Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har kasan kwanan waje watoh shine kaja Lahab kuka fita tare Koh?

Sunkuyar dakai Majid yayi,ya jafar Kam ransa in yayi dubu ya bace,hannu ya mikawa Majid,bani key Inda kaje ka d'auka har kana fita ta back door watoh Majid Ni ban Isa da kaiba har barayi kake nunawa kofar sirri na gidan ku?

Hannu Majid yasa a Aljuhu ya zaro key in ya mikawa dady ba alamun damuwa a fuskar sa,juyawa ya jafar yayi ya koma falon daya bar lahab,har lokacin Yana tsaye kallon sa yayi, Lahab Bari kaji zaman ka a cikin gidan Nan bazaiyu ba bazaiyu kazo ka zauna ku taru ku lalace ba don haka kaje daki ka jira muzammil anjima zaizo ku tafi,Yana karasa maganar ya juya yabar falon.

Nanne da ya Hashim kam fada Suka rufe Majid dashi kafun Suka juya Suka bar Masa wajen,dakin sa ya shiga,Lahab dake tsaye a falon Shima dakin Majid in ya tura ya shiga.

Majid dake tsaye a tsakar dakin ne ya kallesa,sannu Lahab haka mukayi da Kai sai ka tashi ka shigo gida bazaka tadani ba ai shikenan hankalin ka ya kwanta ai yanzun,ban wayata?

Koh kallon sa Lahab baiyi ba ya bude wardrobe nasa yadau jallabiya tube kayan jikinsa yayi ya zura jallabiyar,ga kansa dake Masa ciwo ciwo na rashin bacci da bai samu ba jiya.

Magana fa nake maka Lahab,shuru Lahab yayi bai amsa Masa ba ya nufi kofar dakin shakumosa Majid yayi cikin zafin Rai yace,kaban wayata daman Lahab a cike yake tam jiran kadan kawai yake ya fashe a take ya bangaje Majid Suka kaure da fada fada suke sosai ya d'aga Majid ya buga da tiles wani Kara Majid ya sake da karfi Yana Kiran nenne.

Nanne dake zaune a falo tana bama Mai aikin ta ordern abinda zata d'afa musu na karyawa da Sauri ta Mike Jin Majid na kwala Mata Kira da karfin cin tuwo,da Sauri ta nufi falon nasu tana shiga ta tura kofar dakin sa ta shiga,subhanallah me Zan gani haka Lahab sakesa Mana tace tana kokarin shiga tsakanin su Amma Ina Lahab yayi zuciya sosai kin barin fadan yayi da gudu nanne tayi dakin Hashim tana kwala Masa kira da karfi tana salati,bude kofar yayi fuska ba walwala don duk abinda suke Yana jinsu Sarai tunda dakin na manne da nasa da gangan ya barsu suyita dakuwa.

Hashim fitoh kazo ka raba yaran Nan Lahab zai kashe Majid ka Sansa da zuciya baisan Bari ba kayi Sauri tace tana Kama hannunsa Suka shiga dakin tare,da taimakon Hashim aka raba fadan Amma dai Majid ya daku Kam.

Juyawa kawai Lahab yayi ya fita a dakin bayan ya hashim ya rabasu fadan,fita yayi a flat in gabaki d'aya ya nufi gate budewa yayi ya fita ya tare Mai keke napep ya hau direct gidan mamin sa ya nufa don yasan muddin ba gidanta yaje ba baisan Inda zaije da sassafen Nan ba, knocking na gate in yayi sau uku kafun Mai gade yazo ya bude ganin shine yasa sa basa hanya ya wuce tare da maida kofar ya rufe.

Bude kofar falon Mami yayi a hankali yasa fuskarsa ya leka falon ganin ba kowa yasa shi Shiga cikin Sauri ya nufi wani kofa dake falon.

tura kofar yayi ya shiga extra room ne ba kowa a ciki ya maida kofar ya rufe zare jallabiyar jikinsa yayi ya kwanta akan gadon yaja bargo ya luluba Koh 3 minutes baiyi ba wani wahalallen bacci yayi awun gaba dashi.

ta bangaren Nnenna Kam tun 4 na asuba Mom tazo ta tada ta haka ta Mike jikinta ba kware ta shiga toilet ta wanke fuskar ta, jikinta da sauki sai dai hannun tane takejin sa ba dadi,sharan falon tayi da kitchen da baranda tayi mopping duka ta share tsakar gidan duka,wanke wanke dake kitchen duk ta wanke gidan shuru kowa na bacci sai ita kadai kawai tana aikace aikace,sai misalin 6 na safe ta Fara daura breakfast golden yam ta soya musu sai tie ibawa Kiki tayi tadau roban takeAway in Lahab ta zuba rabonta a ciki tasa tie a flask nasan Kamar jiya ta jera a laidan ta aje,kulolin ta jera musu a dinning lokacin karfe 7:00 yayi,daki ta shiga tayi wanka ta sanya uniform nata ba tare data tsaya taga saukowar jama'ar gidan ba ta sabe jakanta da laida tabar gidan.

Adewale haka ya kwana bai rumtsa ba sai kusan 4 na asuba ya samu yadan kwanta,misalin karfe 7:30 papa yazo ya Fara surfa Masa matsifa akan ya tashi su tafi makarantan su Kamar yanda principal yace,shi Kuma Adewale yace babu Inda zashi baida lafiya sosai rikici ya barke mama ta rasa bayan wa zatabi na Ade Koh na papa,karshe ma da Adewale ya gaji fita yayi a gidan yabar papa sai masifa yake Wai ya raina sa.

Ade na fita d'aga gidan su rasa ma Ina zaije yayi bazai iyya zuwa gidan su Nabeel yanzun ba saboda mubeena haka Koh gidan su Lahab bazai jeba,gidan su David dake kusa da gidan su ya Shiga dayake David irin yaran Nan ne da iyayen su ke musu part nasu daban hakan yasa sa wucewa part nasu David in yaje ya kwanta don duk basa Nan sun tafi makaranta.


Mubeena yau haka ta tashi jiki ba kwari kome take a sanyaye Wanda har inna sai da ta gane Mata Amma ta Mata tambayar duniyan Nan amsa daya take Bata shine babu kome,shiryawa tayi cikin abaya baki da gyalensa ta rataya school bag nata a kafada kallon Inna tayi,Inna Ni Zan wuce!!

Au yauma akwai makarantan ne shine kike kome a sanyaye?

Eh Inna akwai makaranta yau Muna da paper da safe.

Ke Kika San paper ni ban Sansa ba yanzun dai ga wannan saikiyi kudin machine chanjin ki rike a hannun ki,karba mubeena tayi tare dama Inna godiyan.

Har tasakai zata fita a kofar saiga bappan su,tsungunawa tayi ta gaidashi,Ina kwana bappa?

Lafiya mubeena sai Ina haka da sassafen Nan?

Makaranta zanje bappa.

Toh Allah ya bada sa'a Amma nidai bason wannan karatun nake ba kawai ki sanar da Ahmad in ya turo don Ni na gaji da wannan fikilin da sunan karatu in so yake kiyi karatun toh ya aureki Mana kicigaba a dakin ki baifi ba Amma ace budurwan shekara 20 tana gantali a titi wai ku yaran zamani Yan boko.

Shuru kawai mubeena tayi Harya kareshie mitarsa tamar sallama ta wuce abinta.

Bappa Ado da sallama ya shigo cikin gidan,amsa Masa Inna tayi,ah ah lale lale Ado ne yau a gidan mu wata Sabon gani.

Hmmm Inna kenan wallahi abubuwan ne sai a hankali Amma Ni Karan kaina Ina son shigowar akai akai.

Kaidai ka jiyo ganinan dai Nina haifeka sai kafi wata baka takoni ba gamu baki da hanci amma dayake ita asabe uwar matar kace gaka koh wani juma'ar Allah sai kaje gaisheta.

Yanzun dai Inna don Allah kiyi hakuri Kuma wani munafukin ne ya kawo miki wannan gulmar?

Nice munafukar dana jiyo gulmar Ado,shine amsar da Inna ta basa don ranta ya Soma baci.

Kiyi hakuri inna?

Daman baka mini kome ba duk Wanda yayi na gari dai don kansa ne,yanzun meke tafe dakai don nasan in ka taki kafarka a gidan Nan nakane ya kawo ka.

Sunkuyar dakai yayi cikin kunya yace,Inna daman jiyane principal in makarantan da yaron nan Nabeel ki ciki ya kirani akan yau yanason ganina dashi Nabeel in duka shine yanzun nazo mu wuce muje muji Koh lafiya?

tafa hannaye Inna tayi,watoh wani abin Nabeel ya sake jawowa kenan don in kaga irin wannan Kira daga shugaban makarantan kasan bana lafiya bane oh ni fatu Naga ta kaina,Bara na Kira maka shi Yana daki Yana baccin asara shi bai tsaya ya muri arziki yayi karatun ba shi baije shago ya nemi kudi ba tunda ya iyya dinkin Nan sai Kura dayake hadawa kansa,ya dawo gida ya zauna ya zanyi da wannan yarone Ni fatu tunda Nina haifi ubansa Kuma maraya dole dai Ni Zan zauna dashi in ba don hakan ba ardun Allah Koh hanya Ado bazan yarda mu had'a da yaron Nan ba, tana maganar tana nufan dakin Nabeel.

tura kofar falangen tayi ta yaye yamusheshen labulen kwance yake akan katifarsa dake zagaye da kayan sawan sa Mai datti duk Akan katifar yake titd'awa in dare yayi ya kwanta akan su,daka Masa duka tayi a gadon baya Kai Nabeel tashi don uwarka.

Mikewa yayi Yana yamusa fuska haba Inna wannan wani irin zalunci ne ace mutum na kwance Amma zakizo ki tasheshi da sassafen Nan Kamar na daukar Miki kudi Koh naci bashi?

rufe min Baki shashasha ba gwara ma ka daukar min kudin ba Koh fitinan zata tsaya iyya kaina.

toh yanzun dai menene da Zaki ta dani.

Bappa Ado dake sauraron duk abinda suke cewa daga waje, d'aga murya yayi yace,melene dan kaniyanka innar tamu kake fadawa haka don baka da mutunci toh Maza saka kayan makarantan ka ka fitoh muje muji Kiran me ake Mana.

Waro Ido Nabeel yayi da Sauri Jin muryar bappan sa da Kuma abinda yake cewa Wai suje school shap? ya tabbatar yau Ade da Lahab ba zuwa zasuyi ba karshe hukunci ya Kare a kansa shi kadai wallahi Bai Isa ba wane shi.

Wai Ina nabeelu ne,ganinan bappa Ina zuwa ,sai Kuma yayi kasa da murya cikin magiya yace,don Allah innata kice Masa bari nayi wanka kinji dan Allah?

Hararan sa Inna tayi tare da fita a dakin,Shima mikewa yayi ya dau rigansa yasa wayar sa dake zaune a gefe ya d'auka yasa a Aljuhu tare da daukar soson wankan sa Kamar gaske,ya fitoh a dakin tsungunawa yayi ya gaida bappan nasa,amsawa yayi sama sama,lafiya kaga Nabeel kayi Sauri kayi wankan kazo mu tafi nabar shagona a rufe fa.

toh bappa yace da Sauri ya Mike yadau bokati ya ibi ruwa ya wuce bayan gida,Yana shiga aje ruwan yayi ya Kama ginin bayan gidansu daman guntune ya d'ale abinsa ya dirka ta lungun unguwan su,karkade wandonsa yayi ya Kara gaba abinsa.

Yau ne gobe ne Nabeel bai fito ba tun bappa Ado na tsaki Harya Fara mita Yana kwalawa Nabeel Kira,gajiya yayi da jiran nasa ya tashi ya tsaya a hanyan kofar bandakin,Kai Nabeel chanja fata kake ne Kome?wanka Kamar wankan amarya,shuru make ji ba'a amsa ba.

Inna Kam wani tunanin tayi sai Kuma ta girgiza Kai,Ado shiga ban dakin nan ka duba in dai na canki daidai toh Nabeel baya gidan Nan yanzun.

da mamaki Ado yace kamar ya Inna baya gidan Nan?

Kaidai shiga ka duba,ba musu ya shiga Aiko ba kowa sai ruwa da soso fitowa yayi Yana masifa,wallahi Inna Nabeel ya Raina Ni Sam baya ganina da gashi harni zai rainawa wayo toh na fasa zuwa makarantan ina da abinyi Amma saboda shi nabar kome nawa nazo muje naji dalilin Neman sa shine zai min iskanci?

Ah ah baza'ayi haka ba kayi hakuri kaje kaji dalilin Neman naka karka Zama irin sa Mana shi yaki zuwa Kai kaki zuwa ai sai ran shugaban makarantan ya Kara baci kaje kaji in.

Shikenan Inna saina dawo,toh Allah ya dawo dakai lafiya Ado,fita a gidan bappa Ado yayi.


***********

Mubeena Keke napep na tsaidata a kofar school nasu ta d'auka biyan sa kudin sa tayi ta Soma takawa a hankali jiki a sanyaye tana ratsa makarantan tafiya tayi Mai nisa sosai kafun ta iso department nasu,Hawa block in tayi ta shiga Hall in lokacin dalibai sun cika tim a ajin ana jiran lokaci yayi wasu na zaune wasu na karatu wasu na hira wasu na tsatsaye a window d'aga kaga irin cikan nan kasan lokacin jarabawane Koh test kawai ake wannan sammakon da yawan,acan kujerun tsakiya ta hangi kawarta Ruky zaune da wasu friends nasu biyu Suna Hira ana dariya.

Nufarsu tayi tana kiyastawa Ina ma inama itama tana da daman walwala Mana kamar da,ai data mure,Assalamu Alaikum.

Amsa Mata sukayi dukansu Suna had'a Baki tare da kallon ta hannu Suka Bata Suka gaisa tare da matsa Mata itama ta zauna,kallon ta Ruky tayi,ya fama da karatu bestie?

Alhamdulilah Ruky,shuru tayi kawai tana sauraron surutun su Ruky Amma ita Bata saka musu baki ba illa takardan ta data fitar tana bita kafun lokacin shiga jarabawan su ya cika.

Misalin karfe 10 lecture in ya shigo,Suka Soma jarabawan,Basu Suka fitoh ba sai 11:30 gabaki dayan su suka zazzauna akan kujerun dake gindin bishiyar gefen block nasu don Suna da jarabawa anjima,daya kawar tasu ce ta Mike tare da musu sallama zataje hostel ta dawo.

Kallon mubeena Ruky tayi sannan ta Soma Mata magana cikin hikima,mubeena meke faruwa? na fahimci tun jiya kike cikin damuwa duk da kina kokarin boye mini Amma ai labarin zuciya a tambaye fuska meya faru?

dan murmushin yake mubeena tayi,babu kome Ruky kawai dai gajiyane da rashin samun isheshen bacci kinsan in exam yazo bani da nutsuwa sai anyi an gama?

Haba mubeena Koh Zaki boyewa kowa kome bazaki iyya boye mini ba sai dai in Baki yarda dani ba, Koh Baki daukeni a matsayin aminiyar da Zan Baki shawara ba?ta karasa maganar ranta adan bace don tana Jin matukar haushin halin mubeena wasu lokacin akwai zurfin ciki da muku muku.

Mubeena sauke ajiyar zuciya tayi Uhmm Ruky bansan ta Ina Zan Fara ba kinsan kaf duniya bani da kawa Kuma aminiya sama dake Amma akwai abinda baki sani ba guda d'aya, daya Jima Yana damuna Ina boyewa saboda kunya kaina da kaina nake,amma a Y'an kwanakin Nan na rasa meke tadomin dashi ga wani irin tsoro da fargaban rasa abun da nake.

Wani Abu kenan da ban sani ba?

gyara Zama mubeena tayi,tace Ruky a gaskiya bazan boye Miki ba zuciyata bata kaunar Ahmad?

Kamar ya mubeena bata kaunar Ahmad daman bason Ahmad in kike don Allah ba kike tare dashi kike nuna wa duniya kina sonsa?Koh dai kin samu Wanda ya fisa kin wuce chaptern sa yanzun kina son sauyawa da wani? bara na fada Miki wallahi mubeena zakiyi dana sani a rayuwar ki ki dubi irin d'awainiya da Ahmad yake dake duk wani fadi tashi nasa akanki ne shine yau rana tsaka Zaki kawo min wani zance Wai baki sonsa?

a zahiri ne Ruky kuke ganin haka amma a can cikin zuciyata bashi nake so ba na saurare Ahmad ne saboda nace mini da yake da irin yanda yake nuna tsananin Sona,na karbesa ne a matsayin masoyi saboda a tunanina Koh bashi dama da zanyi a rayuwata ya canja min ra'ayin dake zuciya ta amma fa ki sani tun kafun nasan Ahmad na Fara sonsa.

Son waye kenan kike Kuma? bangane kin baiwa Ahmad dama dan ya chanja ra'ayinki ba kimin bayani yanda Zan gane manufarki da kyau.

Mikewa mubeena tayi tsaye ta juyawa Ruky baya tayi dan taku kadan kafun ta tsaya hade da hade hannayen ta biyu waje daya hawaye ne Suka cika a idanunta har Suna sheki da zummar saukowar Kan farin kumatunta.

Itama Ruky mikewa tayi ta matso gareta ta dafa kafadun ta,lalle wannan al'amari Mai girmane mubeena wakike ma wannan so haka wanene shi.

Juyawa tayi Suna fuskar tan juna, hawaye Nabin fuskarta ta Soma magana,Ina sonsa najima da sonsa Ina Jin kunyar sa nayi iyya kokarina na ganin na binne abinda ke Raina ba tare da kowa ya sani ba amma Ina na kasa.

Ki sani mubeena barin Kashi a ciki baya maganin yunwa wa kike son?

Ba kowa bane illah lahabbbbbbb.............






*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*

Page 47&48
Wani Lahab kike nufi mubeena ban gane ba?

daman bazaki taba ganewa ba Ruky ni Karan kaina ban ganewa kaina ba.

Ki fahimtar dani wani Lahab kuma.

Kinsan kanina Nabeel?

Kwarai nasan Nabeel Mana sau nawa Ina zuwa gidanku Ina samun sa Yana tsananin Kama dake fari sol kamarke in ban manta ba?.

Yauwa akwai wasu yara biyu da Zakina ganinsu tare da dashi yawanci a gidan mu ma mutum yazo da wuya yatafi bai gansu ba.

gyada Kai Ruky tayi,tabbas na gansu su biyu sa'o'in juna dayan black beauty sosai handsome dashi ruwan Fulani sai dayan Kuma wankan tarwad'a amma Kamar kabila kabila.

Yauwa Ruky kin musu kyakkyawan sani,wannan black in shine Lahab Brown in shine Adewale,wannan Lahab in nake so sannan jiya Kuma Adewale ya tare Ni da wata magana daya matukar tayarmin da hankali don furtashi baraza nane gareni da Kara nisan tani da abinda nake so.

Ruky Kam tama rasa wani hauka ne mubeena take,yanzun mubeena kina nufin wannan yaro friend na kaninki inne kike so sannan wannan kabilar daba musulmi bama kikace yace Yana sonki?

Eh Ruky na Fara son Lahab ne tun da jimawa dayake tare Suka taso da Nabeel Kuma rashin jinsu daya tun Suna yara suka Soma abota,lokacin da Lahab yakai shekara 16 a lokacin sai na Fara Jin wani yanayi daban a tare dashi in har baizo gidan muba sai naji na matukar damu duk lokacin da yazo sai in jini cikin farin ciki na tsane Naga yazo gidan mu zai tafi sai inji tamkar na bisa mu rayu tare a duk lokacin da Suka samu matsala da Nabeel Suka daina ma juna magana Koda kuwa na wuni gudane sai naji tamkar na shekara ne, gashi ba zuwa nake gidan suba duk saina birkice na rasa meke damuwa har sai na gansa natsuwata take dawowa.

A lokacin da na Kara girma saina fahimci babu abinda ke d'awainiya dani face son Lahab,nashiga tashin hankali nayi kuka na roke Allah ya ciremin sonsa a raina Amma Ina kullum Kara Jin sonsa nake na jiya yafi na yau,Yaya zanyi Ruky taya Zan fuskance duniya in d'aga yatsa in nuna Lahab a matsayin Wanda nake so So ma irin na aure?

dole tasa na daina sakar musu fuska na ringa nuna Masa hali Koh Allah zaisa na daina damuwa dashi Amma na kasa na kasa Rukayya,sai kuma ta fashe da matsananci kukan tana dukawa akan gwuwuwin ta.


Itama Rukayya dukawa tayi ta kamo kafadar mubeena ta mikar da ita,hannunta ta Kama suka koma Kan kujera Suka zauna ganin hankalin mutane ya Fara dawowa kansu.

Ke share hawayen ki mubeena shifa so haddin Rabbine,Allah shike dasa so a zukatan bayinsa ba wayonki Koh dabarar ki bace zai rabaki da abinda kikeji ba, illah Addu'an Allah ya zaba Miki abinda yafi Zama Alkhari a gareki.

mubeena hannu tasa ta share hawayen fuskarta insha Allah kuwa Ruky,sannan ta cigaba da Bata labarin,toh ganin sonsa sai dad'a ninkuwa yake gaba d'aya,bangaren Ahmad Shima Yana mutuwar Sona duk irin wulakancin da Zan Masa haka ya nace mini,d'aga karshe dana zauna nayi tunanin Mai zurfi saina gano lallai Ahmad najin zafin abinda nakeji taima ma Harya fini tunda Ni so kawai nake Ina hauka na Ni kadai shi kuwa ya furta Amma bai samu karbuwa ba?

Hakan ne yasa na basa dama,tun a farko da zancen aure yazo hakan yasa na Soma Masa kolo kolo nace saina gaba secondary bayan na gama ne ya sake tada maganar akan shi yanzun Yana son aure ne,Nan ma nace saina juna gaba da secondary saboda irin son da yake min yasasa amince wa duk da kullum Yana sanar dani mahaifiyar sa na nuna Masa bacin randa akan kin Saida maganan auren sa da baison Yi.

gashi yanzun na samu shiga college duk Kuma a cikin Aljuhunsa kome nawa shike min Kama d'aga kudin makaranta suturu duk shike saimin in Kika cire Inna da itama tanamin daidai gwargwado Amma Yan uwan babana dana mamata basu San Koh a sallah su saimin turmin zani ba.

Amma fa ki sani har gobe son lahab na d'awainiya dani Kuma ganin da nayi mundin na aure Ahmad shikenan Zan daina ganinsa,shine dalilin na na kasa baiwa Ahmad daman aure na har yanzun,ga Kuma Adewale daya bullo Wai Yana Sona Kuma na tabbatar Lahab zaisan maganan Nan saboda duk wani Abu da Ade zaiyi saiya shawarce Lahab sama da Nabeel Yaya zanyi Rukayya wallahi kirjina zai fashe zuciya ta ta kasa mini Adalci taso abinda bazata samu ba taso abinda zai Bata wahala wayyo Allah na,tana maganar tana kuka ita kanta Ruky Saida hawaye ya cika Mata a ido.

Handkerchief nata ta d'auka tasa a fuskar mubeena tana goge Mata hawaye kafun a hankali ta fara Mata magana,mubeena da ace Lahab da Adewale sun dai 25 ko 30 kinsan shawaran me Zan Baki?

girgiza Mata Kai mubeena tayi.

toh da sai nace Miki ki hakura da Lahab kiyi accepting na Adewale Koh don saboda soyayyar ki dake ransa zai Zama sular musulun tansa in Yana da rabon musulunci,Kinga kema kinyi jahadi,Amma Kinga Lahab baisan kinayi ba sannan baisan kina sonsa ba ga aminin sa na sonki kinsan da wuya ya amince,nidai Zan Baki shawara karki kuskura kiyi Wasa da daman ki sama sau daya yake zuwa wa mace na zaben mijin da taga dama tana so daga xaran shekaru sunja sai dai fa a koma Addu'a Allah ya bada mijin Koh ma yayane.

Kin gannin Nan mubeeena a shekarun baya ba irin sonda Nazeer Bai nuna mini ba yasoni Kamar hauka Amma kullum cikin wulakantashi nake yasha turo abokansa suzo su min magana akan irin tsananin son da yake min Amma na kekashe kasa naki kememen na nuna bana kaunar sa Amma Sam ba haka bane a cikin zuciyata Ina sonsa na Kuma kasa sanin me yasa bana nuna Masa son.

A karshe wata cousin nasa ya aura Wance ta fini kyau da kuruciya nayi bakin ciki nayi kunci,gashi yanzun Koh da kudi aka basa akace ya aureni bazai yarda ba gashi nima yanzun babu wani tsayaye gajiya da zaman gida yasa mahaifina sani a college,gashi haryau babu Wanda yake zuwa da sunan Sona a kofar gida sai dai samarin online.

Ki dubi malamar mu Nan ga ilimi ga kyau ga kudi Amma babu miji,sannan naji labarin ta a wajen aunty laure tace min lokacin da suke Yan Mata baiwar Allah Nan tayi farin jini Kamar na hauka kowa yazo tace sai boko ita bazatayi sure ba wasu sun yarda zasu aureta ta cigaba a gidan ta Amma taki,ki dubeta a yau ta haura 30 da wani Abu Amma babu miji.

don haka kima kanki karatun ta natsu tun duniya Bata Miki ba karkice Zaki biyewa kawa zuci ta kaiki ta baroki in ba rashin tunanin ba Ina ke Ina Lahab bare Ade Suna da abinda zasu rike kansune bare su rike ki? duk da Suna yaran masu kudi Koh dangin su zasuyi maraba dake?in Kuma kikace Zaki jirasa sai ya girma toh shi Kuma a lokacin zai zabo santaleliyar yarinya ya aura a barki da dana sani.

Dan Allah Rukayya ki dakata ya haka kina ta zancen lokaci lokaci karfa ki manta aure nufin Allah ne duk wayo Koh sakaci Koh dabara baya Hana aure baya saka aure don haka kawai in zaki bani shawara ki bani Kuma har yanzun akan bakana nake Ina son Lahab tamkar numfashina Kuma ba'a haifi Wance zata rabani dashi ba muddin Ina numfash.....kafun ta karasa sukaji faduwar mutum a bayansu ji kake timmmmmmm




******************
ta bangaren gidan su lahab daman tun da su muneera suka dawo makaranta ba Lahab muzammil ya tambaye su sukace yaje school Amma da aka tashi yabi su Nabeel Sam sunki fadawa kowa gaskiyar abinda ya faru.

principal na makarantan su Lahab ne ya Kira muzammil akan gobe Yana son ganin su shida kanin sa a school day safe,hakan ya tabbatar wa da muzammil lallai akwai babban abinda Suka aikata kenan tunda gashi har yamma lilis bai dawo gida ba.

Wasa wasa har mangariban ba Lahab hakan yasa hankalin Abbu tashi don yasan duk yawon Lahab baya dare a waje, waya ya d'auka ya Kira Mami Amma tace Lahab baya wajen ta,take ya tuna toh Koh gidan jafar yaje, muzammil ne ya d'aga waya ya kira ya jafar Kuma ya tabbatar Masa Lahab nagun su yaso a daren yaje ya dauko sa Amma jafar yace ya barsa ya kwana da safe yazo ya d'auke sa.

Washe gari misalin karfe 7 na safe a gidan jafar ya samesa amma Ina ya makara kafun yazu ma Lahab ya Kara gaba abin ya Kara kula muzammil sosai ya cika tim gashi yazo yaji labarin sunje party sun kwana a bakin Hashim don Hashim daman haushin su yakeji kaf familyn su su ukun Nan sun ishesu Amrat Majid Lahab,Kuma yanajin dadin yanda muzammil kecin ubansu sosai.

muzammil da kansa yaje har gidan Mami lokacin mijinta baima fita ba Suna karyawa a dinning da yaransu ya shigo Alhaji kawai ya gaishar don daman basa shiri da Mami sam,Amina

Please Login or Register in order to submit comment