Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

karasa maganar da zama a 1 sita.

Hararan ta Lahab yayi da suka had'a ido Amma batace kome ba, sai maida hankalin ta da tayi a wajen abbu dake magana, wallahi wallahi lahab ka shiga taitayinka dani a gidan nan, kar kaga duk abinda kakeyi an zuba maka ido babu mai hukunta ka sai muxammil, ka d'auka koh tsoron ka akeji.

kallon Abba yayi cikin hade fuska yace"toh ni me nayi koma?koh nace me aka sake kullamin"?

Tsawa abbu ya kara daka masa sai da ya razana wallahi irin unexpected in nan, wallahi summa tallahi lahab ka kiyaye kanka da bacin raina zaka ga ba daidai ba randa ka kaini bango?banda rashin hankali da rashin tunani ace saurayin diyarka yazo, ta masa girki sai kazo ka sabe ka kara gaba dashi?

Muna barin ka da yunwa ne a gidan nan koh me? da bazaka tambayi abinci ba saika d'auki abinda ba naka ba ina rabaka da d'aukar kayan mu a gidan nan.

Kayi hakuri Abbu, Rahab yace hawaye na cika a idanunsa ji yake kamar shi yayi laifin, sabanin lahab dako a jikinsa TV kawai ya kurawa ido kamar pusta.

Amma dai kai Lahabu anyi shegen gari ana maka fad'a shine zaka basa keya kana kallon d'an iskan TV?

Juyawa yayi yana kallon Addayiya cikin masifa da haushi yace, "wallahi addayiya ki fita harkana nace miki koh? koh dole ne sai kin shiga abinda babu ruwan ki"?

Kai na shiga!! nace na shiga!! d'an batalon uba, yanda kake baki haka zuciyar ka take.

Kwarai kuwa addayiya ni wallahi inso samu ne ma kawai a mayar dashi wajen dadyn su Taimiya.

Kama baki Addayiya tayi tana kallon mamu dake maganar nan, Eh lallai halima sai yanzun nasan zaman da kike da yaran nan, sai kuma ta fashe da kuka tana rufe fuska da gefen hijabi, toh wallahi bari kiji na sanar dake da kowa ma na gidan nan wallahi koh bayan raina ban yafe maka ba umar in yaran nan tagwaye suka bar gidan nan mundin ba aure koh karatu koh son ransu bane yasa su fita sai masifar Matan ka koh yaranka.
Wallahi koh bayan Ran mijina bazan wufantar da amanar da ya bamu nida umar ba, ai yasan da Jafar in yace umar ya kular masa da yaransa,ta nuna mamu ke asuwa da zakice yabar gidan uban sa? ai kece ma zaice ki kara gaba, in kin manta bara na tuna miki lokacin da umaru ya tashi auren ki yar haka kike kamar kishiyar mayya.

Amma dubeki yanzun kin zama buhu kici ki koshi kiyi kashi kice zaki raba zumunci, wallahi baki isa ba kai lahab tashi ka tafi abunka ka d'au abincin dan uwar ki umaimah bazaiici kayan yayan sa ba, sai ya zama zaraba toh yaci din Lahab tashi ka tafi.

Mikewa Lahab yayi cikin kuri ya nufi kofa yayin da mamu taji kamar ta tona kasa ta shiga musamman ma dariyar da ummu ta sake, irin dariyar nan na jin dadi.

Abbu kam sai ido, ya rasa meke damun Mamar tasa itace tayita uzzura Abinda lahab yayi, sannan yanzun tazo ta juya zance kuma, duk da abinda mamu tace bai dace ba sam shima baiji dadin abinba d'an uwa ba wasa bane.

Lahab na shiga d'aki kwanciyar sa yayi koh abinci baici ba.

Washe gari jafar da babban d'ansa, Taimiya suka diro tun safiya a d'akin su Anwar Taimiya ya sauka dayake duk sa'o'ine, sai abokan Abbu, tun safe su mamu ke shirye shiryen tarban baki.


Sai da yamma iyayen sadeeq suka zo anyi kome a mutunce sun kawo goro da Sadaki tare da yanka sarti duka, saboda nisan dake tsakanin sun, gari ba daya ba. sonyi kome lokaci d'aya, ya rage saura kayan aure da rana, daman sadeeq da umaimah sun jima tare jira yake ta kammala karatu gashi yanzun har ta fara zana final exam nata.


A Ranan ma Lahab koh wuni baiyi a gidan ba sanin da yayi mamin sa na zuwa kuma yasan tabbas tazo ta samesa zuwa school ya kamasa kenan.



*****************
Nnenna dake bacci hankali kwance ji tayi kamar ana son tabata kamar da mutum a kanta don ita duk nauyin bacci muddin mutum ya tsaya akan ta tana farkawa, bude idanunta tayi da sauri yayin da ta damko hannun mutum dake kokarin kaiwa jikinta.


Ware ido tayi da kyau ganin Abraham ne duke akan ta sanye yake da gajeren wando da single, wantsalowa tayi gefe tana kare jikinta, hade da masa mugun kallo.

Shikam sai kara matsowa kusa da ita yake, baby ya naga kina kwana da wuta gashi koh sleeping dress babu?

Mikewa tayi tsaye tare da nuna masa kofa cikin bacin rai tace," get out Abraham wallahi ka fita koh na illataka"

Da mamaki yace nida gidan mu zakice zaki illata ni kina mace ina namiji har akwai wata illar data wuce nina miki?

"Tabbas akwai don ni illar da zan maka na har abada ne babu sauran gani bare wata rana ka manta, fitar miki a wajen kwana naji gidan kune amma d'akin nan ance nashiga don haka fita kaban waje"tana maganar cikin fad'a fad'a tsawa tsawa.

Zaro ido yayi da mamaki don shikam bai d'auka haka yarinyar take ba gashi dare ne kar tayi ajisu da sauri yayi mata magana kasa kasa, ke menene haka?

"Fita"!!!!!!!!!!

Da sauri ya juya ya fita, itama Nnenna mikewa tayi ta rufe kofar duk da bata iyya ba amma haka ta tura da karambani ta murd'a ki tare da zarewa ta aje a gaban katifar ta koma, zata kwanta sai kuma ta kalli makwancin kulenta, zaune yake yana kallonta alamu madai ya jima da farkawa.

Wutar d'akin ta kashe ta kwanta tare da rungumar kulenta.

Washe gari da misalin karfe 3 na asuba taji ana buga mata kofa da karfi ana kiran sunan ta, mikewa tayi ido duk bacci, haka ta mike zaune da lalube ta kunna hasken d'akin, key ta d'auka tana kokarin bude kofar aka bankosa ta waje, sai da ya buge mata goshi kara ta sake tana dafe wajen, kafun ma ta dawo hayyacinta taji an sake mata dundu mai zafi a baya hade da zagi.

Ke yar kauye ai bacci bai kamaki ba yar wahala muna bacci kina bacci fita zakiyi ki share gidan nan tsaf, har compound kiyi mooping kiyi wanke wanke in peace ta fitoh breakfast zata had'a miki d'aurayan da zakiyi.

Gyada kai kawai tayi amma batace kome ba sai bin bayan jennifer tayi har tsakar falon tsintsiya ta watso mata da sandan mooping da sauran kayan gyara, ta koma dakin ta ta kwanta, Allah ya kyauta don ta azabtar da baiwar Allah kawai ta tashi.

Tsintsiyar Nnenna ta d'auka ta share falon har wajen compound unguwan tsit babu motsen kowa sai kukan karnuka ga sanyin asuba dake tashi haka Nnenna ta share gidan tas da falo, amma ta rasa ya xatayi mooping karshe ma jika musu falo tayi da ruwa tirim.

Wanke-wanke tayi a kitchen lokacin gari ya fara waye wa 5:30am na asuba saiga Peace ta fito a kofar d'aken kusa dana Nnenna sanye da kayan kitchen, bin falon tayi da kallo sai kuma ta sake kallon Nnenna da kyau, ke wace irin wawo yace ya zakizo ki jika tiles haka da kumfa?

Nnenna kam shuru ta mata don ta rasa me yasa take da bakin jini ne, koh ina taje bata farin jini, karban mopper in Peace tayi ta gyara tiles in falon tare da nuna mata yanda zatayi mooping in kayan falon karta narkawa kayan wuta ruwa.


Tana aiki peace na girki a kitchen, tana gama aikin d'auraya peace ta lafta mata a waje,ta had'a mata da sabulu da omo ga dam a gefe na ruwa.


Tun tana tsammanin gamawa da wuri har d'aurayan ya fara shiga jikin ta, wanki take tun safe tana kallon yanda yara 'yan makaranta keta wucewa daga musulmai har Christian da ma'aikata, har lokacin da Dady ya fita shima ba'a jima ba saiga momy itama ta fita aiki, jennife ma ta fitoh zata makaranta ita da sarah tana sanye da uniform a jikinta, Abraham ne karshen fita, yana fitowa wajen da Nnenna ke zaune ya nufa zama yayi a bakin barandan kamar yanda tayi, beauty kin tashi lafiya Am sorry da abinda na miki daren jiya?

Kala batace masa ba sai mikewa da tayi tana shanya kaya a igiya, shima mikewar yayi sai magana yake mata yana binta Amma taki kulasa, peace dake tsaye tun d'azun a bakin falo sai binsu take da mumunan kallo especially ma Nnenna, tsaki taja da karfi wanda ya jawo hankalin su duka harda Abraham.

Amma baice kome ba ya juya ya shiga motar sa yaja yabar gidan, itama wanki ta cigaba dayi sai kusan 12:00 ta gama sauran omon ta wanke kayanta kala biyu da sukayi datti daman kayan kala hudu ne, uku shayibu ya sai mata da wanda ta shigo gari dashi.

Cikin gidan ta nufa a gajiye direct ta wuce kitchen don yunwa take ji sosai, peace ce tsaye tana had'a lunch, koh kallon Nnenna batayi ba itama bata wani damu ba ganin kula a rufe yasata nufar wajen ta bude farfesun kazane, rufewa tayi da sauri ta bude d'aya kwanon taga taliya ne, rufewa kawai tayi ta had'awa kanta tie a kofi sai kulenta data ibawa naman kazan kadan a kwano, ta fita a kitchen in bata damu da tsakin da peace ke bugawa ba.


Tana shiga d'akin ta ajewa kulen abincin sa itama ta kama shan shayin ta, turo kofar akayi koh excuse babu, d'aga kanta tayi ganin Abraham ne yasata maida kan kasa taci gaba da abinda take.

Shigowa yayi ya zauna a kujeran mirrow hannun sa rike da laidodin kaya, hiii baby yace yana murmushi.

Nuna masa kofa Nnenna tayi da hannu.

Da mamaki yace korina kike Nnenna?

"No fita zakayi don baka nemi excuse nawa ba ka shigo"


Amma ai naga gidan mune koh?

"Na sani koh d'akin momy ne ya dace a nemi excuse "

Ba musu ya mike ya koma bakin kofar ya nemi Izini ta basa kafun ya shigo, direct bakin gadon yazo ya zauna kusa da ita, da sauri ta matsa gefe tana hararan sa.

Sorry yace yana d'aukar laidan ya aje kusa da ita, kallon laidan tayi tare da tambayar sa menene?

Kayane na sai miki masu kyau da kayan amfanin ku na mata?

"Bana bukata"

Saboda me?

"Nawa ya isheni"

Amma menene laifi don Brother ya sai ma sistern sa kaya?

"Toh ai kai ba brother na bane cousin ne"

Amma ai duk d'aya ne koh?

"Ba d'aya bane kowa da matsayin sa"

Nidai kiyi hakuri d'an Allah ki karba"

Kallon sa tayi sai kuma ta tuna in fa bata karba ta wata rana kaya zai gagare ta, amma bata son ta basa kofar da zai na shiga jikinta"OK thank you"tace tana d'aukar kayayyakin ta maida gefe mikewa tayi tsaye hade da ce masa zata shiga wanka.

Ba damuwa ki shiga ki fita ina jiran ki kinga ma saiki gwada kayan na gani?

Wani mummunan kallo da Nnenna ta masa baisan lokacin da ya mike ya bar dakin ba, yana fita da sauri ta bisa ta rufe kofa, laidodin ta bude kayan ta juye akan gado, tana dagawa tana dubawa jeas ne pencil kusan hudu sai t-shirts harda towel da brush da maclen ga shampoo duka, dasu turaru ka, tad'an ji dadi kad'an jera kayan tayi ciki wardrop harda vest da lagies.

Wanka ta shiga tayi brush, tana d'aure da towel ta wanke kayan da ta cire a toilet in ta fitoh dashi a boket, mai ta shafa ta sanya wando tasa vest ta d'aura riga akai, duk wanda ya ganta yasan bata saka brz ba saboda yanayin yanda kirjinta ya fitoh sosai gashin kanta dake tufke koh warware sa batayi ba saboda wahalar kimtsawa da yake bata, boket in ta d'auka cikin jin dadin shigarta na yau don bata taba saka kaya mai kyau irin na yau ba, gashi tana jinta free ba kamar kananun siket ba koh dogon riga wannan wandone har kasa, ga silifas na roba mai flower a kafarta irin na yayin nan akalla zaikai 3k.


Tana fitowa falo tayi kicibis da peace na jera kuloli a daining cikin haushi take binta da kallo itakam koh a jikinta shanya kayanta tayi a waje ta koma daki.


Da yamma lilis dady da jennifer suka dawo, aiko tana dawowa haka ta ringa masifa sai Nnenna ta cire kayan jikinta bazata saka ba saida Abraham ya mata kaca kaca kafun ta natso, sai kuma tace sai Nnenna ta tattaro kayan da ta wanke ta gogesu.

Haba jennifer muna da injin wanki menene nasa ta ta wanke sannan yanzun bazaki bari gobe ta goge ba sai kice yanzun.

Jin abinda dady ya fad'a yasa jennifer fashewa da kuka irin na sangartatun nan a take baban sa ya rikice ya fara rarrashin ta tare da baiwa Nnenna dake gefe umurnin taje ta tattaro kayan ta goge.

Mikewa tayi Abraham ya bita da kallon tausayi, taje ta tattaro shanyan dakin guga ta wuce taje ta fara goge kayan nasu daga ita sai kulenta suke zaune a ciki.


Har dare tana guga karshe ma bacci ne ya d'auke ta a dakin ba tare da ta gama gugan ba.


Washe gari ma da bautan ta tashi haka ta ringa rayuwa a gidan cikin bakin takura na Abraham da jennifer har gwara sarah sau dubu akan momy, ga dady baya cewa kome akan abinda suke mata.

Dady Ya tura ayi bincike akan Nnenna kuma ya samo cikekken bayanai akanta da abubuwan da suka faru da ita harta gudo zuwa gombe, sosai ya shiga shock karfa da gaske mayyar ce, amma bazai iyya kin riketa ba tunda shine kad'ai nata da ya rage.

Kasa fad'awa momy gaskiya yayi don yasan tabbas, zaman Nnenna bazai yuba tare dasu, sai dai ya kira Nnenna ya mata warning akan inta kuskura ya kamata da wani laifi na maita koh na illata wani zai d'auki babban mataki akanta,don nan birni ne ba kauye ba kana kashewa za'a kasheka bare suna Christian a cikin musulmai dumu dumu ta iyye bakin ta.

Kuka take tana gyada kai koh banza ya taimaka mata, tunda ya amince zai rayu da ita a karkashin sa, neman Alfarmar koma wa makaranta ta nema duk da ta sanar dashi ta gama SS 3 Waec ne batayi ba amma tana son ta cigaba da zuwa har lokacin waec yayi.

Ba musu yasa aka d'auko mata result nata a kauyen su, washe gari ya aike Abraham kasuwa ya sai mata kayan makaranta ya kai dinki,yasai mata sabon eye glass mai kyau da tsada, da sauran abubuwan da zata bukata akan zuwa Monday zasu kaita school a mata Interview duk ajin da ya dace a sata sai a sata, don su sun d'auka bata da kokari sosai.


Jennifer kamar ta wura wuta ta shiga jin Nnenna xata shiga school inda take sosai ta haukace wa momy akan ita bata yarda ba wallahi, momy ma ta nuna akan sai dai a sata a govorment school Amma Dady yace ya gama magana.


Wannan abu yama momy ciwo a karon farko dady ya bijirema bukatar ta, amma kuma tasan me zata kulla koh Nnenna ta shiga school in sai taji bata kaunar xama tare da jennifer.



************************
Lahab yau ball suka tafi tun safe bai dawo gida ba, daga ball suka je gidan su adewale da yake iyayen sa sunyi tafiya acan sukayi wanka suka saka kayan sa dukan su, suka wuce birthday party wani school mate nasu,

sai yamma lilis ya nufo gida tun daga nesa ya hango sa zaune, sai da gaban sa ya fadi sanye yake da 3quater na sojoji sai t-shirt baki, yana zaune a bakin get kan kujeran roba.

Ai da sauri yaja ya tsaya shikenan yau dai tashi ta kare, Amma yan gidan nan munafukai ne ace babu wanda zai sanar dashi uncle muzammil na zuwa yau, ya wuni a gida sai aki sanar dashi da yau ai ya kaima islamiyya ziyara.

Ji yayi kamar ya juya Amma babu hali dole tasa ya nufi get in zuciya na duka, Amma san koh nuna alamun ya gansa ma baiyi ba, ya sa hannu zai bude kofar.

Lahab!!!!!!! Muzammil ya kwala masa kira da karfin gaske.

Aiji yayi kamar an tsikare ransa da tsinke, cikin sauri yace"na'am uncle daman wallahi ban ganka bane"

Na tambaye kane lahab ka ganni koh baka ganni ba?

"Kayi hakuri don Allah uncle"

Hakurin uwar ka?ina kaje?

"Uhmmm naje lesson ne gidan su adewale"

Ina takardun?

Kallon hannunsa yayi sai da ya hadeye yawo"uncle nabar takandun a gidan su"

Gyada kai muzamminl yayi, oh watoh boko yafi Arabic kenan?

"Ah ah uncle"

Ok toh me kake nufi naga dai islamiyyar so biyu ake zuwa a sati kai kuma naga a karshen satin ma kaje lesson koh?

"dan Allah uncle kayi hakuri"?


Hakuri?meka mini ai duk abinda kayi kanka kama bani ba, ka wuce muje sallah bazaka shiga gida yanzun ba muje, yace yana nuna ma lahab hanya babu alamun wasa a fuskar sa, da sauri lahab yayi gaba muzammil na binsa a baya har bakin masallaci.

Alwala yayi suka zauna har aka kira sallah kafun yan gidan su suka fito tun daga nesa suke gulman lahab suna dariya ganinsa zaune samo samo kamar na Allah.


Ana idar da sallah suka shiga gidan da sauri lahab ya nufi kofar falo, tsawa muzammil ya daka masa, Lahab dawo nan ban sallame kaba?


Ba musu ya dawo ya tsaya a jikin motan kaman yanda yaga uncle in yayi, bude kofar motan Muxammil yayi ya shiga hade da basa umurni ya shiga.

Shiga yayi yaja motar suka nufi barin gidan, suna fita shagon aski suka nufa tunda lahab yaga anyi packing a bakin shagon yaji ransa yayi mummunan tashi ba shakka yau gashin da yake ta kashewa kudine za'a cire masa.

Fita yayi a motar yabi bayan muzammil cikin shagon, sun samu layi dole tasa suka zauna har akai isha'i, sukaje sallah a masallacin bakin shagon suka dawo kafun layi yazo kansu, nuna ma mai shagon kan lahab uncle yayi tare da ce masa ya aske kan kwalkwal a cire gemu.

Ihu lahab ya sake kamar an burma masa Allura"wallahi uncle ban yarba ba haka kawai a aske mini gashi kamar wani kafuri kwalkwal,kuma a cire mini gemu duka? ai gemun sunnah ne manzon Allah ne yace abar gemu.

Mikewa muzammil yayi lokacin da lahab ke surutun ji kawai yayi an wanke masa fuska da mari mai azaban zafi, dafe kuncin sa yayi yana mai duban uncle in nasa, da tsananin mamaki wai shi lahab har yanzun ake duka.

Kallon mai shagon yayi, aske masa kamar yanda nace, kallon uncle mai asken yayi pls oga kayi hakuri nad'an rage masa gashin sosai yayi daidai, gemun kuma a bar masa don Allah yace cikin d'ari-d'ari fahimtar da yayi ran sojane ya baci, ba tare da muzammil yayi magana ba ya basa izinin yayi hakan da hannu.

Zama Lahab yayi akan kujera har lokacin hannun sa dafe da kumatun sa, mai asken ya fara aikin sa.

Gashi mai tsawon nan duk an aske yayi daidai da kan nasa sai gyaran goshi da aka masa sosai askin ya masa kyau ba kad'an ba, muzammil dai sai kallon mai kaman harara yake masa.


Ana gama askin suka nufo gida, bayan sun tsaya uncle ya sai gasheshen kaza kusan biyar, suna isa gidan da sauri lahab ya balle marfin motar ya nufi kofar falo, kwala masa kira Muzammil yayi akan yazo ya d'auki laidan kazan ya shigar ciki, Amma lahab koh juyawa baiyi ba kuma sarai yasan uncle yasan yajisa.

Yana turo kofar falon, family ne zaune a tsakar falon ana ciye ciye harda Nazeefa matar muxammil da yaransu Tirmizi da islam, nufar kofar sashen su kawai yayi koh amsa wa matar muzammil dake masa magana baiyi ba, don daman ba shiri suke da ita ba, kamar yanda baya shiri da mijinta, dariya 'yan falon suka sake da karfi ganin kan lahab yau a aske sai gashi kad'an, don kan Rahab ma yafi nasa gashi.


Yana shiga d'akin akwatin sa ya d'auka ya aje a kasa tiles, ya fara iban kaya a wardrobe yana zubawa a ciki, don Wallahi gudu zaiyi ya koma wajen yaya jafar nasa haka kawai ya zauna wannan mugun soja ya kashesa a banza bai isa ba, don wallahi mami batace masa jika ka gani ba.

Turo kofar akayi da sauri ya soma boye kayan gudun kar wanda ya shigo yagani, amma ina kafun ma ya boye har an shigo, tsaki yayi ganin Rahab ne.

Da sauri ya karaso kusa dashi, Lahab lafiya yana ga kana had'a kaya a jaka?

Kallon biyun nasa yayi da kyau hatta magana in sunayi iri d'aya ne,"wallahi rahab bazan zauna a gidan nan ba, sai muzammil yabar sa ya wani ibo 'ya'yan sa da shegeyar matar san nan zasu zo su sani a gaba"

Yanzun lahab tafiya zakayi ka barni ni kadai kenan?

"Tafiya kam kaman nayi na gama babu uban da ya isa ya hanani"


Sai dai in bana gidan nan?sukaji magana daga bakin kofa, da sauri lahab ya sake kayan dake hannun sa ganin wanda ke tsaye a kofar ga dukan alamu ya jima a tsaye.............






✨Ruqeenjalal✨



πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€ΉπŸΏβ€β™‚οΈ *ALKAWARIN MASOYA* πŸ€ΉπŸ»β€β™€οΈ
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya Ibrahim*πŸƒ

✨Tsokaci ALKAWARIN MASOYA na kudi ne gamai bukata naira 300 ne kacal ki tuntube ni ta layin nan whatsApp only 07044407979πŸ‘Œ

Free page🀧


*EXQUISITE WRITER'S FARUM*


page2⃣3⃣&2⃣4⃣
Uncle nasu ne fuska ba walwala ya karaso tsakiyar d'akin, kallon lahab yayi da kyau, amma wallahi ka bani mamaki dom na damu da rayuwar ka kake zagar mini mata da shege ya?

Dam-dam haka yaji kirjinsa ya buga amma bai nuna ba"nifa bada kai nake ba wallahi uncle"

Kala baice masa ba illah nuni da yayiwa lahab da hannu akan ya wuce su fita a dakin, ba musu yayi gaba uncle na binsa a baya, daining zaka nufa.

Aiko daining in ya nufan yana isa ya nemi kujera yaja ya zauna hade da zuba tagumi ya kurawa waje d'aya ido.

Muneera!!! Muzammil ya kwala mata kira.

Yes uncle, tace tana mikewa ta taho wajen su da sauri ta tsaya tana kallon su.

Ki zuba masa abinci, da sauri ta d'auki plate ta zuba masa aje masa tayi a gaba shima uncle ta zuba masa nasa ta aje, shukali kawai lahab ya d'auka ya soma cin abinci duk wanda yaga fuskar sa yaga tsantsan bacin rai harda na sai dawa.

Addayiya dake zaune a falo tun d'azun sai kallon su take fuska a hade don gaskiya abin na muzammil yayi yawa taya zai sawa amanar ta a gaba haka?kuma babu halin magana.

Abinci ne dai sai da ya cinye tass, kafun ya barsa ya tashi mikewa yayi ya nufi dakin su yana shiga wanka yayi ya sanya kayan bacci zama yayi yana zullumin yanda zai bullowa lamarin uncle, take ya sake murmushi watoh yasan abinda zai kulla musu ai in sun san wata basu san wata ba.

Takardun Rahab ya d'auko yana dudubawa, sai kuma ya aje da sauri jin wayar sa na ring, d'auka yayi ya dube mai kiran nabeel ne ke kiran sa, picking yayi ya kara a kunnen sa.

"Hello nabeel"

Ta d'aya bangaren aka amsa masa, kai shegen ba nabeel bane .

Oh Adewale uban me kake da wayar nabeel kuma war haka"?

Yazo tayani kwana ne shine nace koh kaima zaka fatso mu kwana tare?

"Amma dai baka da hankali wallahi tunda nake da kai na taba yawon mangari ba"

Amma ai naga gidan mu zakazo koh?

"Toh Bazan zo ba "

Jin Amsar da lahab ya basa yasan lallai akwai matsala, guy lafiya kuwa koh file naka aka girgiza ne?

Harya bude baki zai sanar dashi muzammil yazo sai kuma yayi shuru, wallahi yanda yaji a jikinsa suma sai sunji a jikin su, shuru zaiyi Allah yasa gobe suyi gangancin xuwa gunsa suma su kwashe rabon su.

Misalin karfe 10 cif Rahab ya shigo d'akin tare da Tirmizi, kallon yaron Lahab yayi cikin zare ido yace"kai ina xaka ka shigo mana daki"?

Uncle a dakin ku zan kwana?

Ai jin amsar da tirmizi ya basa yasa sa mikewa da sauri, Allah sarki yaron na ganin haka dayake ya saba da gudu ya ruga ya nufi kofar d'akin cikin gudu ya bude kofa yafita.

Koma wa lahab yayi ya kwanta a shimfidar sa, Rahab kam

Please Login or Register in order to submit comment