take hannu yasa ya tabata da Sauri yaja baya zafi jikinta jaujau"subhanallah Labiba tun ba yauba nasan baki da lafiya amma rashin jin da Kika kakkabawa kanki yanzun ya hanaki Bari muje hospital"?kasa amsa Masa tayi bakinta ya bushe sosai hakoranta har haduwa suke da juna,mikewa yayi da sauri ya nufi wardrobe nata budewa yyi ya dauko Mata wando da riga amma irin bujennan masu Fadi yasa Mata hijab ya dauko cikin Wa'inda ya sai Mata duk da ba amfani yake dasu ba Kuma hijab in irin have Sunnah ne.






A daren nan Lahab ya dauketa sai Wani hospital Mai tsada, a cikin daren Nan aka amsheta zuwa lokacin zazzabine yaci karfinta sosai ruwa Suka daura Mata tuni tayi bacci sai gwaje gwaje da aka mata,a asibitin Lahab ya kwana tare da ita tana farkawa da safe ta Fara Neman abinci Kuma ta tashi garau abinta,fita yayi ya sai Mata abinda zataci taci kana aka sake daura Mata ruwa.




8:21pm zaune Lahab yake a Kan kujeran dake dakin dayake kowani mutum d'aya dakinsa ne guda ba'a had'a wani da wani zaune take ta tasa kaza a gaba tana ci hannun ta d'auke da ruwa a makale, don Koh barin a cire batayi ba ta Soma ci shi Kuma Lahab ya Barta Bai Kira nurse ba gudun kada ace ya kawo cinnedu amusu dariya,wayarsa ne yayi Kara zarowa yayi yayi picking up"Lau Ade Labiba ce babu lafiya Muna hospital amma karka damu fa jikin da Sauki sosai"yayi shuru Yana sauraran abinda Ade ke cewa sai Kuma yace"no ka tafi school kawai yauma sukace zasu sallame mu basai kazo ba sai Kuma ya katse wayar"Kara kallonta yayi ganin tana tauna kashin kaza"Amma wallahi kin chanja haba Dan Allah kece ci Kamar me Amma Baki karuwa sai ma rama da kikeyi sai haske amma dai ba kome hips da breast sun ciki"?





Kala batace Masa ba dan yanzun Sam babu irin kunyan da a tsakanin su bare taji kunyar sa Koh kunyar abinda yace"amma dai da ace bakicin nama har yanzun da anyi babu ke tsabar dadi har kashin cinya kike tumurmusawa,dan Allah kici Naman dake gefen plate in kibar kasusuwan Nan in Naman ya Kare Zan sayo Miki wani amma ace mutun ya aje nama ya kamacin kashi salon wani ya shigo muji kuny..................bai karasa ba aka bude kofar dakin da Sauri Nnenna ta sake kashin hade da boye plate in gudun Kar aga taunannun kasusuwan data aje a ciki.




Dariya kawai Dr tayi ta karaso cikin dakin,hade da turo kujera d'aya ta zauna kusa da Lahab kana ta kalli Nnenna ta kalli Lahab tace"Kamar u look familiar"dan murmushi yayi yace"Hassan Lahab the footballer"?oh oh really great footballer nice to meet,am Dr jeme John by name"hannu lahab ya Bata sukayi musabaha, don tsohowace ba yarinya ba,had'a fuska Nnenna tayi amma batace kome ba kallon ta again Dr tayi tace"gaskiya ya Kamata ki fito da abinki kici gaba daci,ba kunya ta dauko plate nata taci gaba dacin Naman Amma Bata tauna Kashi, kana tacewa Lahab wacec ita Nnenna a wajen sa"?





dan shuru yayi sai Kuma ya cije yace matarsa ce, waro Ido baturiyar tayi ya nuna Nnenna yace matar ka?gyada Mata Kai yayi, shuru tayi don ita duk zatonta Koh yar'uwa Koh friend ne Koh girlfriend,tunda taga irin kyau da Nnenna kedashi gashi zaman turai ya karbeta sosai tayi fresh da ita sai Kuma ta d'aga kafada kana tace,ok anyway congratulations ur wife is pregnant.



Ji kake karaaararam plate na nama ya Fadi a hannun Nnenna saiga hawaye Shar mikewa tsaye Lahab yayi da karfi yace"what?...........................






da mamaki Dr tace yes she is pregnant bakace wife nakace ba"?komawa Lahab yayi ragob akan kujera gabaki d'aya yanayin sa sun sauya sabanin Nnenna da tayi shuru tana dai zaune a Bakin gado ba yabo ba fallasa ta sanya hannayenta ta cikin rigan tana shafa cikin,da Sauri Lahab yace"how many months ne Dr,Mika Masa result na hannunta tayi jikinsa a mace ya karba yayi Sai Kuma ya rumtsa idanunsa da karfi cikine na wata uku da sati uku,kallon Nnenna yayi sai yanzun yaga irin chanjawar da tayi amma dai ckinta Na nan a shafe Kamar babu halitta a cikinta.





Shuru yayi Bai Kara magana ba haka zalika itama Nnenna batace kome ba har ruwan ya Kare aka sallame su tare da bude Mata file na zuwa Ayo a wajen su,haka suka Kama hanyar silently Suka koma gidan yayi parking budewa yayi ya fita ba tare da yajirata ba itama binsa tayi a baya hannu yasa ya bude kofar flat nasu, Adewale dake zaune a falon tun safe mikewa yayi Yana tambayar Lahab Ina Mai jikin,bai rufe Baki ba sai gata ta shigo,wucewa dakin sa Lahab yayi ya maida kofar ya rufe ba tare daya baiwa Ade amsa ba sai Nnenna data tsaya Suka gaisa ya tambaye ta jikin nata kana itama ta wuce dakin ta.




Tura kofar dakin Lahab yayi ya Shiga zaune ya gansa yayi tagumi,tsayawa yayi a bakin kofar ya harde hannu don har lokacin Lahab baisan ya shigo ba,matsowa yayi ya dafa shi sai a lokacin ya dawo hayyacin sa ya kalli Ade sai Kuma ya sake tsaki"Wai Lahab lafiya meke faruwa ne wai me akace Yana damunta donni Karan kaina Naga Rama a tattare da ita Kuma kace tanacin abinci sosai"?Mika Masa paper kawai Lahab yayi Baiyi magana ba"amsa Ade yayi ya duba sai Kuma ya sake murmushi yace"daman irin wannan Rana nake guje maka Lahab shiyasa tun farko na nuna maka illan wannnan sure da zakayi"





"Wallahi Ade nayi auren Nan bada niyar a waye gari tayi ciki ba"oh kana nufin ka aure tane don ka ringa sex da ita karta haifi Y'ay'a Kamar kowace mace"?bazaka gane ba Ade taya Zan dau ciki Koda nakai nageria a matsayin nawa kasan Abune Mai girman gaske"




Cikin mamaki Ade yace daman tunda ka Fara kwanciya da ita baka tanadi abinda zaka fadawa gidan ku ba akanta nufinka Randa zaka koma gida rabuwa zakuyi Koh yaya"Koh saboda yanzun ka zama celebrate shiyasa bazaka iya Zama da ita da ciki ba"?da Sauri Lahab yace Ade bazaka gane abinda nake nufi ba wallahi Koh sau daya ban taba tunanin rabuwa da Labiba ba Amma Ina Jin tsoron kada mu tafka kuskuren da bunayya da muwaddat(Aisha bagudu)sukayi"Aiko ku kunma fiso tunda su Koh banza iyayen su Sunsan da auren jama'an garine Basu sani ba dasu kansu ma'aurantan Saida Suka tafka aika aika Amma daga karshe duk da haka an Kira cikin ta da shege bare kaida babu Wanda yasan zance.





Yanzun Ade menene mafita"mafita dayane Lahab ta haihu ka tattarata ku koma nageria Kama danginka bayani insun amince ai shikenan"wani kallo Lahab ya Masa kana yace karfa ka manta bari na tuna maka Nnenna suspect ce a naija komawarta yanzun bazaiyu ba haka zalika tinkaran iyayena yanzun matsala ne babba kawai Ni na yanke shawara za'a zubar da cikin kawai muyi planning sai lokacin da Zan koma nageria Inna kammala karatu saimu koma daidai lokacin case nata ya mutu"





Kai Lahab kana da hankali kuwa an gaya maka Nan nageria ne da zubar da ciki ya Zama abin sauki cikin ma na wata uku Yana kokarin shiga na hudu Koh kunyar halinda yarinyar mutane zata shiga bakayi toh wallahi karka kuskura karka Fara abinda zaija maka matsala a kasan Nan kaji na gaya maka"



"Koh baka fada Masa ba Ni bazan amince ba"juyawa dukan su sukayi wa zasu gani Nnenna ce Wance ke tsaye rike da kofa ga dukkan alamu ta Jima a wajen,sai hawaye kebin kumatunta bata taba tsammanin hakan daga wajen Lahab ba Wai zubda ciki"mikewa yayi yace"ciki Kam tunda Ni nayi nace a zubar Koh y'ay'a d'ari kike so daga baya mu Haifa Amma Banda yanzun kwata kwata shekaruna nawa da Zan kakkabawa kaina yaya"?




"Lahab bazan taba zubar da cikin Nan ba,domin shikadai ne ya ragemun Wanda Zan daga hannu na nuna nace ga dangina nan Banda kowa nawa sai shi Taya Zan zubar in Kuma Banda rabon wasu cikin a duniya fa sai wannan fa Kai kana da daman aure amma Ni har abada ka cuceni"Zan rike duk abinda na Haifa Koda kuwa baka so ni Mai iya cewa ba d'anka bane,Ni Zan zamo Masa uwa da uba bazanji kunya ba,amma wallahi banda zancen zubarwa Ina son jinina Ina son cikina Koda kuwa kowa zai gujeni"mikewa Lahab yayi Yana nuna kansa kana yace"Ni kike gayawa haka"an gaya maka Lahab na gaya maka indai akan cikin Nan ne"toh nace bana bukatar cikin"Ni ina ruwana Kuma daga yau Ina so ka manta cewa akwai sure a tsakanin mu da Kai haka zalika bazan Kara cin abinda ya zamo naka ba muddin dai zanci yaron cikina ya rayu"






Juyawa tayi tabar dakin tana kuka,kallon sa Ade yayi cikin tausayin su duka don wallahi sun basa tausayi yace"Lahab karka kuskura ka sake zancen zubda cikin Nan itace uwa ita keda ra'ayin haihuwa Koh ah ah don haka ka zamo Mai adalci,karfa ka manta Koh a addinin ku haramun ne abortion ka kula da ita Lahab ka tausaya Mata,daga haka shima yasa Kai yabar dakin,har yamma Lahab na dakin sa,mangariba nayi yayi sallah mikewa yayi ya shiga toilet,wanka yayi ya fito ya sanya Kaya fita yayi a dakin ya leka kitchen yaga kome net babu alamun ma Nnenna ta dau wani Abu a ciki.




Fita yayi ya sayo musu abinci laida biyu bude kofar dakin nata yayi ya shiga zaune take da kayan da Suka dawo asibiti Koh chanjawa batayi ba idanunta jawor da gani tun kukan safe da tayine Suka rine,shigowarsa baisa ta motsa daga inda take ba aje laidan yayi ba tare da yayi magana ba ya fita a dakin,washe gari da safe Kamar yanda ya aje Mata laidan haka yazo ya gani da mamaki yake kallon ta sai Kuma ya kasa hakuri yasa hannu ya dago blanket in, kwance take amma Bata dago ba"meya hanaki cin abinci"?ba abinda ya shafeka bane"abinda ya shafeni ne Mana kina ikiraren kinason abinda ke cikin shine kikeson kasheshe da yunwa"




Wani kalllo ta Masa sai Kuma tace"babu ruwan ka daya mutu Koh yayi

Please Login or Register in order to submit comment