Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hankalin dake cinta,a irin wannam yanayin abbaa ya dawo kawo mata hisham.


Shi kansa hankalinsa ya daga da yanayin daya taddasu,kasa ce ma abbaan komai tayi,sai sanya kanta itama a kafadarsa da tayi ta rushe da kuka kamar yadda bilkisun itama ke kukan,saboda labarin ya zame mata tamkar fami ne a ranta
"Bazan qyalesu ba abbaa,bazan rabu dasu ba,dukkansu kowa saiya dandana,kowa saiya debi sakamakon abinda ya aikata,har masarautar kaisan bazan qyaleta ba,koda dukkan abinda na mallaka zai qare sai nayi shari'a dasu" abinda take fada kenan,shidai baice komai ba face lallashinta da yake,yana rarrashin bilkisu kuma da baki,daga qarshe har bilkisun da share hawayenta amma kukan anty zuhuriyyan yaqi tsaiwa,daga qarshe janyeta yayi suka fice daga dakin.


Basu dawo ba sai bayan mintuna wajen arba'in,tsakanin miji da mata sai Allah,sanda suka dawo kukan ya tsaya,saidai fuskar nan tata a dinke take tsaf,bayansu likitane suka shigo tare dashi,yakuma dudduba bilkisu ta tabbatar masa batajin wani ciwo sannan ya rubuta mata sallama.


Cikin motar abbaan ma kusan shirune yayi musu rakiya,kowanne a cikinsu sai sauke ajiyar zuciya yake,bilkisu bata fuskanci inda suka nufa ba saida anty zuhriyya ta masa maganar titin da zaibi,wanda babu tantama titin gidansu ne
"Yanzu zuhriyya ba zaki bari ba zuwa gobe?" Ranta tasake batawa sosai tana dubanshi
"Abbaa,na riga dana maka bayanin komai,na rantse ko awa guda dukkan abinda ta mallaka bazai qara ba cikin gidan,kayi haquri bawai naqi bin umarninka bane,amma ta gama zama qarqashinsu har abada,koda bana raye na tabbatar dangina idan suka samu labarin komai ba zasu barta a qasar nan ba" shima bai sake cewa komai ba,saiya sauya akalar motar zuwa inda take kwatanta masa din.


Mintuna kadan suka isa qofar gidan nasu,ita da anty zuhriyyan ne suka fito,abbaa na xaune cikin motar suka shige ciki.


Tayi sallama saidai ciki cikin yadda ba kowa bane zaiji,anty ce zaune a falon ita da mama ladi,irin zaman da saikace dole aka musu,don kowacce tata ce ta zaunar da ita,don kusan rabin xaman kishi ne ke kawoshi,bata kalli kowacce cikinsu ba fuskarta kamar hadari tace da bilkisu
"Ki shiga ki tattaro duk abinda kikasan kina da buqatarsa kuma nakine kizo mu wuce" kai bilkisun ta gyada mata cike da taraddin anya idan mahaifinta yaji wannan zai yarda?,zata iya tuna kadan daga cikin dauki ba dadin da akayi tun tana mitsitsiyarta kan za'a dauketa ya hana,baya ga haka da wayonta ma ansha gwagwarmaya da duk wadanda suka zo daukan dansu da suka haifa cikin gidan,amma duk da haka bata tanka ba ta wuce ciki,saidai wani bari na zuciyarta 'yan uwanta ne maqale a ranta.


"Waike wacece da zaki dinga shigowa mutane gida haka kai tsaye?,sannan kuma ki tsaya kina baiwa yarinyar mutane umarnin ta hada kayanta ku tafi,kuje ina?" Cewar mama ladi data miqe cikin son nuna ita din wata abace.


Wani mummunan kallo daya baiwa mama ladi mamaki ta jefeta dashi,qoqarin tausar zuciyarta take don kada ta kai mata mari,da qyar ta ragewa kalamanta zafi sannan tace
"Kije ki tambayi wanda ya ajeki wacece ni,sannan koshi din a yau bai isa ba yayi kadan ya hanani tafiya da bilkisu,idan kuma kuna musu bismillah" jin kalamanta ya bata mamaki,saita juya cikin rawar jiki tayi dakunan malam don ta kirashi.


Ba'a jima ba sai gasu tare yana qoqarin sanya hularshi aka,da alama tasowar gaggawa yayi
"Lafiya zuhriyya?" Shima din sai data soma watsa masa banzan kallo,tanajin kamar taje ta shaqeshi,banda maganganun da sukayi da abbaa da kuma yadda takejin kanta a yau ba shakka daga malam.bilyan har tarkacen matansa yau babu wanda xai tsira gurinta
"Au dataje ta taso ka bata gaya maka dalilin zuwa na ba?" Isowa yayi sosai tsakiyar falon
"Ta gayamin,kuma kinsan babu wannan maganar tun shekarun baya bare yanzu,bilkisu tana gidan ubanta,kuma nan ne ya dace taci gaba da zama kamar sauran 'yan uwanta" wani tururi taji zuciyarta zuwa fuskarta sunayi,saita gyara tsaiwa sosai yadda zataji dadin fidda kalaman bakinta da suka cika qirjinta,dama neman rage wasu daga ciki takeyi
"Wanne uban?,ina uban yake?" Ta maimaita tambayarta tana kallon hagu da damarta alamun nemansa take,sai data gama waige waigenta sannan ta dawo da dubanta kanshi
"Wai kai ne?,to indai kanka kake kira da sunan uba ba shakka ka cuci iyayen qwarai,kuma kayi gaggawar cire kanka daga wannan sahun,don baka da wani abu daya da zaka iya bugar qirji dashi wanda zai sanya ka samun matsayin shiga sahun iyaye,sam halayya mu'amala da dabi'unka bana iyaye bane,kafi kama da wanda baisan ciwon haihuwa ba saboda bai taba yi ba,hakanan kafi kama da d'an kama karya kuma azzalumin uba,uban da baisan komai na diyoyin daya haifa ba,uban daya gwammace ya saida 'yanci da mutuncin yarsa sabida abun duniya fararre qararre,uban daya baiwa zalunci sunan adalci,uban dake tarwatsa rayuwar 'ya'yansa da hannunsa....tir da wannan uban daya manta cewa akwai hisabi tsakanin iyaye da 'ya'ya,ya manta da hadisin da yace dukkaninku masu kiwo ne,kuma za'a tambayesu game da abinda aka basu kiwo,ya manta da zai tsaya gaban zatin Allah ya fadi yadda ya riqe ya kuma tarbiyyanci yaran da aka bashi,bana shakka bilyamin akwai tsantsar jahilcin ilimin addini bisa kanka,wanda hakan ya sanya tun karon farko da 'yar uwata ta zabeshi xabin tumun dare tayi,ba shakka mummunar qaddara mai qarfi ya sanya 'yaruwata saliha baiwar Allah,wadda bata zalunci ta hadu dakai harka shiga qaddararta ta hada zuri'a dakai,saidai duk hakan mu a matsayinmu na musulmai munsan cewa haka Allah ya qaddara"


"Hakanan barin bilkisu da nayi a baya babban kuskure na tafka,amma shima nasan cewa qaddarar saika aikata mata zaluncin daka yine,saidai a yanzu ina mai farincikin shaida maka,ka bude dukkanin kunnuwanka kaji,ni zuhiryya,indai an haifeni da jini kuma halastacciyar 'ya ce,bilkisu tabar gidanka da sunan zama har abada,ina kuma mai jaddada maka cewa a yau,koda sama da qasa zasu hade,koda zan rasa lafiyata ko numfashina bazan fita daga gidan nan ba sai tare da bilkisu" sosai maganganunta suka tsumashi da kyau,saidai yaji kunyar yadda ta gaggaya masa maganganu gaban matanshi da yake cikawa baki,wanda tunda suka san juna da zuhriyyan duk da babu jituwa tsakaninsu amma bata taba gaya masa maganganu irin haka ba masu zafi.


Bilkisu dake daki tare da qannenta data samesu zaune waje daya cike da alhini suka ruqunqumeta cike da farincikin ganinta,don dama tun randa suka dawo basu sameta ba suka cika da zulumin inda taje,suka soma tunanin kodai ta sake tafiya ta barsu ne?,jin muryoyin mahaifinta dana anty zuhriyya ya sanyata fitowa,dukka yaran suka biyo bayanta.


Fitowarta taja hankalin anty zuhriyyan,ta dubeta da idanunta da suka sake birkicewa da bacin rai
"Waima kayan da zaki dauka ba daga azzaluman masarautar can kika samesu ba?" Kai ta gyada mata,cikin daga murya tace
"Bana buqatar ki dauki koda tsinke wanda ya fito daga hannunsu,ki tattarawa ki barwa masu zalama da son zuciya su qara kan yanke talaucin da suka basu,iya gyambon ma da suka barwa zukatanmu ya isa,wuce muje" a sanyaye bilkisun ke takowa zuwa qofar fita,tausayin 'yan uwanta yana ratsata,tana son cewa wani abu amma tasan yanzun ba qadamin yin magana bane.


"Ke mai gado,karki kuskura fa ki fita" ya fada yana takowa,sai anty zuhriyya ta tsaya,ta waiwayo tana dubansa
"Kar kayi gaggawar kai kanka mana gidan yari tun lokacin shari'armu baiyi ba,ka bari har sai zuwa sanda na makaka a kotu kaida masarautar kaisa tukunna" daga haka taja hannun bilkisu suka fice.


Tana iya hango qannanen nata dakuma jiyo muryoyin kukansu,da alama baban nasu ke korasu ciki suna son ganin 'yar uwarsu,hakan ya sanya ta fashewa da wani sabon kukan
"Kada ki damu,za'a kula dasu,tunda suma 'ya'ya ne kamar yadda kike 'ya,na miki alqawarin bazan qyalesu rayuwarsu ta tagayyara ba,zan basu dukkan wata gudunmawa da zata iya sanyasu kasancewa cikin farinciki saboda albarkacinki" anty zuhriyyan ta fada a tausashe,kai bilkisu take kadawa,tanason buda baki tayi mata godiya amma ta hanata,tadai buqaceta kawai data tsaida kukanta,tayi qoqarin yin hakan.



Sauke ajiyar zuciya sosai anty zuhriyya tayi tana sake rungume hisham daya soma bacci a qirjinta tana tsara yadda zata tafi da komai,abbaaa yayi murmushi
"Yaudai burin zuhra na shekara da shekaru sun cika" ya fada cikin salon tsokana,murmushinta jefeshi dashi kawai,don yau bata da bakin rama tsokanarshi,abinda aka yiwa bilkisun ke mata ciwo sosai a rai,tabbas ba zata bari ba,ba zata qyale ba kamar yadda taci alwashi......



*Alhamdulillah*

*_cikin ikon Allah da nufinsa a nan zamu dakata zuwa hutun azumin ramadan,sai kuma bayan sallah idan Allah ya bamu aron rai da lafiya,muna muku fatan Alkhairi,tare da fatan za'a yi ibada lafiya,Allah ya sadamu da alkhairinsa_*ðŸ™ðŸ½ðŸ™ðŸ½ðŸ™ðŸ½
7/11/21, 4:33 PM - My Mtn Number: 39
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*
*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070
_____________________________






A falo suka tadda najwa ateeq da mai aikin anty zuhriyya suna kallo,dukkansu suka taso suna rige rigen yi mata sannu da zuwa,ta amsa na mai aikin tana miqa mata hisham
"Jeki kwantar dashi a dakinsu,ki taho min da muqullan dakunan nan"
"To anty" ta fada cikin girmamawa tana daukar hisham daga kafadarta sannan ta wuce ciki.


Waiwayowa anty zuhriyya tayi tana duban bilkisu
"Dauhgter....ya haka,a gidanku fa kike" ta fada ganin yadda take tsaye tunda suka shigo,murmushi bilkisu tayi kana ta samu daya daga cikin kujerun ta zauna tana dan qarewa falon kallo,wannan ba shine gidan anty zuhriyya data sani ba kafin suyi tafiya,wannan yafi wancan kyau da tsari,da alama sun sauya gida ne kafin dawowarsu,kuma wannan din na nuna cewa sabon gida ne kuma sabon gini ne,haka nan duk kayan dake cikinsa da alama sabbi ne.


Babu jimawa ta dawo da muqullan,anty zuhriyya ta karba tacewa bilkisu ta taso suje,miqewa tayi ta bita a baya tana sake duban hanyar da suke bi.


Wani corridor suka shiga,wanda ke dauke da dakuna guda hudu,bibbiyu suna kallon juna,sai babban window daga can qarshen corridor din,daya daga cikin dakunan ta bude ta shiga bilkisu na biye da ita.


Babban dakine wanda ke dauke da gado two bedside drower wardrobe sai kuma madubi,malale dakin yake da tiles kalar kayan gadon,sai wata qofa dake rufe cikin dakin wanda babu tantama bandaki ne.


Gefan gadon anty zuhriyya ta nuna mata,ta isa a hankali ta zauna,juyawa tayi ta soma qwalawa mai aikin nata kira,nan da nan ta qaraso
"Ina sabbin curtains din nan da aka kawo?"
"Suna inda kika ce na ajiye miki"
"Oya maza debosu kizo ki tayani sakawa". To tace sannan ta juya ta fita,babu jimawa ta dawo dasu a hannunta,karba tayi tana nuna mata toilet
"Shiga ki dubashi da kyau ki wankeshi fes da Allah haula"
"To anty" ta sake cewa tana nufar bandakin.


Bilkisu dai na zaune antyn tasoma sanya labulayen da kanta,taso tayata amma ta dakatar da ita
"Kin manta daga gadon asibiti kike?,hutu yanzu shine abinda yafi dacewa dake" tana ji tana gani ta zauna ta barta da aikin,tana aikin tana janta da hira,tun bata sakewa harta soma sakin jiki tana bata amsa,wani abun kuma kawai tayi dariya,don har yanzu qannenta na maqale a ranta,tana tunanin halin data barsu.


Cikin qasa da awa guda dakin ya koma cikakken daki,haule ta qarasa gyarashi tas,tasa aka dauko spare plasma da sauran kayan kallo aka maqala,tunda dama already akwai gurbin sanyasu a dakin,sanyawar ne kawai ba'ayi ba,wala'alla saboda ba'a buqatar dakin babu mai zama a ciki.


Agogo anty zuhriyyan ta kalla
"Yanzu ki kwanta ki huta sosai,idan lokacin sallah yayi zan tasheki kiyi sallah" kai ta gyada mata,cikin sassanyar muryarta tace
"Na gode anty"
"Shshshsh!!,banason ki sake cewa komai,idan ba haka ba zanci qaniyarki,don na miki abu shine zaki godemin?" Murmushi ne ya subuce mata,itama saita sakar mata murmushin kana ta juya ta fice daga dakin tana sakin ajiyar zuciya.


Sai yanzu tadan samu nutsuwa kadan data soma yin abinda ya kamata akan bilkisun,saidai tana jin cikin wajiban da suka hau kanta batayi komai ba,so take ta taba rayuwar bilkisu sosai,ta goge duk wani bacin rai qunci da tabo data taba fuskanta,duk da tasan cewa duk.yadda kakai gason goge wani tabi a rayuwar mutum,yakan iya tafiya amma lallai zai bar maka burbushinsa,walau a zuciyarka ko rayuwarka.


Duk da taso tayi baccin amma hakan ya gagara,saboda tunane tunanen da suka cika mata qwaqwalwa,lissafe lissafe na rayuwa,kusan haka dai ta cinye lokacin da anty zuhriyyan ta dibar mata ba tare data iya runtsawa ba.


Sanda antyn ta shigi fes da ita,da alama tayi wanka ta canza kayan jikinta,baki ta kama
"Daughter,kada dai kicemin bakiyi baccin ba" murmushi kawai tayi
"Baccinne baizo ba"
"Ki tashi kiyi sallah to,saiki fito falo muci abincin rana"
"Toh" tace tana saukowa,ta shige bandakin ita kuma ta fita.


Dukkansu ta samesu saman dining,da alama ita kadai ake jira,cikinsu ta shige itama amma ta kasa sakewa saboda abbaa dake wajen,hakanan ta tsakuri abincin ta miqe,antyn ta karanceta,hakan ya sanya ta saka haule ta bita da wani daki.


Ranar gaba daya kusan wuni sukayi tare da ita,basu bata wata dama da zata kebe ba bare wani tunani ya dameta,saidai duk da haka lokaci lokaci qannenta suna fadowa a ranta.


Da daddare bayan tayi wanka tana shirin kwanciya anty zuhiryya ta shigo dakin dauke da leda,already ta riga data saba da yin wanka kafin ta kwanta tun xamanta a mexico
"Ga kayan bacci nan,da kuma wasu kala biyu spare,sai zuwa jibi idan kin huta sosai idan Allah ya kaimu zamu fita inyi miki siyayya,ki rubuta duk abinda kike buqata ki ajjiye,idan ba so kike ranki kuma ya baci ba kada ki soma cewa zaki muna alkunya,ki sanya a ranki kamar yaaya maimuna ce tace ki rubuta duk abinda kikeso" murmushi dai still tayi mata kamar yadda ta saba,sannan tayi mata godiyar data nuna mata sam bata so.


Kwanakinta biyar a gidan basu fita ko nan da can ba,antyn natason haifar da sabuwar shaquwa tsakaninsu,tana ta son bilkisun ta sake suma yaran duka su sake da ita sosai yadda ta kamata,cikin kwanakin sosai bilkisu taga kulawa da tattali,kullum cikin ina ka saka ina ka aje anty zuhriyya keyi da ita,bata fita ko ina duk da cewa ranar data diro qasar daga filin jirgi sai gidan malam bilya,tana da buqatar zuwa wasu gurare amma dukka ta soke tace saita gama settling din komai.


A kwana na shida ne da yamma tasa ta shirya ita da yaran duka suka fita a motarta,ita ke driving bilkisu na zaune gefanta riqe da hisham wanda yasoma sakin jiki da ita,ateeq da najwa suna baya.


Sai da suka hau titi sosai sannan anty zuhriyya tace da ita
"Wanne abu kike ganin ya kamata a yiwa 'yan uwanki?" Duban anty zuhriyya tayi da sauri sannan tadan kautar da idanunta,bata zaci maganar nan kusa haka da wurwuri ba,idan ason ranta ne,kuma daso samu ne kowacce ta koma gaban mahaifiyarta ta kula da ita,saidai hakan kuma zai iya zama naqasu ga burinta nasin kasancewa tare dasu da kuma cikar burikansu,don babu lallai a inda zasu koma din su samu ingantacciyar rayuwa,wala'alla iyayen nasu sun jima dayin aure,babu tabbacin kuma wanda suka aura din zai riqe musu yaran nasu,dole sai hannun kakanni,wadanda suma wasunsu suna ta kansu ne bare su dauki wahalar riqe jikoki.


Maganar anty zuhriyya ta katse mata tunaninta
"Inaga a nawa ganin,kawai mu kula da iliminsu su samu ingantaccen ilimi a makaranta mai nagarta,da sutturar sawarsu zuwa walwalarsu cikin gidan,inaga wannan shine abinda sukafi buqata" kai take gyadawa tanajin wani sanyin dadi a ranta,ba shakka wadan nan kusan sune jigon komai,kuma tana fatan idan suka samu haka ka'in da na'in komai mai sauqi ne.


Godiya sosai ta yiwa antyn duk da ta nuna bataso,amma bata fasa ba,sai albishir na biyu daya sake faranta ran bilkisun,har ya sanya fuskarta ta washe qwarai
"Abu na gaba da nake tunani shine,zan daukeki muje ethopia,asalin danginmu dukka suna nan,jinin abbanmu can ne tushenmu" nannauyar ajiyar zuciya ta saki,karon farko da zata taka cikin ahalinta na uwa,zataga dangin mahaifiyarta wadanda kusan zata iya cewa tun tashinta bata sansu ba sai a yanzu,farincikinta ya kasa boyuwa,wanda hakan ya sake farantawa anty zuhuriyya.


Daya daga cikin manyan shagunan saida sutturu da dukka kayan qyale qyale na mata suka sauka,kaya sosai anty zuhriyya ta dinga lodar mata kai kace idanunta a rufe yake,kamar kuma batasan ciwon kudin ba,sannan ta koma bangaren mayuka zuwa turaruka suma ta musu diba son ranta,hakanan mayafai gyalulluka zuwa takalma,sarqoqi da kayan makeup,sai data ji a karan kanta ta gamsu da siyayyar data yi sannan taje aka mata total ta biya,babu abinda ta siyawa yaranta don bata su take ba,burinta kawai ta maida bilkisun asalim bilkisunta.


Cikin satittika qalilan ta soma komawa hayyacinta,sati hudu kacal tayi wani irin kyau,ta cika sosai fiye da yadda anty zuhriyya ta tsammata,kai kanka idan ka ganta sai kayi mamaki,dukkansu sun alaqanta hakan da nutsuwa da kwanciyar hankali data fara samu,don tuni antyn ta fara maganar yadda zata zana neco da waec,tunda lokacin zanawa ya sake zagayowa,wato shekara iwar haka akayi mata karen tsayen da yaso kassara rayuwarta,ta wani bangaren kuma tana shirin yadda zata maka masarautar kaisa da malam bilya a kotu.


Da qyar abba yasha kanta,a wani dare bayan ta gabatar masa da abinci yaci,ta kwashe kwanukan ta gyara wajen tsaf,saita dawo inda yake
"Abban najwa.....nace idan babu wani ni zanje nayi wani aiki?" Saiya daga kanshi yana dubanta cikin mamaki
"Wanne aiki ummin najwa zatayi da zaisa ta barni ni kadai?" Saita gyara tsaiwarta tana fata ya fahimceta
"Kasan na fara tsara yadda zan shigar da qarar bilkisu da masarauta da kuma mahaifinta,to so nake cikin satin nan na kammala komai a soma shari'ar,banason abun ya dauki dogon lokaci" ajjiye takaddun dake hannunsa da yake dubawa yayi,sannan ya gyara zamanshi sosai,saiya nuna mata gefanshi
"Zoki zauna muyi wata magana" a hankali cikin sanyin jiki ta tako ta zauna a inda ya nuna mata,kiran sunanta yayi cikin sautin dake nuna zancan da zaiyi mai muhimmanci ne
"Inda zakiji shawarata zuhra da kin ajjiye maganar shari'a a gefe,saboda wasu dalilai da nake ganin koda an soma shari'ar babu lallai a cimma nasara,dalili na farko shine,dukkan abinda ya faru ga bilkisu masarauta bawai gaban kansu ko qarfa qarfa sukayi suka dauke bilkisu suka aurarwa dansu ba,a'ah,sun nemi aurenta ta hannun mahaifinta wanda dama shine yafi cancanta daya aurar da ita,ya amince ya aura musu ita bisa sadaki da kuma amincewar dukkan waliyyan yaran,kinga ko a nan hujja ta qare,ba saceta akayi ba,ba'a daura auren ba saida amincewar waliyyi wakili kuma mahaifinta,abu na biyu wannan shari'ar zata zama tamkar tonon silili ne ga bilkisu,wanda baisan batun bama ya sani,ta zama abar nunawa aduk inda zata shiga,shi nasu dan namiji ne,wanda wala'alla ba kowa bane ma yake da matsayin ganinsa ba bare a nunashi,koda ana ganinsa wala'alla sau daya ne a shekara wajen hawan sallah,wannan zai zame mata qalubale wajen wanda zata aura a gaba,koshi ko ahalinsa,hakanan zai zama takura a rayuwarta,tunda shari'a ce da manyan mutane,dole zata shiga jaridu da mujallun qasar nan,hadi da gidajen tv dana redio,kuma hade da hotunanta da nashi,abu na uku,malam bilyaminu mahaifin bilkisu ne,mahaifi kuwa har abada yana nan a matsayinsa na mahaifi duk lalacewarsa,duk tarin zunubansa,ba'a sauyawa tuwo suna,hakanan zai.iya yiwuwa a sanda kotu ta yanke mishi hukunci hakan ya sosa ran bilkisu,ya kuma hanata sukuni da walwalar da kikeson sama mata.....zuhra....inason ki duba dukka wadan nan hujjojin nawa,bawai don bamu da kudin da zamu iya tsayawa bilkisu ba,saidai wasu abubuwan mukan dauke kai daga garesu,mu kuma yi kamar basu faru ba,kamata yayi yadda kika dauko hanya nason inganta rayuwarta ki dora daga nan,ki mance komai don kada ya hanaki yin abinda ya kamata" shuru tayi tana jujjuyawa gami da tattauna kalaman mijin nata,tabbas maganganunsa suna bisa hanya,saidai tanajin kamar shari'a dasu ce kawai hanyar da zata sanya ta huce,amma dole ta tsaya ta duba abinda ya kamata kamar yadda yace,da wadan nan kalaman ta haqura,ta kuma watsar da abunda daa ta qudurta aiwatarwa.

***** *****"""""***** ******

A hankali yake fidda kayan jikinsa bayan dawowarsa daga zaman fada na musamman da aka gudanar a yau,cike da gajiya da qosawa yake rage yawan kayan dake jikinsa,fuskarshi kamar kullum babu walwala babu annuri,komai ma baya masa armashi ko dadi,ji yake kamar wanda aka sanya qaton kwado aka qulle rayuwarsa.


Sai daya gama cire kayan duka sannan ya doshi bandaki,ya sakarwa kansa ruwa mai sanyi wanda ya dinga ratsa sassan jikinsa,idanunsa a rufe amma qwaqwalwarsa ta tafi tunanin data saba,tunanin daya zame mata tamkar al'ada matuqar ya tashi daga gadon baccinsa har zuwa sanda zai koma ya kwanta zuwa wani daren,tunanin dake azabtar dashi qwarai,ya kuma dauke dukkan wata walwala tashi cak fiye da yadda aka sanshi a baya.


Yana dakinsa yana tsane lemar jikinsa,tare da ci gaba da tattaki zuwa bakin mudubi,kansa yake kalla yana kuma sake goge jikinsa,baisan me yasa ta zauna masa daram cikin kwanyarsa ba,baisan me yasa tunaninta ya zame masa jini da tsoka ba,yabi dukka wata jijiya ta jikinsa,yakeson hanashi zama lafiya ba,wannan wanne irin tunani ne mai naci?,wanne irin memory ne dayake kasa barin zuciya da tunani su huta?,a iya tunaninshi komai ya qare tsakaninsu,tunda igiyar alaqar data hadesu ta jima da warwarewa,yana ganin bai kamata komai yayi zurfi haka ba,tunda dama an shirya shine na taqaitaccen lokaci,amma me yasa?,me yasa komai yake zaune daram a kwanyarsa kamar a yanzun komai ke gudana?.


Tsaki yaja yana ja da baya daga gaban mudubin bayan ya dauki manshi da yake shafawa ya koma gefan gadon yazauna yasoma shafawa,yana kokawar kauda komai daga kansa kamar yadda kullum yake wannan yaqin,saidai kusan duka a banza ne.


Wayarsa dake gefe ta dauki tsuwwa,saiya waiwaya ya duba,ammi ce ke kira,ya sanya hannu ya amshi kiran ba tare daya dauki wayar a hannunsa ba,saidai ya sanyata a handsfree
"Kana sassanka ne?"
"Eh ammi"
"Ohkey,ka sameni a sassana,falo na uku,zamuci abincin dare tare anjima"
"To in sha Allah" ya amsa mata yana latse kiran.


Misalin takwas na dare ya shirya cikin qananun kaya,wadanda sukayi bala'in amsarsa,kyansa da kwajininsa dukka sun fito,ya dauki wayoyinsa sa'annan ya baro sashen nasa.


Hadiman dake sassansa sunso masa tattaki amma ya dakatar dasu,ya nuna musu bashi da buqata,don haka shi kadai ya dinga ratsa cikin gidan nasu da ya wadata da hasken fitilu tako ina saika rantse rana ce,yanayin iskar kadai ya dinga sanya zuciyarsa cikin yanayi na daban,yaci gaba da takawa a nutse zuwa sassan amminsa.


Daga nesa ya hangosu sun taho,sun jero da juna shi da ita,suna nufo sashen da yake shima,kanshi ya dauke kamar bai gansu ba,saidai kwarjininsa daya cika shi dashi tun daga nesa ya gaza wucewa shima,ya tako zuwa inda yake ya masa sallama yana miqa masa hannu.


Amsa mishi yayi ya bashi hannun shima ya soma gaidashi ya amsa yana duban walida,wadda baqinciki da takaici kamar ta mutu,ya jefa mata wani kallon gargadi sannan yajuya yaci gaba da takawa ya barsu a wajen.


Kitceh kitchen tayi da ranta,saiya saki murmushi
"No way idan ka ganshi dole ba

Please Login or Register in order to submit comment