Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ana idar da la'asar saiga ammi fulani ta iso,kamar kowanne lokaci ta rungume bilkisu a jikinta,harga Allah yanxun wata qaunarta ta daban takeji cikin ranta,abinda safwa da sukayi shekara da shekaru ta kasa yi ita gata zaune kawai saboda azeez din,tabar komai saboda shi da sunan jinyarsa,duk da manyan manyan zunubansu a wajenta,safwan da har yau nata kuma zuwa dubiyarsa ba,sai mamarta ke aikin aiko da abinci da saqon gaisuwa,da sunan safwa din bata da lafiya,mura waike damunta,hakanan tun daga wancan lokacin daidai da second daya bata taba ganin wani kallo na rashin girmamawa ba daga bilkisun.


Saida suka gama gaisawa sannan ta isa ga yariman,bilkisu ta dinga jefa masa harara a fakaice,sai a bayan idanun fulanin ya koma kamar wani yayayye,amma data iso saiya koma.namiji sosai,musamman idan ta shigo ne da afnan ko wasu daga cikin barorinta,yanzun zai aro dukka izzar mulkinsa.


Suna fita din kuwa ya kalli fulanin
"Ammi qafafuna babu dadi,a taimaka min a wankemin su,na rasa wanda zai wankemin"
"Ba matsals,sai na gyara makan,duk da banga wani datti ba sosai ba" ta fada tana miqewa,tilas bilkisu ta tarbeta,ta amshi aikin,qasa qasa tana jifarsa da harara,shi kuma yana qumshe dariyarsa,gamida jifanta da wani irin kallo me kashe jiki.


Qafa daya aka wanke fulani ta duba agogon gold dake daure a tsintsiyar hannunta
"Gida nakeson komawa,akwai wasu mutane da nayi musu alqawarin zamu gana" ta fada tana duban yariman kai ya gyada,yasan bazasu wuce daya daga cikin qungiyoyin tallafinta ba da take dasu,cikin tausasawa ta dubi bilkisu
"Diyata,na gode sosai kinji" cikin jin kunyar fulanin ta saki murmushi kawai,ta musu sallama ta fice.


Sai data biya wajen likita ta masa magana ya rubuta musu sallama nan da gobe,saboda tana ganin lokaci yayi zuwa yanzu da zata qarasa aikin data fara,babu musu ya amsa mata,don shima ya idanunsa sun soma gajiya da ganin tabarar da yariman keyi.


Sai data gama dukkan abinda takeyi kana ta isa turakar me martaba,bata taddashi ba sai itama bata damu can ba,saboda kusan ta saba yanzun da halin ko inkula da yake nuna mata,sabanin daa da yake nuna zumudi da kulawa duk lokacin daya kasance zata kwana wajensa,tsufa ko shekaru duka basu canza wannan ba,saboda tasan kanta sosai.


Bandaki ta shiga tayi wanka,sannan ta dawo cikin dakin tana shirya jikinta cikin qamshi,sanye da rigar towel yalwatacciya.


Dai dai lokacin da me martaba ya turo qofar dakin ya shigo,bakinsa dauke da sallama,ta waiwaya ta amsa mishi,saita dauke kanta tana ci gaba da shafa man da takeyi,zuwa yanzun tana jin nauyin dake qirjinta yana yin nashi waje,tsoron dake danqare a zuciyarta yana kwaranyewa,tana jin nutsuwa sosai irin wadda ta jima bataji irinta ba,domin kuwa tana jin a yanzun ta aikata abinda ya dace,wanda yake shine dai dai,ta hada ahalin da ada ta zama silar tarwatsewarsu,sukayi nesa da juna,irin nisan da daya bai iya ganin daya.


Yadda tayi mishin saida murmushi ya kubce masa,duk tsufa ko girman mace baka rasata da wasu halaye irin na quruciya,a hankali ya qarasa bayanta,kana ya sanya hannunsa ya riqo nata hannun ta baya.


Waiwayowa tayi ta dubeshi,saita sake dauke kai ba tare da tace komai ba ta maida hankalinta ga madubi,tana jin wani rauni yana ratsa zuciyarta
"Aisha" ya kira sunanta a tausashe,wanda ta jina rabon data ji hakan,kiran daya mata ya qarasa tsinka zuciyarta,sai kawai ya waiwayo gaba daya ta fada jikinsa gami da sakin kuka.


Tsam ya riqeta yana jin sautin kukan nata har zuwa wani lokaci ba tare daya hanata ba,sai data sassauta sannan ya janyeta zuwa bakin gadon ya zaunar da ita.


Kansa a qasa ya saki ajiyar zuciya,sannan cikin nutsuwa ya soma magana
"Ta kowacce fuska matuqar kana son ka zama cikakken adali,wanda zaka tsira gaban ubangiji ranar gobe qiyama,to ya zama qarqashin jagorancinka babu bambanci,hukunci yana iya hawa kan kowa a duk sanda ya saba tsari da qa'ida... Koda kuwa a karan kanka ne ka sanyawa ranka cewa hukuncin na iya biyoka ta kanka idan har hakan ta kama,babu babban soyayyar da zan nuna miki aisha daya wuce a duk lokacin da kika aikata ba dai dai ba na doraki kan hanya,na kuma nuna miki kurenki ta duk hanyar data dace,ta kuma yanayin da nasan ba zaki manta ba,kuma nan gaba ba zaki sake yunqurin aikata wani abu me muni makamancin haka ba,kin riga da kin gane kuskurenki tuni,tunda har gashi kin gyara,kin dawowa da azeez din iyalinsa har inda yake kwance kamar yadda kika nesanta su a baya"


"Aisha...kudi mulki ko dukiya duka zancan banza ne,duk da kike ganinsu masu qarewa ne wataran su barka daga kai sai mahaliccinka da kuma abinda ka aikata,duk d'an da yake masarautar kaisa ina masa kallon uswa aafiya aafra sumaira afnan nimra ko zunaira ne,wato kamar yaran cikina ne,dukkan abinda ka yiwa dan wani kamar naka ka yiwa,saboda Allah bazai qyale ba,sakamakonshi bashi da iyaka,xai iya juyewa kan yaranka a lokacin da wala'alla ma baka raye cikin duniyar"


"Abdul'azeez.....Allah ya baki yaro daya tamkar da dubu,yaron da bai taba sabamin ba kamar yadda kema bai taba saba miki ba,duk da yana da tsatstsauran ra'ayi,aqida tarin miskikanci da nashi tsarukan,amma akanmu yakan zub da wannan gaba daya yabi namu zabin da ra'ayin,koda bai dace da nasa ba,a matsayinki na uwa,a maimakon ki fahimci zurfin haquri da kawaicinsa,ki barshi yayi aure a sanda yaso,sai kikace a'ah...." Shuru yayi yana sauke ajiyar zuciya sannan ya dora
"Na godewa Allah,kuma ina godewa Allah da yayimin babban rufin asiri da kuma gata,ya tsaremin yarona daga sharri da dattin mummunan aiki,mummunan zunubi dake tarwatsa dukkan wata al'umma,komai kwanciyar hankalinta da wadatarta wato ZINA,zunubin dake tarwatsa ahali,ya gadar da baqinciki da baqinjin cikin wannan ahalin dama al'umma gaba daya,ni nasan ba wayo ko dabarata bace ta tsaremin shi,mahaliccina ya dubeni ne,ya dubi zuciyata,ban taba rabar diyar kowa ba da nufin aikata mummunan aiki ba,kamar yadda mahaifiyarsa take,shi yasa ya dubeni ya tsaremin nawa ahalin,na gode masa qwarai da wannan"


"A wannan lokacin da kika hanashi auren,idan da Alla ya qaddara mana jarrabawa,a yadda yake da tashen quruciya,da farinjini irin wanda nida ke duk bamuyi irinsa ba,Allah ne kadai yasa me xai faru,da wala'alla har yanzu yana cikin qazantacciyar rayuwar da ni dake duka bamu isa mu fiddashi ba,qila da wadan nan kyawawan 'yan biyun ba'a samesu ta hanyar halas ba,tunda Allah ya riga daya tsara lokacin haihuwarsu yayi,dalili kenan daya sanya wani lokaci nake baki uzuri dan qarami kan abinda kika aikata,lokacin zuwan yaran duniya ne yayi,kuma dole sai sun shigota"


"Yaro baya qanqanta da aure kamar yadda yarinya batayi,wani tunani da shirme ne maras tushe bare makama da muka azawa kanmu,wanda babu shi cikin adininmu face zallar yahudanci,wanda hakan ya jagoranci rayuwar al'ummarmu data yaranmu wajen rugurgujewa,kuma har yau mun kusa waiwaye muyi dubayya wa kusakurenmu mu gyara ba"

"Shin me yasa ba'a haramta zinar wuri sai auren wuri?,ba inda musulunci ya qayyadewa wani mutum shekarun da zaikai kafin yayi aure,akwai sahabin da yayi aure yana da shekaru goma sha bakwai kacal a duniya,randa aka kai mishi matar ya kwana da asuba aka fita yaqi dashi yayi shahada acan ba tare daya samu damar yin wankan janabar daya samu daga matarsa ba"


"Ta yaya mutanen da suka fimu tsarkin jiki zuciya dana zamani gaba daya zasu dinga aurarwa kamar yadda ya kamata,amma mu zamu rintse idanunmu,a dai dai lokacin da zamani ya lalace,mu aro aqidun mutanen da basa tsarkin kashi,basa wankan janaba,zina abar ado ce a wajensu,mutanen da suke qasqantattu,mutanen da Allah yayi alqawarin gadar musu da qasqanci ya zama tambari a garesu,mu dauki aqidar sai yaranmu sunkai wani matakin kafin muyi musu aure koda suna da buqatar hakan,a daidai sanda zamani yake sake lalacewa da tabarbarewa,bama tunani ko hango illar abinda zai faru,muna ganin kamar ci gaba ne,eh ci gaba ne,amma irin namai haqar rijiya,yana ganin haqarsa na zurfi saidai qara limewa qasa shidin yakeyi,koda yaushe karki bari magauta su tunxuraki ki aikata abinda ba dai dai yake ba,nafiki sanin yawan magautan da kike cikinsu,hagu da dama,gabas da yamma kudu da arewa,Allah ya doraki a kansu saboda jajircewarki,karki bari ki aikata abinda zai xame miki abun dariya da gwalo tir da Ala wadai"


"Naji dadi da kika gano kuskurenki aisha,kika kuma gyara,ina fatan hakan zai zamo darasi a wajenki" cikin gamsuwa da bayanansa,da kuma matuqar sanyin jiki take gyada kai,saita zame daga gefan gadon ta gurfana gabanshi
"Tun daga randa na hada wannan abun ban kuma samun cikakken nutsuwar ruhi na ba,kullum tunani da fargabar abinda xai je ya dawo nake,ko iya wannan nutsuwar da Allah ya ciremin tabbas ya horani,banda sauran abubuwan da suka biyo baya,ba shakka nayi nadama....nayi nadama ta gaske,ina fatan kaima zaka yafemin mijina,kayimin afuwa"
"Na yafemiki,Allah ya yafe mana gaba daya"
"Amin" ta amsa,saiya saka hannunshi ya dagata daga durquson da tayi yana cewa
"Miqe maza maza,kada barori da bayi suga uwar sarki zube a qasa" murmushi tayi tana rausayar da qwayar idanunta
"Nidin ba kowan kowa bace matuqar ina gabanka,wannan dukka suna tasiri ne a ayayin da bana gabanka ina tare da wasu mutane daban" murmushi ya saki sosai har fararen haqoransa irin na azeez suka bayyana,har abada yana alfahari da aisharshi,ta iya kalamai masu kwantar da zuciya,da sanya miji cikin nutsuwa.


*_ASIBITI_*



Shuru ne yaci gaba da wanzuwa bayan ficewar fulani daga dakin,saidai gaba daya jikinsa ya gama macewa,saboda yadda take mishi wankin qafar sai.yakeji kamar wani susa ko tafiyar tsutsa take masa,ya saki jikinsa gaba daga jikin filon daya kare bayanshi dashi yana ci gaba da qare mata kallo.


Babu abinda jikinsa ke buqata a lokacin illa yaji duminsa,ya kuma san cewa ba zata taba yarda tazo ta sauqi ba,don haka saiya saki qaramar qara yana rintse idanunsa gam.


Da sauri ta dago tana dubanshi,ganin tsahon minti guda shuru yasa ta motsa labbanta a hankali
"Mene ne?" Shuru ya mata bai amsa mata ba sai sake rintse idanunsa da yakeyi,shurun nasa yadan daga hankalinta,saita saki abinda takeyi ta tako gefansa a hankali
"Amm....nace lafiya?,menene?" Bata qara sakan guda ba ta tsinci kanta a qirjinsa,ya matseta gam yana sakin lallausar ajiyar zuciya dake nuni da cewa sai yanzu zuciyar ta samu nutsuwa,hannunsa ya dora saitin zuciyarsa
"Nan ne yakemin ciwo sarauniyata....." Saiya kama hannunta ya dora saitin wajen,sannan ya dora tafin hannunshi saman hannunta,dumin hannunsa ya ratsa har qwaqwalwarta,ya sanyata rintse idanunta ko zata samu sassaucin abinda takeji
"Bansan ya zan fasalta miki yadda nakeji ba kullum kwanan duniya bilqees....abinda na sani shine,tunda ammi ta kawoni duniya ban taba son wani abu makamancin son da nake miki ba,banyiwa saninki wani dogon zango ba,amma abubuwan da suka faru cikin gajeran zangon da mukayi tare dake shekaru dubu sunyi kadan su ginasu a zukatan wasu masoyan....don Allah" ya fada yana kamo habarta da hannunsa,wanda hakan ya bashi damar kallon tsakiyar qwayar idanunta,kamar yadda itama take kallon nashi idanun da suka wani narke,suke nuna zallar shauqi da shagala cikin duniyar soyayya,idanun da takeson ta daina kallonsu don kada suci gaba da yi mata illa amma ta kasa,kamar mayen qarfe,ya riqe ganinta cikin nashi ganin,yana kuma aika mata da wasu irin saqonni da duk juriya dakiya ko girman kan mace bata isa ta kubce masa ba,daya daga cikin irin tarin baiwar da Allah yayi masa,iya jefa soyayya cikin mintina qalilan a zuciyar duka wadda yaso.



Saiya sake qas da muryarsa,ya sanya bakinsa saitin kunnenta
"Don Allah....ki bani dama koda baki sona ne nemi soyayyarka da qarfin qwanjina,idan na kasa nida kaina zan baki dukkan damar da kikeso" kamar ta kurma ihu haka takeji soboda yanayin daya saukar mata,kanta takeson qwacewa amma ya zare duk wata laka dake jikinta,yana shirin sake furta wani abun bayan ya kuma kusantar da bakinsa cikin kunnenta aka tura qofar dakin.


Qarat faduwar wani abu dukka yaja hankalinsu,saiya daga kanshi yana duban qofar dakin,kamar yadda bilkisu data zame jikinta take duban qofar.


Matashiya ce wadda aqalla zatayi shekaru talatin zuwa da biyar,doguwa fara sol,idunta a warwaje kamar wadda aka watsawa barkono tana kallonsu,dukka jikinta ko ina rawa yakeyi,da alama magana takesonyi amma ta maqale mata a baki.


Ta fannin azeez safwa ya gani,saiya janye idanunsa daga kanta a hankali yana duban bilkisu da tuni ta tashi a jikinsa tana gyara rigarta daya cukuikuyeta,fuska a hade murya a dake kamar bashi ba yace
"Zoki qarasa wankemin,lokacin magrib ya kusa" daga kai tayi ya dubeshi da niyyar gaya mishi saidai ya qarasa,amma duba daya ta ma fuskarsa taga ba irin ta daxu bace,wannan a daure take tamau zallar kwarjini ya cikata,saita kasa masa musun,ta qarasa gabansa ta duwa ta riqe qafar,daidai lokacin da sautin
"Prince!!!!" Da qarfi ya fito daga bakin wadda ke tsaye bakin qofar.


A nutse ya waiwaya ya dubeta sau daya tak,saiya yaga hawaye ne ke saukowa saman kuncinta,a lokaci guda kuma tana girgiza kai,saikuma ta juya da gudu gudu sauri sauri tabar wajen.


idanunsa ya janye daga wajen yana lumshesu gami da jan tsaki,da mamakin sauyawarshi haka ya sanya bilkis daga kai ga dubeshi,tambayar fal ranta,wacece wannan din?,meye alaqarsu?,me yasata furgici haka da ganinsu tare,amma ganin bai sake wani motsi ba ita dinma saita share kawai taci gaba da aikinta,wanda wannan karon harta gama baice komai da ita ba,hakanan bai sake wani motsi mai qarfi ba,saidai fuskarsa kawai ta nuna kamar akwai alamun bacin rai haka.
7/11/21, 4:36 PM - My Mtn Number: 76

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070




Dukkansu tsaye suke a harabar asibitin ana gyara tsaiwar motocin da zasu wuce gida a cikinsu bayan likita ya rubuta musu sallama.


Gaba daya ya kafa ya tsare,hakanan yana gadin duk wani motsinta da idanuwansa cikin wani zazzafan kallo,saita basar taqi dubar sashen da yake,duk da tanajin tasirin kallon har cikin bargonta.


Sau tari takanyi mamakin kanta,takanji cikin jiki da ruhinta kamar ta jima da saninsa ko sabawa dashi,takanji komai nashi daban a zuciyarta,ta gaza cankar meye wannan din.


Dai dai lokacin da wasu barori suka qaraso inda suke,cikin girmamawa suka rusuna
"Ranki ya dade,fulani tace ki qarasa mota ki shiga ku tafi" azeez dake tsaye ada yayi gyaran murya,duk sai suka shiga nutsuwarsu,cikin wasu sakanni suka bar wajen.


A hankali yataka zuwa inda fulanin ke tsaye,yadan shafo sumar kanshi kadan sannan yace
"Da wai na dauka zamu wuce ne"
"Ina?" Ta fada tana balla mishi harara,saiya kasa amsa mata
"Ka turomin ita mu wuce,lokaci na qurewa" ta fada tana shigewa mota,kamar ya saki kuka haka ya dinga ji,amma babu yadda ya iya,haka ya juya murya a cushe yace mata
"Ki qarasa ammi na jiranki" batace komai ba ta soma takawa inda fulanin take,saidai tana ta qumshe dariyarta ne,sannan bugu da qari ita kanta hakan ya mata.


Shuru ne ya ratsa cikin motar sanda suke keta titin zuwa masarautar kaisa,wanda ta fuskanci ba xasu maidata gida ba kenan?,don ko anty zuhriyya da sukayi waya daxun a wayar fulani kamar abinda ta nuna mata kenan
"Abdul'azeez ya shaida miki yana da wata iyalin bayanke?" Muryar fulani ta katse mata tunaninta.


Kaman daga sama taji xancan,amma zuciyarta data gaya mata mutum kamar abdul'azeez din,matsayi daraja da daukaka irin tashi ace ace daman tsayin wadan nan shekarun bashi da iyali,don haka ta aro nutsuwa ta sanyawa kanta,sannan ta girgixa kai a nutse
"Bai gaya min ba" sai fulanin ta saki ajiyar zuciya,a hankali ta soma warware ma bilkisun irin yanayin da azeez din ya shiga bayan rabuwarsu,ciwon da yayi bayan ya amince zai rabun da ita kamar bazaiyi rai ba,da kuma aurensa da safwa.


Can qasan zuciyarta ta saki wata sassanyar ajiyar zuciya,tana jin yadda zuciyarta ke sake nutsuwa dashi,amannar data gaza bashi sai taji a yanzun ta bashi,wani girma qima da darajarsa ta dagu cikin idanunta.


Laifinsa dan kadanne,amma saboda girma da qimar mahaifiyarsa ya gaza gaya mata ainihin waye me laifin har kawo yanxu,sai data ji daga bakinta tukunna,lallai ya cika da na halas,domin kuwa kowanne mutum yunquri yake ya kare martabar mahaifansa a idanin duniya,komai tarin zunubi laifi ko lalacewarsu
"Ina fatan wannan ya wanke dan abinda yayi saura a zuciyarki,naga har yanzu jama yaron nawa rai da aji akeyi" ta fada cikin tsokana da barkwanci,duka sai taji kunya ta kamata,ta sunne kai kawai tana murmushi.


¶¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶¶¶


Cikin hikimar nan tata ta gama tsara yadda zata bayyanawa duniya yarima azeez da iyalinsa boyayyu wadanda ba'a sansu ba.


Tunda ta tafi da bilkisun ta hana kowa ganinta,daga ita sai afnan sai mutum biyu na musamman data dauko masu gyara bilkisun suke ganinta,sai kuma amintattaun hadimanta dakewa bilkisun karatu kan yadda gidan sarauta yake,yayin da ita kuma a gefe daya da kanta take xama ta koyama bilkisun hanyoyin kama zuciyar miji da kuma mallakeshi babu boka ba malam.


Abun na saka bilkisu cikin kunya mai yawa,tun tana kunya harta sake saboda ta soma sabawa da jin kalaman bakin fulanin,a hankali saita fahimci ita din macace me hikima da fasaha,Allah ya hore mafa dabaran zaman duniya,wanda lallai dole tayi xarra tsakanin abokan zamanta.


Ita kanta a jikinta tasan cewa akwai sauyi mai yawa,gyara ne data sameshi ciki da waje wanda ya sake bayyana zallar baiwar kyau da Allah yayi mata,ya kuma maisheta wata jinsi daban.


¶¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶¶


Zazzafar iska ya fitar daga bakinsa yana sauke wayar daga kunnensa bayan ya gama sauraren kalaman safwa,kai yake gyadawa kawai,kana daga bisani ya nitsa yatsun hannunshi cikin sumarshi.


Wai me yasa mata aduk sanda suka sanyaka a tarakunansu idan bakayi wasa ba dukka lissafinka saiya tarwatse,ba dauki matsalar safwa wani abu ba,amma ayau tabbas banda tana cin albarkacin ammi ne da bata isa ta gaya mishi wadan nan kalaman data gaya masa a yanzun ba.


Gefe daya ga bilkisu,yarinyar da yakejin ta jima da zams mahadi na numfashinsa bama rayuwarsa ba,wadda yakeji a yanxun itace duniyarsa,idan babu ita tabbas duniyarsa zata tarwatse ne gaba daya,saidai itama a yanxun ta masa tsada,ko sau daya ammi taqi bari ya ganta tun randa ta daukota daga asibiti,ta kaita wani waje daban ga boyeta,duk wayo da dabararsa amma ya gaza ganinta,da qyar yake samun barci sau tari,ga uban ayyuka da suka shafi kasuwancinsa,wadanda a yanzun suna tafiya ne slow sabida rashinsa a gurare da dama,yaci burin ya ragesu gami da gyara wasu abubuwan ko daga gidane kafin komai ya daidaita ya koma kan harkokinsa amma hakan ya gagara,bilkisu ta hana ruwa gudu gaba daya.


A wajen twince dinshi kawai yake rage zafi,wadanda ammin taja mishi kunne kan ko sau daya kada ya shigo dasu masarautar,tana jiran lokacin shigo dasu yayine,sanda ta shaidawa maimartaba ta kuma yi shawara dashi kan abinda ta shirya murmushi kawai yayi
"Aisha....aisha sarkin dabara,Allah ya bamu aron rai da lafiya" ya fada kawai yana dubanta.


Sosai yaran ke debe masa kewa,yakan kwashesu ya kaisu gidansa na musamman wato village,su kwana biyu tare,shike musu wanka ya hada musu abinci,idan kuma suna da abinda sukeson ci xaisa a musu order a kawo masa har gidan.


Wannan ya haifar da shaquwa da kuma sabo mai yawa tsakaninsu,jini ya soma aikinsa,soyayyar uba da 'ya'yansa ta soma zagayawa tsakaninsu,har wani lokacin sukan kwana su wuni basu tambayi mamarsu ba,sosai yake basu kulawa da dukka qarfinsa.


Miqewa yayi yana sanya hannayensa cikin aljihun wandonsa yana sauke ajiyar zuciya,yanajin ayauma zai gwada sa'arsa ko xai samu damar ganinta,ya zura wasu lausasan rufaffun takalma na sarauta a kyakkyawar qafarsa,sannan ya isa gaban madubi yana sake kallon kyakkyawar fuskarshi,wadda kwanakin baya ba haka take ba,a yanxun ta sake kyau saboda aski da gyara data samu,gami da nutsuwar samun abinda ruhinsa keso kusa dashi,fuskar tashi ya shafa yana sakin murmushi shi kadai,duk sanda yako tunata takan sanya murmushi saman fuskarsa,shi kansa yana jinjinawa irin son da yake mata,duk wani bacin ran safwa sai yaji cikin kaso dari babu kaso tamanin,juyawa yayi ya taka a hankali ya fice daga katafaren dakin gadon nashi.


Duk wanda yayi yunqurin masa rakiya dakatar dashi yakeyi,shi sam baison irin wannan bibiyar ta gidan sarauta,shi yasa yake tsara yadda zai kwashe iyalinsa gaba daya suyi gaba,suje su bude rayuwarsu iyasu isu,babu takurawa bare sanya idanu ko matsi.


Tunda ya shiha sashen fulanin suke zubewa suna miqo gaisuwa har ya dangana da falonta na qarshe.


Babu kowa cikin falon sai afnan dake zaune tana kallo,ta daga kai a hankali tana amsa sallamar da yayi wadda take ciki ciki kamar wanda aka yiwa dole,dama tasan idan bashi ba babu me aikata hakan,yana daga tsayen ya tambayeta
"Ammi fa?"
"Bata nan,tadan fita"
"Ina princess?" Ya sake tambayarta yana kallonta kanshi tsaye,sarai tasan da wadda yake,amma saita dake ta kuma gimtse kamar bata gane ba,bayaga haka ammi ta ja mata kunne karta bar kowa ya ganta ma,yanzun nan ta shiga ciki daura alwala da wala'alla yadda basusan da shigowar nan tashi ba ya cimmasu tare
"Wa....?"
"Keep quit,ni abokin wasanki ne?" Ya fada a hankali yana fidda mata idanun nasa masu tsananin kwarjini,take ta shiga taitayinta,ya kuma tuna mata yariman na asali,qasa qasa cikin qunquni take fadi bayan ta nuna masa dakin da yatsanta
"Ni ina ruwana,ni nakar zomon?,ko ratayar ma ni ba'a bani ba" baijita ba,don tuni yasa kansa cikin dakin cikin sauri kamar wanda za'a kama.


Tana tsaye baki mirrow tana goge ruwan alwalar dake fuskarta,wanda saboda tsabar kyau da gyara da fatarta ta samu ruwanma bai zama sosai saman fatar tata,ta gama ta dauki comb ta gyara gashinta daya wargaje wajen shafar kai,tana qoqarin maidashi ta hadeshi waje guda ta hangeshi dab da bayanta ta cikin mudubin,saita zaro idanu tana niyyar juyowa,saidai tuni yayi caraf ya kama qugunta ya kuma mannata da jikinsa,cikin taushi da sanyi ya dora kanshi saman kafadarta,bakinsa da hancinsa duka suna sansanar wuyanta,wanda hakan ya sanya tsigar jikinta tashi lokaci daya,hakanan ya kashe dukka wata laka ta jikinta,saitayi collapes cikin jikinsa,tana tsintar kanta itama da kallonshi ta cikin mudubi kamar yadda yake duban qwayar idanunta shima.


Kamar masu kallon quda haka suka dinga kallon juna ta cikin madubi tsahon lokaci,kowannesu saida jikinsa ya gaya masa sannan ya juyo da ita suna fuskantar juna,still idanunsa cikin nata,ya sanya hannu ya gyara mata gashinta daya sauko gefan fuskarta,cikin sanyi ya sunkuya ya sumbaci tausasan labbanta kana yace
"Ko kadan baki kewata madam?,dake za'a hada kai a sake bani wahala ko?,kina so ne na sake komawa gadon asibiti karo na biyu?" Maganar tasa sai taso bata dariya,ta saki murmushi
"Gadon asibiti kuma?" Gira ya dage mata
"Eh yes,gadon asibiti" dan qwace jikinta tayi tana murmushi gami da bashi baya
"Nifa gaskiya ban shirya zama da ragon namiji ba" sake kamota yayi,don tsaiwarsu ta mishi dadi,baison ta raba jikinta da nashi,cikin zuciyarsa yasaki murmushi yana taune lips dinsa kadan na qasa,shi kadai yasan meya tuna sai yace
"Aiko ki shirya zama da raggo,don a kanki kam bani da wata juriya ko kadan....but saidai kinsan a inda ragwantaka take aiko....i mean ba ainihin ragon da kike magana bane,tunda kin dan shaida idan xaki iya tunawa...." Saiya duqa saitin

Please Login or Register in order to submit comment