Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

in cewa,bara na Shiga na dauko Miki mma ke babu halin ki shiga yanzun.

Toh shine abinda Nnenna tace tana tsaye har tashiga dakin Bata Jima ba sai gata ta dawo hannunta d'auke da Kudi harda ATM card nasa duk ta had'a ta mikawa Nnenna, karba tayi ta fita a hall in kirga kudin tayi 12k ne sai ATM pharmacy ta shiga ta basu list in ta sayi duk abinda aka bukata sannan ta koma cikin clinic in takai kayan aiki daidai lokacin aka soma kiraye kirayen sallan mangariba Zama tayi akan kujera.

Sai kusan 8 na dare kafun likita ya fita a dakin sannan ya tura a kirata,tashi tayi tabi nurse in har office nasa,musulmi ne dan gatane sannan daga ka gansa kaga dan kwalisa tunda Nnenna ta shigo yake binta da wani shegen kallo Yana bin sharaban kafanta dake waje da kallo dayake uniform ne har lokacin a jikinta,get a sit my friend Yana maganar Yana nuna Mata kujera Zama tayi sannan nurse in ta fita,am kece Kika kawo Hassan Alhassan?yayi Mata maganan cikin hausa

dan gyara Zama Nnenna tayi duk tana wani Jin kanta uncomfortable tarasa me yasa bata iyya sakewa da Koh wani namiji in ka cire papan ta sai Lahab"pls can u speak English?


Sake Baki yayi Yana kallonta da yanda take magana Kamar yanga take Masa donshi a ganinsa iyayine kawai bawai batajin hausa ba amma sai ya basar ya soma mata magana,am Zaki iyya shiga daki Mai number 7 Yana ciki sannan zai iyya tashi 3 Koh 2 na dare za'ana shiga ana dubasa in Kuma ya farka babu wani a kusa kizo ki sanar da nurse.

Ok sir kawai tace tana kokarin mikewa

Am sister why not ki Kira gida azo a kula dashi ke Kuma ki koma ki kimtsa naganki sanye da uniform ga school bag maybe ma Koh gida Baki koma ba.

Kala batace ba ta bude kofar ta fita shikam sai kallon kofar yake tunda yaji hausan ta ya tabbatar ba Yar Arewa bace sannan ga tsananin kyaun da take dashi gata tana yawo ba hijab Kuma ta kawo musulmi asibiti me alakarsu kenan?.

tana fita d'aga office in tabi daki daki tana duba number har tazo Kan number dakin nasa tura kofar tayi ta shiga,kwance yake sanye da vest sai wandon jikinsa an cire Masa rigansa dayazo dashi sai hannunsa da aka daure da farin bendeji a hannunsa,takowa tayi a hankali zuwa bakin gadon kurawa fuskarsa Ido tayi fuskarsa tayi fayau sai dan tsukeken bakinsa da yayi jajazir ga dogon hancinsa a tsaye sosai ta Kura Masa Ido sai Kuma taji hawaye ya cika Mata Ido"Hassan ka shiga rayuwar ta batare da kasan Koh Ni wacece ba kayi hakuri na raunana ka hannu da yaban abinci bai cencenci karaya Koh tsageba.


Sai Kuma ta Mike ta dauko kujerar dake dakin fari na roba ta aje kusa da bakin gadon aje school bag nata tayi a kasa ta zauna akan kujeran ta bude jakanta ta dauko littafin ta tana dudubawa,aje littafin tayi ta zuba tagumi tana tunanin kikin ta da yau haka kawai taji tanason ajesa a gida ashe rabon zasu hadu da Lahab ne don tun Randa ya nuna Mata ta daina zuwa school dashi.

Zafi ake sosai ga gari ya gume Hatta fankan dake dakin Hura zafi yake botur in rigan uniform nata ta soma ballewa Harta gama hannu ta cire ta Kwabe rigan jikinta ya rage daga ita sai vest in jikinta sai siket hannu tasa ta zare sandal nata ta cire socks in ta duka ga wani gyangyade take ta zare glass in fuskanta ta aje akan drawern dake gefen gadon ta zare barect in kanta ta warware gashin nata ya sauka har gadon bayan ta don ita bata son bacci da gashi a kuller,gyara Zamanta tayi ta kwantar da kanta a bakin gadon jikinta nakan kujera tare da lumshe idanunta a hankali bacci ya fizgeta Mai dadin gaske.



******************
ta bangaren Mami sosai taji hankalinta ya tashi meya Kai Lahab hotel a daren jiya me yasa muzammil ke neman sa kasa hakuri tayi tadau waya ta Kira muneera ta tambaye ta Koh Lahab ya koma gidan amma muneera ta bata tabbacin Lahab bai dawo ba Zama tayi ta buga tagumi tayi shuru kawai


da misalin karfe 8 na dare zaune suke a falo ita da mijinta da yaranta sunata Hira Inka cire Mami data buga tagumi tayi shuru abin duniya ya dameta sau biyu tana Kiran muneera amma amsa daya take Bata Bai dawo ba Alhaji sulaiman daya fahimci tunda ya dawo akwai abinda ke damunta shuru kawai yayi saboda yara bai tambaye taba amma yanzun Kam kasa hakuri yayi ya kalli mahraz dake zaune Yana zana mutum a caborn paper,Mahraz tashi kuje dinning ka xuzzuba musu abinci kuci Muna zuwa daga baya nida mamin ku.

da Sauri Mahraz ya aje pencil in hannuda tare dasa hannu ya dau Yusuf dake kan cinyar kanwar sa wasila suka wuce dinning,kallon Mami Alhaji yayi sannan ya soma magana,Amina meke damunki tunda na dawo na fahimci kina cikin damuwa matuka Koh?

dan shuru tayi don ita kwata kwata batason ta tattauna matsalan y'ay'anta da mijinta tafi sakewa tayi zancen su Lahab da su Addayiya da sauran Yan uwan tsohon mijinta da y'ay'ansa Amma Bata sonyi da mijin nata shiyasa ma yanzun ta dan murmusa tare da cewa,babu kome dadyn Mahraz kawai dai bana danjin dadin jikina ne.

Uhmm Amina kenan nafi kowa sanin halinki Koh kin manta tare muka tashi tun kina yarinya namiki kyakkyawan sani nasan yanda kike in kina farin ciki bakin ciki damuwa da Kuma ciwo,Amina damuwa ne a ranki ba ciwo ba in ma matsalar da bazaki iyya sanar dani bane Ina rokonki akan ki sawa kanki natsuwa in ma matsalar yayanki ne bazan hanaki boye mini ba,tunda bani na haifeki ba amma ki sawa kanki natsuwa kowa da kalan yarantan sa da Kuma tashensa dole iyaye su kasance masu hakuri dama yayansu addu'an shiriya bawai kisawa kanki damuwa ba Amina?

Nagode kawai tace ta tashi ta Shiga dakin ta,waya ta d'auka tama rasa wa zata tambaya haka kawai yanzun gidan yayanta muneer dan tasan kaf Yan uwan babansa bazashi gunsu ba tunda zasu sanar da gidansu yaje tasan Yan uwanta sune zai nufa,bugawa ya muneer waya tayi ta Kara a kunnenta.

Tana jinya d'auka tayi sallama, Assalamu Alaikum

Waalaikumu Salam taji muryar yayan nata ya amsa

An wuni lafiya ya munir?

Lafiya Amina ya maigidan naki da yara?

Lafiya sai godiyan Allah

Masha Allah haka akeso ince dai lafiya Kika kirani a daren nan?

Lafiya klau daman Zan tambaya ka Koh Lahab na wajen ka?

Ah ah Amina d'azun dai dana dawo kasuwa salamatu tace min yazo yayi wanka ya fita tun da yamma ince dai lafiya koh dai wani abune ya faru?

Gudun karta d'aga Masa hankali yasa ta ce Masa babu kome kawai d'azun face min zaizone shine na Kira na tabbatar Koh yazo kasan yaron Nan baijin magana.

toh Amina Allah ya bamu Alkhari sai da safe shine abinda yace Yana katse wayar,juyi tayi akan gadon ta rafka tagumi tana tunanin Ina danta ya shiga a daren nan hakan yasa ta daukar waya ta ringa kiraye kirayen tana tambayar Yan uwanta da duk tasan Lahab zai iyya zuwa wajen su Amma duka amsa dayane bai zo ba.



da misalin karfe 2 na dare dakin shuru gashi ba haske babu motsen kome saina Karan gudun fanka ga wani irin hadiri daya karade sararen samaniya yayi bakikkirin sai walkiya dake tashi ya haska duhun hadirin dan motsene ne ya Fara dan tashi a jikin window tare da yayewar labulen window,wani kasurgumin kulene ya shigo dakin idanunsa jajazir yayi wani irin super daga bakin window zuwa Kan Lahab kafun kafafunsa su sauka akan lahab...............,.





*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*

Page 53&54




Nnenna dake kwance da Sauri ta zabira duk da dakin da duhu hakan bai hanata ganin abinba da Sauri ta kwanta akan lahab tare da Masa rumfa ta bashi kariya d'aga sauka akansa da kulen zaiyi da Sauri kulen ya sauka a gefen gadon bai Fado akan bayanta ba sannan da Sauri ya juya ya fita ta window,mikewa Nnenna tayi a hankali ta zare jikinta a nashi lalubar glass nata tayi ta saka sannan ta kunna wutan dakin daidai lokacin aka soma yayyafe yafyaf bargo dake kusa da gadon ta d'auka ta warware ta lullube Lahab dashi Jin an Fara sanyi sosai riganta ta d'auka ta maida jikinta sosai takejin sanyin Hawa gadon tayi ta zauna Wai zatana gadon Lahab don ita tasan tabbas akwai abinda ya shigo dakin Kuma ta gansa, jingina tayi da jikin ginin dake manne da gadon a take bacci ya shureta.


Misalin karfe 3 na asuba Lahab yadan Murda tare da Ware idanunsa yana bin dakin da kallo,ganin duhu yake gani yasa sa dan d'aga hannun nasa Kara yadan sake don shi Yama manta ya samu karaya in ba yanzun ba hannu Mai lafiyan ya d'aga ya Kama blanket in ya yaye a jikinsa tashi yayi zaune yasa hannu Yana Tattaba gadon,a bazata yaji hannunsa ya taba fatar mutum Mai shegen laushi.

cikin zafin nama Nnenna ta damko hannun Lahab dake Kan cinyanta har lokacin Yana shashafa wa don ya gaza ganin jikin wa yake tabawa don bai kawo a ransa itace be sai da yaji muryar ta, bayan ta rike Masa hannu tace"Lahab ka tashi"?

Shuru yayi bai bata amsa ba sai ma yanzun ya tsoma Jin haushin abinda ta Masa gashi Nan taje ta karyasa a banza d'aga make Masa hannu sai tsagewar Kashi mace Kamar Mai Kashi daya amma ta wani bangaren yaji dad'i kula data nuna Masa gashi har kwana zatayi dashi,Koh dayake ma ai ita ta raunana sa,,Yana jinta tana Kara tambayarsa amma baibata amsa ba,sai kokarin sauka yake akan gadon,itama da Sauri ta sauka ta nufi switch na dakin ta ketta take haske ya gauraye dakin d'aga Ido yayi ya kalleta sai Kuma ya maida kansa a tiles in Yana Neman takalminsa don baison taka tiles in asibiti.

Fahimtar abinda yake nema yasa ta saurin matsowa garesa ta cire sandal in kafarta ta tsunguna hade da kama kafar nasa Wai zata saka Masa takalmin, shuru kawai yayi baiyi magana ba Harta gama sawa mikewa yayi ya nufi toilet,itama Zama tayi akan kujera tayi shuru duk sai taji ya shiga damuwa sosai wallahi,bai wani Jima a bandakin ba ya fitoh Hawa Kan kadon yayi ya kwanta tare dasa hannunsa Mai lafiyar ya lulube jikinsa duka harda Kai.

Mikewa tayi ganin ya kwanta taje ta kashe wutan dakin duk da Dr yace inya tashi takirawo nurse kin kiransu tayi,a hakan dai tana Kan kujera ga kafarta a waje har bacci ya dauketa shikam kasa baccin yayi dan zazzabi zazzabine a jikinsa kwata kwata yaji baccin ya Kare Masa,a hakan yayita jujjuyawa har aka Kira sallan asuba mikewa yayi daga Kan gadon ba tare daya kunna wutan ba ya Shiga ban daki Alwala yayi duk da zazzabin da yake ji Amma bai sawa hannun ruwa ba.

Dudu ba dakin yayi baiga sallaya ba dan tsaki kawai yayi yakai dubansa ga Nnenna dake bacci a zaune gashi bazai iyya zuwa masallaci ba har lokacin ana yayyafin ruwa rigansa ya d'auka ya shimfida a kasan tiles in ya Kama sallah Yana idarwa daidai lokacin nurse ta shigo ganin ya farka yasa ta cikin fara'arta tace,ah ah Hassan ka farka ne?

"Eh na farka sister"Yana mamakin Ina tasan asalin sunan sa waya fada Mata sunansa?

Ok Baku da sallaya ne Naga kana sallah da riga bara na kawo muku amma yanzun akwai Inda ke maka ciwo ne?

"dan zazzabi zazzabi nakeji ga nauyin da kaina ke mini"

Ok toh bara na Kira doctor,tace tana fita a dakin, Nnenna da tun tashin Lahab ta farka shuru kawai tayi Harya idar da sallan,bude Ido tayi ta kallesa a hankali ta sauka akan kujerar tasa gwuwuwinta a kasa ta hade hannayinta sannan ta soma magana"kayi hakuri Lahab badon niba badon halina ba ka yafe mini nasan ban kyauta ba Kuma wallahi Koh Ni ban d'auka zaka cutu har hakanba pls forgive me"

Kauda fuska yayi Koh kala baice Mata ba,itama ganin hakan yasa jiki a sanyaye tace"ya jikin naka"?Nan ma shuru ya Mata Kamar ta shuka dusa,turo kofar da akayi yasata mikewa ta koma Kan kujerar da ta tashi likitane ya shigo nurse in dazun na binsa a baya hannunta d'auke da sallaya, Assalamu Alaikum

"Waalaikumu Salam"Lahab ya amsa tare da gaishe da likitan.

Amsawa likitan yayi ya daura Masa laidan ruwa ita Kuma nurse in ta aje sallayan a gefe tace, sister ga sallayan Nan sai Kuna amfani dashi daidai.

Lahab ne ya Mata godiyan don ita Kam Nnenna bama tasan me take cewa bama sai wani harhada fuska take ganin yanda likitan sai binta yake da Ido duk yabi yasata susuce,ashe Shima Lahab ya lura da hakan sosai ya had'a fuska tare da kallon laidan ruwa da aka saka Masa tunda yake ball kullum mami na Masa bariya akan yabar ball yana Karya mutum Amma gashi yau ball bai karyashi ba Nnenna ta tsaga Masa Kashi ba'a taba daura Masa laidan ruwa ba tunda yake har wani fariya yake babu kamarsa a gidan su gashi yau tasa an daura Masa sannan ga wani shegen kallo da yaga likitan ke Mata ita Kuma tabar kafafu a wajen ganin likitan ya fita yasa sa CE mata,"keee

dan kallon sa tayi ganin yanda ya wani had'a rai irin ba wasan Nan yana kiranta mikewa tayi tazo bakin gadon ta saya batayi magana ba,"in tambaye ki Mana?

"Ina jinka"

"Wai a addinin ki ance ki ringa saka suturan da zaina fallasa tsiraicin kune"?

Itama had'a ran tayi tana Masa kallon mamaki amma batace kome ba Shima ganin bata da niyar basa amsa yasa ta ce Mata"ATM nawa da Kika amsa jiya ki fita bakin asibiti baza'a rasa shagon Kaya a wajen ba kije ki sayamin Kaya so nake na chanja na jikinta,kema ki sai naki kibar daukar Alhakin Maza.

Jin ya gama maganar yasata juyawa kawai Bata ce kome ba ta bude jakan makarantan ta ta zaro card in da flask nasa dayake school dashi ta nufi kofar"zo taji yace dawowa tayi ta tsaya tana sauraron sa"ki sayi abinci"toh tace ta fita a dakin komawa yayi ya kwanta .



****************
Hmmm gidan su Lahab da sun shiga tashin hankali na rashin d'ansu domin Wasa Wasa Saida muzammil ya ringa bin gida gidan Yan uwa Yana tambaya Amma sai suce Basu ga Koh keyar Lahab ba,Mami ma ta Kira Addayiya ta sanar da ita Lahab yazo wajen ta amma ya fita,Wasa Wasa har dare ba labarin bawan Allah Nan Addayiya kuka ta Soma tana amanar umaru ya bata me zaicewa ubangiji an basa amana yaro ya Bata gidan su Adewale da Nabeel duk anje sunce su rabon su da Lahab tun shekaran jiya da Suka bugi malami a school

Rahab shi Karan kansa kuka yake amma fa Abbu ya bada guarantee Lahab ba bata yayi ba,akwai dai Inda ya shiga yanzun yanda kowa ke ruruta rashin jinsa aka fitar da zancen ba'a gansa ba wasu zasu ce duniya ya shiga Koh Kuma yafi karfin iyaye da yayunsa tunda daman shi dan Adam baka iyya masa haka baka guje masa kome abin magana ne.


Muzammil Kam yasha alwashi idonsa idon Lahab kashesa ne kawai bazaiyi ba Amma Shima ya mugu mugun shiga damuwa sosai.


ta bangaren gidan su Nnenna Suma sunsha mamaki ganin har dare babu Nnenna especially da yanzun ita ke musu girki gashi dady zai dawo gobe duk mom ta rikice batasan me zatace wa Dad ba tunda Bata San takamemmen Inda ta shiga ba a daren haka yayita sake sake,washe gari da safe Dad ya Kira ta ya sanar da ita Yana Kan hanya kitchen ta shiga ta girka musu breakfast sukaci kafun Sarah da Jennifer Suka tafi makaranta.



Mubeena a daren nan ta kwana a zaune ga wani irin bugawa da kirjinta yake ta rasa meke Mata dadi tabbas da tasan Ahmad zaiji abinda tace wallahi da Bata fadawa kowa ba tabar abin a ranta yanzun wani hukunci Ahmad zai yankewa alakarsu Koh banza Mai kyautata maka randa bashinan sai kaji ba dadi,bare Ahmad daya Mata kome a rayuwar baicacanci wulakanci Koh ki ba haka bataso yaji kome ba,washe gari hakan ta tashi idanunta a kumbure sosai Wanda hakan ya matukar damun Inna ajeta tayi ta tambayeta meke damun ta Amma kememen mubeeena tace ba kome.

Toh Koh kunyi fada da Ahmadun ne?Inna tace Mata.

Babu abinda ya hadamu Inna.

Toh Amma Naga jiya baizo ba Kuma nasan Ahmad in ba ruwa ake ba babu abinda ke hanasa zuwa.

Inna nace Miki babu kome fa shuru kawai Inna tayi bawai don ta yarda babu abinda ke damun ta bane,da misalin karfe 8 na safe sai ga Rukayya ta doka sallama a kofar gidan nasu tare da turawa ta shigo.


Waalaikumu Salam barka da zuwa takwara,Inna ta amsa Mata tana shimfida Mata taburma,yauwa Inna Ina kwana mun tashi lafiya tayi maganar tana Zama a taburman Zama itama innar tayi tana amsawa lafiya Alhamdulilah ya jatumar Taki?

tana lafiya Inna mubeeena na Nan kuwa?

tana Nan yarnan gata can kunshe a daki duk abin duniya na damunta Kuma Taki fadamin ki shiga ai in akace maka mutum bafulatani an gama magana.

Murmushi Rukayya tayi ta nufi dakin tana tsokanar Inna,ai kawancen ne aka daina dake kin tsufa Bari Kiga na shiga fadamin zatayi.

dariya kawai Inna tayi yayinda Rukayya ta Shiga dakin kwance ta tarar da mubeena Koh sallamar da tayi ma Bata amsa ba Zama tayi a bakin gadon a hankali tasa hannu ta girgiza ta,firgigit ta farka d'aga nannauyan tunanin data tafi,Haba mubeeena Zaki kashe kanki ne Koh Yaya irin wannan tunanin da damuwa da Kika daurawa kanki da wannan kwanciya naki da Alwala kikayi kikayi sallah Kika roki Allah ya yaye Miki dayafi?

Uhmmm Ruky bazaki gane halinda nake ciki ba ni kadai nasan yanda nake ji.

Koma me kikeji ba daidai bane ace kina sakanki a damuwa har kinsa tsohowa ma a cikin damuwa haba mubeena?

Ruky dole na damu bantaba Jin kunya irin na jiya ba da wani Ido Zan Kara ganin Ahmad tana maganar tana kuka.

Mubeeena ki kwantar da hankalinki yanzun ma zuwa nayi ki tashi muje asibiti mu duba jikin nasa ya ya kwana tunda yau bamu da exam.

Haba Ruky wallahi bazan iyya zuwa ba innaje nace meye?

Kinga mubeena gwara dai ki tashi muje ki dubasa Amma rashin zuwanki ma wani rauni Kika fame Koh iyayen sa zasuyi mamakin ki in Baki je ba karfa ki manta Koh ciwon Kai kikayi haka Yan uwansa zasu yita zuwa dubaki dan Allah ki daure muje kinji Koh?

Mikewa zaune mubeena tayi jiki ba kware ta fita a dakin tabar Ruky ita kadai ruwa ta Iba tayi wanka ta shirya Suka ma Inna sallama Suka fita a gidan,tun d'aga nesa ta hangesa tsaye a wajen jiya gabaki d'aya yabi ya rame itama Kara had'a fuskarta tayi daman a hade yake tafiya suke yayinda ya zuba Mata Ido shi Kuma tun d'aga nesa,har suka karaso Inda yake zasu shari kwana matsowa yayi kusa dasu tare da musu sallama Kamar cikekken musulmi, Assalamu Alaikum


Waalaikumu Salam Rukayya ta amsa Masa mubeeena Kam Koh kallo Bai isheta ba bare ta amsa Masa sallaman ma sai ma kokarin geftasu da take da Sauri yasha gaban ta tare da Ware hannayen sa ya tare Mata hanya sannan ya Soma magana, mubeeena bancancanci wulakanci a wurinki ba mubeeena bazan gaji da fada Miki wannan kalma ba Ina sonki Koh da bazaki karbi soyayya taba dan Allah ki sakar min fuska Koh Zan samu sassauci da sukuni a zuciya ta.

Adewale ka bani hanya na wuce na fada maka bana son ka banason ganinka ana dole ne ?Koh Ni sarar kace?ta karasa maganar tare da zagayesa ta wuce d'aga shi har Ruky da Ido Suka bita Harta tare Keke napep tahau bata ma saurare jiran Ruky ba.

Kallon Ruky Adewale yayi ya Soma Mata magana,Ina kwana kawarmu?

dan murmushi Ruky tayi,lafiya Alhamdulilah Adewale Koh?

Hh ta Baki labarina kenan?

Eh toh banace ba.

Hh pls kawarmu ki taimaka ki ringa nunawa mubeena abinda ya dace bazan iyya cigaba da jure abinda take minin Nan ba.

Karkaji kome kaima Ina so kayita Addu'an Allah ya zaba muku abinda yafi Zama Alkhari ka Kara hakuri Ade mubeeena nacikin damuwa ne a Yan kwanakin Nan.

Da mamaki yace damuwa Kuma?meke damun ta?

Kaidai abar zancen kaga Bai Kamata na Fadi abinda Bata sani ba Amma kana Mata uzuri.

Ba kome nagode,wucewa Ruky tayi tana maijin haushin halin mubeena Keke itama ta tare,tana Isa clinic Keke ya dauketa ta Shiga gate in mubeena ta gani tsaye tana jiranta Koh kallonta Ruky batayi ba ta wuce ciki mubeena tabi bayanta.

Suna Isa kofar dakin da aka kwantar dashi jiya Ruky tasa hannu ta bude kofar bakinta d'auke da sallama.

amsa Mata kanin Ahmad yayi fuskarsa a washe shigo sukayi ya mike ya Basu kujera Suka zazzauna Ahmad dake kwance tun shigowar su yake bin mubeeena da kallo kawai kalllo ne irin na mamaki,kanin sa fita yayi ya basu waje, Ruky ne ta katse shurun da gaidashi,Ina kwana ya Ahmad ya jikin naka?

ajiyar zuciya ya sauke,lafiya Alhamdulilah da sauki.

Jikin mubeeena a mace Daman tunda ta Shiga dakin bata yarda sun had'a Ido ba kanta a kasa yanzun ma muryarta har rawa yake ta soma gaidashi,i........in...naa...kwana?

Lafiya shine kadai abinda yace sannan dukansu sukayi shuru mikewa tayi ta aje laidan fruit data saya a hanya don ta fahimci hankali bai Gama isar mubeena ba,am rukayya ki zauna maganar da zanyi ya shafeki kema no need ki bamu waje Ahmad yace ganin Ruky zata fita a dakin.

ras ras haka gaban mubeena ya Fadi,komawa Rukayya tayi ta zauna a hankali Ahmad ya Soma magana,a gaskiya ban taba tunanin bana fahimta ba sai jiya tun farko mubeeena ta nuna bana kauna na amma na nace na kasa rabuwa da ita saboda tsananin sonta da Allah ya daura mini,a lokacin da na Fara ganin tana sake mun fuska sai nayi tunanin toh Koh ta Fara sonane ashe hauka nake Ni kadai,sai Kuma ya kalli mubeeena meyasa mubeeena Baki gayamin akwai wani a ranki ba da tun farko ban nace lallai nayi so maso wani ba,amma ba kome Alhamdulilah tunda yau nasan matsayina,insha Allah d'aga yau mubeeena bazan Kara tinkarar ki da rokon so Koh maganar so ba.

Kukane ya kubcewa mubeena tasa hijab ta rufe fuskarta wani irin zafi takeji da Kuna a zuciyarta especially da taji abinda yace,sannan ke Rukayya na Jima banga mace Mai tunanin Mai zurfi da fadin gaskiya da girmama soyayya ba irin ki a yau Ina Mai rokon Alfarmar so a wajen ki inkin amince daman iyayena sun takura min Kuma sun ban lokaci na fitar da Mata Kuma a yau Naga matar da ta dace dani Ina so Zan aure kiiiii..............




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*

Page 55&56
Aure aure fa kace Ahmad?wannan wani irin abune kana saurayin kawata kazomin da wannan zance Ahmad?Ruky CE tayi maganar tana mikewa tsaye.

tabbas Rukayya aure ba Kuma auren huce haushi Koh auren tushi zanyi dake ba so nake na nema a wajenki in Zan samu amma ba roko nake ba don nayi hakan banga da kyau ba, maganar kawa Kuma ai ba a bayan idanunta akai komai ba a gaban idanunta ne shiyasa na fada a gabanta karma ta kiraki Maci amana, Rukayya naji kince lokacin Abu ayishi mutum in yasamu dama a dama dashi bance ki aure Ni don naji bakida manemi ba illah gaskiya da naji kike fada Mata dan haka nake son ki Amince dani na Zama shugaba a gareki na biya sadaki mu shiga d'aga ciki.

dakata Ahmad wani irin magana ne wannan kake haka kasan kuwa wacece a gabanka Rukayya kawar budurwar ka haba dan Allah ana barin hallas dan kunya.

Ah ah Rukayyatu karki ce haka abinda Addini bai haranta ba aikatashi bai Zama aibu ba na

Please Login or Register in order to submit comment