Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dabi'arsa da halayen sa Suka sauya, hankalin ta atashe yake gabaki d'aya yaron ya koma Kamar wani baki a cikin familyn sa baya sakewa da kowa magana wannan bayayi sai yaga dama yake,Kuma duk a dalilinta ta rabasa da duk wani yakini nasa akanta,da ciwa yarinyar da bataji ba bata gani ba mutunci,yanzun burinta Bai wuce aga Nnenna ba.





*****************
Abbu ne yace bata Isa ba Lahab ya koma ya jona masters nasa yaci gaba da karatu in ma ball inne yaje yaci gaba da bugawa Allah ya bayyana Masa iyalansa,bazasu sake Bari Mami ta karasa shiba a banza, inya zauna a gidan ma hankalinsa bazai kwanta ba tunda kullum tunani yake matarsa na kasar,haka Koh akayi Lahab ya tattara yanasa yanasa yabar NAGERIA shida Adewale don Ade Yama samu aiki a London yanzun Kuma har gobe ba'a ga sulaiman ba.







*********************
BAYAN SHEKARA GOMA
Ihune ya cika cikin stadium in dake kasar Egypt,Wasa ne ake bugawa tsakanin NAGERIA da EGYPT Kuma a lokacin wannan gorzon footballer yayi winning nasu Yan NAGERIA dake zaune tuni suka mike Suna ihu ana Kiran"Hassan Lahab Hassan Lahab gabaki d'aya sunan ne ya cika stadium in Mai girman gaske dake dauke da dandazon Al'umma na kasashe daban daban,jarumi Kuma sadauki shiya bayyana a tsakar filin Yan uwansa bakaken fata kuma Yan team nasu sun dagasa sama ga coach nasu dake ta murna hannun sa d'auke da wani tafkeken cup an Masa Ado a ciki sai walwale yake Golden colour,kowa ka gani indai bakin fatane fuskarsa a washe yake sabanin Wanda yaci kwallon babu alamun fara'a Koh alamun Jin dadi a fuskar sa Wanda jama'a basu damu da hakan ba don Inda sabo sun Saba da wannan dabi'ar tasa,Saukesa akayi a hankali ya Soma tafiya sanye take da kayan ball wando da riga damtsen hannun sa d'aure da shaid'an Captain na Yan Wasa, Yana fita a stadium kwata-kwata mutum ya gansa bazaiyi zaton Yana da wannan kuzari na buga kwallo ba sai dai Yana dauke da manyan 6pack ga muscle nasa masu girma sosai tafiya yake kansa daya sha aski irin na Yan kwallo Yana duke a kasa Bai dagowa bare yaga Yan jaridu dake binsa Suna jefo Masa tambayoyi,matashi ne a kalla bazai wuce shekara 30 zuwa 31.




Zaune yake a cikin hotel Inda aka Kama musu shi kadaine a dakin sa a zaune ya zubawa waje daya Ido,turo kofar akayi amma Bai wani dago ba,wani kyakkyawan matashi brown colour dashi kudi dajin Dadi sun ratsa shi sosai fuskar sa d'auke da farin ciki ya shigo dakin cikin Jin dadi baiyi wata wata ba Koh shakkan Wanda ke zaune fuska a hade ba yazo ya rungumesa da karfi,amma Koh gizau bawan Allah nan baiyi ba.





Haba Lahab yaufa ranan murna ce dan Allah ka sake fuskar Mana friend"?hannu Lahab yasa ya ture Wanda ke bayan nasa har Saida ya kwanta akan gado kana ya dago kansa ya kallesa sau daya ya sake kauda fuskar tasa,shikam dayeke ya Saba da halin Lahab Bai wani Bata Rai ba sai mikewa da yayi ya zare P-cap dake kansa take yalwatancen gashin kansa ya bayyana harma da tabon sallah da yayi radau a goshin sa yayi bakikkirin Wanda ya Kara haska annurin fuskar sa"ya sake kallon Lahab in yace"kaga lokacin sallan mangariba ya kusa ya Kamata ka tashi kayi wanka mu tafi masjid time na wucewa"





Kin mikewa Lahab yayi tsungunawa guy in yayi ya kamo takalmin ball in kafar Lahab ya zare ya zare socks in, wandon ball in waist in Lahab yasa hannu zai zame wani irin damko hannun sa Lahab yayi hankali tashe cikin muryarsa Mai amo da girma yace"Kai Adewale a u out of ur sense"?kyalkyalewa da dariya Ade yayi haryana kwanciya kana yace"toh bagashi nasaka kayi magana ba ace mutum tunda ya tashi da safe banji yace kome ba"?tsaki kawai Lahab yayi ya mike ya Shiga toilet in bai Jima sosai ba sai gashi ya fito da towel lokacin Ade baya dakin.




Sanye yake da jallabiya fari sai hulama fari tas takalmi ya sanya kana ya fita a cikin hotel room in,laft ya hau ya saukesa kasa,fitowa yayi haraban Hotel in gabaki d'aya larabwa ne ke shawagi a wajen duk Inda ya wuce sai kaga ana nuna sa da hannu Koh ana kallon sa masallaci ya shiga anan ya hadu da Ade a ciki.




Bayan an idar da sallah har mutane sun watse lahab Bai fita ba hakan yasa Ade tashi ya fita sai da akayi isha'i kusan karfe 8:00 na dare lahab ya mike yabar masallaci,Yana Shiga cikin dakin nasa ya samu Ade zaune agaban system Yana dannawa amsa Masa sallamar yayi bawai don yaji sallamar ba sai sanin da yayi yayi kafun ya shigo dakin, Kwabe jallabiyar yayi ya kwanta akan gado,ga abincin Kanan ninaci nawa"Ade yace kala Lahab baice ba Kuma bai Mike ba shima Ade bai Kara magana ba har kusan 9:00 na dare Suna dakin bawai Hira suke Koh wani abuba ah ah Lahab na kwance Ade na aiki a system,d'an d'ago kai yayi ya kalli Lahab kana yace"Wai friend kasan gobe zamu bar kasar Nan Koh pls wannnan Karo kabi Yan team naku ku koma NAGERIA Mana shekara da shekaru ka bar kasa, Kai an zuba maka Ido ma bakasan anayi ba"





Shuru Lahab yayi again amma ya Kara tamke fuskar Nan tasa tamau Babu Koh digon fara'a"maganar gaskiya nefa Lahab wannan Karo ya Kamata ka d'aure muje naija Mana Kai baka gajiya da zaman London da sauran wasu kasashe amma baka tuna kaifa cibinka a naija yake"?karkaga shuru da Mami da Abbu Suka maka kazaci Koh Basu damu da Kai bane Koh basa sonka a kusa dasu Dan Allah ka musu adalci mana"





"Adewale gaskiya bazan je naija yanzun ba daga Nan Libya Zan wuce"da mamaki Ade yace"Libya Kuma Lahab wani wasan kake dashi ne a can don Ni na gaji da London Nan so nake na leka nageria"?MAXHEAL pharmaceutical's(Libya)Ltd, industry akwai wasu pharmacist da akeso nayi aiki dasu acan Suna so mu had'a hannu ne da industry nasu akwai wasu magunguna da sukeso su bugane"gyada Kai Ade yayi cikin happy Jin yanda Lahab yayi dogon magana yau kana yace"toh Allah ya bada sa'a amma Ni gaskiya Ina ga Zan wuce London daga Nan Zan wuce naija"?





Gyada Kai Lahab yayi ya koma ya kwanta abinsa shi Kuma Ade ya sake cewa"Wai Lahab bazaka ci abincin bane"?Nan ma Bai basa amsa ba ya juya ya gyara kwanciyar sa........................









*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*




Washe gari da safe Yan team in su Lahab sukayi bankwana dashi zasu dawo gida yayin da Ade ma yabi jirgin London ya rage saura shi kadai washe gari shima ya d'aga daga Egypt xuwa Libya,saukar sa kenan daga jirgi yaji wani irin duka da kirjinsa yayi haka kurum yaji wani irin kwanciyar hankali da natsuwa daya tako kasar,sunan sa da yaga an rubuta a jikin wani karamin board a hannun wani balarabe yasa shi d'aga hannu Yana nufar wajen mutumin da Sauri mutumin ya gyara tsayuwar sa Lahab na fitowa ya Kama bag na kayan sa sai sannu da zuwa yake Masa Suka fita daga cikin airport in,mota Mai zafin gaske baka ya budewa Lahab ya Shiga shima ya shiga Yaja motar Suka bar airport in.





Babban gidane Mai shegen kyau Wanda Industry ta basa ya zauna a ciki har su kammala meeting Inda ya kawosa akwa kome na bukatar dan Adam a ciki ga masu aiki Kota Ina,Suna Isa wanka yayi Suka Soma jajjera Masa abinci kad'an yaci ya kwanta,sai Kuma ya zaro wayar sa number Abbu ya Kira Suka gaisa Yana tambayar sa ya kafar Addayiya don kwana biyu ance Masa batajin dadi ba kafarta na ciwo sannan ta kirata itama.




washe gari da safe dayake meeting in Suna dashi ne karfe 10 na safe shiyasa bai tashi ba sai kusan 9 na safe wanka ya Shiga ya shirya cikin wani Arnen suit wando Baki sai rigan ciki fari kana ya daura baban rigan akai,ba karamin kyau yayi ba kannan nasa ya tajeshi sosai kana ya dau bakin glass ya kwaba a fuskar sa Sabon labcoat nasa ya d'auka ya rike a hannu kana ya bude kofa ya fito haraban gida da gudu drive yazo ya bude Masa mota shiga Lahab yayi da Bismillah gateman ga bude gate Suka bar gidan ,tafiya suke hankalin sa nakan wayar sa Yana dannawa Koh xai samu sukuni don kwata kwata yau ya rasa sukunin sa.






Suna ssa industry sosai yake bin wajen da kallo bawai kallon kauyanci bane ah ah sai kallon naira tayi kuka daya Mata, labcoat in ya sanya kana ya gyara zaman glass nasa ya sauka a mota,yayi cikin meeting room in dake cikin wajen.



Zazzaune suke akan kujerun a kalla pharmacy da Kuma pharmacology da likitoti akallah sun Kai ishirin Amma gashi goma da wani Abu yayi na safe an kasa Fara meeting in adalilin mutum daya dabai iso ba Wanda Lahab baisan Koh wanene ba guntun tsaki yaja don shi a duniya ya tsane African time bare har zaizo yana jiran mutum d'aya,mikewa yayi da niyar barin dakin hakuri manyan ma'aikatan suka Soma bashi akan yayi hakuri Wanda ake jiran ma ta karaso,ransa ne ya Kara baci Ashe ma macece ya tsaya Yana jira badon yanajin kunyar idon mutane ba yau Babu abinda zai sashi cigaba da Zama a wajen Nan,komawa yayi ya zauna yasha mur dashi.




Turo glass na kofar akayi da Sauri gabaki d'aya jama'ar dakin suka juya Dan ganin Mai shigowa sabanin Lahab da kansa nakan wayarsa Yana dannawa Yi yayi Kamar baisan da halinta ta shigo ba,wow Masha Allah taku take daya bayan d'aya macece Mai cikar Kamala natsuwa da haiba ga wani irin kyau dake tattare da ita Mai sanyi da sanyaya zuciya farace Sol Kuma tass dogowa Mai jiki daidai fuskar ta d'auke da medicate glass, suit na Mata ta sanya ruwan toka wando da riga ta daura lab coat akan kayan ta farin hijab data sanya karami iya wuyanta Wanda Harya bata daman da gashin gaban koshinta kwantattu Suka dan leko,kafarta sanye da takalmi Mai tsini kujerar da aka tanadar dominta ta zauna ta Soma gaggaisawa da sauran jama'ar dakin,muryarta ta dan makale kad'an lokacin da idanunta sukaci Karo da Lahab Wanda ya sata kasa karasa gaisuwar data Mika Masa shikam kansa har lokacin na kasa Yana Jin duk abinda ke gudana amma bai dago ba.





Jawabi aka Soma da tattaunawa kowa kokari yake ya zuba bajintar sa Kuma ya nuna kwarewarsa a harkar sanin magunguna,Deyana Abbas Ali shine sunan da Lahab yaji an ambata da sunan ta mikewa tayi a hankali ta Soma jawabi sai a lokacin ya d'ago ya kalleta had'a ido sukayi a tare dukansu suka kauda idanun su ana juna, meeting yayi zafi kowa mikewa yake Yana jawabin sa,har aka zo Kan Lahab.




1:20 cip aka tashi meeting in a hankali aka Soma fita one by one abinka da cikakkun Yan boko wa'inda suka San abinda Suke Babu wani hayaniya Koh ture ture Lahab da Deyana duk Basu mike ba sai da jama'an dakin Suka fifita saura bai wuce mutum biyar ba Suma Suka mike a tare kamar haden Baki,itace a gaba yana baya Suka Soma tafiya sosai ya zubawa jikinta Ido Yana kallon duk wani taku da take,yayinda ita Kuma kafafunta sai hardewa suke na rashin sabo.



Suna fitowa haraban wajen yaga wasu manyan bodyguards a kallah sunyi goma manyan maza majiya karfi sai Mata guda biyu,d'ayar ta bude Mata mota zata shiga kenan ya ratsa tsakanin su, ba tare da yayi magana ba yasa hannu ya Kama nata hannu tare da juyar da ita da karfin sa"tamkar wasu mayunwatan zagi haka Suka yunkura Masa da Sauri ta d'aga musu hannu,Kuma sukabi umurnin nata Suka tsaya, kallon hannun nata tayi fari tass dashi ta Kara d'ago idanunta ta kalli fuskar sa"irin kallon Nan na tambayar dalili"?ganin baice Mata kome ba yasa ta fizge hannun ta ta juya ta Shiga motar aka ja Suka barsa a wajen a tsaye da Sauri yaji an dafasa,dagowa yayi ya kalli mutumin a kalla zasuyi sa'o'i Kuma ya shaidaishi Yana daya daga cikin likitotin da sukayi meeting yare"kaga bawan Allah kada ka wahalar da kanka aka baiwar Allah Nan ba irin naci daban nuna Mata ha amma Koh kallo ban isheta ba tsawon shekarun Nan Koh haduwa mukayi nunawa take bata taba kallo na ba alhalin Kuma a hospital d'aya muke aiki"kala Lahab baice Masa ba ya juya shima yabar wajen.






Yana Isa gidan sa waya ya d'auka ya Kira Ade Ade na d'auka yace Masa"duk abinda kake ka bari pls kazo Libya Zan turo maka address na wajen da nake yanzun"keet ya kashe wayar ba tare daya jira abinda Aden zai fada ba"tsawon kwana uku Lahab na sintirin neman information akanta Amma ya kasa samun hakan Adewale yazo amma Lahab baice Masa kome ba, sosai yaji haushi sai masifa yake ma Lahab shidai Lahab baice kome ba sai visan sa daya dauka ya boye,yau tunda Suka tashi da safe ya shirya ya tafi meeting Inda za'a sake, yau sai xuba Ido yake ya ganta amma har aka tashi batazo ba.




Jikinsa a sanyaye ya dawo gidan tura kofar falon yayi ya shiga Ade ne zaune da wani balarabe Suna hira,ganinsa da Bako yasa sa bude muryarsa yayi sallama amsa Masa sukayi dukansu kana ya karaso falon nufar bedroom yayi da Sauri balaraben ya mike Yana sake gaidashi dawowa Lahab yayi ya zauna akan kujeran wajen Nan balaraben ya gabatar da kansa amasayin sa na coach khamaludeen saboda kaunar da suke Masa shiyasa Suka had'a Wasa dan Allah Suna so ya hallarta wasan ya buga da yaran su in Basu takurasa ba zasuyi farin ciki inya amince,da fari yaso yaki zuwa Saida Adewale yasa Baki sosai yayita basa Baki akan Bai Kamata mutane su nuna Masa kauna sannan Yana banzarar dasu ba hakan yasa sa hakuri suka saka Rana da venue.





Monday afternoon Lahab ne sanye cikin kayan ball farare tass har takalmin kafar nasa farine,sai Adewale dake rataye da sport bag na Lahab, shikam sanye yake da kananan Kaya,mota Suka shiga a tare driver yaja Suka bar gidan.






****************
Stadium cike yake da larabawa especially yara matasa sun cikane makil har wajen Zama yama wasu kad'an,shigowar Lahab filin wasan wani irin ihu wajen ya d'auka ana Kiran sunan sa,karasowa yayi ciki gurin da aka tanadar na zaman Yan Wasa Zama yayi Nan Yan Wasn Suka ruga wajen sa wasu suna sanye da Jan jese wasu Kuma Kamar na jikin sa watoh fari kenan, Nan suka Masa caaa kowa nason su musaba'ha dashi hannu kawai yake Basu Suna musaba'ha.





Wasa aka Fara cikin nishadi sosai su Lahab ke Shan yaran Wasa duk da yaran ma na bugawa iya kokarin su don sai su Lahab sunyi da gaske suke Shansu,an tashi Wasa su Lahab nada 3 goal yayin da yaran Suka tashi da 1 ihu wajen keyi da karfi ana Lahab Lahab Lahab da gudu wata balarabiyar yarinya sanye da jese sak na jikin Lahab sai dogon wandon roba pencil shima fari kanta dauke da hulan sanyi Babu Koh hijab a jikinta a kallah zata Kai shekara 13 don harta Soma Zama budurwa ga kirjinta cike da no-no tsallakowa tayi Kamar namiji ta hayo inda aka saka tsakanin Yan Wasa da Kuma yan kallon Wasa rugowa tayi da gudu duk kokarin tareta da ake kin tsayawa tayi ta nufi Lahab da gudu cikin larabci tana cewa akheeeeeeeeeee.




Da Sauri security Suka kamota sai kokuwa take dasu su barta ta Isa wajen Lahab sai cewa take ita fan nasa ne,so take suyi photo dan dakatawa Lahab yayi Jin Amon muryarta daya cika wajen muryar so familiar to him waro Ido yayi lokacin da Suka had'a Ido da yarinyar,nuna wa security yayi da hannu su barta ta karaso,Aiko Suna saketa da karfin cin tuwo ta ruga ta nufi wajensa shidai tsayawa yayi kawai Yana ganin ikon Allah a casa'in, kafarta kawai yake kallo dake cikin boot tana zuwa har zata rungumesa sai Kuma ta saya cikin fara'a tace"Ni Ina daga daga cikin fans naka ne Koh da yaushe Ina kwallon wasan ka ba Wanda yake wuceni dan Allah muyi hoto,gyada Mata Kai yayi da Sauri tasa hannu zata dau wayarta a Aljuhunta sai Kuma ta zaro Ido ganin Babu waya,Fara dube dube tayi Wanda hakan yasa Lahab yafito Ade dake tsaye nesa dasu tashi Ade yayi ya shigo wajen dan tsayawa yayi Yana bin yarinyar da Ido sai Kuma ya waro Idon ya kalli Lahab.




Zaiyi magana Lahab ya girgiza Masa kai hannu kawai yasa ya amshi bag NASA budewa yayi yadau wayarsa ya Mika Mata gashi toh ki dau hoton da wayata in yaso inkinga taki saiki tura ki bani tawa,da Sauri ta amshi wayar tsayawa tayi sai Kuma ya mikawa Ade tace"pls brother Amana hoto"amsar wayar Ade yayi Yana murmushi yayi musu kala biyu Suma Yan jarida sai daukar moments nasu suke,juyawa yarinyar tayi tabar filin,shikam Lahab na tsaye harta mule Masa.





***************
lahab na Shiga motar sa Adewale ma ya shigo harsunyi nisa Lahab ya amshi wayar Ade ya Kira wayar sa Saida yayi five miss call kafun ta d'auka cikin ihu take magana Hello bamai wayar bane tace cikin larabci"Hassan Lahab ne nace kin koma gidane ya maida Mata maganar da turanci"da Sauri yaji tace ba ma fito a cikin stadium in ba"ok toh ga munan a waje kizo"sai Kuma ya yanke wayar kallon driver yayi yace ya koma baya"shidai Ade Bai Kara yunkurin magana ba.





Aiko tun daga nesa Suka hangota tana dube dube,tsayawa motar tayi a gabanta Dan ja baya tayi sai Kuma ta matso kusa da motar ganin Lahab a ciki kawai ta bude motar ta Shiga shima Lahab baice kala ba yace direban yaja,tafiya suke yarinya Koh a jikinta wayar sa dake hannun ta take daddan nawa saiji tayi sunyi parking kallon Inda suken tayi sai Kuma ta waro Ido cikin zazzakar muryarta tace"ah Ina ne Nan Kuma Nan fa ba gidan mu bane big brother"?kala baice Mata ba ya bude motar ya fita shima Ade budewa yayi ya fita itama budewa tayi da gudu ta nufi gate na gidan da niyar barin gidan da gudu Kamar giftawar Ido Lahab ya damkota kamo hannun nata yayi duka biyu,ihu tasa tana cewa ya saketa itakam gida zata koma daman ummen ta bata San ta fita ba ya rufa Mata asiri ta had'asa da Allah koh sauraronta baiyi ba fiiiiiiiiiiii ya jata tare da bude kofar falon ya turata ciki fuska Babu walwala.





Saura kad'an ta Fadi sai Kuma ta fashe da kuka ta zauna a kasa tana cewa"nifa fan's naka CE wallahi daman tunda Aunty Esha ta ganka a TV tace da gani Kai mugune Ashe shiyasa Al'ameen baya kaunar ka Kuma yace shi ba Fan's naka bane,baya sonka"shut up rufemin baki nonsense kawai"shine abinda Lahab yace Mata cikin tsawa Yana shigowa falon,Ade na bayan sa,kuka ta Kara fashewa dashi da karfi da Sauri Ade ya shigo falon Jin kalan kukan da take Kamar an yankata dagata yayi daga zaunen da take tana ihu duk ta cika gidan da kara......................






*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 08084453785 tare da shaidan biyan ki*



Keee rufemin baki Koh yanzun na Saba Miki"? jiki na rawa ta rufe bakin Nata maida kofar falon yayi ya rufe da key kana ya matso kusa da su don har lokacin Ade na kusa da yarinyar fizge wayarsa yayi ya nufi daya daga cikin dakunan,mikewa Adewale yayi yabi Lahab cikin daki zaune ya samesa ya tallafe kansa"Lahab mekake ne haka"?uhmmm Adewale don Allah don annabi ka kalli shigen dake jikin yarinyar Nan ace yarinya tana by this age a barta babu suturan kirki haka mukayi da Labiba?don ita Bata sallah nace ta barmin yara haka kara zube ne"?






Waro Ido Ade yayi cikin mamaki yace"Wai Lahab ban gane ba daman kasan yarinyar ne Koh me"?wani banzan kallo ya maka Masa cikin haushi yace"yanzun Kai fisabililahi saina fada maka Kai daga ganin yarinyar Nan baka ga alama ba"cikin danne dariyan sa Ade yace"alaman me ranka ya dade"?tsaki kawai Lahab yayi ya mike ya fita a dakin yana Jin zancen da Adewale ke Masa Akan ya Kamata a maidata gida Kar hankalin iyayen ta ya tashi,shi kuma Lahab ya Kulla Niya a ransa sai uwarta ta duri ruwa yau,yana fita tsawa ya daka Mata hade da karbo abinci ya Mika Mata yace taci ba musu ta karba ta Kama ci da mamaki yace yanzun ci take bataji tsoron cin abin hannu mutane Koh Kuma damuwa na rashi komawa gida ba?abin haushi amsar da ta basa shine ai kwara ta mutu a koshe data mutu tana Jin yunwa.




Fita yayi Bai Jima ba ya dawo da Kaya dogon rigane na Arab gown sai hijab ya Bata yace ta canja na Jinkin taje tayi sallan mangariba, masallaci yaje ya dawo yace ta tashi tayi sallah a idon sa ya gani,tana kunkuni ta tashi sosai ya yaba da ibadar nata ajeta yayi ya zauna shima Yana cin abinci Yana Mata tambayoyi ta fannin addinin koma sosai yaga alamu yarinyar ta samu koyarwar addini,sunan ta ya tambaye ta Wai sunan ta "Meera Hassan Lahab Amma Sunana na gaskiya nazeefa Kuma in gaya maka saban sonka da nake har cewa ake Wai Muna Kama shiyasa nakewa yaran ajin mu karya nace Kai yayana ne"gyada Kai yayi yace meyasa bakice musu Ni Abien ki bane"?






Wani kallo ta Masa sai Kuma ta rufe fuska tana dariya hararanta yayi ba Wasa yace toh dariyan me kike Kuma ke kin sannni kuma"ah ah kawai dai dariya nake Taya zance wa kawaye na Kai abie nane D'an wannan dakai"ai gwara uncle Usman shidai Zan iya cewa babana"murmushi Ade daya karaso wajen yayi ya zauna kana ya jefo Mata tambaya"toh ke Ina baban ki tunda wannan abie ya Miki kadan"uhmmm babana dai Bayanan Koh rasuwa yayi Koh guduwa yayi Ni ban sani ba ummi batason mu Mata tambaya a kansa kullum ai tace Mana wata Rana zaizo Kuma haryau baizo ba"Aiko Kisha kuruminki yazo Kam"waro Ido tayi da kyau tacewa brother ka sanshi ne"?





Gyada Mata Kai yayi Nan fa tadi ya barke a tsakanin su shidai Lahab nasa Ido har kusan 11 na dare kafun Suka kwanta amma Lahab ya kasa bacci bini-bini saiya mike ya fita a dakinsa yaje ya leka yaga Koh tayi bacci gabaki d'aya gani yake Kamar inya kwanta zai farka yaga mafarki yake Koh ya tashi yaga ta gudu.





Washe gari da safe suna karyawa yarinya gabaki d'aya ta sake jikinta dasu Babu wani tsoro Koh kewan gida abin Yama Lahab ciwo gani yake kamar Nnenna bata Basu tarbiyar daya dace ba,mace ace tabar gidan su tun jiya amma Bata damu ba,Suna kammala karyawa Lahab ya tasata agaba Suka nufo gidan su Meera harda Adewale,tunda Suka nufo unguwan suke jinjina kudin da mamallakan gidajen kedashi wani hamshakin gida Suka nufa Wanda Meera ta nuna musu a matsayin gidan su gidane Mai kyaun gaskiya,horn Suka danna wani security yazo ya leka ganin Meera yasa shi saurin bude gate in Suka kusa Kai ciki.






Akallah gidane da za'a Kira unguwa guda Mai girman gaske dauke da part part masu zafi Kuma iri daya a kalla security dake kewaye da gidan sunfi hamsim ga police da Suka gani a gidan sai jama'ar dake tsattsaye Suna magana da police in sun Kai su Sha biyar gabaki dayan su Suka juyo Suna fuskan tan motar su Lahab bude motar Meera tayi da gudu tana Kiran ummi ta nufi wajen jama'ar,matar da Lahab ya gani a wajen meeting ita yaga ta Mike cikin tashin hankali fuska a kumbure alamun kuka Tasha bana Wasa ba ta nufi yarinyar da Sauri,yarinyar na Isa ta rungume ta fizgo yarinyar tayi ta wanketa da Mari Mai zafi ba Wasa a fuskar ta tana cewa zata kasheta ne tasan halinda ta sata a ciki yanzun inta Bata me zata cewa mahaifin.................makalewa sauran maganan yayi ganin Lahab da Ade da Suka sauko a motar.




Gabaki d'aya mutane tsakiyar gidan da mamaki suke kallon

Please Login or Register in order to submit comment