Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kauda kanta tare da zura takalmin ta ta nufi kofar fita.

"Ah ah big Aunty sai Ina Lahab yace Yana kallonta"

Mtwss Inda ka aikeni, shine amsan da ta bashi tana fita a gidan Inna Kam Ido kawai ta zuba musu irin kallon Nan na tuhuma da haushi don haryanzun Bata bar Jin haushin abinda Lahab yama jikanta ba gashi Kuma yau ta gansu tare duk buga Masa gargadi datayi bashi ba Lahab d'aga yau.

Adewale Kam saurin juyawa yayi tare da zaro wayarsa yahau wayar karya Yana fita a gidan Lahab Kam da kallon tuhuma ya bisa Amma Nabeel bai kawo kome a ransa ba ya nufi dakin sa Lahab na binsa a baya harsun kusa Isa dakin da Sauri Inna ta Mike kaiii lahabu dakata Ina zakaje badai dakin jikana ba kamko???Mara mutunci.

Dakatawa dukansu sukayi suna kallonta da mamaki bare ma Lahab Inda sabo dai ya Saba da masifar ta Amma bata taba koransa ba,"oh Inna yanzun ni kike kora a gidan Nan"?

Eh na koreka lahab,shine amsar da ta basa tana Masa kallon uku saura kwata.

"Kaga Nabeel shiga ka dauko mini kayana na shanja"

Shiga dakin Nabeel yayi Kamar yanda Lahab yace Masa don baison shiga rigimar su da Inna,kayan ball in Lahab da yake bari a gidan su ya dauko Masa da takalma duk ya fitoh masa dashi,kallon Inna yayi dake tsaye ta rike kugu yayi kawai ya girgiza Kai tare ta mikawa Lahab kayan,gasunan Lahab.


Amsa Lahab yayi ya aje akan dogon igiya dake tsakiyar gidan ya makala kayan ya aje takalmin a gefe,rigan uniform dake jikinsa ya cire tare da vest ganin addan Nabeel Bata gida yasashi Kwabe wando ya rage dagashi sai gajeren wandon jikinsa salati Inna ta buga,innalilahi wa'inna'ilahu raji'un mezan ganin nan dan duniya tsirara kayi a gaban jama'a nashiga ukuna,tana maganar tana tafa hannaye.

Shikaran kansa Nabeel mamakin iskancin Lahab yake wallahi ace mutum baya shakkan kowa.

Bucket Lahab ya d'auka batare dayabi takan masifar Inna ba yaja ruwan sa ya wuce bayi bayan yadau kayan daya makala a igiyan, wanka yayi ya zura kayan ball in abinsa ya fitoh daidai lokacin Nabeel ya dauko musu kwanon alele da Inna tayi a kitchen aje musu yayi a tsakar gida ya shimfida musu taburma,Lahab ga abinci fa ka fara ci Bari nima nayi wanka.

gyada Masa Kai Lahab yayi ya zauna tare da tambayar sa"wai har yanzun Adewale bai shigo bane"?


Nabeel najan ruwan Yana basa amsa,wallahi bai dawo ba nayi tunanin Koh fa ya wuce gidane.

"Anya kuwa Nabeel kasan yaufa akwai show bazai koma gida ba"


Kai gaskiya hakane fa Bara nayi wanka kaci alelen ka rage Mana daidai na fito wanka maybe ya dawo.

Bandaki Nabeel ya Shiga yayinda Lahab ya bude kwanon yayi Bismillah ya Soma cin alelen da Miya Inna Kam sai hararansa take makokonta cike yake tam da haushi ita da gidan ta ta kasa koransa.



Ta bangaren Adewale Kam Yana fita ya hangeta a bakin titi da Sauri ya nufeta,Assalamu Alaikum Gimbiya mubeena sai Ina haka.

Kallon sa mubeena tayi, waalaikumu Salam lafiya Kam?

Lafiya mubeena nace Ina Zaki?

Cikin yanga tace school zani wani abun me?

No ba kome Kuma in ba damuwa Zan iyya rakaki?

Kallon sa tayi da kyau itafa lamarin dan yarobawan Nan ya Fara isarta,akan me zaka rakani cema akayi bansan hanyar bane Koh me?

No ba hakan bane mubeena me laifi dan na nuna Zan rakaki school Naga dai duk Inda kaga kyautatawa da kulawa alamune na.................sai Kuma yayi shuru Yana kallonta kamar yarda ita ma ta juyo gabaki daya tana mamakin mezai ce kenan.

Uhmm uhmm a gaskiya mubeena nagaji da boye abinda ke Raina na gaji da hakuri da abinda ke cutar dani,nagaji da lallashin kaina wallahi Ina cutuwa mubeena bazan iyya daurewa ba nayi iyya yina Amma nakasa juriyar hakan.

Zuciyar ta bugawa take sosai Wanda har Saida ta dafe kirjin ta kafun ta daga idanunta tazuba Masa a hankalin ta bude bakinta ta Kara tambayarsa a Karo na biyu,menene wannan abin Adewale??...........





*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*

Page 39&40

Ina sonki Ina kaunar ki Ina bukatar ki a rayuwata,dan Allah karkice ah ah zuciyata bazata jure hakan ba ki tausaya min, Adewale yakarasa maganar cikin wani yanayi na fargaba.

Wani irin gyara tsayuwa mubeena tayi cikin Al'ajabi da mamaki take bin yaron da kallo don Koh a cikin su ukun shine karami su Lahab da Nabeel sun Dan girmesa kusan da shekara daya ma Koh watannni,Amma Kai dai baka da hankali Koh ince baka da mutunci yanzun Kai Inba tsaurin Ido da samun wuri ba ka rasa wance zaka kalla kace kanaso sai ni? sa'ar kace Koh tsarar kace ni toh wallahi d'aga yau sai yau magana makamancin wannan ta sake shiga tsakanin mu sai nayi mummunan Saba ma aikin banza kawai da wufe,ta karasa maganar tare da juyawa tana tsaida Mai keken da zai wuce.

Adewale dayayi mutuwar tsaye a wajen ganin Mai keken ya tsaya har tana kokarin Shiga yasasa saurin Kama Mata hannu,pls Mubeena ki tsaya ki saurare ni don Allah zuciyata bazata juri wannan horon da kike Mata ba.

Tasss kakeji mubeena ta wanke Adewale da Mari tare da fizge hannunta ta shiga keken tare da cewa Mai keken,malami dan Allah ja muje.

Adewale na dafe da kumatunsa Yana bin keken da kallo Harta cila,dafe kansa yayi a take yaji Kan na Masa wani irin ciwo kirjinsa na mugun bugawa juyawa yayi zai tsallaka titin,Sukayi Ido biyu da Lahab dake tsaye a nesa ya zuba Masa Ido alamu ma ya Jima agun.

Lahab Kam tunda Nabeel ya Shiga bandakin haka kawai taji hankalin sa ya kasa kwanciya ta fitar Adewale Kuma ya tabbatar bin mubeena yayi,hakan yasasa kasa hakuri har Saida ya rufe kwanon alelen yasa silifas din mubeena dake waje duk da ya Masa kadan Amma haka yasa.

Inna sai masifa take,Kai lahabu cire takalmin Nan wannan kafa naka kamar doya manya manya zaka saka Mata a takalmin ta Mai number 10 da rabi so kake ka tsinka Mata ai kafarka sai number 11 da rabi.


Kin kulata yayi ya wuce ya fita don ya gaji dasa boot takalmin ball in Kuma so yake inyasa Kar ya cire saiya dawo ball,fita yayi a gidan sanye da kayan ball in jikinsa tun d'aga nesa ya hangesu tsaye Suna magana hakan yasa shi jingina da ginin kofar gidan su Nabeel in ya hade hannu a kirjin Yana kallon su Amma baijin abinda suke cewa,bai Gama Shan mamaki ba Saida yaga mubeena ta wanke fuskar Adewale da Mari.

takowa Lahab yayi har Inda Adewale ke tsaye hannunsa ya Kama suka ye bakin wani dakali Suka zauna dafa kafadar sa Lahab yayi,"Adewale Koh baka fadamin ba na fahimci meya faru tun farko abinda na Fara guje maka kenan nace maka ka maida abinda kake kokarin bayyana wa saboda babu alamun nasara a tare da hakan.

Haba Lahab yazakace haka sannan laifine dan na nuna Ina son mubeena dahar zata d'aga hannu ta mareni,saboda na Kama Mata hannu Koh don nace Mata Ina sonta zata gaggayamin magana Koh saboda ni kabila ne kuke kyamata?

Kaga Adewale maganar gaskiya Zan fada maka,ni bana kyamar ka bama Kai ba duk wani mutum Mai hali irin naka ba abin kyama bane Kuma maganar banbancin kabila babu shi Koh na addin dazan nuna maka,kowa da addinin sa da kabilar sa Amma nasan mu Yan kasa dayane,kaima shaida me da ace mun nuna maka da bamu kai warhaka tare ba, Amma fa ka sani Ade mu a addinin mu bai halatta mana mace musulma ta aure Christine ba sai dai an hallata ma namiji musulmi auren Ahlil kitab,kaga Kenan a addinin mu bai halatta Mana ba,kaga kenan babu amfanin Neman soyayar mubeena tunda babu aure a tsakanin ku,sannan bayan Nan ka dubi shekarunka ka dubi nata atleast ta Baka 3 years a yanzun ita take bukatar abokin rayuwa,Kai yanzun ka aureta Ina zaka kaita nasan zata iyya kula da hakkin ta na aure don namiji baya kadan muddin ya balaga,Amma fa ka tuna cinta Shanta sannan iyayen ka kana tsammanin hakan zaiyu aikin me kake da zaka riketa? All this well Addinin mu bai hallata Mata ba don haka maganar gaskiya ka janye maganan Nan kodon cigaban alakarka da Nabeel don kasan in yasan zancen Nan Abu bazai maka kyau ba na tabbatar mubeena bazata fada Masa ba Amma Inka cigaba da yada manufarka gareta wata rana zai gane"

Bude Baki Adewale yayi zai Yi magana Lahab ya girgiza Masa Kai tare da Masa alamun yayi shuru ganin Nabeel ya nufo su,guys ya haka dukan ku kun fitoh kunzo kun zauna a waje gulman wa kuke?

Murmushi Lahab yayi cikin basarwa yace"Kai Nabeel aimu munfi karfin gulmar mutum sai dai mu tinkaresa da zance"bai bawa Nabeel daman magana ba ya kalli Adewale tashi muje Ade ka chanja uniform Nan mu wuce ball yamma na karayi fa"?

Ade dake zaune dafe da Kaine yace,gaskiya kuje ni yau babu Inda zani tare da mikewa tsaye gaskiya ninama wuce gida sai goben ku,Yana karasa maganar ya ratsasu ya wuce,da Ido Suka bisa Harya tsallaka titin ya wuce layin su,Yana bace muzu Suka juya a tare Suka kalli juna cike da mamaki Nabeel yace,lafiyan Adewale kuwa meyake faruwa ne?

d'aga kafadar sa Lahab yayi irin Shima baisanin nan ba,shuru kawai Nabeel yayi bawai don ya yarda ba,Mikewa sukayi suka koma cikin gidan, alelen da Basu karasa ciba Kenan Suka fita filin ball.

ta bangaren mubeena Kam tana shiga keken napep kuka kawai ta kamayi tama rasa meke damun ta guda da'ya Wai ita Adewale keso wannan shine so maso wani.

Baiwar Allah nidai Zan Baki shawara a matsayina na babba karki sake d'aga hannu ki dake namiji irin haka baida kyau zuciya baida Kashi wani inkin maresa ya barki wallahi wani bazai barki ba,Mai keken yace Yana kallon ta ta madubi.

Toh baba na gode amsar da ta basa kenan tana share hawaye dake bin kumatunta.


Adewale na Isa kofar gidan su hannu yasa ya tura get in ya Shiga har cikin falon su ya Kama hanyar corridor dazai sadasa da dakin sa idanu jazir.

Ade Ade mamar sa data fitoh d'aga kitchen rike da plate d'auke da nama soyaye.

Tsayawa yayi Yana kallonta sai Kuma ya kauda fuska,good afternoon mama.

Uhmm,cikin yare tace,toh yau Kuma ni kake gaidawa toh ma tsaya inaka fitoh ne?

School ya Bata amsa har yanzun idonsa na kasa.

School??ok Ina schoolbag first,shi sai yanzun ma tuna da school bag nasu shi da Nabeel Amma ya tabbatar friends nasu zasu daukar musu,mama banjin dadine shiyasa nabarwa Nabeel ya wuce min dashi.

Ok Amma yaushe ka Fara wuni har 4:00 a school,bude kofar dakin nasa kawai yayi ya shiga ba tare daya Bata amsar taba,Zama yayi a bakin gadon sa ya buga tagumi abin duniya ya damesa.

Mama dake tsaye aje plate in tayi tabi bayan dan nata,turo kofar tayi ta shiga a yanayinda ta gansa ya mugun d'aga Mata hankali Ade ne ke kuka ya rufe fuskarsa da tafukan hannayen sa, Jesus Ade what happen??meyasa kake kuka?

Da Sauri ya goge hawayen sa, nothing mom kawai kaina ke ciwo.

Kanka na ciwo Adewale yauka Fara ciwo ne? da bansan kaba me zakace ciwo ne ya saka kuka.

Nace Miki nothing mama,girgiza Kai mama tayi sai Kuma tayii murmushi tace,wace ce?? Kuma tace Bata sonka Koh?

Da mamaki yake kallon maman nasa shikaran kansa wani lokacin Yana mamakin yanda take saurin karantansa,Kwabe fuska yayi mama...

Shiii ba wani mama,nace wacece?

Shuru yayi sai Kuma ya rufe fuska Yana dariya hawaye Nabin kumatunsa.

Ok tunda bazaka fadamin ba is ok bazan takura maka ba Amma nasan wata Rana da kanka zaka fada basai na tambaye kaba,yanzun dai ka tashi Maza kayi wanka ka cire uniform, tana maganar tana shafa Masa Kai.

Mikewa yayi ya nufi toilet in ta bisa da kallo Harya bude kofar sai Kuma ya juya ya kalleta mama ya akai kikasan na Fara sonta Kuma tace Bata Sona.??

Hhhh Adewale kenan nice fa na haifeka nafi kowa sanin son nawa nasan babu abinda zaisaka kuka haka da damuwa sai so saboda nasan yarona ba rago bane sai a soyayya.

Murmushi yayi cikin Jin dadi ya shiga bandakin,mikewa tayi ta fita a dakin Naman ta d'auka dake plate ta wuce kitchen abinci ta zuba Masa ta shigo dakin aje Masa tayi tare da ruwa,fita tayi a dakin ganin har lokacin bai fitoh ba.

Adewale na fitowa yasa night Wear nasa abincin ya d'auka yadan ci duk da babu testing Koh kadan a bakin da Amma saboda Kar hankalin mama ya tashi yasa sa d'an Sakura yaci ya kwanta Yana ta tunane tunane abinsa.

ta bangaren Nnenna tana Isa gidan nasu dakinta ta shiga tayi wanka ta chanja kayan ta ta sanya wando fari da rigan t-shirt sauran indomie Mai sanyi ta baiwa Kiki yaci laidan ta d'auka ta nufi kitchen,falo ba kowa wanke Robobin tayi ta zubar da coffee dake flask ya Soma baci tayi ta dauko takai dakin ta ta aje, zata fita kenan saiga mom ta Shigo,keee Yar iska saiki fitoh ai Koh? peace taje kauyen su don haka ki fitoh ki daura Mana dinner tunda ba hutu kikaxoyi gidan Nan ba ai.

Gyada Kai Nnenna tayi tare dabin bayan mom data fita,tana binta a baya har kitchen,cikin store mom ta shiga,keee ki shigo store in Mana kin tsaya a kitchen Kamar na ubanki.

Shiga Nnenna tayi ta tsaya tana sauraron lissafin da mom ke Mata,

ga yam ki Mana sokora da miyan Stew kisa tsokar kaza a ciki sannan miyan Mai zakiyi karki kuskura Naga Mai yayi kadan Koh yawa hakama Magi Koh pepper,wallahi in abincin Nan bayi Dadi ba nida ke.

Gyada Kai Nnenna tayi again ta tsunguna tana daukar doyan,ke magana zakiyi min ba gyada Kai ba,ok mom kawai tace tana fita a store in itama mom fita tayi ta wuce falo ta zauna tana girgiza kafa.

Nnenna Kam doyan ta fere ta wanke ta kunna gas ta zuba a bujuwa ta daura tare da sa ruwa ta rufe,tattasai da tumatur sai tarugu da Albasa Mai ganye(lawashi) ta had'a ta gyara ta zuba a blander ta markad'a a take lawashin ya rinjaye colour tattasan ya zama green,bude fridge tayi ta dau kaza ta wanke ta yayyanka ta zuba a bujuwa Albasa da attarugu ta yanka a ciki ta zuba kori kadan da tafarnuwa kadan tasa Magi da gishiri tare dad'an shitta da masoro ta daura a huta ta rufe daidai lokacin Kuma doyan ta ya nuna saukewa tayi ta dauko wani bujuwan ta d'auka ta zuba Mai a ciki ta yanka Albasa Yana soyuwa ta zuba nikekken kayan miyanta ta fitoh da turmi tana zuba doyan a ciki tana dakawa gabaki d'aya ta hada gumi gashi daman ba isheshen lafiya bane da ita kanta ma wani ciwo yake Mata da hannunta gurinda aka da Mata ruwa.

ta daka doyan ta rage kadan Wanda zata ci sakwaran ta mulmulasu a laidan ta zuba a kula kayan miyan ta ringa juyawa Yana Shan wuta ta ibi kadan ta zuba a kwanon Miya ta aje a gefe ta zuba Naman Kazan ta Kara soyawa kafun tasa ruwan zafi a ciki Magi ta Kara kadan ta rufe miyar.

Doyan da ta ragen tasa a plate tadau miyar data zuba a kwano tasa a Kai tare da Barbara Magi ta Kama cin kayan ta Saida tacinye doyan duka tass kafun ta wanke hannunta ta duba miyar ya nuna saukewa tayi ta juye a kula yayi kyau sosai gashi ganyen albasar ya kawata miyar,tare da daukar daya bayan daya tana fitarwa a kitchen in tana jerawa a dinning Harta gama ta jera su plate da cups spoon ta goge kitchen in ta share, lokacin ma kusan 6:30 na yamma a gajiya ta wuce dakinta ba tare data wanke kanukan ba don wallahi ta gaji tana shiga ruwa ta d'auka tasha maganin ta ta kwanta sai baccin gajiya.


Ta bangaren Lahab Kam d'aga filin balls Basu dawo gida ba sai kusan mangari ba wucewa gidan su Nabeel yayi yayi wanka yadau jallabiyar Nabeel ya sanya lokacin mubeena na alwalan mangariba fuskar ta tamke Koh kallon arziki basu samu ba masallaci Suka nufa sukayi sallah mangari ba d'aga Nan Nabeel yace su koma gidan su suci abincin dare Amma Lahab yaki yace shi zai wuce gida.

Ok yanzun Kai Lahab gida ka nufa kenan?

"No Nabeel yau dai gidan Yaya jafar zani nida gidan mu Kuma sai muzammil ya Barta"

Au laifi kayine kake tsoron zuwa gida?

"Kutt Kai harka manta abinda yafaru kenan Nabeel toh nidai ban manta ba kasan maganar dole xai dawo gida don haka bani ba komawa gida"

Kai Kuma fa hakane Lahab, toh shikenan sai da safe Amma dai gobe ba Shiga school kenan Koh?

"tam Nabeel kenan in kaga zaka jeka nidai nayi Nan"

Dariya Nabeel yayi yabi Lahab da kallo Harya share kwana.



******************
Adewale Kam Yana kwance har 7 na dare Yana dakin sa a zaune Kamar d'aga Sama yaji papan sa na kwala Masa kira Adewale Adewale.....

Mama dake zaune a falon da Sauri ta Mike ah ah papan Ade ya haka d'aga dawowar ka Koh hutawa bakayi ba koh daki baka shiga ba ka Fara kwalawa yaro Kira.

Kinga tsaya nifa na Fara gajiya da halin kin Nan duk abinda yaron Nan yake aikatawa harda daurin gindin ki Nasha fadamiki banason Ina kallon Adewale da yaran hausawan Nan na tsane su banason ganinsa tare dake Amma ke nafahimci Koh a jikin ki ma Koh??

Kai papan Ade yanzun me nawa a cikin maganan Nan Kuma?Naga dai yaran Nan tun Suna yara suke abota duk abinda zakayi ka rabasu kayi Amma Basu rabuba sai yanzun da Suka Fara girma,Kuma a irin wannan age yara irin su basa bukatar fada Koh duka Koh tsawa Nasiya da lallashi daja a jiki sukafi bukata a yanzun.

Do Allah rufemin Baki nonsenses wance batasan ciwon kanta ba Taya zakice bazan ma yarona fada ba who I u??

Am ur wife Kuma uwar Ade Amma tunda kace hakan shikenan Allah baka hakuri yanzun dai meya faru???

Ina yake na tambaye ki ya dawo ne Koh bai dawo ba?

Ya dawo Yana bedroom,ai da Sauri ya nufi dakin yana surfa masifa binshi tayi a baya har cikin dakin.


Adewale tun Kiran farko ya Mike ya zauna Yana Jin duk cacar bakin da suke har nufo dakin Nashi,Yana jiran isowar papan Nashi,turo kofar tayi da karfi ya shigo tsayawa yayi akan Adewale Kai who I u da zanna kiranka kana jina ka kasa fitowa Kai wanene?

Kauda fuska kawai Adewale yayi donshi bai taba ganin baba masifaffe irin nasa ba ace mutum baida sassauci Kuma Wai a hakan shi pastor ne guda Amma baisan ya sassautawa iyalansa ba.

Ina magana ka manna mini hauka?

Am sorry papa

Sorry for ur self,me ka aikata a school principle naku ya kirani dazun da rana akan gobe yanason ganina Kuma na tabbatar tare da Kai zanzo.

Haba papa yazaka zo kana tambaya ta ai shugaban makarantan zaka tambaya bani ba?

Kai Ade kul karka sake gayawa baban ka magana like this,mama tace tana kallon sa.

gyada Mata Kai yayi,papa Kam cewa yayi keee barshi bayana ji da tashen balaga ba dole ya fadamin abinda ya fitoh a bakin sa.

Mikewa Ade yayi domin ransa ya Fara bace,kaga papa pls a hate noise tunda dai kazo ka tambaye nace ban sani ba pls u can leave now na gaji da surutun Nan ka barni naji da abinda ke damuna.

Kaiii Ni da gidana kake cemin na fita a dakin dana gida da kudina?

Bude kofar toilet in kawai Ade yayi ya Shiga hade da banko door in da karfi ya rufe Wanda Saida mama ta dafe kirjinta alun sanun tabar daki Bata Kara magana ba sai papa dake ta surfa masifa Yana zagin Ade..........





*Littafin nan na kudi ne gamai so naira 300 ne vie* 2185602275 *Rukayya Ibrahim UBA bank koh card na MTN zaki tura ta wannan layi 0816 464 2820 tare da shaidan biyan ki*


Page 41&42

Masifa papa yayita surfawa,Ade na toilet kin fitowa yayi Kuma yaki tanka Masa Harya gaji ya fita a dakin don kansa.

Jin ya fita yasa Ade ya fitoh yazo ya rufe kofar dakin sa ya kwanta.


************
Lahab Kam Keke napep yahau har unguwan su Yaya jafar"a kofar wancan gidan zaka tsaya Mai Keke"

Kallon gate in Mai keken yayi gate ne tankameme Mai shegen kyau da daukar hankali gaskiya kudi yayi kuka a gidan sauka Lahab yayi ya zaro lalitar sa ya Ciro dari biyu ya mikawa Mai keken,nufar kofar gate in yayi yasa hannu ya kwakwasa da karfi,ba'a Jima ba security yazo ya bude kofar Yana sanye da bakaken Kaya Kuma d'aga ganin sa madakin katttine,Yana ganin Lahab ya fadada fuskarsa,ah ah Rahab sannu da zuwa shigo Bismillah.

Shiga Lahab yayi ba tare daya mabi takan maganar Saba ya Soma ratsa tsakiyar gidan rufe gate in security yayi yabi bayan Lahab Yana Masa magana Amma Lahab Koh takan sa baibi ba yayi kofar falo dake manne a flat babba Wanda yafi Koh wanne kyau a gidan tura kofar yayi bakin sa d'auke da sallama, "Assalamu Alaikum"shuru babu amsa bin Koh Ina na falon yayi da Ido ganin ba kowa yasashi nufar upstairs dake falon ya Haura sama,Harya Isa babban falo dake saman binin bai hadu da kowa ba dan tsiririn corridor dake falon yabi direct ya bullar dashi wani kayatacen falo madaidaici Mai d'auke da kayan alatu na mure rayuwa.

"Assalamu Alaikum"ya Kara sallama a Karo na biyu Jin motsi a dinning area dake falon, waalaikumu Salam yaji an had'a Baki aka amsa Masa don ba kallon mutanen yake sosai ba,saboda labule daya karesu da falon Amma ana ganin alamun mutane a zaune,muryar wa nakeji kamar ta Rahab ka karaso Mana ka tsaya a falo kaman Bako?

takawa yayi a hankali zuwa dinning in hannu yasa bayan ya haura dan steps dake wajin ya yaye labulen,Yaya jafar ne sai matarsa nenne da yaran sa guda hudu Fatima da Hashim sai Aisha sai autan su Abdulmajid(gagararre),laa Uncle Rahab sannu da zuwa, shine abinda Fatima tace tana jawo Masa kujeran dake gefen ta, ba musu Lahab ya matsa wajen kujeran ya zauna,"Ina kwana Yaya Ina kwana nanne"?

Lafiya Rahab ya gida yasu Addayiya da Hamma Umar(Abbu)?

"Lafiya Yaya sun ma ce a gaida Kai"?

Rahab ya gida ya kwana biyu shuru Koh lekamu bakwayi harma gwara Kai da dan uwan ka Kam rabona dashi ai harna manta Koh gidan naku naje bancika samunsa ba.

"Alhamdulilah nenne kowa Lafiya"kawai Rahab yace don baison maganar tayi Nisa hannu ya baiwa Hashim sukayi musaba'ha sai Abdulmajid daya Mike yazo ya rungumesa"Kai man kwana biyu bama haduwa Koh wajen ka nazo uncle bai Bari na ganka ranan naje school naku ma Mai gadi ya hanani shiga, Wai Ina labarin Rahab ne mun kwana biyu da shegen wallahi?

"Kai da Allah sakeni karka karyamin kafadu ka bar Addayiya da wahala"Lahab yace Yana banbare Abdulmajid daka kafadar sa sake sa Majid yayi ya koma ya zauna Yana dariya gaisawa yayi dasu Aisha,kafun Fatima ta Mike tazo ta zuba Masa abinci ba musu yayi joining nasu Suka Soma cin tare.

Suna tsaka da cin abincin suka jiyo takalmi na kwaras kwaras alamu dai wani na taka tiles na falo kaf nasu babu Wanda ya dago Kai ya dubi Mai tahowan kowa cin abincin sa yake sabanin Lahab daya dago Kai ya kalleta, budurwace zatakai shekara 17 Amma kallo daya zaka Mata kasan akwai rawan Kai bana Wasa ba Koh d'aga yanayin tafiyarta ma kadai zai nuna Mata stubborn ce.

Shima sauke kansa yayi yaci gaba dacin tuwon dake gaban sa yayin da hankalisa ya Soma tafiya tunanin Nnenna Koh yanzun me take warhaka,wani hali ya tafi ya Barta a school ya jikin nata Kai Amma gaskiya ya Zama dole gobe da safe yaje ya ganta,Jin mutum a kansa yasa sa saurin kallon Kan nasa, yarinyar d'azun ce tazo ta tsaya Masa akai tana sanye da wasu matsatsun Kaya dinkine na riga da zani.

"Kee da Allah lafiya zakizo ki tsayamin akai in Zaki zauna akaina Zaki xaunane Koh Yaya"?
gabaki d'ayan su kallon Lahab sukayi Suna mamakin masifar sa don Sunsan Rahab na zuwa Amma babu ruwan sa da CeCe kuce asalima shi bai kaiwa mangariba a gidan d'aga yamma yayi yake tafiya gashi yau yazo da mangariba Kuma a fusace.

Amrat Kam kallon sama da kasa tayi Masa Amma dai batace kome ba taja kujeran ta zauna

Please Login or Register in order to submit comment