Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

girgixa kai kawai yayi baice kome ba gudun masifa don yasan yanzun D'an uwan nasa a cike yake dam jira kawai yake a tabosa ya sauke.

Wanka yayi yazo ya kwanta, amma baiyi bacci ba har kusan 11 ganin da gaske Lahab ba kwanciya zaiyi ba yasa Rahab tambayar sa, lahab bakajin bacci ne?

"Kaga malam kayi baccin ka kawai ni ba yanzun zan kwanta ba"

Kamar ya ba yanzun zaka kwanta ba, lahab bayan mun saba kwanciya tare kuma bama kai warhaka?

"Yau kuma nace banaji koh? ka rabu dani mana"

Kwanciya yayi tare da kashe wutar dakin, amma bai kwanta ba ganin lahab a xaune yana danna waya.


Har 12 yau basu kwanta ba tun lahab na d'aukar abin da wasa, Rahab keyi harfa ya fahimci da gaske yake, in bai kwanta ba shima baxai kwantan ba, kwanciya yayi hade da rufe jikinsa ya kashe wayar yayi likimo kamar yayi bacci, aiko ganin haka yasa Rahab shima gyara kwanciyar har bacci ya d'auke sa.

Misalin karshe 1 na dare wanda yayi daidai da nauyin baccin rahab, mikewa lahab yayi da sauri ya kunna wayar sa ya haska lahab don kara tabbatar wa yayi baccin da gaske.

Toilet ya nufa da sauri ya d'auko abubuwan aski, zama yayi a gefen Rahab daman shikam akwai nauyin bacci d'aga kansa yayi kad'an yasa clever yana aske masa gashin kai, sosai ya rage daidai irin nasa, gemun ma ya gyara sa sosai kamar yanda tasa yake yana gamawa da sauri ya maida kome toilet.

Jan Rahab yayi ya maida shi kan katifar sa ya lulube sa, ya d'auko jakan Rahab ya juye takandun sa a nasa boron, ya sanya nasa ana Rahab, sai kuma ya kakkabe katifar rahab ya kwanta akai.


***************
Nnenna ce zaune akan gado ta fifitar da kayan makarantan ta tasa a gaba tana kallo, koh abincin dare bata ciba ga gajiyar aiki da tasha, amma ta kasa bacci ji take kamar inta kwanta ta tashi da safe za'ace mafarki take.

Turo kofar akayi tare da Neman excuse, riganta ta d'auka da sauri ta saka jin muryar Abraham ne, tana sanyawa ta amsa masa ya shigo, kallon ta yayi ya sake kallon kayan sai kuma yayi murmushi yazo ya zauna a bakin gadon, beauty hope kayan sun burgeki?

Gyada kai tayi kawai tana tattara kayan tana ajewa a gefen gadon cikin zumudi shima baice kome ba, sai kallon ta yake sai kuma ya mike tsaye ganin ta sa hannu ta kashe wutar dakin ta kwanta ba tare da tayi masa magana ba, yana fita ta rufe kofar ta kwanta har bacci ya d'auke ta.



*****************
Misalin karfe 4 na asuba Muzammil ya farka kamar yanda ya saba, daman lokacin tashin sa kenan, mikewa yayi ya sanya kayan sport a jikin sa.

D'akin su lahab ya nufa hannu yasa ya tura kofar kaman yanda ya tsammani basu rufe ba, shiga yayi ganin dakin da duhu yasa sa lalubar makunni ya kunna wutan d'akin, katifar Lahab ya nufa, yasa hannu ya d'ana masa duka a baya ji kake dom.

Innalilahi Rahab yace da sauri yana mikewa zaune cikin Al'ajabi yake bin uncle in nasu da ido, uncle lafiya?

Uwarka ne tashi ka sanya kaya mu fita jogging?

Ni kuma Uncle?

Eh koh akwai wanda nace wane bayan kai?

Amma uncle ai naga l.....

Bai bari ya karasa ba ya daka masa tsawa, mike nace koh jikin ka ya gaya maka.

Mikewa yayi cikin magagin bacci don shi baima fahimci katifar ba tasa bace da sauri ya nufi wardrop nasa, ya d'auko wando da riga na basketball ya sanya toilet ya shiga ya wanke bakin sa.

Fitowa yayi tare da marairaice murya Ayya uncle nifa banason jogging in nan Lahab nefa ke zuwa.

Zaro ido muzammil yayi yana tambayar Rahab, wani Lahab in bayan kai kuma, ni zaka mannawa hauka d'an iska?

Wallahi uncle bani bane ga lahab a kwance.

Make masa keya muzammil yayi, shige muje banason karajin wata magana a bakin ka, shasha sha kawai kullum musu a cikin ka, watoh na fita jogging kafun na dawo ka sa kafa kabar gidan koh? shige nace.

Tsamo-tsamo haka Rahab ya ringa binsa a baya ga sanyi kamar yayi me sai yanzun ya gano Abinda lahab ya masa especially daya taba kansa yaji ba gashi.

Lahab dake kwance yana jinsu jin sun fita yasa sa kyalkyalewa da dariya don daman tunda Uncle ya shigo yake matse dariyar karta fitoh,dawowa katifar sa yayi, gyara kwanciyar sa yayi yaci gaba da baccin sa.

Rahab kam a gaba Uncle ya sashi suka ringa zagaye tun daga unguwan su har round about suka sake bin bayan layin su basu suka gangaro gida ba sai 5 In mutum yaga Rahab sai ya tausaya masa gabaki d'aya ya shanja yayi wujiga-wujiga dashi.

Suna shiga gidan a lokacin jama'ar gidan keta Alwalan asuba,umurni ya bawa Rahab akan yaje yayi wanka, ya basa 5 minutes shap-shap yana maganar yana shigewa d'akin sa dake gidan.

Rahab na shiga dakin daidai lokacin Lahab ya fitoh toilet sanye da gajeren wando da gani Alwala ya d'auro, shakosa Rahab yayi cikin masifa yace, me yasa Lahab zaka aske mini gashin kai?meyasa zaka maidani shimfidar ka meyasa? yana maganar yana girgiza sa da karfi.

Turesa Lahab yayi cikin shekiyan ci yace"kowa kai yake so, kowa kai yake gani a matsayin nasa, ni babu mai sona a gidan nan hatta mamin mu kai tafiso dani, a wannan karon kaima zansa kaji yanda nake ji"

Nina hanaka ka zama na kirkine koh ninace karsu soka?tayama zasu soka a haka, yace yana nuna lahab da yatsa.

"Ok shikenan gani gaka kaima sai ka d'an d'ana abinda nake ji" ya karasa maganar cikin bagu ya taka har bakin katifar sa ya zauna ba tare daya saka kaya ba.

Da sauri Rahab yayi wanka ya fitoh jallabiya yasa fari sai hula shima fari silifas yasa a kafarsa ya fita a d'akin yabar Lahab har lokacin zaune akan katifar sa.


Ganin ya fita yasa lahab mikewa da sauri bude tasa wardrop in yayi ya zaro jallabiyar sa fara kal sabuwa irin na Rahab dan daman koda yaushe in za'a sai musu kaya iri d'aya ake saya, indai na sawa ne a baiwa kowa nasa, amma shi sai dai ya ajesu yasai irin nasa, saka jallabiyar yayi ya d'auki hula ya saka irin na Rahab ya sanya takalmin sa irin na d'an uwan nasa.

Murmushin mugunta yayi sai kuma da sauri ya fita a d'akin jin uncle na kwala masa kira a falo, fitowa yayi ya kalli Uncle in, "ah ah uncle barka da asuba Lahab fa ya fita masallaci yanzun nan"?

Ok toh muje Rahab na d'auka koh bai fita bane ai d'an banzan yaro sai nayi da gaske kafun nabar gidan nan, don naga su yaya sun zuba masa ido yana abinda yaga dama.

Da sauri lahab yace"wallahi kam uncle koh school baya zuwa"

Karka damu ai yau kafata kafarsa har makaranta d'an iska, sawa zanyi a shanja masa aji bazai zauna da abokan shashancin nan nasa ba.

"Hakan ma yayi uncle"ya karasa maganar daidai da isar su bakin masallaci, shiga sukayi aka tada sallah.

Ana idarwa suka fifito daga masallacin sai kuma su Abbu suka bisu da ido cikin mamaki ganin su yau sak iri d'aya, uncle ma zaro ido yayi kai menene haka yau kuka sanya kaya iri d'aya?sai kuma ya nuna rahab kai shige muje.

Zaro ido Rahab yayi wallahi uncle bani bane ga lahab nan, da sauri lahab ya nuna sa da ido, "kai lahab ka shiga taitayin ka banason iskanci fa, uban wa yasa kasa kaya irin nawa"

Kama baki Rahab yayi bangane ba bani na fara fita a d'akin na barka zaune ba?..

Kafun ma Lahab yayi magana da sauri Uncle yace d'an banza watoh kaika fara fita ka barsa a dakin kenan, dashi mukazo masallaci shige muje nace maka koh?

Ba yanda Rahab ya iyya haka yabi Uncle a baya yayin da Lahab yabi su Amma cikin natsuwa, kamar na Allah suka nufi babban falo yayin da uncle ya wuce da Rahab garden.

Suna shiga ya tsunguna kamar yanda Rahab keyi ya gaida Abbu sauran yaran suka gaggaishe sa gaida Addayiya yayi dasu mamu kafun ya wuce d'akin su, kwanciya yayi abinsa har bacci ya d'auke sa.

Da misalin karfe 7 Rahab ya shigo d'akin jikinsa duk tabo Alamu dai gyaran flowers sukayi kafa yasa da karfi ya tunkude Lahab dake kwance, mikewa yayi da sauri ya kalli Rahab sai kuma ya ruga da gudu yayi toilet saboda Agogon bango daya gani, wanka yayi ya fitoh yana kallon Rahab"sannu biyu na zoka wuce kaje kayi wanka,

Tsaki kawai Rahab yayi ya wuce toilet, mai Rahab ya shafa a jikinsa ya d'au uniform nasa ya saka, wando ne nevy blue sai riga fari tas mai dogon hannu, neck-tie nevy blue ya d'aura a wuyansa, socks ya d'auko baki ya zauna a bakin katifar sa ya sanya, sai boot nasa baki mai igiya ya d'aura a kafar sa, agogo ya d'aura shima baki sai jakan makarantan sa shima baki ya rataya turaren Rahab ya fesa da sauri ya ruga yayi waje jin motsen d'an uwan nasa na kokarin fitowa daga toilet.

Yana fita a d'akin daidai lokacin tirmizi ya fito a d'akin su uzaifa, harda uzaifan ma da sauri lahab ya kwala masa kira kamar yanda Rahab keyi"kai angon addayiya wannan wanka duka nata ne"?

Hade fuska tirmizi yayi aini uncle babu ruwa na da kai, tunda dai jiya kuka koreni a dakin ku?

"Ayya ango kayi hakuri kaji ni babu ruwana"

Amma ai uncle Lahab ne, meyasa baka masa magana ya barni ba kana gafa har son dukana yayi?

"Yi hakuri zo muje daining koh"koh bazaka daina fushi dani bane"?

Na d'aina uncle, yace yana kama hannun lahab suka fita a falon su zuwa babban falo, gabaki d'aya mutanen gidan ne zazzaune a daining inka cire matan gidan dake zaune a falo suna cin abinci, sai Rahab da uncle da basu fitoh ba, da sauri Lahab ya gaida Nabeela harda kiran ta da aunty nabeela, amsa masa tayi tana yabon hankalin sa.

Zama yayi akan kujera zulaihat ta zuba masa breakfast nasa ya soma ci duk a tsammanin su Rahab ne.

Uncle muzammil ne ya fitoh cikin shirin jamfa da riga harda hula, da sallama ya shigo falon Amsa masa akayi duka aka sake sabon gaggai sawa, bin falon yayi da kallo har idanun sa suka sauka akan lahab dake zaune hankalin sa kwance yake yagar kazar sa yana ci, kai Rahab ina d'an uwan naka.

"Wallahi uncle yana ciki taima baza shi makarantan bane"

Da sauri mamu tace, aiko wannan karamin aikin sa kenan daman ba zuwan yake ba aini nagode Allah na godewa muzammil.

Gyada kai muzammil yayi ya juya ya nufi kofar falon su Lahab, yana shiga lokacin Rahab ke sanya uniform nasa, ai uncle na zuwa ya rufesa da masifa yana tsaye har ya gama kimtsawa gabaki d'aya hawaye ya cika masa ido, shidai ya shiga uku ace wai jama'a bazasu iyya gane saba koh banban tasa da lahab.
.
A gaba Uncle yasa sa har falo zama sukayi akan kujera suka soma karyawa, kallon Lahab zulai tayi, uncle Rahab ina assigment ina.

Da sauri Rahab dake gefe yasa hannu a jakan sa zai d'auko takardan Zukaihat duk da bashi ta tambaya ba amma yasan shi ta baiwa takardan ta, yana sa hannu kawai yaga takardu da ba nasa ba budesu yayi dakyau koh shakka bayayi takardon lahab ne.

Mikewa yayi tsaye hade da kallon lahab dake mikawa zulai takardan ta, lahab wallahi wasan kwaikwayon nan ya isheni haka ka bani takardu na, koh na maka mugun duka agidan na.

"Kallon sa lahab yayi, wai menene haka lahab tun asuba saice mini kake wai nine kai menene riban ka tsakani da Allah fa"?


Wani irin fusata Rahab yayi da mugun haushi ya sake takardun makarantan sa ya nufi lahab, don yana ga duka kawai zai iyya masa yaji sanyi a ransa, kai mara kunya????yaji uncle yace cikin bacin rai, wallahi lahab ka kuskura ka tabasa saina mugu-mugun saba maka munafuki daman ka aske masa kaine don kayi basaja.?

Tsayawa kawai yayi yana bin kowa dake falon da kallo, sai kuma kawai ya sabi jakan nasa ya nufi barin kofar, kiransa Uncle yake amma yaki juyowa, da sauri muzammil ya bisa yana kokarin fita a falon ya fizgosa wanke masa fuska yayi da lafiyayun mari wanda yasa gaban Lahab dake zaune faduwa bai d'auka abin zaikai harga duka ba amma dai baice kome ba.

Kai karamin d'an iska ina maka magana kana tafiya saboda kaje ka hadu da yan iskan abokan nan naka ku shiga gari koh? toh yau kafata kafarka har makarantan naku abincin ma bazaka ciba.

Shuru kawai Rahab yayi yana dafe da kumatun sa yana kallon d'an uwansa yana mamakin Faruwar Al'amarin.


Suna tsaye har aka gama karyawa Uncle ya durasu a mota dukan su rahab ne lahab ne muneera da zulaihat, yaja motar suka nufi school nasu.....





***************
Nnenna tun asuba ta farka da sauri tayi brush ta sanya d'aya daga cikin kayan da Abraham ya sai mata, dogon riga ne bai iso koh gwuwa ba, sai hulan sanyi data saka, fitowa tayi cikin murna ta fara aikin ta, watoh share-share da goge-goge har tsakar gidan ta goge tiles duka, wanke-wanken dake kitchen duk ta tattara ta wanke tas.

Daki ta shiga tai wanka, uniform in ta sanya siket ne nevy blue sai riga mai dogon hannu, stokin na rigan tayi a cikin siket in, hannu tasa tadau nect-tie nata blue ta sanya dayake tasan yanda ake nade abin tunda papa na makalawa, socks tasa fari sai boot nata nevy blue, empty jakan ta nevy blue shima ta d'auka, amma babu takardu a ciki kulenta dake gefe ta d'auka ta sanya a jakan, barect nata ta kafa akai daman gashin ta a tunkushe yake bata warwarewa ma bare.

Agogo ta kallah karfe 7:00pm daidai ta fito a d'akin taku take a hankali tanajin ta wani iri cikin kayan uniform nata, tana isa falon gabaki d'ayan su suka bita da ido, ganin wani irin azabebben kyau datayi kamar dan ita akayi uniform in, jennifer turmude fuska tayi cikin hassada, Abraham kam kamar ya taso ya rungume ta haka yakeji koh zaiji sanyi.

Tsungu nawa tayi akan gwuwar ta tana gaida dady dake zaune akan daining, Amsawa yayi sai kuma ta gaida Abraham ya amsa da sauri haka ma sarah ta amsa ba walwala, sabanin momy da Jennifer da sukaki Koh amsa mata ma.

Kallon ta dady yayi, daughter gashi yau dai zaki fara zuwa makaranta, abinda nake so na fad'a miki shine kinga makarantan da zakije ba irin na kauye bane? wannan makaranta ne na birni sannan Muslim and Christian ne, babu ruwan ku da yaran hausa wa kar naji kar na gani, kika kuskura naji labarin an ganki da yaran Hausa wan nan, toh sai na cireki kuma banda kawayen banza,kiyi abinda ya kaiki kinji koh?

Dukar da kai tayi sosai"i promise u Dad bazaka sameni da sab'anin hakan ba"

Ok daughter ni zan fita ga Abraham zai kaiku school na basa kudin da za'a cherge ku.

"Thank you Dad"

Ur welcome daughter yace yana mikewa tsaye ya sabe jakan dake zaune akan kujera ya bar falon, kallon ta abraham yayi, Beauty kije kitchen ki ibo abinci time na gudu.

Mikewa tayi da sauri mom ta daka mata wata uwar tsawa, koma ku zauna yar iska bakauyi ya, babu inda zaki duk rawan kafarki yau bazaki school din nan ba,nuna jennifer tayi ke Jennifer tashi brother ya kaiki school karkuyi late.

Kallon ta Abraham yayi, haba mom ya haka bakiji Dad yace na kaita school ba?

Naji, ni kuma nace bazata ba, kuma wallahi ka kuskura ka sanar da mahaifin ku saina saba maka.

Jin abinda mom tace, yasa Nnenna sake kuka da karfi shikenan murnar ta zai koma ciki.....................







✨Ruqeenjalal✨





πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya Ibrahim*πŸƒ

✨Tsokaci ALKAWARIN MASOYA na kudi ne gamai bukata naira 300 ne kacal ki tuntube ni ta layin nan whatsApp only 07044407979πŸ‘Œ

Free page🀧


*EXQUISITE WRITER'S FARUM*


page2⃣5⃣&2⃣6⃣
Kuka Nnenna take Amma koh tausayi babu haka mom tasa Abraham d'aukar Jennifer zuwa school sarah ma makaranta abinta ta tafi, mom yau koh aiki bataje ba, dole tasa Nnenna komawa daki ta kifa kanta tana kuka sosai, koh karyawa batayi ba a haka tayita zama a daki.

Shima Abraham da sauri ya aje jennifer a tunanin sa mom ta tafi hospital, amma me yana zuwa yaga mom xaune a falo, haka ya sake komawa da baya yabar gidan kawai.

Har azahar Nnenna na xaune a dakin tana kuka koh kayan bata cire ba.

Dad dake wajen aiki ne, Abraham yaje ya samu ya sanar dashi abubuwan dake faruwa, sosai yaji Ransa ya baci matuka bai taba zaton yawan amsa wa mom bukatun ta babu musu shiyasa ta d'auka koh tsoron ta yake ji.

A fusace ya nufo gida cikin bacin rai...

*******************
Lahab kam suna isa makaranta haka yayita bin makarantan da ido rabon sa da zuwa school tun komawar muzammil barrack, suna isa makarantan daman shike zaune a baya dasu muneera Rahab na gaba tare da muzammil in.

Yana packing duk suka sassauka, hannun Rahab muxammil ya kama suka nufi office in principal, yayin da su lahab suka shishige Ajujuwan su.

Lahab na shiga ajin wajen da Rahab yafi zama watoh benchin gaba agun ya zauna tare da fiffito da takardun Rahab ganin maths teacher nasu ya shigo.

Ta bangaren Rahab kam suna shiga office in Muzammil ya bada sanarwa akan so yake a shanja ma Lahab aji a ciresa daga A zuwa B class sannan su saka masa ido duk lokacin da ake lesson baya aji a kirasa kuma a tabbatar ana binciken littatafan sa, yayi rubutu koh ah ah, 20k ya baiwa disple master nasu akan lahab, zaina zaman extra lesson da hadda, in yazo tun safe sai 5 na yamma zaina komawa gida.

Rahab kam hawaye ne kawai yake bin kumatun sa lokacin da disple master ya tasa keyar sa zuwa B class.

Muzammil na komawa gida zama yayi ya karya,suna hira shida addayiya a falo, don matar sa ta tafi gidan su da yaran sa ba kowa a gidan sai su ummu suma suna daki,ji sukayi ana kwala sallama a bakin kofar falo, addayiya ce ta amsa duk da ta gane masu muryar amma bata nuna ta ganesu ba sai ma tambayar su datake akan su wane ne su shigo.

Muxammil kam mikewa yayi da sauri yabar falon, aiko suna shigowa suka soma gaida Addayiya, yamutsa fuska tayi ta amsa ba yabo ba fallasa, lafiya kuwa yan duniya na ganku anan?

Nabeel ne ya bata Amsa, lafiya addayiya munxo wajen lahab ne, da safe bai fitoh jogging ba gashi wayar sa munyita kira ba'a d'agawa da safen nan.

Ok toh ku shiga d'akin nasa ku duba taima yana aikin nasa watoh bacci.

Mikewa sukayi suka nufi dakin su lahab, suna shiga suka ga ba kowa a d'akin, toilet Adewale ya nufa hannu yasa zaiyi knocking kawai yaga toilet in ya budu, tsaki yaja mtwsss wallahi nabeel ba kowa a dakin nan, sai Allah ina ya shiga yau kuma tun safe.

juyawa sukayi zasu fita a dakin sai kuma suka ja da baya ganin Muzammil tsaye ya harde hannu.

Da sauri dukan su suka tsunguna suna gaidashi, d'aga musu hannu yayi ba tare da yayi magana ba ya musu nuni da hannun sa akan su biyo sa.

Fita yayi a d'akin suna binsa a baya saida sukazo falo, sai kum ya tsaya tunawa da yayi karfa ya fita dasu compound su arce a d'ari don halin sune dagasu har abokin nasu lahab gudu ba abin kunya bane a wajen su.


Kofar dake falon ya turasu wanda zai kaisu har garden, suna dai binsa a baya har garden yayin da ransu in yayi dubu ya baci watoh lahab yasan kwanan zancen amma bai sanar dasu boss ya dawo ba, bare ma nabeel ya shaka sosai.

Zama yayi akan d'aya daga cikin kujerun gabaki d'ayan su yasasu linkdown, kallon su yayi, meya hanaku zuwa makaranta?

Uncle munzo duba lahab ne koh lafiya yau bamu gansa da asuba ba, daman in muka dubasa sai mu wuce school.

Ok daman kun daina sa uniform ne?

Ah ah uncle daman in mun zo mun dubasa sai mu koma musa ne.


Makarya ta yace ana d'aukar bell nasa dake gefe, ya zubawa adewale da karfe,kafun ma nabeel ya ruga shima aka zuba masa aiko zurawa sukayi a guje yana binsu abinka da soja tuni ya shawo kansu, ya soma sakasu tsallen kwado daga bakin gate har garden.

Haka ya sasu a gaba sunayi yana binsu a baya akalla saida sukayi kusan 2 hour's har yakai basa iyawa suna farawa suke zubewa kafafu sunyi tsami, nabeel kam har kuka ya fara da gaske kafun muzammil yabar su hade da musu kyakkyawan kashedi akan wallahi gobe in yaje makaranta yaji labarin basuje ba, koh sukaje suka tafi geto koh yagansu tare da Lahab sai jikin su ya gaya musu, babusu babu haduwa da lahab sai an dawo makaranta.

Sudai amsa masa suke da eh kawai, nuni ya musu dasu wuce su tafi, wallahi haka suke tafiya a hankali kafafu duk sun mutu kafun su isa get sai da suka huta a baranda, suna fita ma saida suka huta a kwalbet na kofar gidan, kallo adewale nabeel yayi, wallahi adewale daga yau bazan kara yarda muxammil ya dakeni ba, daman ina rage masa ne Albarka cin lahab, amma tunda dai yace baya bukatar muna haduwa da kanin sa, wallahi daga yau na rabu da lahab kuma makarantan ne dai baxanje ba.

Haba nabeel karfa ka manta yanda xai iyya dukan lahab haka zai iyya dukan mu, menene innar ka da mubeena basama lahab ne?harda zagi amma kaga ya nuna bacin ransa, yar uwarka da shekara 2 ta girme lahab amma bai taba tanka mata ba, sau nawa dad nawa na xagin ku lokacin da muke yara ma sau nawa yana dukan ku akaina, in kuka shigo gidan mu amma na tabbata lahab bai taba cewa zai rabu dani ba, haba nabeel?

Kai kaga zaka iyya nidai nace bazan iyya ba, dukan mun nan munason zuwa school amma saboda lahab bazaije ba haka zamu ki zuwa duk saboda shi, shine yau shi zashi makaranta mukuma munzo muji lafiya bamu gansa ba,wani banzan yayansa ya mana irin wannan duka, lahab in ubana ne.?

Shuru kawai Adewale yayi don yasan wannan surutu da nabeel keyi duk cikin zafin ciwo ne da haushi, amma yana wuce iyya ka ya tabbata wallahi badon Albarkacin lahab ba yasan da sun dade da rabuwa dashi koh don yanda nabeel ke nuna masa banbancin Addnin wasu lokutan, amma lahab babu ruwan sa da nuna fifiko gashi baida zuciya sam koh yayi fushi da abu zai huce ya dawo.

Wucewa sukayi direct gidan su nabeel don kafar nan tasu sai an gasa ta, gashi adewale bayason komawa gida iyayen sa na hanya kar su dawo suga kafar su yasan ba karamin bala'i za'a buga da baban sa ba akan maganar nan.

Tunda suka nufo kofar gidan su nabeel ran adewale ya kara baci ganin mubeena tsaye da wani saurayi suna hira a dakalin kofar gidan su.




*******************
Lahab kam zama yayi a class kamar Rahab daman shi akwai kwakwalwa sosai rashin karatu ke damun sa da wasa ga rashin maida hankali, amma Rahab bazai nuna masa ilimi koh fahimtar abuba, sai dai in baisa kansa ba sosai yau ya maida hankali ana rubutu yanayi ana karatu yana tambayar question kaman dai yanda d'an uwan sa keyi.


Ta bangaren Rahab ya rasa meke masa dadi abokan zaman sa dake A class babu su anan gashi disple daya tasa sa a gaba duk waiga warsa sai ya gansa zaune a bakin window akan kujera yana kallon sa, kwata-kwata ya rasa meke masa dadi ga yunwa dake damunsa.

Misalin karfe 10:00pm aka buga break, mikewa lahab yayi ya fita a ajin magana abokan Rahab ke masa ya musu banza ya fita abinsa, cafe ya shiga yayi ordern abinci a takeAway ya sai nasa ma daban, fita yayi ya nufi B class.

Rahab ne zaune ya kurawa wayar sa dake hannun sa ido ga dukkan Alamu waya yayi da wani, dafasa Lahab yayi,

Please Login or Register in order to submit comment