Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tagama aikinta gida take tafiya koda qarfe nawa ne,ta qaraso tasamu umma luban cikin falonta tana zaune ta qurqurar tv dinta a gaba tana kallo,a zahiri kallo take amma a badani tana tsara yadda zata tunkari bilkisu da maganar ne,harta fahimta takuma amince.


"Au....kin gama kenan?,aida kin tsaya,albashinki nakeson biyanki,kuma inaso muyi magana dake" tafada tana miqewa daga kwanciyar datake,ta janyo jakarta wadda bata rabo da ita a qugunta tazuge,tamkar an yiwa bikisun rahama haka taji,don sam bata tsammaci samun albashinta a yanzu ba,idan tasamu ma to nan sa kwanaki bakwai ko goma masu zuwa ne a lissafinta.


Kudade ta lissafo ta miqa mata,saidai tun kafin takai ga karba tasan cewa kudin kamar sunfi adadin albashinta,karba tayi ta cire kudinta kana ta miqawa umma luba sauran
"Kudin sun haura,na dauki nawa" kai ta girgixa
"Babu komai bilkisu,ki riqe duka" juya kudin tayi fuskarta cike fal da mamaki,a qalla kudin sun doshi dubu goma harda albashinta,mamakinta ya kasa boyuwa,ta daga idanu tana duban umma luban,sai tayi mata murmushi kana ta gyara zama
"Wannan ba komai bane maigado,nan gaba kadan wala'alla ke zaki dinga kyautar kamarsu koma sama dasu,wataqil nan da wani dan lokaci kadan ire iren wadan nan kudaden canji ne a wajenki ba wai kudi ba,amma dukka hakan zata farune idan da amincewarki da kuma yardarki".


Gaba daya kamar ta sanya zare da allura ta dinke qwaqwalwar bilkisun tsaf haka taji,bata gane komai daga cikin maganar da take gaya mata ba,saita samu kanta da zubawa umma luban idanu qur kamar zata samu amsar tambayarta ne saman fuskarta,karo na farko kenan tun sanda suke tare.


"karki damu maigado,yanzu zan miki bayani" cewar umma luban tana sake matsowa daura da bilkisun gamida tattara hankalinta waje guda
"Maigado,wata dama ce tasamu,wanda iya hangena da hasashena babu wadda ta dace da samun wannan damar saike,saboda dama ce dazata fidda ki daga qangin da kike ciki ke daduk wani wanda ya jibanceki,zaki rayu irin rayuwa ta gata keda 'yan uwanki hadda mahaifinki,zakiyi arziqin da babu lallai talauci yasake rabarki...maigado....ana nemawa yarima d'an sarki Abdallah mu'az sarkin kaisa yarinyar da zai aura". Hakanan gabanta yayi wani mummunar faduwa,ta dubi umma luba kafin ta dauke kai,cikin zuciyarta tana mamakin to ita din meye nata a ciki?,wannan ai sam ba maganarta bace,bama abinda ya shafeta bane bare tashiga ciki,meye ma alaqarta da maganar da har zata zama sikar samun sassauci cikin rayuwarta,a hankali cikin sassanyar muryarta tace
"Allah yabashi,yakuma tabbatar da alkhairi" saita motsa da alamun tashi zatayi,da hanzari ta tsaidata
"Ai dukka maganar taki ce" saita kuma dubanta cikin rashin fahimta
"Eh bilkisu,don babu wadda ta dace ta cancanta tasamu wannan damar kamar ke,zaki auri abdul'azeez abdalllah na tsahon shekarun dazaiyi a qasar da yake karatu,aure ne wanda za'a yishi bisa amincewarki data mahaifanki,kuma za'a daura auren ne da sanayyar qididdigaggun mutane,yayi shige da auren sirri saboda ba kowa akeson yasani ba,fadin irin alkhairin da zaki samu daga lokacin da kika amince zuwa rabuwarku,irin sallamar za'a miki ma bata baki ne,ina da imani da yaqinin zaki samu abinda zai sauya rayuwarku keda duka 'yan uwanki mahaifinki dama wanda kikaso kika kuma zaba,ke hatta ni din nan na tabbatar da cewa na gama warkewa maigado ta silarki idan kinso"

*Tirqashi!,yaya zata kaya?!*ðŸ¤ðŸ½ðŸ¤ðŸ½
7/11/21, 4:31 PM - My Mtn Number: *S R B*
17

*_wannan littafin na kudine,kuma amana ce a hannun duk wanda yasiya,ga mai buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadan nan numbers din_*
0903 234 5899
Ko
09033181070
________________________________

*Ina mata 'yan birni 'yan qwalisa masu burin sanyaya gidansu da daddaɗan ƙamshi mai tsayawa a zuciya da ruhin maigida?,shin kina da labarin ANNUR PERFUMES?,wadanda bayan sun gyara miki waje da ƙamshi su kuma gara miki ciki da kayan matsi?sannan su rabaki da infection?,WOHOHO wani kaya sai amale,ANNUR PERFUMES sun shara wajen saida*

*HADADDIYAR HUMRA*
*KWALACTURE*
*TURAREN WUTA*
*MUSK(AL MISKI THAHARA/AYSHA/BLACK AND RED MISKI)*
*DECORATIONS NA TSINTSIYA*

*_UWAR GIDA DA AMARE KUZO GA NAKU_*

*_MAZA GARZAYA GAIDA LAYIN MASALLACIN IMAMU MALIK!_*

*KO A NEMESU TA LAMBOBIN WAYA KAMAR HAKA*

07086341096 ko 07069037534

_muna maraba da masu siyan ɗai ɗai ko sari_🤗🤗

*INGANCI KYAU RAHUSA DA KUMA INGANCI SAI ANNUR PERFUMES*👃ðŸ½
___________________________________

Cak qwaqwalwarta ta tsaya da aiki na wucin gadi,komai yayi mata dif tamkar qwaqwalwar tata bata taba wani aiki ba,ta daina fahimtar komai sai maganganun umma luba dake mata amsa kuwwa cikin kunnuwanta,sun dade suna maimaita kansu kafin tasoma fahimtar abinda takeson gaya mata
"Taje ta bada fansar kanta da budurcinta wa yariman qasar kaisa na tsahon shekara daya" a dunqule idan ta fahimta kamar hakan umma luba take nufi ko?,ta jefi kanta da tambayar,saita daga idanunta dasuke walainiya ta xubawa umma luba su,shin tasan ma'anar abinda take fada kuwa?,anya hankalinta daya?,a cikin hayyacinta ma take?,bataga alamun wasa saman fuskarta ba face tsantsar gaskiya dason isar da saqo bare tace wasa take mata,karon farko data motsa labbanta
"Ban gane ba umma,ban gane abinda kike nufi ba" murmushi tasakar mata dukka bisa qoqarinta na kwantar mata da hankali
"Kin gane maigado saidai kicemin kin rude,kuma tabbas koma wacece da bata zaci samun irin wannan damar ba ta sameta sama taka dole rudani ya shigeta,kije kiyi tunani kawai nan da jibi,saboda kwanaki biyar yarage mana muje mukai duk wadda muka samu" wani abu ya tsaya mata iya wuya,ta fahimta takuma fuskanta,wato bazasu akayi suyi farautar yara marasa galihu irinta,musamman idan akayi katari da masoya abun duniya masu kwadayi shikenan kaya ya tsinke a gindin kaba?,duk haqurinta duk sanyinta ba zata lamunci a qasqanta mutunci da darajarta ba,lallai ya kamata idanma umma luba tana da wani tunani na daban a kanta ta warware matashi,don a gaba bata fata hakanan bata sha'awar ta sake soko wata magana makamanciyar wannan a tsakaninsu iya zamansu,koda tanason aure koda lokacin da zatayi aure yayi ita ya kamata ta zaba bawai a zabeta ba,bare a yanzu da qaramar qwaqwalwarta take cunkushe da matsaloli,gajeriyar rayuwarta take quntace take kuma takure,a gaba daya tunaninta da abinda idanunta suke gabe mata shine,aure gaba dayanshi matsala ne,babu komai cikinsa face jefa kai cikin damuwa da matsaloli,me yasa ma zata yarda anan kusa da qananun shekarunta ta fada matsala kwatankwacin matsalolin da taga umma katti da sauran matan da babanta yake aurowa suke fadawa?,shi yasa ko daya bata sha'awarsa,koda ya zame mata dole tana duban nisan zangon da zata qara diba kafiin ta fada komarsa
"Aure a nawa qaramin tunanin ana yinsa ne a sanda namiji da mace sukaga juna suna so,suka kuma amince da juna,shi namijin zai tattako koya tura wakilansa zuwa gidansu yarinya su nema masa aurenta,baya ga haka babu wani sharadi da ake gina aure a kansa na cewa bayan lokaci kaza akwai wani abu kaza dazai faru,yakan zama tarayya tahar mutuwa a yadda nake ganin yana faruwa a mafi yawancin gidaje,kiyi haquri umma luba,ni bazanyi aure ba,koda zanyi aure toba yanzu zanyi ba,ki nemo musu wata,nasan da yawa zasu amince,zan wuce gida sai Allah yakaimu gobe" da mamaki take duban bilkisu,ashe yarinyar ta iya magana har haka,ashe tana da zurfin tunani da hankali?,koda ba'a gaya mata ba iya zamanta da bilkisu ita zata bada shaidar ta iya talaucinta,hakanan ba makwadaiciya bace,amma bata taba zaton zata bijirewa wannan tayin ba.


Ganin da gaske bilkisun tafiyar xatayi,kuma idan har tatafin wata qatotuwar dama ce mai gwabi da zata subuce mata,wadda samu ko maida kamarta saitaci wuya,wala'alla ma cikin abokan aikinta wata takawo tata kuma a karbeta ta rasa dukkan wata dama matsayi da daukaka da zata samu a masarautar kaisa,zumbur tamiqe tana qwalawa bikisu kira wadda batakai ga fita ba,gabanta tasha tana dubanta cikin kwantar da murya da karyar dakai
"Haba maigado,haba,qauna ce fa tasa na zabeki na tsallake dubbai,ya kamata ki dinga sara kina duban bakin gatari,a yadda kikeson 'yan uwanki na zaci zaki iya sadaukar da farincikinki saboda tasu rayuwar ta inganta?,kin gwammace ku dawwama a haka bilkisu bayan ga dama da kika samu ta fidda kowa daga qangin da yake ciki?,shekara daya tak fa rayuwarki zata inganta,me za'a gutsira daga jikinki?" Idanunta masu maiqo tazubawa umma luban tana dubanta ganin yadda ta haqiqance,itadin ba tsararta bace hakanan basu saba 'yar tankiya ba,inda sun saba din da taji amsa dai dai da ita,datace bata amsa yadda ya kamata,tana tsammanin a yadda idanun al'umma suka rufe kowa ya tasa kudi gaba fiye da mutuncinsa itama bikisun haka take?
"Kiyi haquri umma luba kamar yadda nace miki dafarko bazan iya ba,don Allah ki duba cikin dubban ki zaba wata,nasan za'a dace" daga haka tarabeta tafice daga gidan,tanajin iska na dibanta,hakanan maganar na ratsata fiye da yadda ta tsammata,sai taji tun daga kan hanya kamar zazzabinta daya sauka yana niyyar dawowa,maganganun sukaci gaba da juyin waina a tanda cikin qwaqwalwarta,ta rasa ma wanne zata kama.


Tsaka da haka taji kamar ana ambatar sunanta a sanda take qoqarin shigewa gidansu,yanayin yadda sautin ke fita saitaji kamar tasan me kiran,don haka ta tsaya cak ba tare data waiwayo ba,hakan yabashi damar qarasowa gabanta,abubakar saddiq ne,sanye cikin shadda dinkin tazarce,kansa babu hula,kana masa kallon farko zakasan yana ji da gayu da samartaka,jifanta yayi da murmushi saita janye idanunta daga kanshi,hakanan yake mata kwarjini,tasamu da qyar ta tattara lafuzan gaisuwa saman lebunanta ta aika masa,ya amsa idanunshi kan labban nata dake masifar burgeshi,ya fuskanci bayan kyau yari yar tana da wani qasaita da izza wadda wala'alla itadin batasan tana dashi ba,miskilancinta yana burgeshi,hakanan yanayin dakiya da basarwarta.


"Kwana biyu baki ganni ba,amma koki cigiyata ko?" Yafada yana dan fidda murmushi gami da shafar sumarshi,maganar tasa ta sake tarwatsa tunanin dake fareti a kwanyarta,saitayi kaman zata kalleshi bisa mamakin furucinsa saikuma ta basar,ta nemeshi akan me?,idanma tasan inda yake din ya cancanci ta nemeshi?,yasake sakin murmushi ganin yadda tasake basarwa
"Koda yake bakisan inda nake ba ko?,kuma baki sha'awar amsar numberta ba kosau daya,koda kin saninma nasan masu suna bilkisu da sarauta,da wuya anemi din,to gashi na sake kawo kaina a karo nabiyu,kuma sai naga kamar sauri kike,ko zaki aramin minti goma cikin mintunanki muyi magana?" Da sauri ta girgiza mishi kai alamun a'ah,duk da hakanan take ganin qimarsa,amma a yanzun bata sha'awar dogon magana,dan shuru yayi alamun baiji dadi ba,amma saiya dage kafadunsa
"Ohk,ba damuwa,asake samin wani lokacin saina dawo muga juna....,ko a bani phone num saina kira ko?"


Kafin tabashi amsa babanta yafito daga cikin gidan,tunda taganshi tasan komai zai baci ne,don haka tabude bakinta dasauri tace
"Sai jibi in sha Allahu,babu damuwa" yasaki murmushi,don ba qaramin dadin amsar jibin data bashi yaji ba
"Allah yakaimu,na gode qwarai". Kafin ta amsa ya iso garesu,don haka saita wuce zuwa cikin gida kawai tabarshi da sadiq,koma meye ita bata sha'awar yafaru a gabanta.


Ko kadan a cikin ranta bata ji ta daina zuwa aiki gidan umman luban ba,a nata ganin komai yana da muhallinsa,yadda maganarsu keda muhalli na daban haka aikinta ma,babu abinda zai shafi wani,saidai yadda maganar ta tsaye mata yasanya washegari bata da qwarin jiki dana zuciyar tafiya gidan aikin.


Rashin zuwan nata yasanya umma luba babu abinda bata saqa ba,abu na farko tsoron tawaye daga wajen bilkisun kamar yadda ta raya,don haka wata washegarin ta yanke gwara ta fuskanci fulani da maganar,wala'alla asamu wata mafitar.


Kamar kowanne lokaci idan zatayi ganawar sirri da amintattun nata,waje ne kebantacce wanda yake cike da sirri da aminci,fulanin aysha ce daga tsaye cikin shigar alfarma dake nuna xallar mulki da sarauta,yayin da umma luba ke zube a gabanta,kanta a qasa bayan ta kammala dukkan bayananta.


Tattaki fulani aysha tayi tana nazarin maganar da umma luban tazo mata da ita,tasan tunda lubabatun takasa sukuni kan lamarin babu ko tantama yarinyar ta cika mace,takuma cika dukkan sharuddan data gindaya musu kafin fararwarsu aikin,ba shakka ba umma luba kadai datasan yarinyar ba,har ita kanta tacika da mamakin yadda za'a samu wasu ko wata cikin qasarsu da zata iya bijirewa wannan tarin alkhairi dasu a nasu ganin suke ganin kamar alfarma ce sukayiwa koma wacce diya ce,eh mana alfarma,tunda banda wannan dalilin da ko cikin mafarkinta bata taba hasashe ko hango azeez din yana nema ko auren daya daga cikin yaran talakawansu ba,azeez din mai tsada ne,saboda haka dole komai dazai rabeshi yazama mai tsada mai daraja
"Kin tuntubi mahaifinta?,idan kin tuntubeshi shidin me yace?" Fulani ayshan ta jefa mata tambayar,ta girgixa kanta da sauri
"Tuba nake Allah ya taimakeki,sam sam na manta da wannan,ai Allah yabaki yawan rai ina da yaqinin cewa idan na tuntubeshi ma magana ta qare,yanzu kuwa zan tashi,bazanyi qasa a gwiwa ba zan sami mahaifinta" murmushi fulanin tayi cikin zuciyarta,don idan ka kalli saman fuskarta ba zakaga alamunsa ba,saita soma takawa zuwa saman daya daga cikin kujerun tana dauko wata jaka tana kuma magana da umma luban
"Ki jaddada masa matsayin wanda ake nemawa diyarsa koda shima zaice zaya musa,daga yanzu bana buqatar a sake magana da ita yarinyar,yardar mahaifinta tamkar yarda ce,abunda nake da buqata kawai shine,hoton yarinyar don inason in ganta dakyau,na tantance kuma na tabbatar da dacewarta da yarona" tana kaiwa nan taciro kudade rafar 'yan dubu dubu tana miqawa umma luba,jikinta na rawa cikin sauri ta amshe tana zuba mata godiya kana tataso cikin farinciki tafito daga falon tana cusa kudin cikin zaninta,tana kuma jaddadawa kanta lallai zatayi dukkanin me yiwuwa taga komai yatafi yadda akeso,takuma cimma nasara.


A lokacin da umman luban tazo tana daga daki kwance,taji murya kamar tata,amma sanin cewa babu wani abu da zai kawota gidan saitaci gaba da kwanciyarta tana jan istigfari cikin ranta kamar yadda tasaba yi a yawancin lokuta idan bata da abunda zatayi,ita daya ce cikin dakin tana sanya ran gobe tawuce wajen aikinta,dukka qannenta sun tafu islamiyya,Allah yasanya weekend ne gobe take saka ran zuwa har makarantar boko.


A falon amarya ladidi tasauka,lokacin yana zaune saman daya daga cikin kujerun falon,gama sa'insarsu da ita kenan akan shinkafa,tace haram tabashi abincinta yaci,tunda rabonshi da kawo cefane yau kwanaki uku kenan,yayi barazanar da muzuran duka a banza ladidi ta dauke kanta,yunwa ce kawai ke sadakarshi,gashi babu ko sisi cikin aljihunsa,yasan ko giyar wake yasha bazai tunkari katti tabashi abinci ba,don tunda ya qara auren nan taja masa layi,irin layin da bata taba ja masa ba,ta tattarashi dukka ta barwa ladidi shi,ta yaranta kawai da sana'arta take.


Ya sake shafa cikinsa yana tsinewa talauci karo na babu adadi,sam a rayuwarsa bai taba kawowa zai tsunduma cikin talauci irin na wannan qarnin dana yafa ba,dai dai lokacin da ladidi ta dage labule suka shigo tare da umma luba
"Baquwa ce takeson magana dakai" ladidi tafada tana wucewa uwar dakanta don adana miyarta data gama soyawa,yabi kwanon da ita kanta ladidin da kallo yana hadiyar yawu kamae tsohon maye,don tuni qamshin miyar yagama cika mishi ciki yasake tada mishi yunwarsa.


Gaisuwar da umma luba keta faman rattabo masa tadawo da hankalinsa,saiya maida hankalinsa gareta yana amsawa cikin yanayin nuna rashin sanin mutum,saita taqaita masa wahalar dakai ta gayamishi wacece ita
"Uwar dakin maigado ce,gidan da take aiki" gyara zamanshi yayi gabanshi nadan faduwa,yayin da wani sashe na zuciyarsa yacika da fatan Allah yasa kudin aikinta takawo mata ganin kwana biyu bata je ba ya amsa ya kalmashesu ya rage radadi na kwana biyu
"Au.....to....to,madallah,ina fata lafiya daiko?" Murmushi tayi tana gyara zamanta
"Lafiya lumi,sai alkhairi dake tafe dani" jin haka yasa yasake tattara nutsuwarshi yana dubanta,tadan karkace ta zaro rafa daya ta dubu dubu cikin irin wadda fulani aisha ta mata kyautarta ta aje gefan malam bilya,bin kudin yayi da kallo a mamakance cikin ranshi yana qissima abubuwa da yawa
"Kadda ace kudin aikin nata takawo mata,to amma maigado na karbar maqudan kudi haka masu yawa amma bata taba jin qaina ba?,kodai yau Allah ne ya toni asirinta?"
"Wadan nan....dama wasu masu tarin yawa zasu zama mallakinka matuqar ka aminta da maganar da nake tafe da ita" mamakin jin zai mallaki kudin suka kamashi,saiya dafe kudin yana sake gyatta zamanshi
"Wacce magana ce wannan baiwar Allah?".


Ba tare data boye mishi komai ba tayi masa bayani filla filla,ta shaida masa yadda sukayi da bilkisu a gidanta,sannan ta rufe bayanin nata da gaya masa irin tarin maqudan kudaden da zai samu da alkhairi iri daban daban.


Ba malam bilya bs,hatta ladidi dake daki wadda dama fakare tayi batasan sadda tafito zuwa falon ba tana rarraba idanu tare da qissima yadda zata sake kame mijinta malam bilya matuqar hakan ta kasance
"Kan ubancan!,amma ban taba sanin baqincikin maigado ya ta'azzara har haka ba da tuni na jima da nema mata maganin samun salama,ashe yarinyar nan bata qaunata duk ban sani ba sai yau?" Yafada yana duban ladidi wadda tasamu waje daura dashi tazauna itama tana neman muhallin da zata tofa tata
"Ai malam kada kasake kada kabari wannan damar tawuceka,koda a mafarki kasameta aika more ballantana a gaske" ladidi ta tofa din kamar tadda bakinta yaketa motsi tunda tafito
"Niko ladidi idan nabar hakan ta kasance a cikin tababbu marasa rabo ai nine sahun gaba,maigado zataci ubanta,wanne amfani zatamin na tsahon shekara gudan dazai kawomin wannan alkhairin" da sauri umma luba ta dakatar dashi
"A'ah malam,bada zafi zaka mata ba,kayi mata cikin hikima da lallashi wataqila tafi fahimtarka a matsayinka na mahaifinta,kaga babu yadda ban kwatanta mata ba amma taqi,ni kuma qauna ce tasa na zabeta cikin dubbai,inasonta da wannan alkhairin" wuyar rigarsa daya zame yajawo yazauna sosai saman kafadarsa,cikin nuna isa da hura qofofin hanci yace
"Yo yarinyar dana haifa a cikina ma saina tsaya ina lallabata?,ai indai nine na haifi bilkisu to kije kawai ki shaidawa ranki ya dade.....koma ku rankaya tare mu sanar mata na bawa yarima ita,zan mata lallashi nafarko amma idan na fuskanci asara takeson jaza mana tofa bazan mata ta dadi ba....kekam babu abunda zamuce dake sai godiya,don ba qaramin masoyinka bane zaiga alkhairi haka ya rungumo ya nufoka dashi".


Kowannensu cike da farincikin zuwa gabar samun cikar burinsa sukayi sallama,don bata tsaya taga bilkisu ba bare tasan da zuwanta ko suyi magana.


Miqewa malam bilya yayi yana jinsa yau da wani irin nauyi sanda yake cusa rafar kudinsa a aljihunsa,ganin yasoma haramar ficewa sai ladidin ta lanqwasa murya
"Malam,bakaci abinci ba zaka fice" harara ya watsa mata
"Ki riqe kayanki mana kici ko zaki qara kumari,an gaya miki ni matsiyaci ne?,ni nan da kike gani duk inda nayi arxiqi bibiyata yake a jinina ne"
"Kayi haquri malam....karka watsamin qasa a ido mana,ta yaya zaka iya shawo kan yarinyar nan bayan kasan cewa mace sai mace 'yaruwarta,nina gama tsara yadda zamusha kanta amma naga kana da niyyar botsarewa" jin ta ambaci kalmar shawo kan bilkisu yasan kuma ladidin akwai hikima saiya sassauto,yana wani ciccin magani murya ciki ciki yace
"To yanzu ya za'ayi?" Tamiqe da hanzari tana cewa
"Kasan kwananta wajen nawa kamar bata da lafiya,kuma gidan nan kasan cewa ba wani cikakken abinci gareshi ba,yanzu haka qila tana kwance bataci komai ba,bari na zuba maka abincin saina tasota itama na zuba mata tazauna kunaci tare kana janta da hira harka sako mata zancan" dariya yasaki
"Yauwa ladita,ladi ga tsiya ga dadi" ya qarashe maganar yana komawa mazaunin daya tashi dazu,yayin da itama tasaki dariyar tana wucewa zuwa uwar dakanta,tasamu farantai biyu tayi zubin shinkafa da miya da salad harda nama tafito falon dasu,ta ajesu dukkaninsu a gabanshi kana tafice don kiran bilkisu.


Cikin mamaki ta amsa sallamar jin muryar wadda yau tashigo dakinsu,matar da tunda tazo gidan ko ta qofar dakin nasu bata taba wucewa ba bare tayi batan kan shigowa koda me yake faruwa kuwa cikin gidan.


Tilas tamiqe tazauna ganin murmushi saman fuskar mama amarya makar yadda yaran gidan suke gaya mata,saita qaraso tadan tsaya daga gefan bilkisun
"Sannu maigado,jikinne dai?" Wani mamakin yasake kamata,saita daure ta gyada kai harda qarin bayani
"Alhmdlh nasamu sauqi ma"
"Masha Allah,naji dadi,babankune sai haquri,baya kyautawa wallahi sam,koda baka da kudin hidima da iyalinka amma ai aqalla ka jasu a jikinka ko?,yanzu gashican duka yadamu,yanason miki sannu amma yana nauyin wai bai siya miki magani ba tunda kika kwanta"
"Baban namu!" Tayi subutar bakin fada cikin muryar dake nuna zallar mamaki idanunta kan ladidi,don iya abinda hankalinta zai iya tunawa bata taba ganin alhini saman fuskarsa don daya daga cikinsu bashi da lafiya ba,kai ta gyada tana murmushi
"Shi dinfa,shi matsalarsa idan baida kudi saiya watsar da kowa maimakon yayi bayanin bashi dashi ne,yanzuma shine ya aikoni yace kizo yana son ganin jikin naki" kusan daskarewa tayi,don bata ma gane ba saida ladidin tasake gaya mata,sannan tamiqe jiki ba qwari ta ciro mayafinta dake rataye jikin qofa cikin mutuwar jiki tabiyo bayan ladidi,don hakanan kawai jikinta ya bata dukka abinda yake faruwa ba gaske bane bogine,akwai wani abu aboye a qasa,don ruwa baya tsami banza,dabi'ar data zama jini da tsoka tsahon shekaru sama da ashirin ba qaramin abu bane zai sauyata cikin gaggawa haka ba,amma kome meye zataji zata gani,don kusan tafi kowa karantar halayyar baban nata cikin yaranshi,saboda dogon zama da sukayi tare dakuma baiwar fikira da Allah yayi mata na saurin fahimtar abu.
7/11/21, 4:31 PM - My Mtn Number: *S R B*
18


*_Zafafa biyar na kudine,kuma amana ce a hannun duk wanda yasiya,gamai buqatar mallakar nashi saiya tuntubi wadan nan numbers din_*

0903 234 5899
Ko
09033181070



18




Sanda suka shiga dakin tuni ya soma nisa wajen kai lomar abincinsa,bakinsa cike da shinkafa yake nuna masa inda ya aje daya plate din yana cewa
"Qaraso nan maigado,sannu,Allah yayi miki halin juriya irin na maimunatu na" duk da tazauna a inda ya nuna matan amma bata dubi abincin dake wajen ba,don sam ko kusa ko alama ko amafarki bata taba kawowa a ranta nata bane
"Gani baba" ta fada kanta a duqe kamar yadda suka saba yawancin lokutta,saboda tsananin rashin sabo da rashin jansu a jiki
"Yaya jikin naki?" Sai data masa duban mamaki kana tasake maida kanta qasa ta amsa
"Da sauqi alhmdlh,na warware"
"To madalla,madalla" soma yunqurin miqewa tayi,ya dakatar da ita da sauri
"A'ah,zauna mana ga abinci nan kici,kya tashi bayan ke aka zubowa?" Duban abincin tayi tadubi baban nata,yasan cewa tambayoyine fal a bakinta,amma kasancewarta bamai yawan surutu ba sautari kana gane tana da abun fada ne da hanyar duban abu da idanu
"Zauna kici maza,keda ba isashshiyar lafiya gareki ba" mama ladi tasaka baki,saita koma tazauna cikin matuqar sanyin jiki tajanyo abincin gabanta.


Tsananin rashin sabo da mamaki suka sanyata kasa kai koda loma daya bakinta,sai faman juya abincin kawai take da cokali tana sauraren hirarrakin da baban nata yaketa soko mata,wadda ta kasa bashi cikakkiyar amsar koda abu daya,saboda jinta take gaba daya banbarakwai,har zuwa lokacin daya kammala cin nashi abincin,saita aje cokalin itama tamiqe
"Zauna mana me gado,wai saurin me kikeyi?,magana zamuyi ai" yafadi dai dai sanda mama ladi ta jiye mata ruwan randarta mai sanyi a kofin silba a gabanta tadora da cewa
"Shine ai,kamar ana cizonki".


Shuru ne ya ratsa dakin na wasu mintuna yana kama zaren maganar farawarsa zuwa qarewarsa,sa'annan yaja wata gyaran murya mai kauri kafin yasoma magana
"Wato maigado haka Allah yake lamarinsa,saika haifi yara rututu amma a cikinsu sai Allah ya daukaka darajar wani,yayi masa nasibin da kaf cikin yaran naka babu maishi,wani al'amarine ya tunkaromu na alheri wanda dukkaninmu alherin xaibi ya shafi kowa da kowa haula da zuri'a,amincewarki kawai muke nema harni mahaifinki".


Yana fadin hakan taji gabanta ya yanke yafadi,tasoma ambatar sunan Allah tana addu'ar rabbi yasa ba abinda zuciyarta take raya mata bane,idan kuwa shine ta tabbatar da cewa ta kade daga ita har ganyenta
"Gidan sarautar garin nan suke neman izinin hada zuri'a dani ni malam bilya na shekara daya,wanda acikin shekarar zasu azurtani na zama daya daga cikin jerin alhazawan da ake zance,nasan ke yarinya ce mai biyayya,ba zaki taba cewa komai ba akai,saboda haka tunima na bayar da aiken cewa nabasu ke!" Kamar saukar ruwan sama da tsawa haka taji maganar tashi,ba tare data shirya ba wasu hawaye masu dumi suka soma layi tun daga cikin idanunta zuwa saman kuncinta. Lahaula wala quwwata

Please Login or Register in order to submit comment