Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mafarkan data saba yi,kamar al'amara kamar shifcin gixo sai taji sallama daga bakin qofarsu,sallamar data dauke dukkan wani kuka da take gursheqen yinsa cak! Tashi guda!,kwatankwacin yadda ruwan sama ke daukewa lokaci daya.


Cikin hanxari ta waiwaya,ta waiwaya dinne bawai donta yarda da sautin muryar data ji ta wadda zuciyarta ta dauki shekara da shekatu tana begen sake gani bane,ta waiwaya badon ta yarda da qaryar da kunnuwanta ke mata ba,ta waiwaya ne kawai don taga wacece mai irin muryar halitta mafi soyuwa a wajenta,muryar anty zuhriyya,anty zuhriyyarta,matar da take kallonta a matsayin mahaifiyarta.


Fes idanunta suka sauka a kanta,komai dadewar zamani,komai shudewar lokaci,hakanan komai sauyawar zamani batajin wannan fuskar kamanninta zasu bace daga idanunta,ba mai irin muryar anty zuhriyyar bace,anty zuhriyyar ce da kanta,tsaye daga farkon farkon falon tana dan sake duban falon da alamun tantamar inda take,sanye cikin wani leshi da aka yiwa dinkin doguwar riga wadda ta fito da kyau gayu da tsarinta,hadi da girma dake nuna shekarunta sun fara sauyawa zuwa na babbar mace,bawai babbar macen data tsufa ba,aah,babbar macen da ilimi kudi da wayewa suka sake bayyana aihin wacece ita.


Dukka lebanta na sama da qasa rawa suke,kunnuwanta sun toshe ta daina jin abinda mama ladi ke fada,idanunta kadai sune kewa anty zuhriyya kallo irin na qurill,tana tsoron kada ta bace mata kamar yadda take zuwa mata a mafarki sannan da zarar ta farka ta bace mata.


Duk da idanu da take binta dasu amma bakinta ya kasa furta kowacce kalma,bude baki tayi da niyyar sake yin sallama cikin falon idanunta karaf suka sauka kan bilkisun dake tsaye ta kuma kafeta da idanu
"Dauhgter!"
"Anty!" Suka ambaci sunan juna kusan a tare,kana kowanne ya durfafi dan uwansa da sauri sauri,saidai kafin bilkisun ta isa ga anty zuhriyyar tuni ta sulale a wajen,tana shirin kaiwa qasa anty zuhuriyya ta tallafota jikinta,a take ganinta yasoma daukewa tafara gani dishi dishi,hakanan jinta ya soma yin low,abu daya zuwa biyu ta iya jin muryar mama ladi,sai muryar anty zuhriyya data iya banbance abinda tace saboda tana jikinya ne
"Ke kuma wacece?" Sai muryar anty zuhuriyyan still data sake fada cikin tsawa
"Ahir kada ki sake ambatan sunan maimunatu,don linxami yafi qarfin bakin kaza!" Daga haka taji antyn na sake janta jikinta,daga wannan bata sake ji ko gane ko meye yake faruwa ba jinta da ganinta suka ida daukewa gaba daya......
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 36

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070
_______________________________

Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana binsu da kallo,ta jima zaune a inda suka barta tana tariyar rayuwa da abubuwan dake cikinta,anty zuhriyya?,ina take?,ina tayi?,tayi nisa da ita nisa mai yawa,irin nisan da bata zata ko tsammata ba,har yanzu mafarkin da tayi da ita daren jiya yana nan maqale a ranta,makwafi ce ta mahaifiyarta wadda bata da tamkarta,tunda dangin nasu sun mata nisan da bazata iya zuwa muhallin da suke ba,su din kuma sun manta da cewa dan uwansu ya aurar da diyarsa aqasar harta haifi diya itama ko kuwa yaya?,mahaifiya tabbas mahaifiya wani jigo ne na rayuwa,babban bango ce kuma majingina,wanda duk mutumin daya rasata ba shakka dole yayi kuka,kuka kuma da bazai yanke ba sai ranar da taka ta sameka.


Kamar wani hankali aka qara mata game da muhimmamcin mahaifiya,ta tabbatar da cewa koda mahaifinta yafi qarfin mahaifuyarta,koda tana raye aka mata wannan auren na qarfa qarfa,tabbas bayan ta dawo ba zata fuskanci rayuwar data soma fuskanta cikin gidan ba a yanzu.


Na farko sabuwar amaryar babanta wadda ta gama karantar tsaf kishi take da ita,na biyu daga umma katti har mama ladi duk da cewa ta dade da sanin yadda suka dauketa,amma ta tsammaci yanzun komai zai canza,albarkacin albarkacinta da kowaccensu take ci a yanzu,saidai wani irin mu'amala ce tsakaninsu,idan sun ganta ta gaidasu su amsa,idan basu ganta ba babu mai nemanta ko cigiyarta,koda zata wuni ta kwana cikin daki ba tare data leqo ba,qannenta sune sanyin idaniyarta,abokan hirarta,akwai abubuwa da yawa da suke cunkushe a zuciyarta suke damunta suna dagula lissafinta,wanda tsahon sati biyu da dawowarta harta soma ramewa,baya ga rashin abubuwan more rayuwa yadda tasamesu a baya dakyau wanda yanzun duka sun janye,babu wanda yadamu da yanayin abincin da zataci a gyarashi saboda taste din bakinta ya canza,babu wanda yadamu daya bata kudin sabulun wanka kona wanki,idan an bayarma tona qannenta ne,su kansu basu gama wadata yadda ya kamata ace sun wadata ba,saidai wannan din bata sani ba,shin daga mahaifinsu ne ko daga matansa wakilansa wadanda abun yake biyowa ta hannayensu?,duka bata sani ba,saidai dukka wannan ba damuwarta bane,kome tasamu tana ci,kome yazo.hannunta tana amfani dashi,tunda tasan rayuwar da tayi abaya gaibu ce,wadda tayi dai dai da mafarki.


Komai zai biyo baya ko xai sameta tana da tabbacin rashin mahaifiya nada kaso mai tsoka da kuma muhimmiyar rawa da yake takawa wajen tsintar kanta a kowanne yanayi ma da take ciki,da tana da mahaifiya ko babu komai tana da kafadar da zata jingina tayi kuka,tana da muhallin da zata fadi damurta a fuskanceta,koda ba za'a yaye mata damuwar ba,za'a tallafa mata da addu'a,tana da wajen da za'a tambayeta me ya dameta?,me take da buqata,amma yanzu fa da babu uwar?,saidai tayita cinye damuwarta ita daya,ko tayita magana da 'yan uwanta data tabbatar babu lallai su fahimta abinda take nufi.


Sai datayi wanka,tasamu kaya ta saka tana duba yawan kayanta dake da buqatar wanki amma babu sabulun da zata wanke din,batason taba na qannen nata,saboda su dinma bawai wadatar dasu yayi ba.


A hankali take takawa zuwa kitchen din gidan,ga duk wanda yasanta kallo guda zai mata ya karanci tana cikin damuwa qwarai,akwai tarin damuwa cunkushe a ranta,babu kowa ciki dama shan ruwan shayi ya kawota,don haka tasamu kofi ta diba,duk da tanajin yadda wasu lokutta ake kyarar qannenta idan suka taba kofin daya daga cikinsu,ta dauki salar biredi dake ajjiye harta soma shan iska,wanda ta tabbatar nata ne,don kusan koda yaushe itace ta qarshe a yin breakfast a gidan,babu kuma wanda ya damu da ita bare ya killace mata.


A tsaye takeshan shayin,lokacin ne anty tashgo kitchen din,da alamu ita keda girki a ranar,fuka a gintse,tana ta ciccin magani da harare harare,da qyar ta amsa gaisuwa bilkisun kamar wadda aka yiwa dole,sannan tasoma hada girkin rana,wanda da wurwuri takan gama duk ran girkinta,ruwan mutum yaci ruwanshi ya barshi,tasha jin suna fada da abokiyar yin nata mama ladi akan hakan,da yake ita mutunce maison abinci mai dadi,umma katti kanja gefe ta tafa hannu tace itakam 'yar kallo ce,hakanan ko anqi ko anso itace uwar gida kuma babu yadda aka iya da ita.


"Wato ke babu abinda kika iya tsinanawa mutane,saidai idan an tuqa a baki" taji anty tana fada sanda take dauraye kofin da ta gama shan ruwan shayin,dakatawa tayi tana duban antyn cikin mamaki,don bata gane me take fada ba sam,aiki dai tasan cewa kafin qannenta su fita su suke share falon gidan da baranda tas to bata musu horon ganda ba,itake shiga kitchen ta gyara musu shi fes kullum kwanan duniya ta wanke dukka kwanukan ciki,don tasan babu lallai yaran suyi yafita yadda ya kamata,kuma ita din shaida ce,daga zuwanta gidan zuwa yau kitchen din har wani qara haske yayi akan nada,hakanan duk sanda suka gama cin abinci xata tattara kwanukan tasake wankewa,don ba kasafai ma suke kwana da wanke wanke ba yanzu tun sanda tazo,to batasan wanne aiki takeso ba kuma sama da hakan,kafin tace komai ta yaba mata maganar data tsaya mata fiye da tsammani
"Dama illar zama da gansamemiyar bazawara kenan,tana maka kallon biri kana mata kallon ayaba,idanu sun gama budewa ta gama sanin komai,kai wala'alla ko kwanan aure kayi da ubanta saita gane,mtsewee Allah ya sawwaqa" idanunta ta lumshe gaba daya tana jin wani tashin hankali na rufto mata,sunan Allah tasoma ambata don ya kawo mata agaji,tana jin wani irin zafi yana ratsa zuciyarta,ta maida kofin muhallinsa da qyar sannan ta lalubi qofar fita.


Da qyar takai kanta daki,ta samu qasan tiles din tayi zaman dirshan tana yin filla filla da maganganun antyn,sai taji suna mata wani irin ciwo,wanda daga qarshe sai da suka danganata da zub da hawaye,kalmar bazawa ta sanyata sakr maida kanta cikin duniyar tunani,duk sanda zata daga kai ta kalli fuskarta a madubi sai wannan sunan ya fado mata,ba shakka sunanta ne,sai taji wani irin rauni da tashin hankali sun baibayeta,ba shakka duk wanda ya santa zai kuma ce wani abu akanta saiya laqaba mata wannan sunan,duk wanda yazo da niyyar aurenta sai an alaqantata da wannan sunan,mafi muni ma a cikinsu idan an tambayeta wayeshi din wanda ta aura?,bata da cikakkiya kuma tartibiyar amsa akan haka.


Cikin kwanakin lafazan da antin ta dinga aike mata kenan,wadanda suka zama tamkar guba a zuciyarta,suka tarwatsa duk wani zaman lafiya da salamarta,suka dinga damunta gamida sanyata cikin wata iriyar matsananciyar damuwa,wadda ta bayyana har a gangar jikinta baya ga zuciya.


Abun mamaki sai taga mama ladi itama tabi sahu,ya zamana sun sakata a gaba batare da tasan meta tsare musu ba,duk ranar Allah daga fitowarta zuwa faduwarta cikin kuka da qunci take,hakan yasa cikin lokaci qanqani dukkan wani kyau da kumari datazo dashi yayi nashi waje.


A gefe guda kuma wani irin matsananciyar tsanar masarautar kaisa da ahalinta suka saukar mata,tasan koma meye duk wani hali da take ciki a yanzu sune sila kuma ummul aba'isin din komai,komai lalacewar uba uba ne,amma banda haka da zata iya cewa mahaifinta shine mutum na biyu daya zama sila kuma yake da alhakin komai,cikin qaramin lokaci ta sake tsanar komai ma,ciki harda rayuwarta.

******** ***** ********

"Ya Allah!" Ya fada da sauri lokacin da yake tashi daga shimfidarsa,yaxauna sosai saman gadon dafe da goshinsa.


Ya jima zaune a haka yana maida numfashi da sauri da sauri,sa'an nan ya zuro qafafunsa yasauko,saida yasoma kunna qwan lantarkin dakin,haske ya gauraye ko ina,sa'annan ya durfafi bandakin dake cikin dakin.


Sosai yadinga watsawa fuskarshi ruwa,mafarkin da yayi yanzu sakanni qalilan da suka shude yana dawo masa tar cikin kwanyarsa,tamkar yanxu yakeyinsa,muryarta da fuskarta na gilmawa cikin idanunsa.


Ya jima sosai a haka,sannan daga bisani ya daura alwala,a hankali ya ciri towel yana goge ruwan jikinsa,yana kuma dawowa zuwa cikin dakin,saman gadon ya sake komawa ya kwanta,saidai wannan karon rigingine yayi bayan ya tokare bayansa da filo,lokaci zuwa lokaci yana sauke ajiyar zuciya.


A daren ko kadan bacci bai sake xiyartar idanuwansa ba,yanaji yana gani hakanan yayi asarar daren,bai samu runtsawa ba har sai da ya bada faralin sallar asuba,sannan wani gajeran bacci yayi awon gaba dashi.

***********


Cikin girmamawa dukka barorin dake sassan nata suke xubewa suna miqa mishi gaisuwa,saidai ko sashen da suke baya duba bare akai ga amsawa,takawa yake zuwa cikin sassan nata cike da wani irin kwarjini da cika idanu,saidai kallo daya zakayi masa ka fahimci akwai rashin kuxari da walwala a tattare dashi,musamman ga mutumin da yasan wayeshi.


Bai tsaya ba hakanan baiyi jira anyi masa iso ba,har sai daya dangane da falon da mahaifiyarsa ke zaune tana ganawa da baqi,shigowarsa ya tashi dukka wani baqo dake wajen yafice ya basu guri,saiya samu qasan kilishin da take zaune akai yaja daya daga cikin lausasan tumtum na alfarma da aka qawata wajen ya jingina qafarshi,a ladabce yasoma gaidata.


Idanunta qur a kanshi ta amsa mishi,kana ta jefa masa tambayar dake kai kawo cikin ranta,sati guda kenan daya gabata
"Lafiya qalau kuwa kake yarima?" Dubanta yadanyi kana yayi qas da kanshi,ya shafa wuyanshi zuwa habarshi sannan ya amsa
"Lafiya ammi"
"Amma meya haifar da rashin kuzari da alamun damuwa saman fuskarka cikin satin nan gaba daya?" Shuru ya danyi kamar me neman dalilin daya sanyashi hakan,kusan hakan ne,donshi kansa baisan wacce iriyar amsa zai bata ba,wacce amsa ce kuma ta dace da tambayarta,saiya dan ja tsaki,yana tsammanin kawai shi da kanshi yakeson takura kanshi,ko kuma dan qaramin sabo ne daya gitta ba tare daya sani ba yakeson masa kutse cikin rayuwarshi,amma anya kuwa?,wanne irin sabo ne haka cikin a wannin rayuwarsu da idan aka curesu a haduwa biyu zuwa uku kacal basu gaza awa daya da rabi ba zuwa biyu
"Bana samun ishshen baccine kwana biyu....kuma ina tsammanin gajiya ce,dana gama warwarewa komai zai koma dai dai" tashi tayi sosai ta zauna,sabanin dazu da take a kashingide,fargaba tana shigarta na kada ace daga dawowarsa wani mugun abu na shirin samunsa daga magauta
"Wacce iriyar gajiyace da zata hanaka bacci haka har tsahon mako guda?,anya abdul'azeez?,idan akwai wani abu daban da kakeji ka gayamin tun komai baiyi nisa ba,tun ba'a ci galaba a kanka ba" kanshi ya girgixa yana son tabbatar mata da cewa babu komai
"Babu komai ammi,i wil b okay"shuru ta danyi,sannan ta gyada kai
"Allah yasa".


"Dazu mai martaba ya aika sassanka nima na aika,maisara ya isar da saqon kana bacci,anyi rasuwa ne a gidan dan maje,yaso kuje jana'iza tare amma bai sameka ba....,inaga yana da kyau idan ka fita daga nan ka nemeshi kaji daga bakinsa,idan yana da ra'ayin zuwanka saika shirya ka bishi,ya kamata irin wadan nan abubuwan ka dinga kiyayewa saboda gobenka,kada ka manta,gobe kaine kan matsayin da yake kai a yanzu,shi yasa yakeso ka zamana a gefansa"
"In sha Allah" ya amsa mata,ba tare da yasan wanne irin feeling ne ke cikin zuciyarsa ba game da maganar.


Dai dai lokacin sumaira ta qaraso falon,wadda tayi shirinta na komawa makaranta,kafin ta zauna azeez din ya umarceta ta hada mishi abinci,ta hada masa komai ta aje gabansa sannan ta qarasa wajen ammi suka gama maganarsu sukayi sallama ta wuce.


Bata fi mintuna goma da tafiya ba afnan ta qaraso falon,rungume take da litattafanta ta iso gaban ammi tazube littafan gamida zama sosai a gabanta bayan ta salube jakarta kamar zata shige cinyarta,cike da shagwaba take fidda safarta,idanun azeez da bata ankara da wanzuwarsa a falon ba yana kanta,ba kasafai yake maka magana ba idan kana abinda baya so,yawanci yafi sanya maka idanu harsai sanda idanunka suka ankara dashi
"Wannan karatun akwai wuya ammi....wallahi kamar na gudu" murmushi kawai ammin ta saki kana ta dubeta
"Dadi ne yayi miki yawa auta....mutum nawa ne suke neman dama irin taki amma basu samu ba?" Shuru tayi na dan sakannin da basu wuce uku ba kana ta gyada kai
"Gaskiyane fa ammi,har kin tunamin da BILKISU" kanshi ya daga da hanzari jin afnan ta ambaci irin sunan,sunan da baisan me yasa ya fara zaune masa cikin kwanyarsa da tuninsa ba,ba tare data lura dashi bs taci gaba
"Tana da qoqari sosai ammi,gasar karatu muke da ita,duk da bamu saba ko shaqu da ita ba....amma kowa yasan mayyar karatu ce,burinta a rayuwa tayi karatu....Allah sarki bilkisu,rana daya babanta ya cireta daga makarantar,yayi mata auren dole....."
"Har yanzu baki manta ba afnan,har yau?" Ammi ta fada,wanda sai a sannan ta tuna afnan din ta taba zuwa mata da qorafin akai.maganar zuwa ga mai.martaba,duban ammi tayi,fuskarta na nuna alamun alhini
"Bazan manta ba ammi,bansan tana da kirki ba nayita gaba da fada da ita,ba ruwanta ammi,innocent kamar bilkisu amma aka hanata cika burinta"
"Gskiyar yayanku da wani lokaci baku shiri saboda dan banzan surutu,idan kin gama saiki tashi ki wuce ciki" langabe kai tayi tana duban ammin,tana shirin sake magana suka hada idanu dashi,ya balla mata harara data sanya bakinta ya rufu gam,tayi gaba da sauri zata wuce
"Saiki turo uwani ta kwashe miki su,kada kisoma zuwamin anjima kina min cigiyar littafanki ina tsaka da hutawa"
"Zoki kwashe" ya fada cikin kaushin murya,ba shiri ta dawo ta tattara litattafanta tayi gaba,ya saki siririn tsaki
"Silly girl,litattafanma sai an kwashe miki an kai miki saboda tsabar sangarta,saina rage dukka barorin dake sashen nan na maida ayyukan kanku" itadai bata da bakin magana ta qara wuta tawuce nasu bangaren,ammi itama naji batace komai ba,sai murmushi kawai datayi,tun ya qarami haka Allah ya halicceshinda wani irin girma cikin zuciya da jikinsa,amma ya manta shima komai hadimaine suke masa?,saita kada kai kawai tana sake sakin murmushi qasan ranta tana binsu da addu'a.
7/11/21, 4:33 PM - My Mtn Number: 38
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*
*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070




Sannu a hankali ta soma qoqarin bude idanuwanta da sukayi mata wani irin nauyi,a qalla ta dauki kusan minti daya tana wannan fafutukar sannan tasamu ta budesu tana warasu dakyau don su daina ganin dishi dishi,cikin ikon Allah ganinta ya daidaita,saita sake ware idanun nata tana kallon dakin da take ciki.


Da fari bai mata kama da dakin asibiti ba,sai data lura da wasu abubuwa da suke kamanceceniya dana asibiti sannan ta tabbatar tana cikin dakin asibiti ne.


Babu kowa cikin dakin,sai fanka da ac da suke aikinsu cikin madaidaitan sanyin da bazai takura ka koya hanaka sukuni ba.


Kallonta tayi qoqarin maidawa bakin qofa sanda taji an turo qofar,anty zuhriyya ce karo na biyu,qara saurinta tayi don ta iso gareta,fuskarta washe da fara'a sosai tana duban bilkisu,bata tsaya ko ina ba sai kujerar dake gaban gadon,wanda dama ita ta tashi daga kai,ta sanya hannunta ta kamo hannun bilkisu guda daya,murmushi da hawaye na qwace mata lokaci daya
"Yanzu ina ne yake miki ciwo?,mene ne yake damunki?"
"Babu komai anty" ta fada itama sabon hawaye yana balle mata,hannu tasa ta fara share mata tana cewa
"Daga yau ba zaki sake kukan baqinciki ba daughter tunda gani....bari naje na kira likita ya sake dubaki" kai ta gyada mata tana binta da kallo.


Tana dab da fita aka turo qofar dakin,babanta ne sanye da shadda da babbar riga,ya sake kutso kai dakin yana ta raba ido,murtuk anty zuhriyya ta hade fuskarta tsaf,maimakon ta fita saita fasa ta dawo cikin dakin.


Ko kallon malam bilyamin batayi ba harya shigo dakin,ya qaraso gaban gadon bilkisu yana yi mata sannu
"Me ya sameki mai gado?" Ya tambaya yana dubanta,kai ta kada
"Nima ban sani ba abba,kawai naji jiri ne saina fadi"
"Ashsha...Allah ya sawwaqe" ya fada yana maida dubanshi kan zuhriyya,tun ba yau ba yasan wacece zuhuriyyan,kuma kwanwarsu bata jiquwa sam
"Saukar yaushe?,ashe kin dawo" ya fada,batako dubeshi ba illa
"Eh" data fada albarkacin bilkisu dake wajen.


Turo qofar dakin da aka sakeyi ne ya katse shurun da yaso wanzuwa a dakin,mijin anty zuhriyya ne da suke kira da abbaaa shida yaransu gaba daua,wanda kafin ta tafin mutum biyu bilkisu ta sani,najwa da ateeq,yanzun kuwa sun zama su uku,an samu qaruwar da namiji haisam,su kansu su biyun data sani dukka sunyi wayau qwarai qwrai,kada ma najwa da take 'yar budurwar taji labari,tana da tsaho wanda da alama tsahon babanta ta dauko.


Babansun na dauke da haisam,najwa da ateeq suna dauke da kwanukan abinci a kwanduna,bude hannunta tayi tana musu oyoyo,yayin da abbaaa ya tsaya gaisawa da malam.bilya,wanda babu jimawa yayi musu sallama ya wuce ganin kamar sun ma manta da wanzuwarsa a dakin.


Ranar kusan wuni sukayi tare,anty zuhriyya sai nan nan take da ita,abbaa mutum ne mai sauqin kai da jan mutane a jiki,bare bilkisun da take kamar diya a wajensa,dukkan yaran kansu sun sake da ita,musamman najwa ita tafi saurin tunota,ateeq sai a hankali a hankali ya dinga tunawa yana kuma sakewa,haisam kam dama sarkin qiwa ne yana kwance jikin mamarshi.


Ko da likita yazo ya dubata sai yace ko zuwa gobe ma zai iya sallamarsu,tunda babu wani abu dake damunta kuma,saidai sallamar washegari bata samu din ba,saboda a daren wani irin zazzabi ne mai azabar zafi ya rufeta,sosai hankalin anty zuhriyya ya tashi,ta kasa runtsawa itama daren gaba daya,sai gab da asuba aka samu ya sauka,bacci kuma ya dauketa.


Kwana biyu kenan tana fama da nataccen zazzabin,abinda ya hana sallamar kenan,sai a kwana na uku ne aka samu ta kwana lpy,washegari da safe kuwa ta tashi da dan qwarin jikinta,hakan ya yiwa anty zuhriyya dadi,da wuri ta sanyata tayi wanka,ta bare mata daya daga cikin sabbin kayan da tun tana kwance tahau siya mata,duk da tayi mamakin kyawawan sitturun data gani a jikinta,ta bata daya daga cikin wanda ta siyo mata ta shirya,tsaf kuwa tafito,ta hada mata tea da chips ta miqa mata tana dubanta
"Yau dai babu sauran ciwo,maza ki cinye wannan tas" murmushi bikisun tayi har fararen haqoranya na bayyana,hakan ya sanya anty zuhriyyan dan zuba mata idanu,saboda yadda kamarta da yayarta maimunatu ta fito sosai,sai taja kujera ta zauna a gabanta tana dubanta sanda take cin abincin,cikinsu babu wanda yace komai sai kallon juna da sukeyi lokaci zuwa lokaci,dakin babu kowa saisu biyun,don tunda safe da abbaa yazo da yaran ya kawo musu breakfast suka koma tare,dama ko sau daya basu yarda sun zauna tare da ita a asibitin ba,sunfi sabawa da abbaansu shi yasa suke maqale dashi,don haka ta barsu tare tunda akwai mai aikinsu a gidan dake kula dasu.


Sai data ci fin rabi sannan ta aje tana cewa
"Na qoshi anty" murmushi ta saki
"To ma sha Allah"
"Bilkisu....jikina ya bani cewa,bayan tafiyata,abubuwa da dama basu tafi dai dai yadda na tsara ko kuma yadda suka kamata ba,duk da nazo na tadda wasu sauye sauye,amma hakan bai kwantar min da hankalina ba....saura shekara biyu mu dawo amma naji dukka hankalina ya karkata nazo na ganki naga halin da kike ciki,ko bacci cikakke bana iyayi ba tare da nayi mafarkinki ba....sanar dani meke faruwa daughter ko kuma meya faru bayan bani nan"


Daga yanayin yadda fuskarta ta sauya tun kafin ta furta komai ya tabbatar mata da akwai gagarumar matsala,kawai kima abinda ya faru mai girma da rayuwarta.


Kasa cewa komai bilkisun tayi sai wani zazzafan kuka daya subuce mata,batasan cewa a baya kuka tayi mara 'yanci ba sai yanzu,sai a wannan lokacin data samu kafadar da zata kwantar da kanta ta fidda duk wani zafi da radadi dake mintsinar zuciyarta,wasu irin hawaye masu dumi suka dinga kwaranya daga kuncinta,wanda ta tabbatar duminsu tun daga zuciyarta yake.


Shuru kawai anty zuhriyya tayi tana bubbuga bayan bilkisun ba tare data hanata kokawa ba,kuma ba tare data ce mata komai ba,zuciyarta cike fal da tsoro da taraddadin abinda kunnuwanta zasuji daga bakin bilkisun,babu abinda zuciyarta bata qiyasta mata ba,bata tsaida ita ba har zuwa wani lokaci da kukan yaja baya,ta miqe da kantabta bata ruwa mai maidaidaicin sanyi dake cikin fridge din dakin,tasha shi kuwa mai dama,sannan ta aje tana maida ajiyar zuciya.


Tiryan tiryan ta soma bawa anty zuhriyya labarin komai,babu abunda ta boye mata har zuwa ranar da antyn ta sanya qafarta a falon gidansu.


Tamkar wadda ta hadiyi tabarya haka ta kasa zama,idanunta tuni suka rine saboda kukan data dinga yi tun farkon labarin,har zuwa lokacin da hankalinta yayi mummunan tashi sanda taji irin auren da malam bilyan ya yiwa bilkisu,diya qwaya daya tilo da 'yar uwarta ta jini ta tafi tabar musu,duk maganar data kwaso saita subuce mata saboda tsabar masifa da tashin

Please Login or Register in order to submit comment