Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

baya.


Madaidaicin daining ne me kyau da akayi da wani irin katako na zamani amma an mishi suffar gargajiya,yadda taga an jera akushi saman teburin sai abun ya sake burgeta harta saki murmushi,shi yaja mata kujera daya ta zauna kana yana daga tsaye ya soma sarving dinta da nau'in abinci mara nauyi
"Yunwa fa" ta fada a shagwabe tana shafa plate tummy dinta,ya gane abu me nauyi takeso,saiya girgiza mata kai
"No my dear.....saiya hanamu rawar gaban hantsi....right?" Ya qarasa maganar yana kanne mata idanu,saita dauke kai cikin kunya,don tuni ta baro jirginsa.


Basu dauki dogon lokaci ba suka kammala,da kanshi ya kaita wani bedroom wanda ta cika fa mamakin tsarinsa shima
"Welcome to my world dear" ya fada yana janta cikin jikinsa,hannayensa saman cikinta
"Anan nake fatan bude sabuwar rayuwa wadda zata jagorancemu zuwa gina wata sabuwar rayuwa cikin sabuwar duniya...."saiya dan zameta daga jikinsa da sauri yana cewa
"Ina zuwa...get ready kafin na dawo" ya fada yana murmushi gami da nunata,bata iya amsa masa ba saboda yadda qafafunta ke rawa harya fita,saita samu gefan gado ta zauna tana qoqarin saisaita kanta.


"Kin manta ke din ba bilkisu bace shekara takwas baya?,yanxun ke dr bilkess ce,maman 'yan biyu,kuma mata ta aure" zuciyarta ta tunasar da ita,hakan ya zaburar da ita ta miqe ta soma shirya kanta cikin yanayin datake da tabbacin zai faranta ran azeez din.


Cikin tattausan rigar bacci wadda ta tsaya mata iya gwiwa ta shirya kanta,ta gyara kanta da kyau cikin mayuka da turarukan qamshi data gani saman madubin,kowanne lungu da saqo.na jikinta ta bashi haqqinsa,sai data kusa kammalawa ta tuna da ledar da ammi ta bata,sai kawai ta janyo ta budeta.


Wadansu irin turarukane designers masu aji tun daga kwalbar ma bare akai ga kudinsu,tun tana kalla a tsaye sai data janyo kujera ta zauna cike da mamaki,ita kadai amma tana jin kunyar kanta da kanta tare da mamakin nau'in turarukan,turare ne na hammata,qasan gwiwar qafa,na gwiwar hannu daban,na bayan kunne daban,na qasan cibiya daban,na matse matsi da cinyoyi,ga wani na gashi shima,harda na mutstsukawa a tafin hannu zuwa yatsu da kuma na jiki gaba daya,sai wata yar qaramar takarda da rubutu da bai wuce layi daya ba.

_kiyi amfani dasu daughter yadda suke,Allah ya albarkaceku_

A nutse ta bude kowanne ta kuma yi amfani dashi a muhallinsa,kana ta baibaye jikinta dana jikin.


Ita kanta sai data lumshe idanu tana shaqar yadda jikinta ya game da wani irin qamshi mai ratsa zuciya da qwaqwalwa jiki da bargo gaba daya,ta sauke ajiyar zuciya tana maida turarukan cikin kwalinsu.


Daidai sanda ta gama ya turo qofar da sallama a bakinsa,sai tayi tsil a inda take tsaye,saboda bataso ya ganta a hakan ba,don ko gashinya bata samu hadewa ba,bayan ta gama feshi shi haka ta sakeshi ta barshi ya bazu saman kafadunta
"Wow....wow" ya fada idanunsa kamar xai fado qasa yana dubanta,saiya kasa qarasowa a hankali ya soma sassarfa,wanda yana zuwa sama yayi da ita gaba daya,sai kuma ya soma shanshanata lungu da saqo a zafafe kamar wani tababbe,cikin wani irin low tune yace
"Ina kika samu turaren da nafiso a rayuwata princess?....na sake yarda na kuma sake tabbatarwa keta musamman ce....kece mahadin rayuwata" tun daga nan ta fuskanci ya soma sakin layi,ba'a rufa minti biyar ba jikinsu ya yiwa qafafunsu nauyi,tsaiwar ta gagaresu,yana riqe da ita ya isa makunnun fitila ya kashe,ya qarasa gefan gadon still ya kunna wata iriyar fitila mai suffar duma wadda take da sauqaqqen haske,kana iya ganin mutum sosai amma ba tarwai ba,ya qarasa saman gadon da ita a hankali ya direta kana ya biyo bayanta.


Wasu irin xafafan saqonni masu narka tsokar zuciya yake aikata mata,wanda duk inda kakai ga dauriya baka isa ka tsallake musu ba,abinda ya bata tsoro shine yadda tun daga nan bakinsa ya kasa shuru,duk inda hannunsa ko bakinsa yakai saiya yaba mishi kafin ya wuce gaba,ga tsoro ga kunyar yadda yake gaya mata wasu irin lafuzza masu nauyi kanshi tsaye,baiko jin nauyi ko tuna komai,ga wata iriyar soyayya dake son narka mata zuciya,daga qarshe jikinta na rawa ta dora yatsanta saman lips dinsa dake rawa kamar wanda kejin sanyi a hankali tace
"Shshshshsh" saiya dago fuskarta gaba daya ta yadda zai kalleta da kyau,ya nutsa duka yatsunshi cikin lallausan gashinta yana dubanta da birkitattun idanunsa data kasa jurewa kallonsu koda na seconda daya kuwa,kansa ya girgiza,cikin rawar murya yace
"I can't,bazan iya yin shuru ba princess....idan nayi shuru abun zaimin yawa,saina haukace,qwaqwalwata ita kadai ba zata iya dauka ba,keta musamman ce,wallahi keta dabance tun daga nan,na gaya miki tun daxun,na soke wata aba mai haruffa biyar a sanda muke tare wato kunya,saboda nan din duniyarmu ce mu biyu,daga ni saike....ki taimakeni don Allah ki kaini duniya ta gaba..." Shuru tayi tana saurarensa jikinta na tsuma,wasu irin hawaye masu dumi na farinciki suna silmiyo mata,bata taba kawowa ko a mafarki rayuwar zata juye musu haka ba ita dashi,bata taba kawowa lokaci zai sauya komai ba a tsakaninsu,harsu sake zama qarqashin inuwa daya ba,a sanyaye idanunta a lumshe ta gyada masa kai,saiya soma jera mata godiya yana sanya harshensa saman fuskarta yana dauke hawayen dake kai,daga bisani kuma taji ya sake kunna daya daga cikin qayayen dakin,hasken ya qaru duk da baikai na farko ba,saita bude idanunta da sauri,ta sake maidasu da sauri ta rufesu saboda kunyar ganinsa da taji ta kamata tana girgiza masa kai alamun ya kashe qwan,saiya girgiza kanshi
"Am sorry my princess,wancan karon a wancan ranakun baki ganni ba,ki bari a yau a yanzu ki ganni,ki ganni a yadda nake,ki ganni a abdul'azeez dina,ta yadda zamu sake sanin juna dakyau,ta yadda zaki sake yarda nidin a wajenki ba kowa bane,ta yarda zai sake yarda cewa idan ina hannun bilkisuna ni ba yarima bane,ba dan kasuwa bane,ba kowa bane face bawa wanda sai yadda taso zata juyashi" kai ta girgiza,har yanzu jikinta rawa yake a tsorace take
"Kayi haquri ka kashe,duka na yarda duk abinda kakeso na yarda dashi din" dole ya rage din kamar yadda ta buqata,kana ta sakar masa ragamarta ya kaita duniyar data manta da kalarta,ta kuma.manta da yadda ake shigarta,sai gashi a wannan daren ya tuna mata da komai,ya tuna mata da wani abu da tayi tsammanin ya faru bazai kuma maimaituwa cikin rayuwarta ba kenan har abada,sai gashi ayau komai.ya dawo sabo fil tsakaninsu.


Shi kansa yasan ba qaramar juriya da jarumta ta nuna ba,saboda shi kansa baisan yawan bashin daya tarawa kansa ba saida akazo wajen,saboda tashin hankalin tunanin rasata daya shiga ya bunne dukkan wani feeling nashi,nutsuwa da kwanciyar hankalin daya samu yanzu suka dawo da komai sabo,hakanan itama ta nata fannin ta tsorata da lamarin,sai taga ashe a wancan karon imani da tausayi kawai ya nuna mata sabanin yanzu data ji a ajikinta bakin gwargwado.


Washegari duk wani bashin tarairaya da kulawa da a wancan lokacin ya bar mama sodangi dashi sai daya bashi kaf,tamkar darensu na farko haka ya lalace wajen kula da ita,ita kuma ta baje kolin shagwabarta son ranta harda mara dalili ma,kwana daya rak ya ida daga mata qafa,next day ya kasa haquri yace shifa saiya koma,babu yadda ta iya haka ta bashi dama,a washegari tayi tunanin zasu je su koma gida amma sai taga shi zama ma kamar lokacin ya fara,data masa qorafi sai kawai ya kalleta,ya miqa mata hannu a hankali ya mata masaki zuwa jikinsa saman cinyarsa sannan ya bata amsa
"Nifa bazan rayu cikin jama'a ba dake,saboda zan iya barin abun magana,sonki yamin yawan da bazai barni na iya katabus ba,koda xamuje musun ma keda fita daga gidan nan saikin goge,kin zama 'yar hannu qwarriya irina,so nake mafa idan mun tashi fita mu fita da tsarabar wasu twince din wa ammi,naga alamun tana buqatar jikoki birjik,tunda du wadan can sun tsaya gayun banza da wofi,basa haihuwa sai bayan wasu shekaru" kunya ta sanyata kwantar da kanta saman kafadarsa tana murmushi
"Amma su amatu fa?" Kanta ya dungure da dan yatsanshi
"Kajimin yarinya,an gaya miki su suna ta tamu ne?,affy ta gayamin ko tambayarmu basa yi sun xama 'yan gida,kina tunanin ma ammi zata bamu su?,gwara ma ki dage ki samo mana namu eheeennn...." Saiya tura hannunshi cikin rigarta,tasa hannu da sauri ta dafeshi tana turo baki
"Haba mana princess,dan kadan fa,yaufa sau daya na ɗana" saiya shiririce mata,yadda ta bada kai da kanta ba tare data shirya ba.


A ranar ya turama safwa sakinta,tare da rufe dukkan wani babi nata,dama nutsuwa yake son ya sake samu,yana sane da rashin albarka da suka sake yiwa amminsa bayan tafiyarsu cikin azumi data aika ma safwan da kayan buda baki da sunan azeez din,abinda yasa yaji har zuciyarsa koda itace autar mata ya barta kenan.


Cikin kwanakin gaba daya basu da aiki banda suci susha su kwanta,sai hirarrki da bitar rayuwar kowa,kowa yana baiwa dan uwansa labarinsa tun daga quruciya xuwa girma.


Labarin rayuwar bilkisun ya karya masa zuciya,ya qasa sanyashi jin cewa zafi ko sanyi,wuya ko dadi babu abinda xai rabashi da ita,ya sake jin cewa ita din tashi ce,haduwarsu wata rubutacciyar qaddara ce daga Allah.


A zaman nasu kowa ya dinga qoqarin fahimtar dan uwansa,bawai bare baki sukayi akayita xuba soyayya tsurarta ba,tunda suna sane da cewa zomu zauna zo mu saba,kuma rayuwar yau zaqi ce gobe madaci,hakanan indai xa'a zauna tare dole wataran za'a samu sabani fada ko rashin jituwa,hakan ya sanya kowanne ta wani fanni yake qoqarin fahimtar ra'ayi zabi da halayyar dan uwansa domin wanzar da zaman lafiya a rayuwar aurensu.


Duk hankalinta yana gida,tanaso ta samu 'yan uwanta maza kamar yadda tayi alqawari bayan ta dawo,hakanan tanason zuwa taga anty zuhriyya,duk kullum Allah sai sunyi waya,amma tana son taje ta ganta,don ba qaramin kewarta tayi ba.


Da qyar randa suka cika kwana goma cikin gidan ta lallabashi ya amince xata,amma qafarta qafarshi,tace ta aminta.


Cikin daya daga cikin sabbin motocinsa dabai taba hawa ba samfurin wannan shekarar suka fita,daga ita saishi sai driver ba tare da rakiyar kowa ba.


A mota yayi xamanshi,yace idan baba yana nan ta mishi magana ya leqo su gaisa,idan kuma bai nan shikenan ta gaida mutanan gida,ta samu malam.bilyan ya dan samu ya fita miqe qafa,umma katti ta aika kan ya shigo ko ruwa yasha amma yace aa,dole suka barshi.


A zaman da tayi dasu ta yanke bude manyan shaguna kowanne dai dai qari akan na mahaifinsu,saidai wannan dinma zai xama kamar qarqashin na malam bilyamin dinne ta wata fuskar kuma kamar nasu,zasu dinga raba ribar da aka samu gida uku,su baiwa malam bilya daya daya su su riqe bibbiyu,uwar kudin kuma a sake juyata.


Hakan ya faranta musu matuqa da gaske,basu taba zaton a rayuwa bilkisun zata musu rana irin haka ba,kudaden data fadi zata zuba cikin kowanne shago kawai ya gaya musu ba qarami shaguna xata bude ba,sun nemi alfarmar ta tayasu da addu'a,Allah yayi riqo da hannayensu.


Daga nan gidan anty zuhriyya ya kaita,ta dinga dariya hannunta riqe da bakinta
"Anya bilkisu wannan komawar itama ba wani rabon ne yayi kira ba?,kinga yadda kikayi mulmul kuwa?,wannan soyayya da yarima ke baki karta sangartaki da yawa" maganar ta sata kunya sosai,tadanfi jimawa wajen anty zuhriyya suna tattaunawa da kuma sauran shawarwari data qara bata,sannan sukayi sallama tare da uwar tsarabar da yarima yasa aka shigo da ita kamar yadda aka kai gidansu,wanda duka batasan dasu ba.


Basu fita a gidan sunje masarauta ba sai da suka kwashe wata guda a gidan,duk da shi yaje ya amsa kiran me martaba,wanda ya dinga fada kamar zai cinyeshi danye kan sakin da yayiwa safwan
"Allah ya huci zuciyarka,banda wani sauran zabi tunda ta nuna ra'ayin bata da sauran sha'awar zama dani,ban isa na mata dole ba,sannan babu wani goyon baya daga wajen magabantanta,suma bamu da ikon tilastasu su bamu diyarsu" wannan furuci nasa yasa fafan baiyi wani dogon zango ba
"Aure rai gareshi,saikaci gaba da addu'a idan da rabo.nan gaba za'a koma dole"
"Rabbi kasa bai cikinnqaddarata har abada" ya fada can wasan zuciyarza ba tare daya bari.me.martaba yaji ba,ita kuwa fulani banu a inda tace banda
"Allah ya kyauta,yasa hakanne mafi alkhairi" dariya yaso qwace masa,bai taba tunanin akwai lokaci da zaizo hakan ta faru ammin ta dauki abun da sauqi har haka ba.


Randa xasu gidan murna kamar bilkisu tayi me,shi kuma ya dinga hade rai,harsai data tambayeshi cikin salon tsokana tsokana
"Da kaje za'a isheka da gaishe gaishe tun daga bakin qofa,ko ina ma'aikata birjik,kuma kome kayima iyalinka saiya wani zama abun kallo,kamar kaidin ba mutum bane kamar kowa" dariya ma ita ya bata
"To ai laifinka,kune idan kuka shiga mutane saiku ishesu da hada gira,ku cikasu da kwarjini,kaga kuwa duk abinda xakuyin zai xama sabo a wajensu" damqa yakai.mata
"Zaki to kuwa jawo a fasa zuwa,tunda kinama goyon bayansu ne" a shagwabe ta kama kunnuwanta da hannayenta biyu
"Tuba nake yallabai,ayimin afuwa,inason naje naga mamata ammi".


Sanda suka isa sassan fulani saita kasa sakewa kamar baya,nauyinta da ada takeji yanxun ya sake daduwa,datace mata
"Baqin haura katanga,babu sallama saidai a lalubeku sama ko qasa a rasa" kamar xata tsaga qasa ta shige haka taji,afnan ta soma taya ammin bilkisu ta jefeta da harara,qasa qasa tace
"Kici gaba,dab nake da tona asirin soyayyarku da baturen likita adamu wajen yayanki" saita kama hannunta da sauri ta riqe tana fadin
"Tuba nake antyna,kimin rai,karki ballomin ruwa,ki bari komai ya gama dai daita don Allah".


Yadda afnan ta fada kusan hakanne,su amatu yaran ko a jikinsu,sunata shagallensu a gidan,suna zuba shagwabarsu son ransu,'yan gata tako wanne fanni,baga ammin ba baga me martaba ba baga sauran jama'ar gidan ba,wanda rashin fulani adama a gidan da lalurar fulani saratu yasa da yawa da basu gane alkhairinta ba wadanda abaya basa jam'iyyarta yanzu ta zama tasu,sun gane ashe a baya bautar banza kawai suke a inda ba'asan qima da darajarsu ba.


Ranar sunsha hira sosai da mama sodangi irin wadda suka jima basuyi irinta ba,batasan tayi kewarta ba sai a sannan,zataso a bata mama sodangi su zauna tare,saboda matar tayi tako ina,amma.batasan ya yanayin tsarin nasu yake ba,batason ta cika azarbabi da yawa.


¶¶¶¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶¶¶


Tare dasu akayi bukin babbar sallah na bana,fulani ita ta sake zama cikakkiyar me masaukin baqi,ta karbi kowa babu banbamci,kama daga yaran adama dana saratun gaba daya,abinda ya sanyayar da gwiwar yaran,suka soma sauya tunani a kanta,tare da sare kaso mafi yawa na qullaci da qiyayyarta da aka dasa musu cikin zukatansu,musamman yaran fulani saratu wanda sun jima da fara saduda,ganin yadda bata bari mahaifiyarsu ta wulaqanta ba daga wajen jama'ar gidan ko mijinta ba,tana bakin qoqarinta wajen ganin ta samu kulawa yadda ya kamata.


Hawan sallar na bana ya bada qaye sosai,tawagar yarima da abdul sunfi kowacce tawaga daukar hankali jan magana da jawo cecekuce,a ranar ko cikin gidan duk inda ka gifta hirarsu ake,saboda kome iri daya suka sanya,sai suka tashi kamar hassan da usaini,banbancin kawai shekaru ne.


Hutun sati guda kawai da bukin sallar ya tashi komawa bakin kasuwancinsa,sanda yake shaidama ammin hade ranta tayi tsaf
"Wai kana nufin na debi yaran nan na baka kuyita yawo dasu,baku nan baku can?,tab....a'ah wallahi bada ni ba,kudai kuje saikun dawo,duk sanda kuka waiwayomu ku kuka jiyo,amma bada jikokina ba".


Koda ya shaidama maimartaba shima bayan ammi ya goya,don shi kansa yaran sun shige jikinsa da zuciyarsa sosai,duk da yana qoqarin boyewa saboda sauran jikoki da kuma idanun al'umma,amma dole wani abun bazai boyu ba,don abudul har kujera guda aka masa kusa data me martaba cikin fada a madadin mahaifinsa,sau tari dashi ake zaman fadar,don dole ya haqura suka soma shirin tafiyar shida bilkisunsa.


Kafin tafiyarta sai data tabbatar an gama kome na kasuwancin yayyenta,malam bilya wannan karan kasa jurewa yayi sai daya saka kuka,yadda ya riqesu a baya da abinda yayi ya dinga masa ciwo,da qyar ta kwantar masa da hankali.


Tun cikin jirgi ta soma jin wani zazzabi na cikin qashi,yarima nata zolayarta dako qwallonshi ya shiga raga ne?,sai tsoro ya kamata saboda tuna azabar da tasha laulayinsu amatu,amma kuma kwana biyu da isarsu data huta taji ta warware sai hankalinta ya kwanta,ta dinga ma yarima daya qwallafa rai gwalo tana cewa
"Dama ni nasan babu wani abu" kaman yayi kuka don har ranshi yaso ace ta kamu ne
"Bari murna yarinya,don ni jikina ya bani,kuma na riga da nasan nayi winning" tana sheqa masa dariya tace
"Shikenan zamu gani ai" qaramin ya tsansa ya miqo mata
"Mu daura....duk wanda yayi winning a tsakaninmu zai sadaukar da wani abu ma dan uwansa"
"Na yadda" ta fada tana miqa masa yatsarta tana dariyar mugunta.


Saidai kuma tun ba'ayi nisa ba ta fuskanci yariman nata ya riga da yaci gari,sai taja bakinta ta tsuke tana tsoron tsiyar da zai mata.


Saida laulayi ya soma tabata ya debe ta suka nufi asibiti sannan komai ya bayyana,murna kamar ya maidata cikinsa haka ya dinga zumudinsa tana kallonshi,ji yake kamar ya lasheta,godiya ya dinga zuba mata kamar ita ta baiwa kanta,kula sosai ta samu daga wajen likitoci da nurses din,wanda hakan ya sauqaqa mata wahalar laulayin ba kamar nasu amatu ba.


Baice mata komai ba saida suka dawo gida,bayan sun samu nutsuwa ya miqa mata hannu
"Alqawarina....me za'a sadaukarmin?" Saita langabe kai a shagwabe
"Pls mana (Ameer),ban da lafiya fa?" Dariya ta qwace masa,yadan mintsini cinyarta,saita sake masa kukan shagwaba gaba daya tana fadawa jikinsa,ya sanya hannayensa kuwa ya tattareta gaba daya cikin jikinsa yana sake shagwabata
"Abu daya fa,abu daya fa baby zaki bani" ta sake tura baki gaba
"To meye?" Sai daya dagata sosai ya zaunar da ita saman cinyarsa,idanunsa cikin nata,ya sanya tafin hannunsa tsakiyar nata
"Rayuwarki nakeso ki sadaukarmin,ki mallakamin rayuwarki,kome runtsi kome wuya ki zama a tare dani" qayataccen murmushi ta saki wanda ya bayyana jerarrun fararen haqoranta
"Wannan ai tsohon alqawari ne tsakanina dakai ameer" kai ya gyada
"Yes na sani,amma wannan na musamman ne" saita kama hannunta ta dora saman qirjinta
"Allah ya zama shaida haka zuciyata cewa na mallaka maka komai nawa,idan nace komai ina nufin komai din" qanqameta yayi sosai cikin jikinsa,yana jin kamar yafi kowanne namiji sa'ar mace a duniya,kamar yafi kowa sa'ar samun soyayya.


Wannan cikin kusan tare sukayi rainonsa,ya kasa shuru sai daya shaidawa amminsa,wanda tsananin murna ya hanata sukuni,ba yadda bata so ya dawo da ita gida ta zauna da ita ba amma ya toge,hakan yasa dole ta shirya mama sodangi ta bisu.


Hakan ya farantawa bilkisu rai sosai,saita kuma sakewa abinta,tana jin kamar wata uwace a tare da ita,zamansu da mama sodangin kamar wancan karon,cikin girmama juna nishadi da walwala.


*_BAYAN SHEKARU BIYU_*



A hankali riqe da hannu juna suke takowa zuwa sassan mahaifiyarsu mahaifiya ga kowa dake cikin masarautar,jarumar mace mai cike da sanin ya kamata,jajirtacciya mai qoqarin kamanta adalci kan kowa kamar yadda ta kurba wannan halayya daga wajen maigidanta wato fulani aisha.


Mutum biyu da suka kasance taurari,abun kwaikwayo,kuma tamkar zuciyar masarautar kaisa wato *_bilkisu bilyamin_* da *_yarima abdul'azeez abdallah mu'az kaisa_* su suka samu tsaiwar mutane da dama makusantansu da suke maraba da zuwansu,bayan shudewar shekara guda basu tako qasar ba,sakamakon wani gagarumin aikin fadada kasuwancinsa daya riqe a zeez din a gurare da dama,ya hanashi shigowa masarautar kaisan,shida mai dakinsa da akoda yaushe take kamar aljihunsa,don idan kaga zara tabbas zakaga wata.


Sarauniya kuma uwargida bilkisu sanye cikin wani material na alfarma kuma na musamman da aka masa dinkin riga da zani da yalwataccen mayafi,sai wasu takalma masu tsinin dunduniya masu madauri,hannayenta saye da wasu banguls masu kyau da nuna alfarma masu hade da zobuna qwaya biyu,sai yar hand bag dake maqale a hannunta wadda ta shiga da kayan jikinta.


Kallo daya zakayi mata ka tabbatar ta gama zama cikakkiyar mace mai cikakken aji ilimi da sanin ciwon kai,fuskarta fadade da fara'a take gaisawa da kowa,yayin da gogan nata yarima ke gefanta sanye da wasu suit da suka dace da matsayinsa da tsarinsa,shi dinma ya sake zama wani cikakken mutum da kwanciyar hankali shekaru da nutsuwa suka ratsashi,yanata shafan sumarshi yana satar kallon ammi wanda yasan ta cika fam dashi.


Daga bayansu kuma mama sodangi ce dauke da wasu kyawawan yara guda biyu,wanda ko ba'a gaya maka ba kasan identical twince ne zubin masarautar kaisa kamar yadda su amatu suma suka dauko gida,yarane masu ban sha'awa da birgewa 'yan kimanin shakaru bibbiyu sanye da suit suma na yara,daya na kafadar mama sodangi da alama bacci ne ya daukeshi,dayan kuma na riqe a hannunta yana takawa da qafarshi,ita kanta mama sodangin kallo daya zaka mata ka karanci qarin samun canji da kuma ci gaba a rayuwarta.


Sosai ta kalli sashen da wata mata ke tsaye wadda keta faman sunne kanta da mayafi,data lura sosai sai taga ashe umma luba ce,murmushi ta saki tana qarasawa inda take ta soma gaisheta,cikin diriricewa ta hau amsawa,sai bilkisun tayi qas da murya
"Komai ya wuce ya kuma zama tarihi,ya kamata ki manta kema" daga haka tayi gaba,wanda maganar ta sanyaya jikin umma luban,ta kuma samu nutsuwa fiye da da a zuciyarta.


Sannu sannu suka wuce dukka jama'ar har suka dangana da falon da babu kowa,daga su sai fulanin saisu da yaransu,ta miqa hannu ta amshi ahmad dake bacci daka gun mama sodangi,ta kama hannun muhammad ta jashi shima zuwa jikinta
"Sannu da qoqari sodangi,Allah ya saka da alkhairi,kunsha hanya,ki qarasa masauki ki huta" murmushi ta sake
"Babu komai Allah ya taimakeki,inajin kamar ina yiwa yarana na cikina ne,ammm mun miki laifi,shi yasa nadan tsaya mu bada haquri" murmushi fulani ta saki tana jefawa yarima harara
"Baki da laifi ko daya adama,rabu dashi ki tafiyarki" cikin girmamawa tace
"Toh,amma dai duk da haka muna neman sassauci,na barku lafiya" ta juya tana murmushi ta fice daga falon.


Waiwayowa fulani tayi tana jifansa da harara bayan ta samu kujera daya ta xauna tana kwantar da mahmud ta dora muhammad saman qafafunta
"Mara gaskiya dama ko a ruwa gumi yake,sannunka da qoqari abdul'azeez,da kana nufin zaka hanata zuwa bikin qannenta har biyu da taka qanwar kenan?,saiyau ranar dinner sannan kaga damar tahowarku,baya ga haka shekara guda baka leqo kaisa ba,to indai zaka ci gaba da hakan ba shakka zaku koma ne babu su mahmud,gwara suma su zauna wajena" kanshi a qasa cikin rusunawa yace
"Afwa ammi,in sha Allah na miki alqawarin hakan bazai sake faruwa ba"
"Yafi maka dai" ta fada tana miqawa bilkisu hannu,sai itama ta miqa mata sukayi musabaha kamar yadda suka saba,tun tana kunyarta harya zame mata jiki,cikin murmushi da nuna kulawa take mata maraba sannan suka fara gaisawa,kullum kwanan duniya qimar bilkisun da iyayenta sake daduwa suke a idanunta,bama kamar yanzu data zama silar haduwar auren dr adam da afnan dinta
"Ammi ina amaren suka shiga ne?"
"Tana can sassan baya ita da qawayenta" saita miqe cikin zumudi
"Bari na gansu" da haka ta fice ta basu sarari ita da azeez din.


Tsalle afnan ta daka ta daneta
"Karki jimin ciwo

Please Login or Register in order to submit comment