Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tasa Masa a baki,atakaice dai Saida Lahab yaci ya koshi kafun Nnenna ta Mike daga Kan gadon laidodin abincin ta aje a jikin drower ta dauki Kaya ta shiga bandaki wanka tayi ta daura towel Inda Lahab ya cire tare ruwa tayi a bucket tayi ta soma wankewa harda na Lahab tas ta wanke kayan ta tsame a bokati,kayan da ta shigo dashi ta saka wandone da riga t-shirt ta dau bucket in tare da bude kofar toilet in ta fitoh.


Lahab Kam tunda Nnenna ta shiga ban dakin ya koma ya kwanta ba tare da ya maida ruwan daya cire a hannunsa ba,haka kawai sai Yana Jin wani irin shauki ji yake Kamar rayuwar aure suke da Nnenna Suna rayuwarsu a daki daya ta basa abinci ta Masa wanka duka da ace matarsa ce janta kawai zaiyi su kwanta tare yaji yanda masu aure suke ji ashe haka rayuwa da mace yake da dadi"Allah ka aurar damu"shine abinda Lahab yace Yana gyara kwanciyarsa Jin Karan bude kofar toilet daidai lokacin aka bude kofar dakin da sallama aka shiga,d'aga Lahab har Nnenna dake bakin toilet dago Kai sukayi sukaga Mai shigowar .................



******************
Ruky ta Jima a tsaye a bakin titi bayan wucewar mubeena ajiyar zuciya ta sauke itama ta tare Keke tare da sanar dashi sunan unguwan su shiga keken tayi Mai keken yaja Suka cillah 30 minutes Keke yai parking a bakin lungun su Rukayya saboda cabalin da unguwar tayi ga ramuka shiyasa masu Keke basa yarda su shiga sai dai a sauke su a bakin lungu,sauka tayi tadau 50 kudin keken ta Mika Masa gangarowa tayi cikin layinsu tana tafiya tana bin Koh Ina da kallo kowa harkan gaban sa yake unguwane na masu karamin karfi sosai,kallon gefen wani madalisa dake gabanta tayi cike yake da jama'a tim,sai tebur dake d'auke da manya manyan kuloli akai kannen Rukayya ne su biyu Wance take binta tana zuba abinci dayan na karba tana rarrabawa matasan dake zazzaune a rumfar,share hawayen fuskar ta kawai tayi ta wucesu ba tare ma da ta d'aga Ido ta Kara kallon madalisan ba suma basu wani lura da wucewar Yar uwar tasu ba saboda ciniki da suke.


tafiya taye kadan kafun ta iso kofar gidansu,gidane irin na da mai Jan block Koh kofa babu sai wani yamutsetsen taburma da aka Kare kofar shiga gidan dashi sai wani tsohon shagon gugan babanta dake kusa da gidan su leka shagon tayi tama baban ta dake guga da dutsen cakwal,baba sannu da aiki?


da fara'arsa ya juyo fuskarnan sharkaf da zufa,yauwa mamana harkin dawo gidan kawar Taki dazun da nashiga gida mamarku kece min kinje gidan kawar Nan taki mema sunan ta farar Nan?

Hhh sunan ta mubeeena baba?


Mubeena Kuma mamana wannan Suna ai sunan yan gayu saiku zaku iyya rikewa.

dariya kawai Rukayya tayi ta nufi kofar gidan nasu d'aga taburman tayi da sallama ta Shiga.


Addanta bazawara dake duke tana sana'an wankau ce ta amsa sallamar ta tare da Mata sannu da zuwa itama Rukayya sannu da aiki tama yayar tata ganin uban wanki da take tana ta shashanyawa,Zama tayi a bakin dakali,mamar tane ta fitoh kitchen da Sauri hannunta d'auke da kullin awara data tsame yanzun daga tukunya ajewa tayi a bakin dakali tare da daura Masa babban dutse akai.

Sannu da aiki mama?

Yauwa Rukayya sannu harkin dawo?

Eh na dawo mama,yauwa tunda Kim dawo ga kwanuka da tukanen abincin Nan kije ki wankesa kafun lokacin fitar kanwarki tuyar awaran yayi kin kimtsa kayan aiki,mikewa Ruky tayi ta Shiga dakinsu ta Kwabe kayan jikinta ta sanya wani kodadden zani ta fitoh bucket ta d'auka ta fita gidan ruwa ta ibi kafa uku saboda yanayin yawan kwanukan abinka da gidan masu abinci da tuya kwanuka bana Wasa bane buhun omon su ta dauko ta aje tasa kujera ta Fara wanke wanken.


Sai can yamma kannenta guda biyu Suka shigo gidan, Almajirai nabinsu da robobi da kulolin abincin nasu,faggawa Almajiran sukayi a mawanki ita Kuma Yar autarsu ta dau awaranta a bucket da abubuwan tuyanta ta fita kofar gida, cefene maman su tama Rukayya saboda itace Bata sana'an kome sai aika da wanke wanke da zuwa cefene in bataje school ba Amma su biyar Mata kaf su hudun Suna da abin yi.


Bayan sallan mangariba zazzaune suke gabaki dayansu a tsakar gidan sauran abincin da bai Kare ba na sairuwa shi gabaki dayan su suke ci shinkafane da Miya sai Kuma tuwo da miyar alaiyahu da aka duma, Ruky duk da abinda ke damunta kokarin boyewa take bata son kowa a gidan su ya fahimci halin da take ciki,Jin ana kiraye kirayen isha'i yasa baban su mikewa ya fita masallaci sauran yaran ma duk Suka mimmike Suka dau buta Suna Alwala.



Bayan sallan Isha zazzaune suke ana Hira a tsakar gida ita Kam Ruky rike take da handout nata tana karatu hannunta rike da dan wayarta Abba gida-gida,yaro ne ya shigo da sallama tare da sanar dasu wai wani na sallama da Rukayya a waje kallon kallo akayi don rabon da azo ace a Kira Rukayya ai an kusan shekara kenan,kaje kace wanene Addan Rukayyar tace,juyawa yaron yayi baijima ba sai gashi ya dawo Wai inji Ahmad,mikewa zaune Ruky tayi duk da tana danjin kunyar babanta dake wajen,ta fahimci wani Ahmad ne cikin sanyi tace kaje kace bana Nan?

Ke tashi dan Allah Mara hankali wani irin aje ace bakenan Mike Maza,-maza Kafun tacewa yaron kai jekace tana zuwa maman ta tace tana zarewa Ruky Ido,mikewa Ruky tayi tadau hijab nata cikin kunya ta fita a gidan.


tsaye yake a jikin ginin gidan su ya hade hannayen sa a kirjin duk da dare ne hakan bai hanata ganin raman da yayi ba, Assalamu Alaikum.


Waalaikumu Salam Rukayyar barka da dare?


Uhmm barka dai Ahmad ince dai lafiya na ganka a irin wannan lokaci Kuma a kofar gidan mu?


Hh lafiya klau Rukys menene zai kawo saurayi irin wannan lokaci wajen budurwa in bada maganar so ba?tukunna ma ba wannan ya Kamata ki tambaye Ni ba jikina ya Kamata ki Fara tambaya.

Kaga dan Allah Ahmad Ni wannnan Wasa ya isheni haka Ina son kawata Ina son alakarmu duk da Koh shekara bamuyi da haduwa ba kaika sani a makaranta muka hadu amma Ina jinta a raina sosai bazan so ka Zama tsilar rabuwar mu ba Koh Ni na Zama tsilar rabuwar ku.


Haba sau nawa Zan sanar dake cewa babu wannan zance na nine sula Koh kece tsila babu wannan magana abu daya na sani shine bamu sabawa shariya ba Kuma ita da kanta tace bata Sona tana da Wanda take so?

Eh hakane amma fa ka sani bazan iyya auren ka ba duniya zasu zageni.


Wani irin zagi?ana gujewa mutan ne Koh bayan aure zasu zo har gidanki su fiddaki ne,Koh zagi Yana mannuwa a jikin mutum ne? Ni abinda nake so dake Ruky ki sani bawai zanyi abin nan dan kuntattawa mubeena bane ah ah wata daya ya rage in ba haka ba baba na ya rantse sai ya auramin Yar kanwarsa Ni Kuma tarbiyarta baimin ba amma kefa na sanki tuntuni bana bukatar tsayawa tantance dabi'unki sai abinda baza'a rasa ba.


dan sauke ajiyar zuciya Ruky tayi,yanzun Ahmad y........baibari ta karasa ba ya dakatar da ita,Kinga Ruky ba zuwa nayi muyita maida zance ba Zan baki Nan da kwana uku kije kiyi shawara Zan dawo ranan talata na amshi amsata duk abinda Kika yanke wallahi bazan Kara akansa ba don haka ki shiga cikin gida Sai da safe.

gyada Kai kawai Ruky tayi ta juya ta shiga gida,tana shiga ta samu baban ta ya tashi yayi cikin dakin sa itama dakinsu ta shiga da Sauri taje ta zauna akan katifar ta ta rufe fuskarta da hannunta cikin damuwa.

Mikewa Addan Ruky tayi ta biyota dakin Zama tayi a bakin katifar ta dafa kafadar ta,Ruky meke faruwa meyasa tsawon shekara kina Neman mashinshini sannan yau kin samu wani yazo shine Zaki ki fita Ruky watoh har yanzun bakiyi karatun ta natsuba kin manta sake da kikayi da Nasir ya tsubce Miki,haba Ruky kinfiso dukan mu mu taru mu zauna kenan Koh me?


Uhmmm Adda Koh kinsan Ahmad Nan dayazo wajena shine zai aure mubeeena?

Rukayya wata mubeena?

Kawata mubeeena fa.

What??wannan ai shirmene akan me zaizo wajen ki bayan Yana tare da kawarki,Zama Ruky tayi ta warwarewa addan ta kome,toh kinji abinda ke faruwa.


Mikewa Adda tayi ta kalli Ruky, Rukayya indai haka abin yake toh Ina Mai Baki shawara ki yarda ki amince da Ahmad wannan shine Allah ya kashe ya Baki.........


🙄*Ruqeenjalal*




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*


Page 59&60



Haba Adda wani irin Allah ya kashe ya bani? karfa ki manta banine a ransa ba mubeena ce wallahi Koh shakka banayi Koh na aure sa bazan samu kulawar da mubeena zata samu a wajen sa ba.

Uhmmm Rukayya kema har yanzun yarinyar ce Ina ruwanki da yafi sonta a kanki,shuru kawai Ruky tayi tana kallon Yar uwar tata sai zuzuta zancen take da Kara jaddada Mata akan ta amince dashi, Rukayya nidai Ina Kara gaya Miki wallahi kiyiwa kanki karatun ta natsu ai dukan kune zakuyi biyu babu ke baki aure sa ba itama ta rasa don haka nidai Ina gaya miki ki amince kinji?

gyada Kai Ruky tayi tace,insha Allah Adda Zan amince Masa Allah yasa hakan shiyafi Alkhari a garemu baki d'ayan mu.

Ameen Adda tace ta Mike tabar dakin,ajiyar zuciya kawai Ruky ta sauke tare da kwanciya akan katifar ta.

Adda na fita daga dakin nasu wajen mama takoma Zama tayi tafara ma mama magana,uhmm mama kinsan Ruky da rashin hankali Wai harxata samu Mai sonta da aure ta tsaya tana yanga?

Mikewa zaune mama tayi d'aga kwance da take a taburma,kaji Yar banzan yarinya zata sake reshe ta Kama ganye watoh abinda ya faru tsakanin ta da Nasir baisa tayi hankali bako?

Kedai Bari mama Wai saurayin kawar Nan tata mubeena take Koh wa? tace batason Yaron shine fa shi Kuma yaga Rukayya Yana so Wai ta tsaya tana lagwa-lagwa Yar banza in tayi aure Ina zataga ita mubeenar bare ta tuna saurayinta ta aura?

Uhmmm lallai Rukayya bata gaji da zaman gida ba Aiko wallahi Koh bataso Ni Zan ma baban ku magana in yaron ya sake dawowa ace ya turo don ubanta a halin da muke cikin Nan Nan gaba ma kudin makarantan nata ba iya biya zamuyi ba sannan ta samu Mai son auren har zata tsaya wani kafli da badi mubeenar kanwar uwarta ne Koh na ubanta?

dariya ne ya kufcewa Adda Jin yanda mama ta zage sai masifa take harda cewa zata shiga dakin nasu ta samu Ruky taci Mata mutunci daker Adda ta samu ta sassauta masifar tare sayin Alwala ta wuce dakin ta bayan tama yaran Saida safe, daman baba ya shiga tuntuni,Adda ne ta Mike taje ta rufe kofar gida ta karkata kannen nata zuwa cikin dakin su kwalli d'aya da suke kwana dukansu su biyar a ciki, Nan ma ta mayar da yaranta biyu kenan gidan baban su shiyasa Suka samu saukin matsin da suke ciki na wajen kwana don daki biyu garesu daya na mama da baba daya nasu.








*******************
Mahaifiyata Kika Mara?kallon Anwar Mami tayi kafun tayi magana,eh na mareta Anwar na mare uwarka Koh zaka rama Mata ne nasan lalle kunsha a no-no?

Umaima data shigo durkusawa kawai tayi a wajen tana kuka Anwar har lokacin Yana Nan a tsaye yayin da Shareef ya sunkuyar da kansa a kasa uwa uwace duk da mamarsu ce bata da gaskiya amma yaji mugun haushin Mami na marar Masa uwa bare ma Mami da kadan ta girme Anwar don kwata kwata bata wuce shekaru 35 ba a duniya ba.

Mamu da tayi mutuwar tsaye hannunta dafe da kumatu tana bin yaran nata da kallo ganin gabaki dayan su babu Wanda ya yunkura zai rama Mata hawaye ne ya cika a idanunta lokacin da takai dubanta ga Abbu muzammil da Addayiya babu Wanda ya nuna Koh damuwa a fuskarsa,da gudu tayi kitchen ba'ajima ba sai gata ta fitoh da tabarya tayi Kan Mami, wallahi yau sai nayi ajalinki saikin gane baki da wayo harni Zaki mara,ta d'aga tabaryar da karfi zata bugawa Mami,gabaki d'aya Yan falon mikewa sukayi cikin bacin Rai Abbu ya daka Mata tsawa,wallahi halima in Kika buga Mata tabaryar Nan a bakin auren ki na gaji da halayen ki a gidan Nan, shekaru sunja amma ke banga hankalinki ya daidaita ba.


Mamu Kam kafewa tayi da tabarya a hannu har lokacin kunnenta baibar jiyo Mata da abinda Abbu yace Mata ba, a tsawon zaman su bai taba Mata wasan saki ba bare barazana sai yau,Wai Ina zata sa Mami ta daina kallonta ne? ga ummu itace kishiyarta amma batajin kishinta Kamar mami,Wai inkin buga Mata a bakin auren ki?ita Haleema Kuma a gaban yaranta.


gabaki d'aya jama'an falon sun girgiza da maganar Abbu sosai Wanda hakan yasa Addayiya kasa hakuri hartayi magana,Kai Umaru wannan wani irin rashin hankali ne mekake cewa haka so kake ka dasawa yaran ka wani tunanin daban a ransu ne Koh Yaya?kace zaka saki uwarsu akan uwar wasu,yau Haleema da Amina Suka Suma tsama ne da zaka Fadi haka kul bana son sake Jin magana irin wannan.

Jan numfashi Abbu yayi sannan a hankali ya koma Kan kujera ya zauna tare da dafe kansa shikaran kansa yasan hakan bai kyautu ba amma ya zaiyi ransa ne ya baci yasan halin Halima da rashin hakuri,ummu Kam Koh a jikinta yima tayi Kamar bata San meke faruwa ba sai daddan na wayanta take,Mami Kam juyawa tayi zata bar falon da Sauri Lahab ya kirata,Mami ayya jirani Ina zuwa minutes biyu tsayawa tayi shikuma da gudu ya mike yayi cikin falon su daki ya shiga a hargitse ya zaro akwatin kayansa ajewa yayi a kasa tare da bude wardrobe na kayansu jido kayayyakin sa yake Yana jugawa a akwatin Koh takan Nade baibi ba takalma duka ya zuzzuba har Saida akwatin ya cika yaja zip da sauri ya dau jakar makarantan sa ya goya tare dajan akwatinsa ya fita a dakin kofar falonsu ya bude ya fita.

duka Yan falon da Ido Suka bisa ganin sa. D'auke da Kaya Niki Niki ya nufi mami hannunta ya Kama Suka nufi kofar ba tare da yayi magana bama,Kai Rahab Ina zaka kayan Nan fa?Abbu yace Yana kallon sa a tsorace don harga Allah baison ganin fushin Rahab gara Masa na Lahab kunayin abu anjima ya watsar amma wannan shegen rikone dashi da d'acin Rai.

Juyowa Rahab yayi cikin girmamawa yace,kayi hakuri yaya ban taba sanin cewa zaman na da dan uwana shiga hakkin ku muke ba sai yau,ga gidan Nan mun bar Mata sai ta rayu daga ita sai yayan ta da wa'inda takeso ba shikenan ba?

Kai ba shikenan ba dan uwarka kana da gidan da yafi wannan ne Koh gidan da zaka yanzun na ubanka ne?Addayiya ce tayi maganar a zafafe Shima Rahab a zafafe ya Bata amsa,bana ubana bane amma Ina da tabbacin babu Wanda zai goranta mini daki a gidan Koh uwata Koda kuwa shekaru dubu zamuyi a cikin sa,mikewa muzammil yayi Jin bakar magana da Rahab kewa mahaifiyar sa,nufo Rahab yayi Kamar wani zaki Yana huci Shima Rahab bai Koh mutsa ba Yana tsaye domin a wannan lokaci ransa yayi kololon baci hannu muzammil in ya d'aga zai kwadawa Rahab a kumatun da Sauri Rahab ya riko hannun nasa jikinsa har rawa yake ya Soma ma muzammil magana cikin kaushin murya,ka tsaya iyya matsayinka na Yayana karka wuce iyyakarka wato na baiwa mahaifiyarka amsa kaji haushi?Ina ga Ni danayi hakuri da irin cin Kashi da kake Ma tawa mahaifiyar baka kallonta da daraja amma a hakan Muke kiranka da wa,don haka baka Isa nima yau kace zaka bugeni akan taka uwar ba,kaji na rantse maka d'aga yau bazan sake bari hannunka ya taba jikina da sunan duka ba in ko ka gwada hakan toh tabbas Zan rama nima karfin Nan babu wanda bai dashi don haka ya isheka haka ya isa bazan lamunta ba bazan lamunta ba kaji na rantse,Yana karasa maganar ya sake hannun muzammil yayi mutuwar tsaye agun Wai shi yau Rahab kecewa inya buga zai rama gara ma in Lahab ne ya fada Masa haka toh bazaiyi mamaki ba amma yau wannan ne ke fada Masa da kansa lallai abin nayi ne,Ni kake cewa zaka buga ai bazanga laifin kaba tunda uwarka bata nuna maka Ina da mutunci ba.

Jin abinda muzammil yace yasa Mami harzuka,Kai muzammil karka kuskura karka soma wallahi in ba haka ba Zan rufe Ido inci ma mutunci kasan Ni nasanka wallahi Ni nafi karfin na nunawa yarana su Raina barema bare dan uwansu kaida yake dama mugun Hali gareka dole kana kallon kowa ma haka,nuna Rahab tayi Kai wuce muje ta bude kofar falon ta fita Rahab na binta a baya da kayansa,mamu Kam sosai taji dadi ganin fadan yabar kanta ya koma na muzammil da Mami gashi Rahab yabar gidan don ita a duniya babu abinda takijini Kamar ta bude Ido taga Mami a duniya da yayan ta Suna walwala Koh cigaban su bataso.

Kuka Addayiya ta sake kafun ta soma magana, yanzun umaru kana ji kana gani amanarka zai bar hannunka karfa ka manta kafun mahaifinku yabar duniya sai da ya baka wasiya Koh bayan ransa y'ay'an sa su zauna a hannunka shine yanzun zaka wani barshi yabi uwarsa yaje Yana agolanci a gidan uban wasu,sai Kuma ta Kuma sakin wani Sabon kukan.


Abbu Kam da kansa ke kasa ji yake Kamar Kan zai tsage ace Yana matsayin babba ga mahaifiyarsa duka zaune Suna fadace fadace a gabansa sannan ga damuwar rashin Inda karamin kaninsa ya shiga na tsawon kwana biyu ga kukan da yanzun Addayiya keyi,dan Allah Addayiya ki rufamin asiri kiyi shuru mubi kome a hankali.

Kin shuru Addayiya tayi muzammil Kam ji yake Kamar ya ketta wa kansa aShana Wai yau shine Rahab yama rashin mutunci gaskiya ne da hausawa sukace karka Kai Mai hakuri bango.





*****************
ai da Sauri Inna ta juya ta kamo kafadun mubeena da karfi ta girgiza cikin masifa tace,keee mubeena ashe baki da mutunci oh baki sonsa toh uban wa kike so nace uban wa kikeso? ki fadamin Mara hankali munafuka kawai Inna tace tana girgiza mubeena dake ta kuka durkusawa tayi a wajen tana wani irin kuka Mai cin Rai da tsoro.

Inna ma Zama tayi a wajen ta Kama Kai tana kuka tana magana,mubeena kin cuci kanki mubeena mekike nema a wajen namiji Wanda Ahmad bai dashi yaro Mai sonki Mai kaunar ki yamiki goma Sha,yanzun da abinda Zaki saka Masa kenan wai kice baki sonsa toh wallahi sai kin fadamin uban wa kike so din?


Shuru mubeena tayi bata yi magana ba haushi ne ya cika Inna Jin sai magana take Mata ita Kuma taki bata amsa,nace Miki wanene In kike so da har Zaki rabu da yaron kirki Mai kawo min goro duk juma'a Ina tambayarki kin min shuru,shuru mubeena bata bata amsa ba hannu Inna tasa ta wanke fuskar mubeena da Mari daidai lokacin Nabeel ya shigo gidan akan idanunsa Inna ta wanke Yar uwarsa da Mari cikin tsoro ya karaso Inda suke ganin su cikin wani irin yanayi na damuwa,Inna lafiya meya faru Aunty mubeena meke faruwa ne?


gabaki d'ayan su shuru sukayi babu Mai magana sai kuka da mubeena keyi Inna na tayata,wallahi ku fadamin meke faruwa Koh Kuma Bari naje na Kira bappa Ado yace Yana mikewa don harga Allah ya tsorata ya d'auka wani babban al'amari ne ya faru bai kawo Koh a ransa akan Ahmad bane.

ganin zai fita yasa Inna dakatar dashi,tsaya Nabeel basai ka Kira bappan kuba zauna kaji abinda munafukar yarinyar Nan tace mini bayan ta gama munafurcinta sannan tazo tasa kanta a damuwa ai ba kuka zatayi ba Murna zatayi.


dan tsaki Nabeel yaja,Kinga Inna Ni kimin bayani yanda Zan gane Mana menene mubeenar tayi Kuma,kunzo kun hadu Kuna kuka Koh wanine ya mutu?

Jin tambayar da yayi yasa mubeena girgiza Kai ta Mike tsaye Shima mikewa yayi ganin ta nufi Kan taburma ta zauna Shima Zama yayi yasa hannu ya Kama nata sosai ya rike cikin nasa a tausashe Kamar ba Nabeel abokin Lahab ba ya soma magana,Kinga mubeena kibar kukan Nan haka ya Isa kimin bayani duk kunbi kun rudani meke faruwa ne?shuru mubeena batayi Masa magana ba sai kallon kasa da take har lokacin idanunta na zubar da hawaye,Taya zata maka magana bayan bata da gaskiya.

Kinga Inna in Zaki fadamin ki fadamin kawai Kuna dad'a rudani fa?

ba kome bane yasamu cikin wannan Hali illah abinda Yar uwarka da bata rike maraicin ta ba ta aikata Wai har yarinyar Nan zataga tsabar idanun yaron Nan Ahmadu tace bata sonsa yaron da yayi d'awainiya da ita tun bata Kai haka ba watoh yanzun ta Zama Yar collegi(college) zatazo ta nuna Masa wayewa banda rashin tunani irin nata ai shiya sata a makarantan.


sauke ajiyar zuciya Nabeel yayi Jin abin ba wani babba bane amma duk da haka Sosai abin ya basa mamaki har Saida ya kasa boyewa,Inna kikace Aunty mubeena tace Miki sun rabu da Ahmad Kuma ita tace bata sonsa?tunda Kika ga hakan Kika sani Koh akwai abinda ya Mata shiyasa tace bata sonsa,tsawon shekarun Nan batace bata sonsa ba sai wannan Karo gaskiya da sakel.


Jin amsar da Nabeel ya baiwa Inna yasa mubeena ta Fara magana a hankali har lokacin kanta a kasa,babu abinda ya hadamu da Ahmad daman bashi nake so ba Ina da Wanda nake sone.

Wakike son kenan sannan tsawon shekarun Nan bakisan baki sonsa ba kuke tare Koh yanzun ne kika ga Wanda kike son Inna tace


Aunty mubeena ki kwantar da hankalin ki ki Mana bayani d'aga Ni har Inna nakine babu bare in baki fada Mana damuwan ki ba wa Zaki fadawa kenan Yar uwa?kinsan mu masu goyon bayan abinda kike sone mundin zai saki farin ciki amma fa in bai sabawa shariya ba.

Sosai maganar Nabeel ya baiwa mubeena karfin gwuwar fadin abinda ke ranta daman tsoro take taya zasu d'auke al'amarin a hankali ta soma magana,daman tun da dadewa bashi nake so ba ku.............


🍀 *By Ruqeenjalal* 🍀




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785tare da shaidan biyan ki*


Page 61&62

Uhmm Aunty mubeena munajin ki ya kikayi shuru Kuma?

dan shuru tayi sannan a hankali tace,toh banace bana sonsa bane Kuma ban d'auka zaiji ba ashe yazo wajena a makaranta bansani ba shine ya yanke jiki ya Suma..........................................daga a har z mubeeena ta sanar dasu duk abinda ya faru amma bata sanar dasu Lahab ne take son ba ta boye musu tadai ce tana da Wanda take so,ajiyar zuciya Inna ta sauke Jin dogon bayanin da mubeena keyi,toh ke mubeena yanzun duk maye saki a damuwa?ai tunda ya hakura abinda ya dace yanzun saiki fitar da Wanda kike son yazo a muku aure bashi kenan ba Shima yaje ya aure takwarana in ba?

hawaye ne ya zubowa mubeena Jin abinda Inna tace,toh yanzun Inna fisabililahi sai Ruky tana kawata sai ta yarda zata aure sa kenan?

toh dan kaniyar ki sai taki ne Koh Yaya a zamanin da ake innan ana haba haba da mijin aure har zata ga bonus ta bari ne?kince baki sonsa don haka kicewa Wanda kike son ya fitoh, nagaji da ganin ki a zaune ba aure in ma karatunne ya ajeki bamuda kudin biya miki yanzun.

Haba Inna da wanne zataji ne Wai guda daya haka, Nabeel yafada wa Inna sannan ya juyo ga mubeena,Kinga Aunty mubeena yanzun kiyi shuru ki kwantar da hankalin ki ki Mana bayani shin Menene ya saki kuka da damuwan so kike Ahmad ya dawo ne?Koh Kuma bakison Rukayya ta aure sa wanne ne baki son guda daya?


girgiza Kai mubeena ta sake tare dajan numfashi Jin tambayar da Nabeel ya antayo Mata Wanda bazama tace eh ne Koh ah ah ba ta rasa wanne ne d'aya? tace bata son Ahmad amma tanajin haushin auren Ruky da xaiyi,nifa ba wa'innan ke damuna ba kawai dai makaranta nane gashi Rabin kayana duk shiya dinka min bazan iyya cigaba da amfani da abinsa ba,sai Kuma ta fashe da kuka Kuma Wanda nake son baisan Ina sonsa ba.

Ai Jin haka yasa

Please Login or Register in order to submit comment