Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har yanzun bai shiga tsakanin su ba Amma akace labarin zuciya a tambaye fuska.






Abbu ya kirasu yace su ukun Nan su fada Masa school Inda suke son shiga a abroad uzaifa ya kammala degree insa a gombe zai Kama Master's shima a abroad Abbu yace su nemi kasa d'aya takamemme, Rahab yace India shi Kuma uzaifa yace Canada shidai Lahab shuru yayi Yana jinsu Suna da CeCe kuce har Abbu ya gaji yace suyi applying na school biyu duk Wanda akayi accept nasa shiken,Aiko Lahab yaji dadin zabi biyun Nan duk da baiyi magana ba ya rasa ya zaiyi da ransa wallahi baison tafiya yabar Nnenna gashi result nasu yayi kyau gabaki dayan su harda Ade,wanka yayi ya fita a gidan directly gidan su Ade ya shiga da yake yau lahadi ne iyayen sa Suna church,zaune ya samu Ade a falo Yana karyawa Zama yayi Suka Soma magana"ah yanzun Lahab bakajin kome ne Wai kayi aure gidan ku basu sani ba Kuma Koh a jikinta"?





d'aga kafada Lahab yayi yace"nikam Koh a jikina wallahi yanzun ma duk ba wannan ne ya dameni ba"da mamaki Ade yace wata sabowa meya sameka Kuma"?badai Akan matsalar yarinyar Nan Bako?dariya Lahab yayi yace"wallahi kasamin Ido na rantse da Allah toh akanta ne"?hararansa Ade yayi yace zaka mutu akan ta wallahi"in mutun Mana Ina ruwan ka"babu ruwana Kam Lahab Ashe na manta"in serious Lahab yace"ya maganan makarantan mune Wani kasa ka zaba"?dan shuru Ade yayi sannan yace "Kai wanne kake so?na bar maka zabi "yace yana jiran yaji me Lahab zaice"tunani ya shiga kafun yace Ina son zuwa University of Canada Koh Kuma London a cikin biyun Nan nake son daya Rahab yace India uzaifa yace Canada zashi Ni Kuma banida burin tafiya school dasu dukansu biyu nafison na tafi da Nnenna abroad bana tunanin Zan iya barinta a kasar Nan bansan halinda zata shiga ba bayan babu Ni"wani banzan kallo Ade ya Masa kana yace kana nufin kacemin wai da yarinyar Nan zaka bar kasan Nan Ina ka samu kudin da zaka biya Mata kudin jirgima bare na tafiya"?





Balance Lahab yayi yace"wallahi Ni Karan kaina na rasa Ina Zan samu kudi ban damu da kudin kome ba irin jirgin da Zan biya Mata shine na yanke shawara Koh zanje na samu Abbu a cikin kudin gadona yaban million daya"da Sauri Ade ya mike cikin masifa yace amma wallahi da zakayi haka kaf duniya babu Wanda ya kaika rashin ta Ido, mutumin da tun kuna yara har kawo yau da kudinsa yake d'aukar d'awainiyar ka bazakaji kunyar tambayar sa gadonka a yanzun ba? wallahi kaban mamaki kabi a hankali Lahab kada makauniyar soyayya ta kaika ta baroka a banza"shuru Lahab yayi har Ade ya Gama masifar sa ya koma ya zauna Yana huci sanan yace toh Ade ya zanyi yanzun dan Allah dai?kawai ka barta anan mu tafi karatun mu shine kawai magana"amma Ade a halinda take cikin Nan tana bukatar kulawa na musamman duk da nasan goggoji zata riketa Amana harna dawo, amma duk da hakan ma gaskiya banjin Zan iyya barinta"da haushi Ade yace toh saikayita fama Allah ya baka sa'a sannan ya mike yabarwa Lahab falon gabaki daya,mikewa Lahab shima yayi ya wuce gida.





Washe garin da safe saiga Adewale yazo wajen Lahab shidai Lahab baice kome ba,wuri Ade ya nema ya zauna kafun yace"nama papa maganan Inda nake son karatu kasan abin mamaki ashe Wai yasa an Masa bincike anji xaku tafi India karatu shine yace na xabi Koh Ina amma Banda India"hhhh dariya kawai Lahab yayi yace shikenan saimu wuce London"gyada Kai Ade yayi yace gaskiya Lahab bai Kamata mu tafi mubar Nabeel ba kasan shi har jamb yayi baici ba kasan abin sa'a ne"d'aga kafad'a Lahab yayi irin I don't care innan yace,"kaga yanzun ta kaina nake bata wani Nabeel ba abinda muka Masa a baya Allah ya saka Mana amma yanzun bazan iya ba in kaga zaka iya Bismillah kayi"



Da lallama Ade yace,haba Lahab gaskiya hakan bai dace ba tare fa muka tashi Kuma kome muka saya sai mun raba tare,da masifa Lahab yace"Wai gidan uban wa Zan samu kudin da Zan biya Masa karatu a London Harya gama ne kanaga kudin da Zan biyawa matata ma bandashi kudin jirgi kawai"da mugun mamaki Ade ke kallon sa Yana mamakin Al'amarin Lahab Baki a ciki bako Jin kunya Wai matansa,ai sai yanzun na ganoka watoh tunda Nabeel yace ya tsani Nnenna Naga gabaki d'aya ka chanja Masa wallahi wata rana har tambaya ta yake Mini, Wai ya kasa gane kanka kwata-kwata yanzun baka shiga shirgin sa"tsaki Lahab yayi baice kome ba Ade ya Kara cewa"Wai Lahab nace Koh zaka ma Abbu magana Koh zai dau nauyin Nabeel kasan Ni Koh hauka nake bazan Fara gayawa papa haka ba,kaga inya yarda Ina da dan million daya a account nawa saina biya Masa Koh kudin flight ne"wani harara Lahab yake ma Ade cikin harzuka yace"Kai Ade kaje Kama Abbu da kanka karka sake cewa na roke kowa kudi babu ruwana an maidani wani dan iska kome Ni ai abbun yafini sanin abinda ya dace in yaga zai iya biyamar ya biyamasa in yaga bazai iya ba bazansa bakina ba"karshe dai haka Ade ya hakura da maganar Nabeel.





After few weeks Lahab ya samu gurbin karatu a London shida Ade amma ba tare da ya fadawa kowa ga kasar da yayi applying ba har Saida yaji Rahab nacewa Abbu zai musu visa kowa ya kawo passport NASA abin mamaki Bai gama kashe Yan gidan ba Saida Lahab yace shi a London ya samu makaranta da mamaki Rahab yace kana nufin ba India zamu ba kenan ranan na tambaye ka kace wajen zaka har uzaifa ya hakura shima ya nemi Nan?Lahab shuru yayi baiyi magana ba Abbu Kam sai kallon sa yake Ido cikin Ido da Sauri Lahab ya sunkuyar da Kai"kai dawa zaku London in"?Abbu da Adewale ne"gyada Kai Abbu yayi baice kome ba sai nuna Masa da yayi ya aje passport in,Aiko take Rahab ya dire yace shima sai London Saida Abbu ya nuna Masa jan Ido kafun ya hakura amma ya zage Lahab Kam iya zagi ya kirasa munafuki duka Lahab Bai kulasa ba dan yasan bai kyautawa dan uwan nasa ba dan tunda Suka tashi sutura wannan Rahab yafison yasa irin NASA shine ke kin yarda suyi anko haka ma makwanci da Lahab baya bacci sai ya Mannu dashi daga baya ne Lahab ya ringa gudun sa har Suka raba shimfida.





Alhamdulilah su Lahab visa insu ya fito saidai su Rahab zasu riga su Lahab tafiya tun saura sati su Rahab su tafi gabaki d'aya ya birkice yace ya fasa tafiyar shi bazai tafi yabar Lahab ba daker aka samu ya natsuwa amma haka kawai inya zauna sai kaga ya buga tagumi ya Fara tunani Wasa Wasa ya Soma ciwo yau ciwon Kai gobe zazzabi kullum Yana like da Lahab Dole aka d'aga tafiyar tasu har yaji sauki,yau saura kwana uku tafiyar su Rahab Lahab Kuma sai Nan da sati daya,wanka sukayi tun safe yau Kaya iri daya Lahab ya yarda Suka saka jamfa da wando yau harda hula,motar Shareef Lahab ya karya su uku harda uzaifa Suka shiga Suka Soma bin gidan Yan uwa Suna musu sallama, lokacin da sukaje gidan ya jafar 100k ya baiwa Koh wannen su nanne ma ta dan Basu wani Abu daga Nan gidana Anwar Suka biya sun samu Aisha na fama da laulayin ciki Anwar ma ya basu kudi har 30k Koh wanne suka Masa godiya daga Nan Suka ringa yawon sai kusan yamma Suka Isa gidan Mami.





tunda Suka shigo da Lahab ya gaidata Bata Kara bi ta kansa ba sai Hira take da uzaifa da Rahab sun dan Jima a gidan lokacin da sukazo tafiya, ta saidasu ciki ta shiga sai gata ta dawo da laida manya manya biyu ta mikawa uzaifa daya daya ta mikawa Rahab tana cewa zata zo ranan da zasu tafin insha Allah godiya Suka Mata sai Kuma Rahab ya kasa hakuri yace Mami Ina na Lahab wani mugun kallo data Masa Bai sake cewa kome ba Suka bar gidan haka Suka ringa yawon gidan Yan uwa sai goshin mangariba Suka nufo gida har sun wuce kofar su Nabeel da Sauri Rahab yace Lahab dan dakata Bara na shiga gidan Inna na Mata sallama rabona da gidan su bazan iya tunawa ba?ba musu Lahab ya tsaya dukansu Suka fito a motar cikin gidan Suka shiga da sallama.





Amsawa Nabeel dake zaune Yana wanki yayi tare da mikewa ganin su dukansu inna ma fitowa tayi Suka zauna ana gaggaisawa Lahab ne ya kalli Inna yace"Inna daman zamu tafi karatu abroad ne shine mukazo mu muku sallama"waro Ido Inna tayi tace inane abmro Kuma"?dan murmushi yake Nabeel yayi yace Inna kasar waje,da Sauri yace ah ah ikon Allah haba shiyasa naganku dukan ku rabona da Rahab yazo gidan Nan harna manta sai yau"murmushi sukayi tare ana ta Hira duk da su Inna ba wani gane Rahab da Lahab sukayi ba kasa hakuri Nabeel yayi yace"daman Ashe zaku bar nageria amma Ade bai fadamin ba"kauda fuska Lahab yayi baice kome ba yasan so Nabeel yake ya gane sa a tsakanin su sai Rahab ne yace"eh wallahi xamu tafi mu gata zamu tafi Lahab da Ade sai next week"gyada Kai Nabeel yayi,mikewa Lahab yayi suma su uzaifa Suka mike Suna ma Inna sallama tsaidasu tayi tace Bara ta Basu kudi ba yawa kin karba sukayi amma Inna tace sai sun karba 150 ta Basu Wai kowa 50 hamsin sannan Nabeel ya rakasu kasa hakuri Lahab yayi ya tambaye sa mubeena yake ce Masa Bata Nan ta tafi makaranta.




Sauka Lahab yayi yace su Rahab su koma akwai wani gidan abokin sa da zaije,Suna wucewa yad'au wayar sa ya Kira faruq akan ya kawo Masa Nnenna,ya Masa kwatancen restaurant da zaizo,zaune yake akan table in an musu ordern abinci Kamar ance ya d'aga kansa ya hangota sanye cikin hijab har kasa Mai hannu fuskarta d'auke da glass Baki wallahi ba karamin kyau ta Masa ba faruq na rike da hannunta Suka karaso ciki hannu Lahab ya d'aga musu,sanann ya mike Suna karasowa ya Kamata ya aje a kusa dashi faruq kin Zama yayi yace zaije ya dawo Yana barin restaurant in cikin alhini Lahab ya kamo hannun Nnenna yace"Labiba"na'am ta amsa masa a hankali"Labiba Zan tafi"da mamaki tace Ina zakaje ya d'aga isowata kace wani zaka tafi"?




Labiba ba irin tafiyar Nan bane dana Saba Zan tafi karatu wani kasa"hannu tasa ta zare glass Inda ke fuskarta saiga hawaye Shar da Sauri yasa hannu Yana share Mata hawaye Yana cewa"bazan wani Jima ba zanna dawowa hutu karki damu kinji"?yanzun kana nufin saina Jima kafun na Kara ganinka"ya zanyi Labiba nayi-nayi kokarina na ganin muntafi tare amma bani da halin haka Koh bashi da kudi Zan karba nasan babu Mai bani bashi"a hankali yace kudine zai Hana mu tafi kenan?kanason tafiya dani"?da Sauri yace sosai ma"d'an shuru tayi tana tunanin wani Abu,da Sauri yasa hannu ya zare tagumin dake fuskar ta Yana cewa"tunanin me kike"da Sauri tace in kanason zuwa dani Zan iyya biyawa kaina kudin jirgi.............................










*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*


πŸ€ *By Ruqeenjalal* πŸ€



*BUZHUWA EmphireπŸͺπŸͺ*
Assalamu Alaikum,Barkanmu da wannan lokacin ,Sannun mu da shigowa Halarar mu na buzaye.... Albishirin ku matan AureπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ BUZUWA EMPIRE ta taho maku da sirrika na MALLAKAR mijin ki yar uwa a hannun ki ba tare da boka ko malam ba. Matan da yawa na fuskatan matsalolin su da maxajen wato kalubalen a gidan auren mu...kuma irin wannan maganin matan Asha tabaje...mene wani shirme wani gayinan dai ,bashi ne ba... Ina macen da daga zarar mai gida yy sallama gaban ki keda yara ya hau fadi?. Ina macen da mijin ta kullum idanun shi na akan matan banxa?. Ina macen da ga kudin mijin yanada amma babu ci sai dai duniya suci yy kyautan riya? Kai duk wani matsalan ki na gidan Aure kizo taskar BUZUWA EMPIRE. zata baki mallaka ta hanyar sirorin kur'ani da dai sauransu.
Mallaka ta hanyar kwai
Mallaka ta hanyar nama ,madara ,kifi , yan shila da dai sauran su..
Ga kuma mallaka ta hanyar suratul yusuf .
Mallaka ta hanyar jauhara.
Mallaka ta hanyar Yaseen
Mallaka ta hanyar fatiha umul qur'an.
Mallaka ta hanyar turaruka da dai sauran su...
Ina Yammata marasa farin jini ?πŸ’ƒ
Kuzo kuma da naku ,sai kaji ana gata mummuna baka kirin amma sai farin jinin manyan alhajazai masu jifa jifai kome take dashi oho..!! Kuji ita tasan inda tazo ta taho taskar BUZUWA EMPIRE . sai kin taho yar uwa gaba daya sirrin nan na farin jini dana mallaka 5k ne duka . Idan kuma mallaka ne kadai munayin na 2k da kuma 3k. Na farin jini kacal 3k ne ,gamasu bukata zasu tuntu6a wannan number 08081202932 09061466409









Ina Zaki samu kudin jirgi kinsan nawane kuwa"?gyada Kai tayi a hankali tace"akwai Wanda na aje kudina a wajen sa"had'a fuska yayi Jin tace wani Wai Kuma ta aje kudi a wajen sa"ganin yanda yasha mur sai taji jikinta yayi sanyi a hankali tace"toh shikenan na hakura da tafiyar hararanta yayi yace"toh wa Kika baiwa kudin Kuma a Ina Kika samu kudin da Kika aje"labarin shu'aibu da haduwar su harma da Alkharin da aka Mata na 500k shuru Lahab yayi sannan yace Zaki iya gane unguwan Kuwa"?Koh sunan sa tunda Baki gani"?murmushi tayi anan take sanar dashi sunan unguwan mikewa yayi faruq ma ya mike tsaye kallon sa Lahab yayi yace"ka maidata gida Ni akwai Inda zani".






Unguwan su shu'aibu Lahab ya wuce daker da kwatance ya gane gidan shayibu bayan yayi sallama Nan wani mutum ya fito yake sanar dashi ai shayibu ya Jima da barin gidan yanzun yayi kudi yana wani unguwa Alfarma Lahab ya nema mutumin ya had'asa da yaron da zai kaisa gidan shu'aibu,Suna Isa kofar gida kwankwasa kofar sukayi maigadi ya leko tare da tambayar su wa suke nema Mai gidan Lahab ya bukaci Gani ba musu ya barsu Suka shiga,zaune Lahab yake a falon gidan yakai kusan minutes Sha biyar kafun wani matashin magidanci ya fito da fara'arsa Zama yayi Suka gaisa da Lahab Yana tambayar sa Bai gane sa ba anan Lahab ke sanar dashi labarin Nnenna da kudinta da zai karba a hannun sa,cikin bakin ciki shu'aibu yace,eh wallahi yaji duk abinda ya faru Kuma ya tausaya wa Nnenna, ya Kuma yiwa Lahab Alkawarin zai basa kudin Nnenna ya Kai Mata haka zalika a Aljuhunsa zai biya Mata kudin jirgi don ba karamin business yanzun yake ba account numbern Lahab ya karba a take ya tura Masa 500k cib da Nnenna ta basa rance yad'au 200k ya aje Mata 300k,amma ya had'a duka ya bata lokacin da Lahab ya Soma zancen kudin sunyi yawa shayibu yace babu abinda zai biya Nnenna dashi sai fatan Alkhari domin itace sular arzikin sa.






Lahab na komawa gida waya ya d'auka ya Kira faruq akan gobe yakai Nnenna a Mata passport za'a nema Mata visa,cikin yardan ubangiji an kammala shirye shiryen tafiyar Nnenna sai rana kawai ake jira,yau ne su Rahab zasu tafi Koh bacci ya kasa na dare bini-bini sai yazo katifar Lahab ya leke fuskar sa sanann ya koma ya kwanta a hakan har asuba tayi sukaje sallah gabaki d'aya mood nasa ya canja yayi wani sanyi dashi,bayan dawowar su sallan asuba ya zauna ya buga tagumi yayi shuru,akwatin Rahab Lahab ya janyo ya Fara had'a Masa kayansa ganin Zama yayi Kuma flight in safe zasubi,kallon sa Rahab yayi a hankali yace"kana murna zamu rabu Koh"?






Da mamaki Lahab yace akan me zanyi murna Koh ka manta ba hakan na nufin mun rabu bane fa,zamuna dawowa hutu haka zalika zamu sada zumunci ai Ni nama fika Kewan rabuwar mu"wani banzan kallo Rahab ya Masa cikin haushi yace da kana kewata bazakayi munafurcin tafiya Kai kadai ba dariya Lahab ya Fara hade da kamo hannun dan uwan nasa har toilet kafun ya fita ya barsa a ciki.








****************
Da misalin karfe 8 Mami ne da yaranta Suka shigo gidan harda Anwar da Aisha duk sunzo rakiyar su Rahab gidan a cike,daga Nan airport Suka wuce gabaki dayan su suka musu rakiya lokacin da Rahab yazo rabuwa da Lahab baisan lokacin da kuka ya subuce Masa ba da Sauri ya rungume Dan uwan NASA haka kawai Lahab yaji gabansa ya Fadi ganin yanda Rahab ya nuna kin son tafiyar,sai da Abbu yasa baki Jin ana Kiran passenger sake Lahab Yayi ya rungume Mami ya had'a da Addayiya sai Kuma ya Kama kafadan Abbu ya runguma kana ya sake su yajuya ya Soma tafiya sai yayi nisa sai Kuma ya juya ya Kara daga musu hannu Harya shiga jirgin,Basu bar airport ba har jirgin ya d'aga suka Lula sararen samaniya kafun Suka koma gida gabaki dayan su.







After one week yau su Lahab zasu tafi tun safe yasha wankan sa yaci abinci ya zauna a Kan kujera ya tasa akwatunan sa a gaba yana duba agogo Allah Allah yake 12:30 yayi Koh su Abbu zasu fito,Maigadi ne yayi sallah a falon amsawa yayi ba tare da ya kallesa ba"am Lahab wata ce ke sallama dakai a waje"waro Ido Lahab yayi yace sallama dani Kuma nidin"?kwarai ma kuwa" farace Koh baka"?farace tass"toh wacece haka sai Kuma yayi tunanin Koh Nnenna ce.





Mikewa yayi da Sauri ya fita wajen da mamaki ya bude kofar gate nasu amma baiga kowa ba harya juya zai koma ciki sai yaji an Kira sunan sa a kofar wani gidan makwacinsu da mamaki yakebin mubeena ganinta tsaye gabaki d'aya ta rame Masa wallahi,"Aunty kece Kuma Kika tsaya a waje Baki shigo ciki ba"?girgiza Kai tayi a hankali tace"basai na Shiga ba Nabeel yacemin Wai yau zaku wuce ga wannan Ina maka fatan Alkhari Allah ubangiji ya baka duk abinda kaje nema muddin Alkhari ne"hannu yasa ya amshi laidan Yana Mata godiya tare da bude laidan Yana kallon meyake ciki sai Kuma ya dago Suka had'a Ido murmushi yake tayi tace"sai wata Rana"murmushi shima yamaida Mata cikin fara'a yace toh sai wata Rana Aunty mubeena Allah sadamu da Alkharin kilama kafun na dawo kinyi aure tunda kince bakison abokina"murmushi yaga tayi sosai yaji mamaki yasan mubeena batason Wasa Sam amma yau ya tsokonota sai Kuma tayi fara'a"sai Kuma ya tsaya ganin har lokacin bata da niyar tafiya sai kallon sa take.




juyawa yayi zai shiga gidan da Sauri ta kirasa cikin dan murmushi tace ga number ta Inka Isa Koh zaka kirani sai muna gaisawa?"la Aunty mubeena Ina da number ki insha Allah Zan kiraki sai Kuma ya d'aga Mata hannu ya shiga gidan, kuka mubeena ta Soma tana tafiya tana share hawaye,Allah sarki uwa uwace duk irin haushin Lahab da Mami keji kasa hakuri tayi tazo rakiyar sa Saida Suka iso airport kafun ta d'aga hannu ta maka Masa dundu Mai zafi Wanda ya sashi Kara Yana kallon ta magana ta Soma kamar haka"watoh Lahab harka Kai matsayinda zaka min abu inji haushi Kuma ka kasa bani hakuri Lahab zaka sa kafa kabar kasar Nan da haushin uwarka Kuma kana tunanin zakaci nasarar abinda kake bukata"




Rungumarta yayi yace"mamina Nina San kin Jima da yafemin Kuma sai hadamun fuska kike shiyasa na kasa baki hakuri"zungurar sa tayi yace"Koh da wuka nake rike dashi Lahab zaka kasa bani hakuri,girgiza Kai kawai yayi ya nemi yafiyar kowa daga danginsa sukayi sallama ya nufi jirgi, Ade dake gefe Suna buga rikici da papa don papa badon kudinsa daya kashe da kamawa Ade gida acan dayayi ba aradu da Ade bazai tafi da Lahab ba baisan da zancen tafiyar ba Saida ya hade da Yan gidansu yanzun a airport ganin Lahab ya nufi jirgi shiyasa Adewale mikewa yabi bayan sa bai damu da masifar papa ba, tunda sunyi sallama da mahaifiyarsa.





tunda Lahab ya juya Yana tafiya Bai Kara waigowa ba Koh sau daya Harya shiga jirgi shigowarsu Kenan ya Soma rarraba Ido Yana neman sit Inda Nnenna ke zaune don shu'aibu yace Masa yabar kome na tafiyar Nnenna a hannun sa har cikin jirgi zaisa a kaita amma Bai ganta ba saboda girman jirgin gajiya yayi da dubawa ya juya zai koma waje amma aka hanasa fita Ade kam na zaune baisan dawan garin ba don sit nasu ba daya da Lahab ba Yana gaban Lahab,Jin rikicin Lahab da ma'aikatan jirgi ya Sasa mikewa yazo Yana tambayar ba'asi da Kuma dalilin dayasa Lahab keson fita waje,kin basa amsa Lahab yayi ya koma ya zauna a filin sa shima Ade komawa yayi ya zauna.




Rumtsa Ido yayi da karfi gaske wannan shine karonsa na farko a jirgi Kuma zaiyi tafiya har wata kasa gashi baida tabbacin Nnenna na cikin jirgin.






Jirgin su Lahab ya sauka lafiya klau a babban birnin London cikin dare, passenger ne Suka Fara fita d'aya bayan d'aya mikewa Adewale yayi Yana kallon Lahab ganin baiyi niyar mikewa ba kala baice ba ya d'au akwatunan sa ya fita waje mikewa Lahab yayi ganin mutane nata fita,da mamaki yaga an bude private sit dake ciki saiga ma'aikaciyar cikin jirgin ta fito tana rike da hannun Nnenna waro Ido yayi da Sauri ya karaso wajen cikin farin ciki ya riko hannun ta da Sauri ma'aikaciyar tace"Kai ya haka ya zaka kama mata hannu?kafun ma yace wani Abu da Sauri Nnenna tace"shine Wanda nace ki dubomin kikace baki ganesa ba,au toh gata shine abinda tace tana Mika Masa jakunkunan Nnenna da shu'aibu ya Mata shopping sosai.





Sauka suke a steps na jirgin a hankali sunyi wani irin masifar kyau sanye take da abaya baki shi Kuma yana sanye cikin kananan Kaya jakunkunan su na hannun ma'aikatan Suna sauko musu dashi,Baki sake Ade yake kallon su daga inda yake tsaye Yana salati cikin tashin hankali ganin Nnenna tare da Lahab a London bai taba kawowa ransa wannan abun ba.





Juyawa yayi ya wuce ba tare da ya jirasu ba dayake Yana da address in Inda zasu sauka Hawa taxi kawai yayi ya Mika Masa address in,Lahab Kam Yana rike da hannunta Suka fito cikin airport in ya tare taxi shima ya hau ya d'ura kayansu Suka d'auki hanya,har sunyi nisa yace wa bature ya kaisu Inda zasu samu abinci watoh restaurant,abinci Lahab yayi order harda laidan Abraham, unguwa ne Mai kyau Mai d'auke da ginunuka iri d'aya akallah kofa-kofa yakai sama da hamsin Kuma Hawa uku,sauka Lahab yayi ya ringa dudduba number floor har Allah yasa ya samo numbern dakin nasu a Hawa na uku suke,nufar wajen Nnenna yayi Yana korafi a ransa wannan ai sai wata rana ya manta dakin nasu ace Hawa har uku dakuna sunkai sama da hamsin amma ace kome iri daya kamo hannun Nnenna yayi yabar jakan nasu a kasa ya Soma haurawa upstairs in da ita Suna taka steps in a hankali Hawa na biyu Suka hau gabaki d'aya taji ta gaji Zama kawai tayi tace zata huta,komawa kasan yayi ya dauko musu kayan su ya hauro dashi har lokacin tana zaune a matakalan,aje kayan yayi ya ciccibeta duk yanda tayita cewa ya sauketa ki yayi Saida ya kaita har kofar dakin su hannu yasa ya bude dakin ya shigar da ita,falone madaidaici sai wasu steps guda uku Wanda Koh ba'a fada Masa ba yasan kitchen ne a wajen ai dakuna guda biyu a falon sauketa yayi ta zauna akan kujera shi Kuma ya koma waje ya dauko bags nasu,kome akwai a falon TV fridge AC abubuwan more rayuwa duk akwai dakin dake hannun hago ya bude Adewale ne zaune akan kujera ya zuba tagumi Yana kallon gefe bude kofar baisa sa ya juyo yaga Wanda ya buden ba shima Lahab rufewa yayi ya bude na dama alamu shine dakin sa.





Ajeta yayi a bakin gadon kana ya aje akwatunan su a gefe,Zama yayi a bakin kujeran dakin ya zare takalmin Boot dake kafarsa ya zame black socks in duka kayan sa ya cire ya rage daga shi sai wando dogo toilet ya shiga yayi wanka da Alwala ya fito bude jakansa yayi yadatu darduma tare da kallon Nnenna dake zaune a bakin gado Yana cewa ta jirasa bari yayi sallah ya kawo musu abinci"gyada Kai tayi tace"so nake nayi wanka tukun

Please Login or Register in order to submit comment