Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tayi cikin kitchen Alhaji ma mikewa yayi yayi part nasa yabar su a falon mikewa Rahab yayi ya shiga kitchen in ya dauko musu kayan marmari ya dawo falon ya aje musu shida mustapha...


Abinci Mai Rai da lafiya Mami ta dafa miyan ganda ta dafa da tuwon rogo,tana gamawa tadau Sabon kulanta Mai kyau ta zuba abincin a ciki ta rufe ta dau sauran ta jera a falo,wanka tama yaranta Suka shirya tsab harda shi Alhaji Kiran sallan azahar da akai shiyasa sasu wucewa masallaci bayan sun dawo ne Suka zazzauna a dinning Sukayi lunch gabaki dayan su.


Bayan sun gama ci hijab Mami ta daukowa wasila da mufeeda Alhaji na rike da Yusuf sai mahzar dake d'auke da kulolin abincin da Mami tace ya dauko a kitchen,mota biyu Suka shiga d'ayan mami keja daya Kuma Alhaji Suka nufi gidan su Lahab.




************************
Adewale basu Suka dawo church ba sai kusan 12:30 Suna dawowa kwanciya Adewale yayi Yana maida numfashi don harga Allah ba lafiya bane dashi turo kofar mama tayi ta shigo dakin ganin sa a kwance yasa ta karasowa kusa dashi tasa hannu tana taba jikin sa tace,Wai Adewale bansan meke damun kaba jikinka zafi gashi yanzun kome sai kanayi a sabule what wrong with u?matsowa yayi ya daura kansa akan cinyarta hannu tasa ta shafa Kan nasa tace,Wai har yanzun dai akanta ne Koh Hala?uhmmm har yanzun mama bansan matsayina a gunta ba?


Murmushi tayi tace,in baka shawara son?gyada Mata Kai yayi baiyi magana b kara shafa kansa tayi ta soma magana,ur too young sosai yanzun ace ka Fara soyayya a dan wannan shekarun naka karatu ya dace kayi ka samu ka Zama cikekken mutum kafun ka Fara maganar mace?kaga yanzun zaka b'ata future naka ne a banza Kota amince da soyayyar ka auren ta zakayi?


d'ago kansa yayi ya kalleta yace,toh mama basai ta jirani na gaba makaranta ba sai muyi auren Koh Kuma keda papa kumin aure sai mu cigaba da rayuwa tare?

Dariya abin ya baiwa mama amma batace kome ba don tasan komame zatace bazai fahimce taba saboda so ya rufe Masa Ido ita Kuma bata San me zata ce Masa ba.

Mikewa Adewale yayi ya shiga ban daki Bai jiba ba sosai ya fito ganin mama tabar dakin yasa sa daukar key in machine nasa ya bar gidan akan machine in roba-roba direct gidan su Nabeel ya nufa Harya share kwana sai Kuma ya tsaya ganin Shareef tsaye a bakin rumfar kayan marmari dake kusa da tsallaken layin su Yana sayan kankana,Jan Machine NASA yayi zuwa Inda Shareef in ke tsaye da sallama ya faka machine in hade da mikawa Shareef hannu,juyawa Shareef yayi ya kallesa sannan ya kalli hannun kin bawa Ade hannun sa yayi sai amsawar da yayi a gatseΓ±e Yana kokarin barin wajen.

danne zuciyar sa Ade yayi yace,Shareef yakake?lafiya klau kawai yace Yana kokarin bude motarsa da Sauri Ade ya sauka a machine in ya nufesa yanace Masa,ayya nace Koh anji labarin Lahab Koh Inda yake?


shekeke Shareef ya tsaya sai Kuma ya bude motar ya shiga yaja kofa ya rufe kafun ya sauke glass yace ma Ade dake tsaye har lokacin Yana binsa da Ido,eh ya dawo Yana gida baida lafiya,da Sauri Ade ya matso kusa da glass in har Yana tuntube yace,ba lafiya meya samesa,oho kashin hannunsa ne ya tsage daga haka yaja motar da Sauri Ade ya matsa gudun karya taka masa kafa, machine nasa ya hau ya gangara gidan su Nabeel paka Machine in yayi a kofar gidan ya cire key tsayawa yayi a bakin kofar gidan Yana kwada sallama.


Nabeel dake Kan Keke sai dinki yake don yau tun da safe Banda sallah babu abinda ya dagasa akai sai cin abincin Rana da yayi ya samu ya dinka riga yanzun ma siket yake dinkawa yaji muryar Ade Yana sallama amsa Masa yayi,ka shigo Mana sai kace Bako,turo kofar gidan yayi ya shigo kansa a kasa,sai Kuma ya dago Kai da Sauri Jin Karan Keke da mamaki ganin Nabeel akai yace,yau wani Rana Nabeel dinkin wace Mai sa'a ce hake kake dinkawa?mtwsss kaga ga kujera zoka zauna bana son wani surutu gabaki d'aya mutane Basu da adalci gabaki d'aya kunsa min Ido,dariyan karfin hali Ade yayi ya juya kitchen Jin muryar Inna na Masa magana,ah ah wa nake gani Kamar bayarbe kwana biyu nace Koh Lagos kuka nufa ai?


Ah ah inna Ina Nan wallahi bandaiji Dadi bane sai yau ya gida?


Alhamdulilah Adewale ya jikin naka Ina labarin lahabu bawan Allah


Wallahi Inna nima yanzun Nan na hadu da dan yayan sa Shareef nake tambayar sa labarin sa yake cemin Wai an gansa Yana gida ya samu tsagin Kashi a hannu zaro ido Inna da Nabeel sukayi kafun suyi magana sukaji Karan Abu a bayan su gabaki dayansu suka juya mubeena ce ta fito wanka daure da zani a kirjin kanta da jikinta naaaaaa...........................




πŸ€ *By Ruqeenjalal* πŸ€




*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*


Page 71&72

Kwandon soso dake hannun tane ya Fadi dukansu kallonta sukayi, tana had'a Ido da Adewale da Sauri ta juya ta koma ban dakin tana tsaki batasan zata fitoh ta gansa ba da Bata fito a hakan ba,sunkuyar da Kai Adewale yayi Yana Jin abinda Inna ke cewa,kee mubeena kin haukace ne Koh me?Kai Kuma bayarbe garin Yaya abokin naku ya samu wannan rauni haka?

Wallahi Inna ban sani ba shiyasa ma na biyo tanan muje mu dubasa da Nabeel, Adewale yace Yana sauraron abinda Nabeel zaice, Ade mu Bari zuwa dare sai muje mu dubasa,da mamaki Inna tace wani irin a bari sai dare Nabeel meyasa baka da mutunci ne Lahab nefa baida lafiya kace sai dare zaku?Kai Inna sofa nake na gama dinka wannan kayan daman Mai kayan taban kudin dinkin rabi Inna Kai Mata sai taban sauran Kinga saimu samu mu sai Masa koda kaza ne.

Murmushi Adewale yayi yace,kaga Nabeel in zamuje mu dubasa muje mu dubasa maganar kaza Koh abinda zamu Kai wannan bazai hanamu zuwa ba kaga saimu koma da daren,gyada Kai Nabeel yayi yace shikenan muje in ba matsala. Sauka yayi akan keken NASA sukayiwa Inna sallama Suka fita a gidan Suna fita mubeena ta fito daga bayin fuska a hade tare da dukawa ta dau sosonta daya Fadi ta kalli Inna da har lokacin tana Kan taburma tace,nifa gaskiya Inna bana Jin dadin abinda yaron Nan yake Mana?da mamaki Inna tace ke mubeena meya Miki da har baki Jin dadi bansani ba Kuma Ni gani nayi yaron Nan baida matsala.


Murguda baki tayi tace nifa gaskiya Inna banson Yana shigowa gidan Nan Kai tsaye irin haka duk abinda zaiyi Koh yakeso ya tsaya a waje Nabeel in ya fita ya samesa acan Akan me zaina shiga haka Kai tsaye yanzun fa wanka na fitoh fa a haka dagani sai zani na gansa a tsakar gidan Nan hakan ya dace kenan Muna barin wannan arnen Yana Kare Mana.

Rike baki Inna tayi cikin mamaki tace,lallai baki da mutunci mubeena yaron Nan sama da shekara goma Yana zuwa gidan Nan sai yau kikasan ya Fara Kare Mana kaji Mara kunya?


Yanzun dai duk ba wannan ba Inna yaushe zamuje mu duba Lahab in,wani kallon mamaki Inna ta Mata tace,keee na hanaki zuwa ki dubasa ne Koh yanzun kikeso shiga ki kimtsa kizo ki wuce nidai sai gobe da safe zani,wucewa kawai mubeena tayi ta shiga daki batace kome ba.






********************
Bude kofar gate in Mai gadi yayi Alhaji sulaiman ya danna hancin motar sa zuwa cikin compound in na Mami na binsa a baya, parking sukayi gabaki dayan su suka fito,tsayawa Alhaji yayi da mustapha a parking space Mami da sauran yaran sukayi cikin gidan tura kofar Rahab yayi suka kusa Kai ciki,babu kowa a falon nufar kofar sashin su Lahab Sukayi har Mami zata bude kofar aka rigata uzaifa ne ya fitoh da fara'arsa ya Soma gaidata,amsa wa tayi tana tambayar sa jikin Lahab,ai Yana dakin Addayiya baya Nan ku Isa, kofar falon Addayiya Suka nufa tura kofar sukayi da sallama babu kowa a falo kofar dakin Suka nufa gabaki dayan su suka tsattsaya a kofar dakin Rahab yasa hannu Yana bubbugawa Yana kwada sallama, Addayiya dake zaune ana yagan kaza Jin ana bubbuga musu kofa kamar Kuma muryar Rahab yasa ta Fara masifa,Kai haba karka ballamin kofa Mana ka jira azo a bude maka banason gaggawa haba?mikewa tayi tana tsude hannu tazo ta bude kofar,waro Ido tayi sai Kuma ta washe baki tace,ah ah wa nake gani Kamar hajiya wasila?


Nine Addayiya Ina wuni?matsawa Addayiya tayi ba tare da ta amsa gaisuwar ba tace ku shigo Mana kin tsaya a tsaye,shigowar dukansu sukayi Suka zazzauna aje kulan mahraz yayi ya matso kusa da dan uwan nasa Yana Masa ya jiki,Mami ce tace, Addayiya da Alhaji mukazo Yana waje zai shigo ya duba Lahab,hijab Addayiya ta d'auka tasa tare da cewa, Bismillah ya shigo fita Rahab yayi yashigo dashi,su Mami basu tashi barin gidan ba harsu Nabeel ma Suka shigo sosai mutane keta shigowa abin sai ya baiwa mutum mamaki duk da kowa baijin dadin Lahab amma Allah ya Masa farin jinin mutane kuma duk Wanda zaizo saiya riko Masa Abu kulolin kaji Kam yafi biyar aka cikawa Addayiya a daki sai yamma sosai Mami Suka tafi amma Rahab bai bisu ba,bayan wucewar su kasa hakuri Lahab yayi ya tambaye Rahab"Wai Rahab lafiya Kam Naga gabaki d'aya kana Nan uncomfortable yau innan meke faru tunda na dawo Banga umaima Koh Shareef sunzo sun dubani ba Koh basa gidan ne"?


Shuru Rahab yayi ganin Addayiya ta shigo dakin shiya hanasa magana,kallonta Lahab yayi yace"Wai Addayiya Ina Yaya muzammil ne Koh fushi yake dani har yanzun bai shigo ya dubani ba haka ma Aunty nabeela"?uhmm ajiyar zuciya ta sauke tare da Zama a bakin gadon ta had'a giran sama da kasa ta kalli Rahab tace,malam fita ka bamu waje zamuyi sirri don Ni yanzun bani ba kai.


Waro Ido Lahab yayi yace"Kai Addayiya Rahab nefa kike kora Koh idanun nakine Suka samu problem"?zanci mutuncin ka lahabu?Jin abinda tace yasa Rahab Hawa Kan gadon ya kwanta Aiko da masifa ta Mike tana cewa sai ya fitar Mata a daki ya tashi ya fita amma haka yaki fita ta gama nacinta da masifarta kafun ta d'ale Kan kujerar dakin ta kwanta harda filo ta daura a kanta Kara tambayarta Lahab yayi ganin bata basa amsa ba"Addayiya Ina uncle ne yau kwata kwata ban gansa ba"


Ya koma tace Masa,zaro ido yayi cikin happy yace"ya koma fa Kika ce haba dai da gaske ya koma Amma Baya ce sai bayan auren su umaima zasu koma ba"?


Eh haka yace amma abinda dnn uwanka ya Masa shiya fusatashi ya tattarasu da sassafen Nan suka koma Inda suka fito,Kama baki Lahab yayi Kamar mace yace"bangane ba Addayiya meya faru meya hadasa da Rahab Kuma"?gashinan a kusa da Kai ka tambaye sa?juyawa yayi ya kalli Rahab dake kwance yayi Kamar baijin abinda suke cewa maka Masa kafada Lahab yayi yace"Kai tashi ka fadamin meya faru"?


Manna Masa hauka Rahab yayi bai basa amsa ba hakan ya Sasa kallonta yace"waini don Allah kumin magana Mana menene haka na Mannin hauka,turo kofar akayi zulaihat ce ta shigo hannunta dauke da plate,uncle sannu ya jiki sai Kuma ta Mika Masa plate in hannunta gashi inji ummu waina kawo maka,karbar plate in yayi yace"gaskiya kice Mata na gode"budewa yayi gasheshen Naman ragone yasha yaji sosai yana kamshi ga cabbage a Kai rufewa yayi ya aje don harga Allah ya gaji da ciman Nan yau yaci nama haryafi a kirga hannun zulai ya rike ya ajeta a gefen sa yace"zauna anan muyi magana"zaman tayi cikin Jin dadi tana kallon sa"meya faru jiya a gidan Nan har Uncle muzammil ya tafi meya had'asa da Rahab"shuru tayi tana kallon sa tunani take ta fad'ane Koh karta fada ga Kuma Rahab da Addayiya dake wajen fahimtar hakan yasa sa mikewa hade da kamo hannunta Suka bar dakin,Zama yayi akan kujeran falo itama ya ajeta yace"toh yanzun ai saiki fadamin abinda ya faru naji"Zama ta gyara a hankali ta soma magana,ba jiya bane Wai Mami ta Mari mamu shine sai Mami ta zageta ran Uncle Rahab ya baci ya tattara kayansa zaibar gidan zaibi Mami shine uncle Rahab yace............................tass ta mayar Masa da yanda abin ya faru duk da a farko Lahab yayi farin cikin barin muzammil gidan Amma yaji haushin abinda Rahab ya Masa,sai kuma ya basar yace"Ni gaba ta kaini tunda bani na zagesa ba bare a sani a gaba"ya mike ya koma dakin yayi kwanciyar sa abinsa.





***********************
Fuskar dady babu walwala daga hospital in station sukaje yayi sign sannan Yama mutumin da yakai rahoton ya ganta a asabiti kyautar 3k amma mutumin yaki karba Sam yace ya yafe wallahi daga Nan gida Suka nufa har lokacin Dad baice Mata kome ba parking yayi a kofar gate na gidan su,bude kofar motar Nnenna tayi da Sauri ta sauka ta tura karamin gate in ta shiga a take karnuka Suka mimmmike Suka nufota itama bata wani damu ba ta soma kiciniyar bude babban gate tsuntsunata sukayi sannan Suka koma Suka kwanta wangale gate in tayi dad ya shigo da motar sa parking yayi ya bude ya fita baibi ta kanta ba ya bude kofar falo ya shiga,binsa tayi a baya a hankali jikinta duk yayi sanyi bataso ta Bata Masa ba itama batasan ransa zai baci har haka ba,mikewa su mom sukayi dake zazzaune a falo cikin alhini,shigowar dad da Nnenna yasa Suka Mike Suna tambayar sa a Ina yaganta kala baice musu ba sai tura kofar Nnenna da yayi ya shiga ya zauna akan stoll na dakin yayi shuru,kanta a kasa ta gaida mom kasa amsawa tayi itama Nnenna Bata damu ba tabi dad dakin nata shiga tayi tana tafiya Kamar Wance kwai ya fashewa a ciki zamowa tayi ta zauna akan tiles har lokacin kanta a duke wani irin tsawa da bata tabajin dad Yama Koda yaran cikinsa bane ya sake Mata"keeee meya hadaki da wannan yaro Mara kunya dan hausa people innan am asking you for the last time wallahi ki gayamin gaskiya.


A hankali tace"am so so sorry Dad ban d'auka haka yake ba don Allah kayi hakuri nima ban Sansa ba accident muka samu lokacin baya hayyacin sa shiyasa na d'auke sa da taimakon Mai Keke mukaje asibiti bai farfado ba sai yau"tana gama maganar ta rumtsa idanunta da karfi saboda karya data fetsawa mahaifin nata duk da ba dabi'arta bane karya amma yau Lahab ya saya tayi.


A fusace dad yace,watoh kece uwar tausayi duk musulmai dake wajen a rasa Mai taimaka Masa saike uwar gwaninta sannan da wani kudi kike kula dashi a hospital in tunda har waya ma baidashi?


Duk da taso tadan rikice amma ta dake tace"akwai kudi a Aljuhunsa masu yawa dasu nayi amfani"Jin abinda tace Sam baiyarda ba ga wani bacin Rai daya tinkaro sa don shi a rayuwar sa yaki jinin musalmai da Christian ta taimakawa dayafi kowa murna,d'aga hannu yayi zai mare ta da Sauri ta Kare fuskarta shima hannun nasa tsayawa yayi Bai mare ta ba don sai Kuma yaji baison Marin nata komawa yayi ya zauna ya sassauta muryar sa ya Soma Mata magana,Kinga Nnenna Nan ba Enugu bane rayuwar Nan daban dana Shan banason ki jajibowa kanki matsala bana son kina mu'amala da ire iren mutanen Nan Baki ganin su Sarah da Jennifer kin taba ganin Koh maganar kirki ya hadasu da musulmai kina ganin layin mun Nan kwata kwata christoti Bamu da yawa Amma bama shiga harkan su don haka bana so karki Kara karki sake daga yau ma Zan nema miki drive da zaina kaiki makaranta tunda Naga Gloria da Abraham amanar da na Basu na tafi ba iyya rikewa suke ba,Yana Gama magana ya mike yabar dakin.


shuru tayi tana tunanin meyasa Wai kowa yake cewa musulmai Basu da kirki ne amma ita Bata ga rashin kirkin su ba ta hadu da shayibu(mijin ma'u) da Lahab Bata ga wani abin aibu a tare dasu ba amma tunda uncle Nata yace ta bari toh zata barin tunda bata San dalilin da yasa yace Mata haka ba wata Kila Suna da wani haline da ita Bata gane ba,mikewa tayi ta soma dube dube a dakin tana Neman Kiki kiransan ta somayi a hankali tana dubasa,,banko kofar dakin akayi mom ce ta shigo ranta a bace ta Soma magana harke kin Isa a dauko Miki d.............................





πŸ€ *By Ruqeenjalal* πŸ€





*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*


Page 73&74

A d'auko Miki driver Jennifer da take Yar masu gida ba'a kawo Mata drive ba saike banza toh wallahi Baki Isa ba ita dai Nnenna na tsaye kanta a kasa shako wuyanta tayi tace,kee magana nake Miki fa kin manna min hauka watoh kin gama karuwan cin ki shine Zaki dawo kuma a nema miki who a u?fisge riganta Nnenna tayi ta bude kofar toilet ta shiga tare da banko Mata kofa,sosai mom ke masifa ita dai Nnenna batace kome ba hartaji mom ta fita a dakin kafun ta fito tana kuka tana Kiran kiki,tsunguna wa tayi tana leka kasan gado duhu ne babu kome bayan wardrobe duk ta dudduba amma Bata gansa ba.


gajiya tayi ta koma bakin gado ta zauna tare da zuba tagumi tana tunanin Koh dai Kiki ya mutune da yunwa toh amma inya mutu Ina gawan sa ai da zata gani,kuka ta Soma a hankali tana cewa"ka taimaka Kiki ka fitoh tsawon shekara 10 Muna tare sanan yau kawai saika tafi ka barni,ta sake sabon kuka da karfi turo kofar akayi Abraham ya shigo dakin da Sauri ya karaso bakin gadon ya zauna hannu yasa zai Kama nata cikin tashin hankali Yana tambayar ta meyake faruwa hannu tasa ta buge nasa tare da mikewa rai a bace tace"fita mini a daki banason ganin ka ka fita nace"tana magana tana kuka sosai.

zamowa yayi daga Kan gadon yayi kneel a kasa ya Soma magana,haba sister meyayi zafi haka zakice Baki son ganina menene laifina kinsan irin tashin hankali dana Shiga kuwa?na rashin ki a kusa dani naji tsoro sosai,komawa tayi ta zauna tana cigaba da kuka Koh banza tad'anji sanyi ashe akwai wa'inda Suka damu da rashinta a duniya,matsowa kusa da ita yayi sosai cikin lallami yace,kiyi hakuri ki sanar dani Ina Kika shiga wallahi na damu rashin ki na samu Dad amma yaki ya kulani pls tell me Ina Kika shiga?

dan shuru tayi sai Kuma tace"accident muka samu a hanyan toh Wanda mukayi accident in dashi ya samu rauni sosai shine na taimaka na zauna agunsa Ina jinyar sa"da mamaki yace toh meyasa ran Dad ya baci saboda dan abinda kikayi Nan sannan nasan saboda baki da wayane da Zaki Kira ki fada Mana amma Bari na fita Zan sayo Miki Sabon system?girgiza Masa Kai tayi shima girgiza Mata yayi yace,saboda me?meyasa duk lokacin da Zan Baki Abu saikin Raina ne?da mamaki tace"raini Kuma"eh mana ya bata amsa dan rufe fuska tayi tace"nifa ba Raina wa nayi ba kawai ka barshi don nasan in mom ta sani ranka da nawa ne zai baci.

Mikewa yayi daga durkusen da yake har lokacin idanunsa na kanta yace,kawai amsa nake son naji kinaso Koh ah ah?nifa bawai bana so bane kawai dai.........dakatar da ita yayi ta hanyar cewa,nifa banson kice kome waya dai Zan sayo Miki sauran aiki ya rage naki,dubeki Kamar Mai wayo amma babu,Yar kauye kawai duk abinda aka baki dole ne saikin nuna an gani kawai boyewa zakiyi kina amfani da abinki Koh su Sarah karki bari su gani kinji ?"toh nagode"tace tana Kara zuba tagumi har ya bude kofar zai fita sai Kuma ya dawo ya tsaya again yace,meke faruwa ne sister Naga Kamar kina cikin damuwa?


"Banga cat nawa ba brother"tace tana Kara fashewa da kuka tana dad'a rufe fuskar ta da hannu, murmushi yayi yace,kiyi hakuri toh Zan samo Miki wani new cat in,d'aga kafada tayi tace"Ni bana son wani kawai so nake na gansa"bude kofar kawai yayi ya fita baice kome ba,jakan makarantan ta ta bude ta dauko uniform nata dake ciki ta aje akan gadon takardunta ta Soma fitarwa sai Kuma ta zaro Ido ganin abinda ya Fadi hannu tasa ta d'aga tana duddubawa ATM in Lahab ne"wash na manta dashi kwata kwata ban basa ba toh yanzun ya zaiyi da bill na hospital gashi babu kowa nasa?"sai Kuma ta danyi murmushi idanunta na zubda kwalla tace"ashe fa ya Kira Yan gidan su,gobe Zan Kai Masa a hospital in duba jikin nasa.






********************
bayan isha'i umaima dake dakin ta a zaune wayarta ne yayi tsowa mikewa tayi ta dau wayar ta Kara a kunnen ta,sallama akayi ta amsa cikin happy tace"ok harka iso ok toh ganinan fitowa,katse wayar tayi ta aje mikewa tayi ta dau hijab nata ta dau turare ta feffesa a jiki sannan ta zura,ta fitoh a dakin nasu kallon su muneera dake zaune a falo tayi ta nufi kofar ta fita.


Tsaye yake Kamar kullum a kusa da motar sa karasowa tayi tana murmushi"barka da warhaka Rabin Raina",da murmushi yace"yauwa dear ya Mai jikin?


Da sauki Rabin Raina Yana ciki muje Bismillah


Bude motar yayi ya dau laidodi manya dake ciki,da Sauri umaima ta matso tasa hannu zata karbi laidan,kaucewa yayi Yana dariya ya rufe motar yace"Kinga Bari Zan idar da ladana basai kin tayani ba"kaga ka bani kawai bakon ka annabin ka kana son mu shiga ciki Addayiya tamin fada ban karbe abin hannu Bako ba, murmushi kawai yayi ya bata laida daya shima ya rike daya Suka jera tare Suna tafiya itace a gaba Yana binta a baya.



Zaune suke a dakin Addayiya kansa a kasa irin anzo gidan surkunayen Nan kansa a kasa suke gaisawa da Addayiya sai umaima dake zaune a bakin gado,Lahab da Rahab nakan gadon a zaune"gaskiya mungode Abubakar Allah yabar zumunci Allah dai ya nuna Mana ranan bikin Nan ayi a wuce wajen, Addayiya tace Kara sunkuyar da Kai sadeeq yayi Yana ma Lahab ya jiki amsawa yayi rahab ya gaidashi ya amsa da fara'a mikewa umaima tayi da Sauri Addayiya tace"Ina Kuma Zaki kibar Abubakar in kuma"zanje na sanar dasu mamu Wai zai shiga falo ya gaidasu" ta bata amsa ba tare data jira abinda zata ceba tafita a dakin,itama Addayiya mikewa tayi tadau laidan daya kawo Mata ta bude wardrobe nata tasa ta rufe tare da fita a dakin,ganin babu kowa daga shi sai tagwaye yasa sa d'aga kansa ya kalli Lahab yace"am in babu damuwa small uncle Niko so nake muyi magana da Kai wata Alfarma nake nema.


"Wace irin Alfarma kenan sadeeq ince dai lafiya"? Lafiya Lahab daman akan maganar kawo lefe ne abinda ma ya dagoni kenan zuwa gombe nazo na sanar Mata akan ranan talata za'a kawo lefe toh saina zo na tarar da abinda ya faru Allah ya kiyaye na gaba,Ameen Lahab da Rahab sukace Suna cigaba da sauraron sa,shine tace a aje maganar kawowa, yau na tashi da niyar wuce wa sai ga kiranta tace min an ganka harma ka dawo gida,dana Mata maganan kawo Kaya shine tace Wai babu Rana sai Randa kaji sauki gashi mom nata kirana akan maganar lefen nakasa ce musu kome pls kasa baki akan maganar na rasa wazan tinkara ga umaima da taurin Kai?


Rahab ne yace kana nufin ita tace babu maganar lefe ba ranna kawowa bayan Kuma date na biki saura wata daya"?cikin dan annashuwa ganin ya samu goyon baya yace"eh wallahi nima shine hankalina yadan tashi"karka damu Zan ma Addayiya magana karku fasa kawowa ranan Tuesday in Ina jibine ma"?eh sadeeq yace sai Kuma yayi shuru ya fasa maganar da zaiyi ganin umaima ta shigo tsayawa tayi tana kallon su ganin Kamar wani abin suke kullawa tace"ka taso muje ku gaisa"mikewa yayi yabi bayan ta Suka fita a dakin,Suna fita saiga Addayiya ta dawo a lokacin Lahab ya sanar da ita abinda ke faru Aiko tace zata samu mamu da Abbu duk da ajesu akan maganar lefen.



Mamu taji haushi matuka na zuwan sadeeq gaida Lahab amma bata nuna

Please Login or Register in order to submit comment