Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har kashin cinya kike tumurmusawa,dan Allah kici Naman dake gefen plate in kibar kasusuwan Nan in Naman ya Kare Zan sayo Miki wani amma ace mutun ya aje nama ya kamacin kashi salon wani ya shigo muji kuny..................bai karasa ba aka bude kofar dakin da Sauri Nnenna ta sake kashin hade da boye plate in gudun Kar aga taunannun kasusuwan data aje a ciki.




Dariya kawai Dr tayi ta karaso cikin dakin,hade da turo kujera d'aya ta zauna kusa da Lahab kana ta kalli Nnenna ta kalli Lahab tace"Kamar u look familiar"dan murmushi yayi yace"Hassan Lahab the footballer"?oh oh really great footballer nice to meet,am Dr jeme John by name"hannu lahab ya Bata sukayi musabaha, don tsohowace ba yarinya ba,had'a fuska Nnenna tayi amma batace kome ba kallon ta again Dr tayi tace"gaskiya ya Kamata ki fito da abinki kici gaba daci,ba kunya ta dauko plate nata taci gaba dacin Naman Amma Bata tauna Kashi, kana tacewa Lahab wacec ita Nnenna a wajen sa"?





dan shuru yayi sai Kuma ya cije yace matarsa ce, waro Ido baturiyar tayi ya nuna Nnenna yace matar ka?gyada Mata Kai yayi, shuru tayi don ita duk zatonta Koh yar'uwa Koh friend ne Koh girlfriend,tunda taga irin kyau da Nnenna kedashi gashi zaman turai ya karbeta sosai tayi fresh da ita sai Kuma ta d'aga kafada kana tace,ok anyway congratulations ur wife is pregnant.



Ji kake karaaararam plate na nama ya Fadi a hannun Nnenna saiga hawaye Shar mikewa tsaye Lahab yayi da karfi yace"what?...........................






.






*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*




Cike da damuwa ya Kara Kiran Adewale amma sai ya danna Masa user busy,baiyi zuciya ba ya tura Masa message dan Allah ya d'auki wayar sa daker dai ya samu Adewale ya dau wayar sannan ya amince zaije ya dubo Nnenna amma daga wannan kada ya sake sakasa a shirgen Nnenna babu ruwan sa,katse wayar Lahab yayi Yana hamdala sannan ya koma cikin dakin har lokacin Rahab na zaune yana jiran sa,yana fitowa ya Mika Masa hannu wayan nasa ya basa sannan ya maida ruwan jikin sa ya kwanta.



da daddare Koh abinci Lahab ya kasa ci sai tsumayen Kiran Adewale yake amma shuru sai kusan 8 na dare Adewale ya Kira Rahab Rahab ya kawo Masa wayar amsa yayi da Sauri ya tashi Kamar d'azun ya shiga ban dakin Kara wayar yayi a kunne ya Soma mita sai yanzun Adewale zai kirasa tun d'azun Yana zaune Yana tsumayen Kiran nasa amma shuru"?yanzun zaka tsaya na fada maka abinda na ganone Koh zaka tsaya min mita na kashe wayata"?da Sauri Lahab yace toh kayi hakuri fadamin inji meya faru"?




Ajiyar zuciya Ade yayi yace ka duba WhatsApp na tura maka hoton ta kaga halinda naje na sameta a ciki zuciyar Lahab Saida ta buga cikin tsoro yace meya sametan,baidai basa amsa ba kawai ya katse wayar,jikinsa har rawa yake ya bude data ya shiga WhatsApp zubewa yayi a kasa ya zauna tabas saban shock Nnenna ya gani kwance Kamar gawa Ido a rufe jikinta gabaki d'aya ya sauya daga fari zuwa yellow sosai ga bakinta yayi jajer dashi rabin fuskarta har wajen wuyanta jijjiyoyine bakekkerin Suka fito rudu-rude jikinsa ne ya cigaba da rawa ya fita da Sauri wayar Ade ya Kira Yana d'auka ya Soma Masa magana"Adewale mutuwa tayi ne meya sameta"kaga Lahab karka sa kanka a matsala nidai goggoji tacemin yau kwana biyu kenan da Fara ciwon Nan nata sun tsorata ainun don numfashin tane kawai zai tabbatar maka tana da rai"innalilahi wa'inna'ilahu raji'un kawai Lahab yace ya katse wayar da gudu ya fito daga ban dakin wardrobe ya bude ya fito da kayansa sakawa yayi ya zaro takalmi zai sa yaga Rahab ya shigo da mamaki yace"Lahab sai Ina zaka a haka Kuma"?




"da Sauri Lahab yace fita zanyi"fita fa kace wani irin fita kake nufi Koh ka manta ne baka da daman fita a gidan Nan yanzun"da Sauri shima Lahab yace Ina da Kai Koh ka manta ne dan Allah Rahab kaje ka kwanta a matsayi na Ni Kuma na fita a madaden ka ka taimaka min wallahi akwai babban matsala"wani kallon tuhuma Rahab ya Masa sannan yace wani irin matsala kenan?



Nidai ka taimaka min kin taimaka Masa Rahab yayi daker ya samu ya shawo kansa kafun ya amince kwanciya yayi akan katifar Lahab yayin da Lahab Kuma yasa Kai yabar dakin Yana zuwa compound na gidan nasu security Suka tashi shiga mota yayi Suma Suka shiga aka jasu suka Soma tafiya gidan ya jafar Lahab yace a kaisa Suna Isa yace su tsaya a kofar gidan basai sun Shiga ba bude kofar yayi ya shiga gidan da Sauri ya nufi falo gashi yammane Kuma goshin mangari ba falon ya bude da sauri ya Shiga babu kowa sashen su Majid ya nufa Yana bude kofar yaga babu kowa Kamar falo sai kida dake tashi a dakin Majid bude dakin yayi da Sauri Majid ya juyo ya kallesa sai Kuma ya juya yaci gaba da rawansa.



Xama Lahab yayi a hankali yasa hannu ya kashe mp in a kufule Majid yace"kaga Rahab banson surutu tashi kabar min daki da Allah"Majid Lahab ne"zaro Ido majid yayi yace kana nufin kaida aka sawa Mari Kaine ka fito"?nidai ba wannan ba taimakona zakayi security na kofar gida so nake ka taimaka nabar gidan Nan ba tare da sun sani ba"kallon sa Majid yayi da mamaki yace"so kake nayi fiffige da Kai mu tashi ta samane Koh yaya Ni ta Ina Zan iya fiddakai"?




"Shuru Lahab yayi sai Kuma yace back door ka taimaka min"d'an dakata Lahab nifa karkazo ka sani a matsala munddin aka nemeka aka rasa Ni za'a zarga karka kiramin ruwa babu ruwana wallahi"dan Allah Majid ka taimaka min Dan Allah nace fa"dan shuru yayi sai Kuma yace Ina zuwa fita yayi a dakin Bai Jima ba sai gashi ya dawo da key yana cewa Lahab ya bari a Shiga sallan mangariba.




Ana shiga sallan mangariba backdoor Lahab ya nufa da Majid bude Masa yayi ya fita harda waya Lahab ya karba a wajen sa Yana barin layin Adewale ya Kira akan ya fito gida Yana bayan GRA,Bai wani Jima ba saiga Adewale daga Nan gidan su goggoji Suka nufa da yake darene babu Wanda ya gane Lahab Shiga gidan sukayi har dakin da Nnenna ke kwance abin tausayi gabaki d'aya kammanin ta sun sauya ta chanja hannu Lahab yasa ya bude kwayar idanunta Saida ya koma baya da Sauri saboda yanda jini ya taru a idanun tim goggoji ya tambaya garin Yaya ta Soma ciwon"wallahi Lahab kwana uku batacin abinci a kwana na hudun ne na matsa Mata akan saita d'anci abinda na kawo daga gidan ku daga saka abinci a Baki Koh hadeyewa bata gama yiba Naga ta damke makogoronta tana amai harda jini a ciki shikenan ta yanke jiki ta Fadi Ido ya rufu har yanzun bata budewa kwana biyu kenan.


Mikewa yayi da Sauri ya nufi kofar gidan Keke napep ya tare sannan ya dawo gidan da Sauri ya ciccibi Nnenna da jikinta ya bushe ta sandare,da Sauri Ade dasu goggo Suka Soma tambayar sa lafiya Ina zaije da ita gudun kada a ganeta a Kamata,kala baice ba yayi kofar gidan da Sauri Ade da goggoji Suka Shiga keken Suma aka bar faruq a kofar gida a tsaye,wani private hospital na kudi Lahab ya kwatantawa Mai keken directly Suka karasawa asibitin ya d'auketa sai ciki ganin halinda take ciki yasa likitoti rufuwa a kanta.




da misalin karfe 12:30am na dare Lahab da goggoji ne a asibitin don Ade tun 9 na dare papa ya kirasa yanata masifa akan ya dawo gida,likitane ya Kira su vayan sun shiga office nasa ya Soma musu tambaya Koh akwai abinda ke damun tane daya shafi iska-iska girgiza Kai goggoji tayi shidai Lahab shuru kawai yayi Yana Jin abinda Dr ke cewa Wai Basu gane Kan cutar ba sun saka Mata ruwa ma ruwan baya gudu haka Allurar ma sun saka amma ruwan yaki shiga a jikinta,su d'auketa kawai jinyan Nan bana asibiti bane,mikewa Lahab yayi da gudu yayi dakin da aka kwantar da ita Yana zuwa kuka kawai ya fashe dashi ya zauna a bakin gadon hade da kamo hannun ta Yana hawaye.



Goggoji ce ta turo kofar ta shigo ta zauna akan kujeran tana kallon Lahab sai Kuma tace"Lahab yarinyar Nan ta Fara bani tsoro gaskiya mezai Hana ta koma wajen danginta kaga halinda take ciki fa"hawaye ya share sanann yace"gaskiya goggoji bazan iya barinta a halinda take ciki ba gaskiya tunda yace abar musu hospital nasu da safe sai mu kaita wani"?



Kaga Lahab Kai suspect ne haka ma ita nasan dai ba kowa bane zai gane Nnenna tunda ita gabaki d'aya jijiyoyin fuskarta sun sauya Mata kamanni bai Kamata ana ganinka haka barkatai ha bugu da Kari Kuma halinda yarinyar Nan take ciki bana asibiti bane gobe in Allah ya kaimu sai muje nida faruqu kauyen mu akwai wani babban malami acan gaba da kauyen, insha Allah koma menene zai kawo karshen sa,d'an shuru Lahab yayi sannan yace"muje dai tare goggoji shi faruq ya zauna a gida bai Kamata na bar Miki d'awainiya haka ke kad'ai ba"




amma Lahab baka gani akwai damuwa na barin gari yanda tsaro yayi yawa a kankan Nan"?karkiji kome goggoji Allah ya kaimu goben"ameen ta amsa,washe gari tun asuba Lahab Suka bar cikin gombe Kuma cikin hukuncin ubangiji Basu samu wani matsala a tafiyar tasu ba,haka zalika baibi takan Kiran da Majid keta danna Masa ba sosai suke ta shiga cikin kauyuka wasu kauyukan ma da machine suka shigesa kafun su Isa kauyen da zasu Saida Suka hau kuran shanu kafun Suka iso wani rugan Fulani.



Zaune suke a gaban wani dattijo ne babba sosai tsohone ga farin gemun shi,Lahab da goggoji ne a gabansa a cikin bukkan sai Nnenna da aka shimfidar akan wani taburman kaba,magana ya Fara a hankali cikin nutsuwa yace"Alhamdulilah Ramatu naji dadi matuka da yanda Kika taimake wannan baiwar Allah Nan ba tare da kinsan wacece ita ba haka zalika Kai Lahab kayi matukar kokari Allah ya saka maka sannan ya kalli goggoji yanzun Ramatu inaso ki sanar dani menene ya faru da ita Koh Kuma me tayi ta Soma ciwon"a hankali goggoji ta rusuna tace abinci kawai na takura Mata taci"wani irine abincin"?shinkafa ne da Miya"a nutse yace dakwai nama a ciki"?gyada Kai tayi ganin haka yasa Lahab saurin cewa ai batacin nama"da mamaki goggoji tace Koh shiyasa Inna Bata abinci Mai nama sai takici amma Bata taba fadamin ba ranan ma nina matsamata taci bata gama hadewa ba abin ya faru.




Mikewa tsohon yayi ya nufi Kan Nnenna masowa yayi sosai yasa hannu ya bude kofar idanunta"sai Kuma ya girgiza Kai tare da d'auko wani magani ya bude xamxam ya juye a ciki ya zuba magani Addu'a yayi sosai ya tofa sannan ya Kira goggoji taxo ta Kamata ya bude bakinta ya Soma zuba Mata maganin tana Sha wasu na zuba sai kawai sukaga ta zabura ta Mike ta Soma aman jini babu gaggautawa harda guda-guda sai Nishi take amai tayi bana Wasa ba,har lokacin idanunta a rufe komawa tayi ta kwanta shi Kuma ya mike ya d'auko magani ya kwaba da man shanu yace ta shafa Mata aduk Inda jijiyar ya fito,Dole tasa Lahab ya fita waje shida dattijon don jijjiyar daga fuskarta ya gangara har wuyanta har Kan kirjinta na hagu ya sauka har kafarta na hagu,fita sukayi goggoji ta gama shafa mata kafun Suka dawo gaushi aka kawo a kasko ya zuba magani a ciki maganin na turnuke dakin Nnenna ta Mike tana wani irin ihu da surutai da Sauri goggoji ta Fadi kasancewar tana da marabai,ya aike Lahab ya Kira wasu sukazo Suka fita da ita shi Kuma ya cigaba da fama da Nnenna Harya samu ta natsu sannan ta koma ta kwanta Lahab kam na bare a waje duk abin duniya ya damesa ya kasa nutsuwa yasan war haka ana neman sa.





***************
Bayan sati d'aya Alhamdulilah jikin Nnenna yayi sauki sosai amma har yau Bata dawo hayyacinta ba gashi idanun nata yadan washe daga jini-jinin zuwa fari tass amma Bata tashi ba jinya dai ake Mata sosai goggoji ta koma cikin gombe tabar Lahab a kauyen su,duk sati faruq na zuwa ya dubasa sannn Yana kawo Masa labarin irin Neman sa da ake Kamar me,dayake garin babu Network Sam tsawon sati d'aya kenan isheshen bacci Lahab baya samu sosai,zaune yake a kusa da ita hannunsa d'auke da kwaryar no-no Wanda aka dama da magani,iba take a ludayi Yana sanya Mata a baki a hankali in Kuma ya gangaro sai ya dau tsumman gefensa ya goge mata Inda ya gangaran a haka ya samu tadan sha kad'an,sai Kuma yaga ta Soma tari sosai tana kwarewa mikewa yayi ya dagata zaune ya jinginar da ita take ta Soma kwarara amai sosai take aman bakikkirin, kaman bakin Mai sosai tayi aman duk ta bata jikinta ta bata Masa jiki babu kyankyami ya Kamata harta gama kafun a hankali ya maidata kwance ya mike yadau babban tsumma ya goge wajen ruwa ya ibo ya wanke abinda ta batan ya Shanya ya had'a da kayan jikinsa ya wanke kayan jikinta matar malam ne tazo ta canja Mata don malam yace haka zatayi tayi ta aman har sai ta dawo aman abinda tasha wato in tasha no-no tayi aman nono.






A kallah Lahab yakai wata yanzun a kauyen Suna jinyar Nnenna Kamar kullum Yana zaune kusa da ita Qur'an ne a hannun sa Yana karanta mata,Kamar a mafarki yaga tana dan motsa hannunta Bai wani yi mamaki ba tunda dai ta Saba motse kawai dai Bata hayyacinta ne,sai Kuma yaga tana d'an bubbude idanunta harta budesu tar a hankali ta Soma magana Wanda yasa Lahab rufe Qur'an in ya matso kusa da kunnen ta Yana sauraron abinda take cewa Jin yanda take Kiran sunansa yasa sa damko hannunta jikinsa har rawa yake yake ce Mata"Nnenna ki kalleni ganinan kusa dake kinji Labiba"?





Hawaye ne ya Soma bin kumatunta da Sauri tasa hannu ta daura a jikinsa tare da jingina a kafadunsa tana kuka take cewa Lahab bata gani ya Bata glass nata da Sauri ya mike tsaye Jin tace bata gani kuka ta fashe dashi itama ta Mike tsaye tana lulubar hannnun sa kamo hannun nata yayi da Sauri ta damke hannun har tana kokarin faduwa na rashin kuzari,kamota yayi Yana cewa ta koma ta zauna amma Ina tace karya tafi ya Barta Dan Allah karya sake barinta"shigowa malam yayi sai Kuma ya tsaya Yana kallon su kauda fuska yayi yace Lahab ya zauna,Zama Lahab yayi itama ta zauna tana rike Masa hannu sai Kuma tambayar da ta jefo Masa"Lahab inane muke waya shigo dakin Nan? bana kallo Lahab bana kallo fa?Ina goggoji ta Miki min glass nawa.




Ki natsu shine amsar da malam ya Bata natsuwar tayi Lahab yadau wulan Fulani dake gefe ya aza Mata akai don gabaki d'aya gashin nata duk sun wargaje sunyi datti,kallon ta malamin yayi babu Wasa a fuskar sa yace"Zan tambaye ki Kuma Ina so ki ban amsa babu karya a ciki abinda Zaki cemin"jikinta har wani rawa take tasa hannu ta rike rigan Lahab da karfi ta gyada Masa Kai"ganin yanda ta rikice yasa Lahab sa hannu ya riko hannunta Yana dan Mata magana a hankali"ki natsu Mana babu abinda zai Miki kawai tambayar ki zaiyi fa"shuru tayi tana Jin abinda malam yake fada Mata.




Koh Zaki sanar dani sunan ki"Sunana Nnenna obinna"ke wace kabila ce"a hankali tace Igbo"toh tambayar da Zan Miki yanzun shine menene halakarki da Mafi'a(secret code)"zaro Ido Lahab yayi sai Kuma yace"haba malam ya zaka..........d'aga Masa hannu malam yayi yace"karka kuskura na sake Jin bakinka a cikin tambayar da Zan Mata karka kuskura"shuru kawai Lahab yayi Nnenna Kam jikintane ya tsoma rawa a hankali ta Soma hawaye sai Kuma ta fashe da wani irin kuka ta koma da baya timmm kakeji ta yanke jiki ta Fadi tayi wani irin sandarewa"salati Lahab ya sake yayi Sauri ya matso gareta ya tallafo kanta Yana Kiran sunan ta amma shuru bata amsa masa ba.





Mikewa malam yayi ya dauko wani magani yazo ya Shaka Mata a hanci saiga jini ya Fara bulbulowa Kamar bakin fanfo Kara Lahab ya sake Yana kuka yana cewa a taimaka Masa karta mutu"Kai ka kwantar da hankalin ka wannan jinin dake fita a jikinta warakane a gunta ka natsu sosai,natsuwa yayi aka maidata Kan shinfidar da ta tashi ,fita malam yayi yace Lahab ya biyo bayan sa bayan sunfita Zama yayi a kasan bishiyar tsakar gidan Zama yayi a gefen sa,magana malam ya Soma Masa Kamar haka"Lahab a gaskiya yarinyar Nan tana cikin gagarumin hatsari bana Wasa ba wanda in aka cigaba da hakan zata iya rasa ranta gabaki daya Dan soyayya ya Fara tasiri a zuciyarta.



Waro Ido Lahab yayi yace"mutuwa fa kace malam dan Allah ka taimakamin kada ta mutu don Allah fa"tabbas Lahab zata iya mutuwa in ba dai wani ikon Allah ba muddin ba'a samu ta dawo hayyacinta ba hakan Kuma bazaiyu ba harsai ta samu wani muharraminta kusa da ita wato miji muddin aka d'aura Mata aure karfinta a kungiyar su zai raunana rauninta zaisa ta samu sassaucin ciwon da take ciki in ba haka ba naman daya wuce cikin tannan zai iya Zama ajalinta......................







*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*


🍀 *By Ruqeenjalal* 🍀



da mamaki Dr tace yes she is pregnant bakace wife nakace ba"?komawa Lahab yayi ragob akan kujera gabaki d'aya yanayin sa sun sauya sabanin Nnenna da tayi shuru tana dai zaune a Bakin gado ba yabo ba fallasa ta sanya hannayenta ta cikin rigan tana shafa cikin,da Sauri Lahab yace"how many months ne Dr,Mika Masa result na hannunta tayi jikinsa a mace ya karba yayi Sai Kuma ya rumtsa idanunsa da karfi cikine na wata uku da sati uku,kallon Nnenna yayi sai yanzun yaga irin chanjawar da tayi amma dai ckinta Na nan a shafe Kamar babu halitta a cikinta.





Shuru yayi Bai Kara magana ba haka zalika itama Nnenna batace kome ba har ruwan ya Kare aka sallame su tare da bude Mata file na zuwa Ayo a wajen su,haka suka Kama hanyar silently Suka koma gidan yayi parking budewa yayi ya fita ba tare da yajirata ba itama binsa tayi a baya hannu yasa ya bude kofar flat nasu, Adewale dake zaune a falon tun safe mikewa yayi Yana tambayar Lahab Ina Mai jikin,bai rufe Baki ba sai gata ta shigo,wucewa dakin sa Lahab yayi ya maida kofar ya rufe ba tare daya baiwa Ade amsa ba sai Nnenna data tsaya Suka gaisa ya tambaye ta jikin nata kana itama ta wuce dakin ta.




Tura kofar dakin Lahab yayi ya Shiga zaune ya gansa yayi tagumi,tsayawa yayi a bakin kofar ya harde hannu don har lokacin Lahab baisan ya shigo ba,matsowa yayi ya dafa shi sai a lokacin ya dawo hayyacin sa ya kalli Ade sai Kuma ya sake tsaki"Wai Lahab lafiya meke faruwa ne wai me akace Yana damunta donni Karan kaina Naga Rama a tattare da ita Kuma kace tanacin abinci sosai"?Mika Masa paper kawai Lahab yayi Baiyi magana ba"amsa Ade yayi ya duba sai Kuma ya sake murmushi yace"daman irin wannan Rana nake guje maka Lahab shiyasa tun farko na nuna maka illan wannnan sure da zakayi"





"Wallahi Ade nayi auren Nan bada niyar a waye gari tayi ciki ba"oh kana nufin ka aure tane don ka ringa sex da ita karta haifi Y'ay'a Kamar kowace mace"?bazaka gane ba Ade taya Zan dau ciki Koda nakai nageria a matsayin nawa kasan Abune Mai girman gaske"




Cikin mamaki Ade yace daman tunda ka Fara kwanciya da ita baka tanadi abinda zaka fadawa gidan ku ba akanta nufinka Randa zaka koma gida rabuwa zakuyi Koh yaya"Koh saboda yanzun ka zama celebrate shiyasa bazaka iya Zama da ita da ciki ba"?da Sauri Lahab yace Ade bazaka gane abinda nake nufi ba wallahi Koh sau daya ban taba tunanin rabuwa da Labiba ba Amma Ina Jin tsoron kada mu tafka kuskuren da bunayya da muwaddat(Aisha bagudu)sukayi"Aiko ku kunma fiso tunda su Koh banza iyayen su Sunsan da auren jama'an garine Basu sani ba dasu kansu ma'aurantan Saida Suka tafka aika aika Amma daga karshe duk da haka an Kira cikin ta da shege bare kaida babu Wanda yasan zance.





Yanzun Ade menene mafita"mafita dayane Lahab ta haihu ka tattarata ku koma nageria Kama danginka bayani insun amince ai shikenan"wani kallo Lahab ya Masa kana yace karfa ka manta bari na tuna maka Nnenna suspect ce a naija komawarta yanzun bazaiyu ba haka zalika tinkaran iyayena yanzun matsala ne babba kawai Ni na yanke shawara za'a zubar da cikin kawai muyi planning sai lokacin da Zan koma nageria Inna kammala karatu saimu koma daidai lokacin case nata ya mutu"





Kai Lahab kana da hankali kuwa an gaya maka Nan nageria ne da zubar da ciki ya Zama abin sauki cikin ma na wata uku Yana kokarin shiga na hudu Koh kunyar halinda yarinyar mutane zata shiga bakayi toh wallahi karka kuskura karka Fara abinda zaija maka matsala a kasan Nan kaji na gaya maka"



"Koh baka fada Masa ba Ni bazan amince ba"juyawa dukan su sukayi wa zasu gani Nnenna ce Wance ke tsaye rike da kofa ga dukkan alamu ta Jima a wajen,sai hawaye kebin kumatunta bata taba tsammanin hakan daga wajen Lahab ba Wai zubda ciki"mikewa yayi yace"ciki Kam tunda Ni nayi nace a zubar Koh y'ay'a d'ari kike so daga baya mu Haifa Amma Banda yanzun kwata kwata shekaruna nawa da Zan kakkabawa kaina yaya"?




"Lahab bazan taba zubar da cikin Nan ba,domin shikadai ne ya ragemun Wanda Zan daga hannu na nuna nace ga dangina nan Banda kowa nawa sai shi Taya Zan zubar in Kuma Banda rabon wasu cikin a duniya fa sai wannan fa Kai kana da daman aure amma Ni har abada ka cuceni"Zan rike duk abinda na Haifa Koda kuwa baka so ni Mai iya cewa ba d'anka bane,Ni Zan zamo Masa uwa da uba bazanji kunya ba,amma wallahi banda zancen zubarwa Ina son jinina Ina son cikina Koda kuwa kowa zai gujeni"mikewa Lahab yayi Yana nuna kansa kana yace"Ni kike gayawa haka"an gaya maka Lahab na gaya maka indai akan cikin Nan ne"toh nace bana bukatar cikin"Ni ina ruwana Kuma daga yau Ina so ka manta cewa akwai sure a tsakanin mu da Kai haka zalika bazan Kara cin abinda ya zamo naka ba muddin dai zanci yaron cikina ya rayu"






Juyawa tayi tabar dakin tana kuka,kallon sa Ade yayi cikin tausayin su duka don wallahi sun basa tausayi yace"Lahab karka kuskura ka sake zancen zubda cikin Nan itace uwa ita keda ra'ayin haihuwa Koh ah ah don haka ka zamo Mai adalci,karfa ka manta Koh a addinin ku haramun ne abortion ka kula da ita Lahab ka tausaya Mata,daga haka shima yasa Kai yabar dakin,har yamma Lahab na dakin sa,mangariba nayi yayi sallah mikewa yayi ya shiga toilet,wanka yayi ya fito ya sanya Kaya fita yayi a dakin ya leka kitchen yaga kome net babu alamun ma Nnenna ta dau wani Abu a ciki.




Fita yayi ya sayo musu abinci laida biyu bude kofar dakin nata yayi ya shiga zaune take da kayan da Suka dawo asibiti Koh chanjawa batayi ba idanunta jawor da gani tun kukan safe da tayine Suka rine,shigowarsa baisa ta motsa daga inda take ba aje laidan yayi ba tare da yayi magana ba ya fita a dakin,washe gari da safe Kamar yanda ya aje Mata laidan haka yazo ya gani da mamaki yake kallon ta sai Kuma ya kasa hakuri yasa hannu ya dago blanket in, kwance take amma Bata dago ba"meya hanaki cin abinci"?ba abinda ya shafeka bane"abinda ya shafeni ne Mana kina ikiraren kinason abinda ke cikin shine kikeson kasheshe da yunwa"




Wani kalllo ta Masa sai Kuma tace"babu ruwan ka daya mutu Koh yayi Rai aikai farin ciki ya Kamata kayi sai Kuma ta Mike ta shiga toilet tare da banko Masa door,fita yayi a dakin ya wuce

Please Login or Register in order to submit comment