Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

flat na Adewale zaune ya samesa Yana karyawa abincin gaban nasa Lahab ya Iba da yawa kana ya koma dakin Nnenna ya aje Mata yabar gidan,haka Suka cigaba da rayuwa kwata kwata Nnenna ta d'auke wuta fadan Mai ciki Bata shiga harkan Lahab abinci ma badon karta mutu da yunwa ba da bazataci ba gashi inta dafa da kanta baya Mata Dadi a Baki amma dataga uwar Bari ci take shi Kuma Bai fasa kawo Mata ba,tun tana dari dari karya sa Mata maganin zubda ciki harta cire tunanin abin a ranta amma Sam Bata yarda sun sake kwana daki d'aya ba ta tatttarasa ta watsar duk lokacin da taji sha'awa na taso Mata saidai ta shiga ruwan dumi shima Bai wani shega harkan nata iyakansa bata abinci akan kari yazo ya duba yanda ta waye gari.




*************
Wasan Lahab ya Fara gaba gaba don yanzun Yana iya barin kasan America ya tafi har wata kasa ball sai dai duk lokacin da zai tafi zai barwa Ade nauyin kula dacin Nnenna Kuma ba laifi shima Yana iya bakin kokarin sa,yau Monday Nnenna ce ta fito daga dakin ta sanye da siker da riga ta dau jakanta ta rataya a kafada sai takalmin ta flat gashinta a sake har gadon baya fitowa tayi daga part nasun ta fito compound na gidan,Lahab dake zaune a waje Yana Shan iska mikewa yayi ganinta tsaye a bakin titi.





Ina Zaki"?kauda fuska tayi ba tare da tayi magana ba,"ba magana nake Miki ba"?Nan ma shuru ta Masa ta tare taxi zata Shiga hannu yasa ya fizgota saura kad'an ta buge da marfin data bude janta yayi Suka koma ciki cikin bacin Rai yace"har zanna tambayar ki kina rainamin wayo Ina Zaki a hakan babu lullubi"kaga Lahab baison surutu da ranan Nan akan me Zan fada maka Inda zani,maganan lullubi Kuma Ni ba musulma bace"dagata yayi sama Suka koma ciki hijab karami ya d'auka ya saka Mata tare da kwace jakan budewa yayi ganin takardun asibiti ne hannunta kawai ya Kama ya rike jakan a daya hannun sa Suka fita daga gidan.




Asibiti Lahab ya wuce da ita aka Mata awo ba karamin shauki ya shiga ba lokacin da likita ke sanar dasu tagwayene a cikin Nnenna amma Bai wani nuna murna a fili ba,wayarsa ya d'auka ya d'auki hoton na'ura daya nuna yaran baro baro Suna kwance gasunan mitsitsi dasu yan 6 month's,kana ya dauketa tana zaune akan gado lokacin likita na Mata bayani ya had'a harda likitan dashi ya d'auki hoto likita sai dariya take don wallahi ita abin ma dariya ya Bata don kwata kwata Basu wuce 19year's ba a lokacin,Suna fitowa Suka samu wata Mata da miji zaune Suna jiran su fita Suma su shiga cikin matan ya girma don zaikai wata 8 sai kallonsu Mata da mijin Suke shidai Lahab baice kome ba ya Kama hannunta Suka fita, saloon ya kaita aka wanke Mata Kai da kafa ya biya duka,don lokacin cikin nata har ya fito ras dashi kowa ya ganta yaga Mai ciki ga jiki data juga Kamar me wuyanta har wani guru guru yayi na jiki ga haske Wanda Bai sani ba zai tsammaci bata had'a dangi da bakaken fata ba.







*********************
Su Lahab an kammala exam na karshen shekara Kuma na chanja aje sun samu dogon hutu na karshen shekara tunda Yan nageria sukaji kammala exam nasu suke sauraron ranan da uban gayyan zaice zasu kamo hanya,Lahab yayi kudi iya kudi yanzun Harya mallake gidan kansa a turai da mototi,sai dai har gobe Basu dawo normal da Nnenna ba lokacin da yaji bukatar matarshi ya tasashi a gaba yaje neman hakkinsa tace batasan zancen ba,shikenan shima ya ajeta a gefe yasa karatu a ga Kuma Alhamdulilah abinda ake tsammani shiya samu yau sati guda da kammala jarabawan,zaune yake a falo shida Ade Suna hiran wasan da Lahab a buga anan Ade ke kawo Masa zancen komawar su gida"gaskiya Ade kayi tafiyarka kawai wallahi Ni bazan iya zuwa Koh Ina ba"




da mamaki Ade yace saboda me"saboda bazan iya tafiya nabar Labiba da cikin 8 month's a jikinta fa,karfa ka manta dogon hutu Muka samu akallah mukai 2 to 3 months a chan nasan halinda zata Shiga bayan babu mu Ina wallahi ah ah"kaga Lahab Bai Kamata ka musu haka ba nasan kana da uzuri a gaban ka amma fa ka sani Suma Suna da hakkin akan ka,Mamu shekara guda Bata saka ka a idanunta ba haka ma Rahab tuni sun koma nageria Kai ake jira"Wai Ade da wani yare Zan maka bayani ka fahimta ne nace maka bazan iya tafiya nabar Nnenna ba"





Amma Lahab tunda Allah ya hore maka why not ka samu wata dattijuwan baturiya ta zauna ta kula maka da ita ko haihuwarce ya tashi ai akwai wata a kusa"wani banzan kallo Lahab ya Masa irin na baka da hankalin Nan"Ade taya Zan bar matata a hannu bayahudiya salon a haifamin yara biyu ta sabe daya ta gudu Koh ace sun mutu saboda da Bata da tsayaye gwara Ina Nan"shuru Ade yayi h?ar Lahab ya gama surutun sa kafun yace"toh nidai Ina kewar kasata Kuma zanje Naga iyayena"Allah ya bada sa'a babu Inda zani harsai Naga gudan jinina a doron kasa"yanzun me zakace musu a matsayin excuse naka"




Cewa zanyi Muna da wasa a France kawai"uhmmmm shine abinda Ade yace Suka cigaba da Hira Nnenna dake cikin kitchen tanajin duk abinda ke faruwa sosai taji zuciyarta tayi sanyi Jin Lahab har yanzun ya damu da lafiyar ta Koda yake ai ya damu da lafiyar ta ya bai damu da lafiyarta ba ai da ta Jima bata gidan sa,ta yarda Lahab na sonta baba Wasa ba.






Allah sarki Lahab bai sanar da gida bazai dawo ba har Saida Adewale ya koma nageria kafun ya sanar dasu sosai ran Mami ya baci tayita fada Akan wasan banza zaiki dawowa hakuri kawai ya Bata,yau tun safe lahab Suka shirya dashi da Nnenna zasu hospital cikin Nan gashinan tirim a gaba sanye take da polon wando sai riga bankacece har gwuwa Mai dogon hannu cikin Nan a gaba gyale tayi rafen nasa a kanta,ta sanya boot a kafarta,Lahab ma sanye yake da kananu kaya,motar ya bude Mata ta shiga Suka wuce hospital,Suna Isa facemask ya d'auka ya sa gudun kada mutane su Soma daukarsu hoto a watsa a duniya ya shiga uku tunda yanzun shima ya Zama popular Koh Ina ya Shiga hotuna ake masa,yauma anyi sa'a sun hadu da mutumin da suke yawan haduwa dasu in sunje asibiti awo matar sa mai ciki Amma ayau sun hadu dasu ne lokacin da suke Shirin shiga mota sai ga Matar da mijinta sai wata tsohowa da baby a hannunta daga gani haihuwa matar tayi Kuma an sallame su,Suka nufi motar su Suma ba tare da sun kula dasu Lahab ba duk da daman duk haduwar su basa magana duk da bakaken fatane sai dai su ringa kallon su Lahab shikuma kallon ke hanasa musu magana tunda barikine kowa zaman kansa yake ba irin Naija bane mutun zaice wane ya ganni Bai gaisheni ba"





Shiga Nnenna tayi Lahab ya shiga Harya tada motar bayan ya zare facemask in fuskarsa sai Kuma ya tsaya ganin motar gayen Taki tashi gashi lokaci d'aya aka Fara yayyafi fitowa sukayi daga motar zasu koma cikin hospital in,da Sauri Lahab ya fito a motarsa hade da musu sallama,da mamaki mijin ya amsa hade da basa hannu Suka sake gaisawa,kafun Lahab yace in babu damu suzo su shiga ya rage musu hanya,tsohowar taso ki amma data ga Nnenna a cikin motar saita amince suka shiga baya gabaki dayan su Lahab yaja mota.





"****************
Kamar nasan fuskar nan taka in ban manta ba Kamar Hassan Lahab Koh?"gyada Kai kawai Lahab yayi,wow gaskiya naji dadin haduwa dakai Ni Sunana Muhammad Auwal wannan iyalina ce Hauwa amma ana kiranta da jidda sai mamata gata ?"nima haka" shine abinda Lahab yace,shuru mutumin yayi ganin Kamar Lahab baison hiran,tsohowar Kam kasa hakuri tayi tace"yaro wannan Yar uwarka ce"saboda ita haka kawai taji ta Kosa Taji menene a tsakanin su tunda matar d'anta tace Mata ai Suna haduwa dasu a hospital sa'i da lokaci Suna zuwa"har Lahab ya bude Baki zaice matar sane Nnenna ta rigashi da cewa"kaninta ne"wani kallo Lahab ya Mata amma baice kome ba yaji matar na hausa da d'anta don a zatonta ko su Nnenna basajin hausa don Basu Mata Kama da Yan nageria ba Nnenna tafi Mata Kama da Yan Ethiopia harda Lahab in ma duk da bakine amma kyakkyawa ne sosai,gulmansu ita da matar suka Fara tana cewa ai wallahi itama Saida tayi tunanin Koh Yan uwane amma meyasa kullum Lahab ke rakota,da Sauri mijin yace"gaskiya mama ya Kamata kuyi shuru babu Dadi Kuma cikin mutane kuma yare zasu tsargu bare Kuma wa'innan da kuka jefawa tambaya.





Murmushi Lahab yayi don yasan Nnenna ba wani fahimtar hausan take ba"mata tsohowan ne tasake jefowa Nnenna tambaya tace"aiko gaskiya yayi tsawon kafa dubeshi Kamar wani yayanki amma ku Yan Ethiopia ne"?haba dan Allah mama kiyi shuru Mata"yaron ya tareta da Sauri Lahab ma juyowa yayi yadan kallesu kana yace"munata tafiya Baku fadamin address naku ba"fada Masa sukayi da mamaki yake kallonsu don kuwa gidan sane manne dana mutumin amma baice musu Suna waje daya ba don baya fatan yayi makwantaka da tsohowar Nan sarkin surutu.





Wuce kofar gidan sa Lahab yayi ya tsaya a kofar gidan mutumin bude kofar sukayi Suka fiffito mikawa tsohowar laima Lahab yayi dake cikin motar sa gudun sanyi kada ya Kama babyn,sai a lokacin ya musu barka da samun haihuwa itama Nnenna ta musu barka harda karban baby tayi ta kalla kafun ta maida musu, number Lahab mutumin ya karba Yana ta godiya kana Suka shiga ciki Lahab Kam reverse yayi ya nufi nasu gidan.




tunda cikin Nnenna ya shiga wata tara shikenan Lahab ya tattara wasan kwallo ya aje a gefe ya koma zaman gida tunda babu makaranta Suna jiran lokacin haihuwarta,yau tun safe lahab yace Nnenna ta shirya bayan sunyi breakfast shiryawa sukayi ita dashi Suka fito zasu fita sayyayyan kayan yara da zasu sayo yayi-yayi ta Masa list yaje shi kadai tace shida baya kaunar yaran yake ba tasan bazai sayo Abu Mai kyau ba,lokacin da Suka fito compound ganin da gaske zata bisan yasa da tsayawa yace"Amma so kike kije ki haihu a hanyane Koh"ai Dr yace saura 2 weeks"da dariya yace waike kin amince da maganar Dr Koh yau in Allah ya nufa Zaki haihu"da masifa tace koma me zakace kace sai make"abinka da gidan turawa na wancan gidan na kallon na wannan kawai cikin magana sukaji an kwala Masa Kira Yana juyawa da mamaki ba kowa bane sai tsohowar Nan tsaye a baranda tana murmushi tare da tafa hanneye daga nesa yaji muryarta Kamar Ansa lasfika tsabar karfi tana cewa"daman Nan ne gidan ku D'an ball ban sani ba ai dana ringa shigowa na huta da zaman kadaici, Kanna kowa saina ringa zuwa wajen mamanka...............................








*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*





Murmushi yake Lahab yayi Aiko da Sauri Mata Kam ta zagayo daga cikin gidan su zuwa nasu Lahab tana washe baki, tace"Ina zakuje ne Koh asibiti ne"?Ah ah mama zamuje sayyayyan kayan babies ne"Nnenna ta Bata amsa Kama Baki tayi tace yanzun da cikin Nan Zaki fita wani sayayya ai saidai kuzo na rakaku muje ki zauna Ina zabar Miki"Lahab baiso ba Amma ba yanda ya iya haka matar Nan ta bisu tafiya suke sai surutu tane musu Kamar me Suna Isa mall Nnenna ta nemi waje ta zauna tsohowa da Lahab ne Suka Soma jidon Kaya"mama kayan tagwaye Zaki d'auka kome bibbiyu ganin ta Soma zaban suturan sawa"toh tace ta Soma d'aukan na jarirai biyu amma kayan da mace Koh namiji zai iya sawa shopping Lahab yayi sosai kama daga gadon yara kayan su bargo set na feeder duk abinda jarirai zasu bukata sai da Lahab Suka saya ya kashe kudi kusan million daya a kayan yara kad'ai sai Yan suturu daya sayawa Nnenna kala goma tsohowar ma ya sai Mata kayan yara yace ta kaima jikokinta inta koma nageria Aiko taji Dadi ainun sosai, yawo sukayi bana Wasa ba,sai kusan yamma ligis Suka kamo hanyar gida.





Mama na baya Nnenna na gaba da Lahab tunda Suka nufo layin Suka hango Yan Sanda a tsaye Suna magana da Muhammad da matarsa duk Suna waje da gani dai a cikin tashin hankali suke tunda motar ta nufi kofar gidan su suke binsu da kallo,bama Kamar lokacin da mama ta bude kofar da Sauri Muhammad ya nufeta Yana tambayar ta"mama Ina Kika shiga kinsa hankalin mu ya tashi haba mama dan Allah Nan fa ba nageria bane,fitowa Lahab yayi ganin yanda ran Muhammad ya baci sosai don mama kam bude boot na motarsu tayi tadau laidan da Lahab ya sayo Mata tana Masa godiya tayi cikin gidan tabar su tsaye a waje.







Hakuri Lahab ya baiwa Muhammad tare da fad'a Masa dalilin da yasa ta bisu,sai anan Muhammad ya sake ransa tare da cewa babu kome yasan halin mama sarai,sallaman yan Sanda yayi tunda anga Wanda ake nema,cikin gida Lahab ya shiga, Nnenna daker take taka kasa ta fito a motar kafafunta sunyi mugun kumbura Kamar me,takawa take a hankali harta shiga falon,kayan Lahab ya ringa daukowa one by one Yana ajewa yaje ya dawo Saida ya kwashesu tas kana ya rufe motar ya shigo gidan,har lokacin Nnenna na zaune a falo Bata tashi ba,dakinsa ya Shiga yayi wanka tare da daura Alwala yayi sallan mangariba,ya fito a dakin har lokacin tana zaune a falo sai had'a zufa take,matsowa yayi kusa da ita Yana tambayar ta lafiya"kafafuna kemin ciwo ga kirjina nauyi"toh ba Dole ya Miki nauyi ba Labiba Saida na hanaki fita Amma saboda tsabar taurin kai Saida Kika fita"ita dai batace kome ba hannu yasa ya zame wandon jikinta yajashi kasa cire Mata wandon yayi ya rage daga Ita sai polon riga don ta riga ta cire gyalen,takalmin kafarta ya cire ya zare socks duka,dukawa yayi ya d'auketa.





Ajeta yayi a bathroom ya had'a Mata ruwa wanka kana ya zare rigan nata da under wear itama Bata Masa musu ba don jikin nata gabaki d'aya batajinsa normal,rigan jikinsa ya zare ya rage daga shi sai dogon wando wanka ya Soma Mata,yana gamawa ya daura Mata towel kana ya ajeta,ruwan zafi ya had'a a baf ya dauko kafar yasa a ciki Yana dannawa,sosai ya dumama kafan kafun ya d'auketa sai cikin daki,ajeta yayi a Kan gado yadau pillow babba ya daura kafarta akan cream ya d'auka Yana shafa Mata Koh zataji saukin kafan,duk abinda yake matan Nan basu Koh ga maciji shurune kawai Kamar wasu kurmaye.





Mikewa yayi ya dauko kayan baccinta dogon riga saka Mata yayi kana ya kwantar da ita ya sanya mata socks na bacci,ya tashi zai fita a dakin hannu tasa ta Kama nasa amma batayi magana ba sai Kuma tace"idan abinci zaka sayo ka Bari kawai a koshe nake banajin yunwa"zame hannunsa yayi yace"na sani inna kawo kada kici"yasa Kai ya fita a dakin.






Yana fita falo ya waro Ido ganin tsohowar Nan dake falo ta wani rungume kuloli a hannu,dan kallon sa tayi sai Kuma tace"Dan ball Aina Jima a falon Nan naku nayita sallama shuru shine nace taima sallah kuke Bari na jiraku,Lahab Kam d'an kunya yaji ganin babu riga a jikinsa da Sauri ya bude kofar dakin sa ya Shiga riga ya d'auka ya dawo falon Zama yayi Yana gaidata amsawa tayi kana ta aje kulan hade da cewa"wannan abincin garin mune,tuwon masara miyan lawashi da kifi harda gyada kasan lokacin da akace min hauwa'u zata haihu duk Saida na tanadi abincin masu jego na tawo dashi,shine nace Bari na zubawa yayarka mema sunan ta"?dafe Kai Lahab yayi yace"Labiba"Labiba Kuma sunane wani irin sunane haka Ina ma laifin a karasa da Habiban ta ai yafi"mikewa yayi yadau kulan kana yace Mata sun gode sai Kuma ya juya zai bar falon.




Am nace ba Ina mamar taku Ina Mai cikin"mama duk Suna bacci ne"bacci Kuma haka da isha'innan Koda yake nasani Koh Yan gayune ku"shuru yayi Yana cigaba da tafiya da abincin yasa hannu zai bude kofar dakin daidai lokacin Nnenna ma ta bude kofar zata fito Jin surutai kad'an kad'an a falo"lai kin tashi"mama tace cikin farin ciki karasowa falon Nnenna tayi tazo ta zauna a kasan carfet da Sauri mama tadau pillown kujera tana cewa maza ta tashi tasa Mata bakyau tana Zama dabas haka a kasa.





Shidai Lahab na tsaya da kula a hannu Nnenna nata Hira da mama mikewa mama tayi ta nufesa hannu tasa ta kwace kulan tazo ta aje a gaban Nnenna babu tambaya ta nufi kitchen Wai zata dauko plates,kallon Nnenna yayi yace"kiyi taka tsamtsam da wannan Mata kinji na fadamiki"shuru ta masa har mama ta dawo Iba Mata tuwon tayi da Miya Nnenna Kam sosai ta zage tayita cin abinta Suna Hira rabonta dacin irin wanann abinci ai anfi shekara.




Lahab na daki a kwance Yana Jin surutansu a falo,har kusan 10 na dare mama Bata koma ba,ya zubawa sarautan Allah ido yaga iya gudun ruwan su, knocking na kofa yaji akayi,da Sauri ya mike ya fito falon kallon mama yayi Wance ta kwanta akan kujera harda filo ana ta Hira,bude kofar yayi Muhammad Ne nan dai Muhammad ya tasata a gaba suka bar gidan duk da ranta baiso ba,washe gari da safe lahab na gida da gangan ya sawa kofarsu key gudun kada mama ta sake dawowa,da misalin karfe uku na yamma ya tafi airport dauko Ade.







Da dare zaune suke dukan su a falo ana hiran yaushe gamo anan Ade ke Basu labarin nageria jakansa daya shigo falonsu dashi ya jawo budewa yayi ya dauko laida babba Bakin laidan ya bude ya fito da maganin kulli kulli Yana cewa"ga wannan gogojice ta ban Wai inji malam Nnenna tana Sha a shayi Koh kunu sai Kuma wannan yace na wankan Kane wa'innan Kuma yace Wai in ta haihu a baiwa yaran susha kafun a Fara Basu nono,a had'a musu da ruwan zamzam"da mamaki Lahab yace"ya akai malam yasan tana da cikine Wai"wallahu alamu shine abinda Ade yace sai Kuma ya dauko wani laidan yace gashi inji mubeena abaka"dariya Lahab yayi yace lallai big Aunty gabaki d'aya na manta da ita wallahi Amma yanzun tayi aure koh"girgiza Kai Ade yayi yace batayi ba.





"Toh ya maganar soyayyar ku"kaima dai Lahab Wasa kake Koh aini inaga na hakura kawai wannan karon ma wulakanci na Tara Saida nazo Mata bankwana na samu fuskar da tacemin na kawo maka sako"bude letter Lahab yayi gaisuwa ne sai Kuma number ta data aje Masa a karshe tare da fatan Alkhari, murmushi kawai yayi lokacin da ya Gama karantawa Yana dago Kai sukayi Ido hudu da Nnenna dake hararansa da Ido Kamar zasu bullokuto waje mikewa tayi cakal cakal irin saurin masu cikin Nan ta nufi daki"







Kallon juna kawai Ade sukayi sai Kuma Lahab yadau laidan maganin ya bita cikin daki,zaune ya sameta ta had'a gabas da yamma Zama yayi a bakin gadon da mamaki yake tambayar ta meya Bata mata rai"tura hannunsa tayi a jikinta ta kwanta hade dajan bargo Bata Kara magana ba,aje magangunan yayi ya fita a dakin,da misalin tagwas na dare Nnenna mikewa tayi Jin Karan bude kofar da rufewa fita tayi a dakin Lahab directly ta wuce budewa tayi ta Shiga sannan ta shiga dube duben abinda take nema da Sauri ta dau lettern dake Kan gadon ta warware kana ta Soma karantawa,cikin haushi ta yayyaga paper tana Jan tsaki,daga Ido da zatayi sukayi four eyes da Lahab dake tsaye harde da hannu.




"Meyasa Kika yaga"shuru tayi Bata ce kome ba"meyasa Kika shigomin daki Ina mun riga mun raba daki bake bane?"Nan ma shuru ta Masa"nuna Mata kofa yayi"fita"a hankali ta Soma takawa sai Kuma ta fashe da kuka tana dafa bango da Sauri ya matso gareta Yana tambayar ta lafiya kasa amsa Masa tayi sai kokarin dukawa da tayi,da Sauri ya tallafota akan cinyarsa Suka zauna,yamutsa fuska ta somayi tana Dan juya Kai a hankali hankali tashe yake cewa meke damunta Amma shuru babu amsa sai lip nata na Kasa data Kama da karfi tana taunasu,mikewa yayi ganin jini ya biyo sahunta da Sauri ya Soma sanati hade da ciccibarta suka fito daga flat nasu da Sauri ta bude motar ya sata tare da zagayowa ya shiga yaja da karfi tunkan ya Isa hospital in ya Kirasu akan Suna zuwa ya sake kiran Ade ya sanar dashi,Suna Isa hospital aka shiga da ita labour room,iya wahala Nnenna Tasha Amma haihuwa shuru Kamar zata mutu tace a Kira Mata mijinta ya yafeta karta mutu Yana Jin haushinta, lokacin da Lahab ya shigo dakin kuka kawai ya Soma Nnenna na kuka tanacewa ya yafe Mata mutuwa kawai zatayi,shi Kuma sai cewa yake bazata mutu ba.




Dr cewa yayi Lahab yasa hannu za'a Mata operation,saboda kasa haihuwa da tayi da kanta ga karfinta ya Kare,hannun Lahab na rawa yayi sign cikin fargaba sai Addu'a yake Allah ya sauketa lafiya,fitowa yayi a dakin Yana hawaye da Sauri Ade dake zaune a waje tuntuni ya mike zuwa yayi ya Fara basa Baki akan yayi hakuri,insha Allah zata sauka lafiya ya Mata Addu'a shitafi bukata.








Zaune suke gabaki dayan su hankalin su a tashe yake cikin damuwa, fitowa nurse tayi ta ce Lahab ya shigo,mikewa yayi yabita har dakin da aka kwantar da babies in tunda yasa hannu ya daukesu kuka kawai ya fashe dashi ya mannasu a kirjinsa mace ne Dana miji aka Haifa yara farare tass Kamar mahaifiyarsa,Saidai fuskar sak na ubansu ne,kuka yake hawaye shabe shabe dagasa nurse in tayi tana cewa kukan ya Isa haka yaran sa kyawawane don ita Bata taba ganin Miji ya kawo matarsa Yana kuka haka ba sai yau tunda daman sun riga Sunsan Lahab da Nnenna yanzun basa mamakin auren nasu,,kiss ya manna musu a kumatun kana ya kalli nurse in"Ya jikin nata?sunkuyar da Kai tayi sai Kuma tace am sorry ka kwantar da hankalin ka muna iya bakin kokarin mu Amma jininta ya tsinke yanzun ma jini ake sa Mata jini na zuba a jikinta sosai ka Mata Addu'a zataji sauki amma maganan operation anyi nasara sai na tsayuwar jini,zaro Ido Lahab yayi yace"tsinkewar jin.......???? Bai karasa ba yaga nurse tasa hannu ta amshi yaran hannun sa tana Kiran Jesus ganin numfashin yara na sarkewa akai akai dukan su biyu................................................









*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*



Salati Lahab ya sake da karfi itama nurse hankali tashe ta kwantar da yaran tare da Kiran likita da telephone Inda ke manne a dakin Koh minutes biyu ba'a Yi ba saiga Dr ya shigo harda gudun sa Suka Soma bawa yaran taimakon gaggawa oxygen Suka saka musu a hanci har lokacin numfashin su Bai daidaita yanda ake so ba,Allah sarki d'a Mai dadi Lahab Bai tabajin yanason wani Abu farar d'aya Kamar yanda yaji wani irin kaunar yaran Nan ba, hankalin sa sosai ya tashi Wanda yasa likitoti koransa waje,Ade Karan kansa ya shiga tashin hankali bare da Lahab ya shiga dakin da Nnenna ke ciki yaga yanda ta jirkita laidan jinine hannu biyu aka saka Mata tsaban irin zuba da jini keyi a jikinta"






Kamar an mintsine sa da gudu ya fita a hospital in gida ya koma ya Soma neme nemen maganin da Ade ya kawo Masa saban tashin hankali daker ya gane maganin fitowar sa kenan a gida zai Shiga mota saiga Muhammad anan Suka gaisa yake sanar dashi d'azun mama tayita zuwa gidan su a rufe lafiya Kam,a damuwan ce lahab yake cewa haihuwa Nnenna tayi tana hospital babu wani kawaici Muhammad yabi Lahab hospital lokacin da ya tsinkawo lamarin sosai ya tausaya wa Lahab don shi Karan kansa yasan tashin hankali daya Shiga lokacin haihuwar matarshi,bare Lahab da aka ma Matarsa tiyata ga tsinkewar jini ga yara babu lafiya Kuma sosai yasha mamakin kasancewar su couple Bai taba tsammanin hakan ba.





D'akin matar sa ya Fara Shiga lokacin ta fita ma a hayyacinta

Please Login or Register in order to submit comment