Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yana tare da mai martaba,abinda ya rage kawai ya wuce zuwa ciki inda akewa manyan mutane irinsa nasu screening din,idanuwan azeez na biye dashi sanda yake wucewar,duk da ranshi a cushe yake amma hakan bai hanashi jin qaunar mahaifin nasa ba,tare da ayyana abubuwa da dama tattare dashi.


Wani irin mutum adali,wanda bai dauki duniya da zafi ba,inda shine ke riqe da ragamar rayuwarshi,yake kuma bibiye da al'amuransa sabanin ammi abinda ya faru dashi zaya farun?,ya jefawa kanshi tambayar da baya da amsarta,saiya kada kai,abinda ya sani kawai shine,qaunarshi ta rufewa ammi idanu,har take ganin duk abinda takeyi saboda shine,kuma bisa dai dai take,amma sai yaushe ne al'amura zasu gyaru?.


Ajiyar zuciya ya sauke yana shirin dauke idanunsa daga inda maimartaba ya wuce wanda tuni ya bacewa ganinsa.


Karaf idanuwansa suka sauka a kanta,cikin kaduwa mamaki da bazata ya qanqantar da idanun nasa yana son tabbatar da gaskiyar abinda suka gano mishi,naci ya sanya sosai tare da sake matsawa kadan daga inda yake tsaye don kuma tabbatar da zarginsa.


Itace a tsaye ana duba passport dinta,sanye cikin doguwar riga saqar qasat dubai mai matuqar kyau da daukar idanu,duk da yalwar rigar amma hakan bazai hanaka hango cikinta daya bullo ta cikin rigar ba,yakuma zauna sosai bisa jikinta,idanunta itama nakan passport din kamar yadda idanun me dubawar yake,bai ankara ba yaga ya miqa mata passport din da dukka sauran kayanta wanda hakan ke nufin xata wuce kenan,zata wuce ciki inda babu lallai ya ganta,idan ta wuce ina take shirin tafiya?,wacce qasa zata?,bai sani ba,amsar daya baiwa kansa kenan,amsar data sanyashi zabura cikin matuqar zafin nama da karsashi ya durfafi wajen,duk bashi da tabbacin cimmata kafin yakai wajen saboda 'yar tazara da dan cunkuson jama'a dake wajen.


Kamar wanda ya fice a hayyacinsa haka ya dinga kutsa jama'a yana neman hanya,wanda hakan ya ja hankalin mutane da dama suka dinga binshi da kallo,wasu da yawa daga cikinsu sunsan wayeshi,sunsan matsayinsa,hakan ya sa ya suka dinga mamakin abinda yakeyi din,saidai shi sam ba wannan bace damuwarshi,damuwarshi ya samota kafin ta bace,damuwarsa ya cimmata,damuwarsa ya ganta a gabanshi,damuwarsa suyi magana,damuwarsa cikinsa dake jikinta,ya tabbata cewa yayi dashe kenan a tattare da ita.


Saidai ko kodan burinsa bai cika ba,domin yana ganota sanda aka bata boarding pass ta bace masa kamar yadda mai martaba ya wucewa ganinsa,duk da hakan bai fasa niyyarsa ba,har yaso tsallake shingen da aka sanya,wanda hakan yaja hankalin jami'an tsaro cikin mamakin ko babu lafiya suka taso suka dakatar dashi suna tambaya,wanda tambayar ya dinga jinta kamar wani qarin bacin lokacin da datsewar burinsa ne,ya dinga fidda numfashi mai zafi yana son su matsa mishi yakai gareta.



Hannunsa da daya daga cikin manyan hadiman mai martaba ya riqe shiya sanyashi maida hankalinsa jikinsa,ya waiwaya ya dubeshi cikin girmamawa da rusunawa yace,murya qasa qasa ta yadda shi daya zaiji
"Allah ya taimakeka dukka idanuwa suna akanka,ko meye kayi qoqarin daidaita yanayinka,saboda girma da qimar masarautar kaisa,da kuma gudun bacin rai fulani" wannan maganar ta sanyashi sauke nannauyar ajiyar zuciya wadda yakejin kamar anyi ajiyar dutse ne a qirjinsa,yanajin tamkar ya bangaje duk wanda ke tsaye a gabanshi ya ganshi ya cimmata,babban burinsa kenan,bai damu da dukkan wanda zai kalleshi ba,amma maganar data fito daga wane sashe na zuciyarsa ta sanya bai aikata hakan ba
"Ganinta anan din tamkar wata nasara ce a gareka,kuma haske ne da zai kaika ga inda zaka cimmata", da wannan kalaman jami'an suka samu suka tafi dashi xuwa wani kebantaccen daki,suka soma bashi kukawa ta musamman kafin su nemi jin damuwarsa.


Sam bai damu da ababen sanyin da aka ajjiye masa ba cikin katafaren office din,gaba daya hankalinsa ya karkata ne kan wanda ke binciken list na sunayen passingers din da suka tashi yanzun bada dadewa ba,wanda dama duka duka a yau din jirgi biyu ne kacal ya tashi,biyu ya sauka,ji yake kamar ya finciki na'urar zuwa gabanshi,gani yake kamar baya sauri,haka ya dinga dunqule hannunshi waje daya yana tausar kanshi da gayawa kanshi ya nutsu,yabi komai a hankali.


Tsahon wasu mintuna da suka biyo baya kafin mutumin ya dago daga allon na'urar,ya zauna sosai yana duban yarima azeez da kuma shugabansa dake zaune gefe shima,a ladabce yace
"Cikin jirgi na biyu daya tashi yanzun tabbas akwai mai suna bilkisu,kuma kusan ita kadai ce ma mai sunan....."
"Wacce qasa ya nufa?" Azeez yayi hanzarin tambayarshi ba tare daya barshi ya kammala jawabin nasa a karan kanshi ba,don ji yake dukka wani bayani da mutumin yake kamar bata lokaci ne,kamar bashi da amfani.


Ganin yadda yanayinsa yake a qagauce yasa shima ya bashi amsar tambayarsa kai tsaye
"Ethopia"
"Ethopia?" Ya samu kanshi da tambayar kansa da kansa,idan yace zai tsananta tunanin abinda zataje yi can din tabbas ya yaudari kansa ne,bai gama sanin wacece ita din ba totally balle yace yasan wani abu daya shafeta,wanda zai bashi hasken tana da alaqa da canne ko 'yar can ce,abu guda daya ne da yakejin zai zame masa mafita shine,ya yanki ticket yabi dukkan wani jirgi da aka samu zashi qasar daga yanzu zuwa kowanne lokaci
"Qasar ethopia nada girma da fadi,bawai qaramin gari bane qwaya daya da zakace kana sauka zakaga wanda ya santa koya hadu da ita ya nuna maka inda take,idan kaje ina zaka dosa?" Zuciyarsa ta antayo masa da duka wadan nan bayanan da rudu yasa yaso mancewa dasu,yanaji cikin zuciya da gangar jikinsa cewa zai iya qarar da dukka numfashinsa wajen nemanta koda baisan inda take ba,to amma hanya mafi sauqi da kwanyarsa ta yi masa hasashe shine,gidansu nan ne muhalli qwaya daya tak da xai samu sahihin inda zai sameta acan inda ta tafin ba tare da jinkiri ko bata lokaci ba,jinkirin da yakejin duk bayan shudewar wasu mintuna kamar yana shudewa ne da farincikinsa,walwalarsa da kuzarinsa,yanajin kamar bashi da dukkan wata jarumta da yasan kanshi da ita.


Da wannan shawarar ya miqe,ya miqa godiyarsa garesu cikin qasaita ya soma barin office din,yana jin wannan karon koma meye zaya faru saidai ya faru,amma babu shakka zai nemo ladingo a duk inda take,zai kuma sanyata ta nuna mishi gidan mahaifan bilkisun,bayajin zai iya jurewa wannan asarar cikin rayuwarshi,idanuwansa sun gane mishi gaskiya da sahihancin abinda ammin ke kokwanto akai,me kuma yayi saura?,har cikin zuciyarsa yana jin wani feeling idan ya tuno fuskarta da cikinsa dake zaune a jikinta,yana jin wani irin yanayi mai nauyi da wuyar fassara idan ya tuna fuskar macen data taba masa sunan matarsa da kuma cikin dake amsa sunan dansa jininsa ne kwance a wajen.


Tunda ya koma gida bai yadda ya hadu da kowa ba,tsarinshi duka shine inda za'a nemo ladingo duk inda ta shiga a masarautar kaisa,sam yama mance da batun bar mishi kula da qasar shida waziri mahaifin abdulrashid da me martaba yayi,don hankalinshi ba'a jikinsa yake ba.


Kwana guda da wuni guda kafin a lalubo mishi itan cikin sirri da boyewa,baya son batun yakai kunnen ammi bare ta samu damar dakatar dashi,yana son kome zai faru ya faru bayan ya cimma gaci.


Tunda masu tahowa da ita zuwa sashen nashi suka risketa gaba daya jikinta yayi sanyi qalau,gabanta ke dukan uku uku,tasan cewa kashinta ya bushe,kuma tata ta qare kenan,saboda bata manta da gargadi da kuma jan kunne da babbar murya da fulani tayi mata ba,bayan ta sauya mata sashe ta dauketa daga cikin gidan sarautar gaba daya,to amma matuqar yarima ke buqatar jin wani bayani daga bakinta tasani cewa akaran kanta bata da zatin da zata iya jaa da kwarjininsa,bare har ta musawa buqatunsa,da wannan tunanin suka iso cikin sassan azeez cikin duhun bayan isha'i,suka ajeta a inda ya buqaci ganawa da ita kafin ya fito,taci gaba da zaman jiranshi cikin fargaba da rudani,ko ina na jikinta rawa yake kamar kazar da aka tsoma cikin ruwan qanqara aka ciro.


Takunshi kawai ya isa ya sanya dukkan wani dake wajen ji a jikinsa,a jininsa yake kuma halittarsa ce,tarin kwarjini da haiba wanda mutane da yawa kan camfa,wasu suce siya masa akayi,wasu suce akwai kalar dabbar da yake ci wanda hakan ke qara masa kwarjini kulli yaumin.


Tun baiyi magana ba ta sake rusunawa sosai tana miqa gaisuwa cike da tsantsar ladabi,kanta a qasa bakinta yana rawa,bai amsa mata ba,saidai ya baiwa dukkan wani mahaluki dake wajen umarni da ido nasu basu waje,cikin qiftawa da bismillah wajen ya zamana daga shi sai ita,ya gyara tsaiwarshi sosai yana dubanta na wasu sakanni,sannan kai tsaye ya jefa mata tambayar data zama silar zuwanta wajen
"Idan kin amsa min babu qarya ko boye boye to ba shakka kin kubuta,ki cire dukkan tsoron wani daga zuciyarki ki bani amsar tambayoyina dai dai,wannan shine kawai mafita a rayuwarki"
"Allah ya taimakeka.....ya qara maka nisan kwana sarkin gobe.....ya qarawa mai martaba daraja da daukaka.....ya qarawa fulani lafiya.....ba shakka kome zaka buqata daga wajena....nidin me biyayya ce ga umarninka" kai ya jinjina yana sauke numfashi,cike da sarauta yace
"Kece mutum daya tak da kikasan gidansu....ina ne gidan mahaifanta?" Ko bai fito baro baro ba tasan wa yake nufi,zuwa yanzu tana jin kamar gudawa zata qwace mata,ko bai gargadeta bama ba zata iya musu dashi ko yi masa qarya ba,tasan cewa wutsiyar raqumi tayi matuqar yin nesa da qasa
"Tana nan unguwar hayin malam amadu Allah ya taimakeka" shuru yayi yana hasashen unguwar da sunanta,bazai iya tuna wacce unguwa bace,mutumin da baiyi cikakkiyar rayuwa cikin masarautarsa bama ina zai san wasu anguwanni cikin qasar tasu,saiya katsewa kansa wahal da tunaninsa da yakeyi yayi magana ta qarshe da ita yana mai takawa yana barin wajen
"Ki zama cikin shiri" iya abinda ya gaya mata kenan ya wuce zuwa ciki.


Cikin dare saiya dinga ganin dare yayi masa mugun tsaho,tamkar gari ba zaya waye ba,kamar safiya ba zatayi ba,wani irin dare ne daya cika fal da mafarkinta da kuma tunaninta,uwa uba kuma tunanin cikin dake jikinta wanda yayi imanin babu tantama ko kokwanton cewa nashi ne.


Baiyi barci ba sai daya kira abdulrashid ya shaida masa komai da kuma aniyarsa na zuwa gidan gobe da kanshi,gami da neman rakiyarsa
"Ko baka fadi ba yarima zuwa ya zama dole"
"Amma inaso mu tafi da mota daya zuwa biyu,itama idan da hali daga cikin motocin gidan mai girma waziri,banason ko kadan motar masarauta ta shiga wajen,don banson labari ya zowa ammi har sai na gama aiwatar da abinda na qudurta"
"Baka da damuwa man" ya amsa mishi cikin qarfafa gwiwa.


******* **** ********


Duk yadda ya dokanta da zuwan washegarin sai gashi tazo mishi a baibai,ta kuma zo mishi da sakamakon da yake gani shine mafi muni cikin kowanne sakamako da aka taba bashi a rayuwa.


Ko cikin motar kallonshi kawai abdulrashid yakeyi,baisan da wanne harshe zai lallasheshi ba,dukkan wanda yasan azeez dakiya irin tashi,jarumta da taurin zuciya,zaiyi mamaki qwarai idan yaga yadda ya sauya lokaci daya,daga sadda jerin gwanon amsoshin suka shiga kunnuwansu
"Tabar qasar jiya ko shekaran jiya,babu kuma wanda ya sani ko yake da masaniyar inda taje ko zataje a can din". Amsoshin dashi kansa abudulrashid suka bashi mamaki,bare azeez daketa jujjuya maganganun cikin kwanyarsa.


Ta yaya ɗa ba bawa ba za'ace ba'asan inda ya tafi ba?,shin bata da mahaifiya data damu da ita ne?,wanne irin mahaifi gareta da zai bar diyarshi tafiya zuwa wata qasa bashi da tabbacin muhallin da zata tsinci kanta?.


Hannunsa dake dunqule tun daxun ya saka ya daki kujerar gabashi,yana jin wani zafi zugi da radadi na ratsa ilahirin jiki da zuciyarsa,amsoshin da aka bayar kamanceceniya suke da ana masa bushara da ya rabu da shukar daya dasa,shukar dake mallakinsa wani bangare na jikinsa,da ko yarsa zasu zama basusan wayeshi ba.


Wasa wasa kafin sukai gida saiga wani irin zazzabi yana neman lullubeshi,tun abdulrashid na daukan abun wasa sai yaga da gaske ne,amma sam azeez din ya hana a shaidawa fulani,duk data aiko jin lafiyarsa saboda rashin ganin gilmawarsa wunin jiya dayau gaba daya,yace a shaida mata lafiya qalau yake,bata kawo komai a ranta ba,saita aza hakan da nauyin da maimartaba yabar musu ne na kula da qasa ya kawo hakan,ta saki murmishi tana jin dadi har cikin zuciyarta,tanajin cewa ko a yanzun babu ko tantama taci riba wajen maqiyanta.


*_BILKISU_*


Tun tana kuka saboda farincikin tarin dangi da gata da suke dashi ita da mahaifiyarta har hawayen suka daina zuba,sai.mamaki daya cika zuciyarta taf,ta sake yarda da cewa mahaifiyarta ta daban ce,hakanan zuciyarta mai tsarki ce,samun irinta cikin matan wannan zamanin abu ne mai matuqar wahala,ta yarda tabar dukkan wani daula jin dadi da arziqi na mahaifanta da danginta ta zauna da mahaifinta,mutumin da ko cikin ma'aikatan gidan akwai da yawa da suka fishi arziqi,amma sam bata duba wannan ba,ta martaba soyayya ta gaskiya,ta bata qima da daraja ta zauna dashi,to amma shin shidin ya biya ta?,ya saka mata da dukkan tarin alkhairinta da kara da yakanar data yi masa a rayuwa?.


Tamkar xasu cinye bilkisu haka kowa ke haba haba da ita,ta sake yadda tabbas maimunatu ta musamman ce cikin danginta sanda taji anty zuhriyya tana qorafi
"Wato kunga makwafin maimunatu shine za'a koma 'yar gidan jiya,aci gaba da nunamin wariyar launin fata ko?,wannan karon kota ni ba'ayi,dadin abundai nidin dai nice na kawo muku ita" ta fada cikin tsokana da zolaya,wanda bilkisu ta lura tafi bada qarfin tsokanar tata ga jakakarsu,wadda ta haifi mahaifinsu,wanda ita daya tal ta rage musu,da alama kuma tare ta rayu dasu tun quruciya tasan quruciyar kowa a cikinsu
"To dama an gaya miki akwai abinda zai ture gwamnatin maimunatu ne a wajena duk da bata a duniya?,ai babushi" yanayin yadda tayi maganar xai gaya maka cewa,duk da tarin tsufanta amma hakan bai hana mutuwar maimunatu sukar zuciyarta ba,uwa uba mutuwar mahaifin maimunatun kanshi bisa dukkan alamu itama bata barta ba,duk sai jikin kowa yayi sanyi a wajen,don har abada ba zasu manta da mutuwar uba da diyarsa ba da suke ababen soyuwa a zukatanta.


Duk yadda zata fadi kasancewarta cikin danginta a ethopia tasan baki yayi kadan ya bayyanashi,girma da tsadar lokuttan qauna kulawa da tattali ya sata ta manta duk wani qalubale data taba fuskanta,takan manta meya faru da ita a yawancin lokutta idan ba cikinta ta shafa ba,wanda yake yin wani irin girma naban mamaki,saidai hakan bai fiya damunta ba,saboda lafiya qalau take jinta,tamkar bata sha fama da azabar laulayi ba kamar bazata kai labari ba.


Sanda suka gama satittikan da suka tsara yi sannan su wuce brasil sai sukaso riqe bilkisun,saidai anty zuhriyya tace samm qafarta qafar bilkisu,akayita ja amma taqiya,daga qarshe abbu yace su barta,don yadda ta kafe din baijin akwai abinda zai sauya ta.


Suma din basuga laifinta can ba,tunda ita tadauko musu ita ta kawo musu,bai kyautu su gwada qarfin dantsensu suce saisun riqeta ba,tsohuwar ta dungure kanta tana cewa
"Ja'ira,har yanzu taurin kai kafiya da tsiwar tana nan,ta yaya bazanfi son maimunatu ba?"
"Eh din,nadaiji" itadai bilkisu na gefe tana murmushi,yanayin yadda suke qaunar junansu tana burgeta,waiyau ita bilkisu ce ake rububin daukarta,ana gasar nuna mata soyayya da gata.


Lallai duniya labari ce,hakanan dukkan tsanani yana tare da sauqi,tunda ko hakane,indai ta manta dukkan wata damuwa da barazana da rayuwarta ta fuskanta a baya,babu abinda xai hana ta shimfida sabuwar rayuwa da zata baro dukkan wani miki data taba samu cikin zuciyarta,duk da tasan cewa an bar mata babban tabon da bazai taba warkewa kota manta dashi ba,saita dora hannunta ta shafi cikinta da a satittikan nan yake yawaita motsi,motsin da aduk sanda suka yishi take sake ganin girma isa da buwayar mahaliccinta daya sanya dan adam cikin dan adam,ya kuma rayashi ya maidashi mutum cikakke.


Kwanaki uku suka qara suka tattara suka wuce brasil,yanayin rayuwar can din yayi mata dadi qwarai,ya kuma sake mantar da ita abubuwa da yawa,ta samu isashshen lokaci ta tsarawa kanta dukkan abinda takeson gabatarwa,da kuma abinda takeson zama anan gaba bayan ta rabu da cikin jikinta,kusan komai sai data tsarashi,wani cikin kwanyarta,wani kuma a rubuce,sannan ta tattara ta miqawa Allah lamuranta,ta kuma duqufa da addu'ar ya cika mata dukkan burikanta data qudurta,tare da bara da roqon kada ya sake qaddara wani abu da xai gilma ya sake ruguxa mata mafarkinta.


*_YARIMA ABDUL'AZEEZ_*



Dukkan wata juriya da jarumta tashi ta qare,kamar yadda tunaninsa kan yadda zai nemota ya qure,zazzafar damuwa ta kwantar dashi,ciwo sosai wanda yake jinsa cikin kowanne lungu da saqo na jiki da zuciyarsa,yana jin zuciyarsa ta masa wani irin qunci,yakanji zuciyarsa tana radadi da ciwo,wanda yake saka ran nan gaba kadan komai zai iya faruwa da zuciyarsa.


Ciwon nashi ya sake daga hankalin ammin sosai,hakan ya sanya ta saka ido sosai kan duk wani lamarinsa,sanya idanun da yayi sanadin binciko abinda ya boye,ya bayyana a gareta yaga bilkisu,ya kuma shiga fafutukar nemanta.


Sosai hankalinta ya tashi,ta rasa inda zata sanya rayuwarta,wai meke faruwa ne?,me yake faruwa?,me yasa azeez ya kasa cire yarinyar daga rayuwarshi?,me yasa ya kasa ajeta gefe yaci gaba da rayuwarsa kamar yadda tayi hasashe ta kuma tsara?.


Hankalinta ya sake tashi sanda ta tuna da zancan safwa,qorafin data kawo mata cikin wancan satin,duk zuwan da take duba azeez yaqi bari ta ganshi,hakanan duk wani kiran waya ko saqo da take aika masa babu feedback ko guda daya,saita alaqanta hakan da rashin lafiyarsa,ta kuma bashi uzuri tare da alqawarin dai daita komai.


Saidai abinda basu sani ba shine,tuni ya yankema ranshi cewa,matuqar ya zauna ya rayu da wata macen cikin nutsuwa da kwanciyar hankali,tamkar ya tafka wani mummunan zalunci ne ga rayuwar wata halitta da bata taba zaluntar tashi rayuwar ba,tamkar ya fasa gobensa ne.


Wadan nan bayanan data samu ya sanyata ta gaza zama,qarfe goma na dare ta shirya daga ita sai kubra ta nufi sashen yarima azeez,ranta a matuqar bace,zuciyarta a dugunzume,tana jin cewa wannan karon zata masa mai gaba daya ne,zata masa mai dungurun gum,zatayi masa ta yanke ta gille mai gaba daya haihuwa da hanji.
7/11/21, 4:33 PM - My Mtn Number: 47
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070



Dai dai lokacin da yake zaune shi daya cikin katafaren falonshi labarin isowar fulani ya riskeshi,ya daga kai ya dubi agogo sai yaga goma harda mintuna na dare,hakan ya bashi mamaki qwarai tare da tabbatar masa lallai muhimmin abu me girma ne yake tafe da ita,sai ya miqe zuwa cikin bedroom dinsa,ya sanyo wata jallabiya ruwan gold mai dogon hannu santsi da sulbi da kuma daukar idanu,sannan ya dawo zuwa cikin falon.


Koda ya dawo tuni ya isketa tsaye tsakiyar falon,goye da hannayenta,idanunta na duban qofar dakin gadon nashi,kallo daya zaka yiwa tsakiyar idanunta kasan cewa ranta yakai qarshe wajen baci,hakanan fushi ne kwance rubuce saman fuskarta.


A nutse yayo tattaki zuwa gabanta,ya rusuna a ladabce yace
"Barka da dare...." Bai qarasa ba ta daga mishi hannu,cikin kakkausar murya ta soma magana
"Ni na dauki cikinka cikin qunci da wahala wata ɗai ɗai ɗai har watanni tara cif,ba tare dana sauke na huta ba harsai da kakai wadan na kwanakin,na tsugunna na haifeka cikin rashin tabbacin zan rayu ko bazan rayu na,nice cinka shanka,fitsarinka,lafiyarka da lalurarka,idan kayi dariya nayi,idan kayi kuka nayi,idan kana da buqatar abu sai inda qarfina ya qare,nakan haqura da komai idan baka sonshi,hakanan nakan dauka kona rungumi duk abinda kakeso,ban daina dawainiya dakai ba da kula da dukkan lamuranka,da kuma duk wani abu da zai cutar dakai ba har kawo yau da kake da shekaru ashirin da shida a duniya......amma yau.....ni aishatu nizan maka umarni kan wasu abubuwa ka nemi bijiremin?,wai shin?,me kake nema wajen yarinyar da babu shi ga sauran mata da har xaka gagara fitar da ita daga rayuwarka kamar yadda na tsara na kuma buqata abdul'azeez!" Ta qarashe maganar cikin daga sauti dake cike da bacin rai,abinda kusan bazai iya tuna yaushe ya taba faruwa tsakaninsa da ammi ba,hakan ya sanya ya sake sadda kanshi qasa,yana jin wani rauni yana mamayarsa,zuciyarsa tana kakkaryewa gami da tsinkewa kamar zare,yayim da sautin muryarta yaci gaba da ratsa falon cikin bacin rai
"Kome zanyi nayishi ne saboda kai wanda kai din na zaka taba fahimtar hakan ba sai nan gaba!,ni na kawo yarinyar cikin rayuwarka nace kuma ta fita,na kawota a sanda baka santa ba bakuma kayi zata ba,a yanzu kuma nace bana buqatar hakan!,shin ka shirya fito na fito dani ne abdul'azeez?!" Ta saje jefa masa tambayar cikin fada sosai,wanda ya sanyashi zamewa saman gwiwoyinsa ya tsugunna anan gabanta,yana jin fadan nata har cikin jininsa,yana iya jiyo sautin bacin ranta daga zuciyarta,cikin taushin murya yace
"Ammi....maganar da sukazo miki da ita kikaqi gasgatata gaskiya ce,zancan yarinyar tana dauke da......"
"Ya isa!....ba wannan naxo ji ba,na jima da bunne batunta,na jima da bunne duk wani daya shafeta,saura ya rage naka,idan aure ne matsalarka.......ka shirya aurenka da safwa nan kurkusa,amma ka sani,dole kaje kayi karatu tuquru ka zama wani,dole matsayin da nakeson ganinka akai ka takashi,dole ka manta da an taba yin wata halitta cikin sa'o'in rayuwarka mai suna bilkisu...inhar ka shirya ci gaba da kasa cewa a sunan dan aisha diya ga sarkin mali!,idan kuma ka shirya cire jinina daga naka!,ka shirya sauya uwa to kaci gaba da dorawa daga inda ka tsaya,ni dakai aga wanda zai fasa abdul'azeez,kaci gaba nace!,amma ka shirya sauya wata uwar bani ba!" Daga haka ta juya tayi tafiyarta ba tare data tsaya taji koda kalma daya daga bakinsa ba,ba tare data waiwaya tayi masa duba na biyu ba,ta dinga takawa tana jin bacin rai sosai da tsanar bilkisu,yarinyar tana son zame mata qarfen qafa,tana son ta zame mata wata katanga daga cikar burikanta kan danta datasha wahalarsa,me yasa tun farko nata sauyawa bilkisun qasa ba ta yadda ba zasu sake haduwa da azeez din ba,banda kyau na fuska bata san kuma bataga wani abu da zaija azeez zuwa gareta ba,me yarinyar keda shi haka?,ta yiwa kanta tambayar da bata da amsarta.


Tunda ta fita bai motsa daga inda yake tsugunne ba inda ga barshi,ji yakeyi kamar wanda ake watsawa ruwan qanqara,tun daga saman kanshi zuwa yatsun qafarshi,a rayuwa bashi da kamar ammi,hakanan babu kamar uwa cikin rayuwar kowacce halitta,kama daga mutum aljani dabba tsintsaye qwari harma da tsirrai,dukkanin wanda zai soka to bazai maka koda kwatankwacin soyayyar datayi maka bane,itace ta soka tun baka zama mutum ba,tun bata sanka da idanu ba,bata taba ganinka ba,kana boye cikin fatar cikinta amma take qaunarka,har kazo duniya baka da hankalin bambance mai kyau da mara kyau,harka zama cikakken mutum da kowa ke qaunar ka rabeshi,akwai soyayyar datafi wannan?.


To amma abu mafi daure kai shine,ina wannan tausayin na daa da uwa?,ina wannan soyayyar?,duka ammi ta

Please Login or Register in order to submit comment