Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuma zancan ci gaba da karatunka ya daidaita,muga wacce qasa yakuma kamata ka canza".


Idanu ya daga ya kalli ammin,har yanzu kenan lokacin da zai zauna a qasarsu cikin masarautarsu baiyi ba kenan,ya raya haka cikin ranshi
"To" ya amsa mata dashi,daga haka wani shirun ne yakuma biyowa baya har zuwa sanda ya kammala cin abincin shima ya shige dakin daya rage guda daya yayi wanka ya sake fita.


Washegari kusan dukansu babu wanda yazauna,duk yawo suka fita,sun zagaya garin na mexico sosai,hakan yasa fulani aisha bata samu sake zama da azeez ba,duk da cewa hankalinta yana kan maganarsu,saboda haka washegari da daddare ta nemi ganinsa.


Cikin dakinta ya taddata ita dasu afnan gaba daya,suna ware wasu kaya da suka siyo,ita kuma tana zaune daga gefan gado,sanye da wata doguwar riga wadda tasha ado daga wuya hannu har zuwa gaban hular dake hade da rigar,idanunta nakan yaran,saidai kallo daya zaka mata ga mai hankali ya fuskanci duniyar tunani tashiga.


Sallamarshi ta sanyasu dukka daga kai suka amsa,suka gaidashi,ya amsa yana nufar wani dan qaramin carfet dake shimfide gaban fulanin ta dora qafafuwanta akai
"Ku bamu waje" fulani tayi.magana dasu sumaira,sai duk suka ajjiye kayan hannunsu suka miqe suka fita zuwa falon gidan.


"Barka da warhaka ammi"
"Yauwa barka kadai" ta amsa mishi fuskarta babu walwala,tana sanya hannunta gefanta ta dauko takarda da biro,wanda da alama musamman ta tanadesu,miqa masa tayi yabisu da kallo,kana ya kalli ammin,sai kuma yasa hannu ya karba
"Rubuta mata sallamarta,don ina tunanin gobe ne zasu koma".


Baice komai ba saiya sadda kai saman takardar yasoma rubutu,sai kuma ya tsaya cak,don baisan me zai rubuta,baisan me ake rubutawa ba,idanun ammin duka suna kanshi,har zuwa sanda ya tsaya din,kai ya daga ya dubeta
"Ammi....bansan me zan rubuta ba,me ake rubutawa?" Fuskarta ta hade sosai kana tace
"Koma meye ka rubuta" shuru yasake ratsawa,haka kawai yakejin banbarakwai a lokacin da yake rubuta kalmomin NI ABDUL'AZEEZ ABDALLAH KAISA NA SAKI MATATA SAKI.....
Jim yayi yana qiyasta saki nawa,saki nawa nema?,maida bironshi yayi ya rubuta adadin da yake gani shine daidai,kana ya ninke takardar ya miqawa ammi,bata damu ta duba ba tunda tana da yaqinin ya aiwatar din ta amsa ta aje gefanta,kana ta dauki wuyarta takira ahmad shima ta nemi ganinsa,sannan ta dawo da hankalinta kan azeez
"Da qarfe nawa za'a fara gabatar da taron naku?,ina tunanin mai martaba zaizo,yakuma buqaci sanin yaushene ainihin lokacin,ban tunanin xaizo ya kawana ne,xaizo a ranar ya juya washegari wala'alla" Miqewa yayi yana amsawa
"Qarfe shida na yamma za'a fara" kai ta jinjina kana yasoma takawa
"Zanje ammi,wala'alla nasake dawowa,wala'alla kuma sai gobe"
"Allah ya nuns mana" ta amsa mishi,yana fita ta sauke ajiyar zuciya,tana jin wani nutsuwa da kwanciyar rai na ratsata,kullum ta Alla cikin fargaba take kan auren nan,kullum babu irin saqe saqen da zuciya batayi mata kan auren,sai gashi duk yadda ta zaci abun yazo mata a dai dai,kuma da sauqi fiye da yadda ta zata.

_uhmmm,nidai nace ba girin girin na tayi mai_😊.

********* ***** ********


Ita kadai ahmad yasamu zaune a falon,duk bilkisu da rakiya na backyard na gidan,kusan tun daxun,batasan me sukeyi ba acan,bata takura musu ba hakanan bata nemesu ba,don ta fuskanci dukkaninsu kowa alhinin rabuwa da dan uwanshi yake,ita dinma kawai dakiya take,amma abubuwa da yawa ne cunkushe a ranta,lamarin bilkisu ya tsaya mata a rai sosai fiye da yadda ta zata.


Lokacin daya miqa mata takardar tuni ta fahimci ta meye,haka ta dinga juyata bayan tafiyarsa,tanajin cikin jininta kamar saqon akanta yake,kamar itace bilkisu,tana jin wani nauyi da jinjina yadda zata miqa wannan mummunan saqo ga bilkisu,inama ace fulani nata dora mata wannan nauyin ba,inama ace ita da kanta ko azeez da kansa ta bari ya bata saqon,da hakan ya fiye mata sauqi,kuma an sauqaqa mata wani nauyin,tanajin fuskantar bilkisu da wannan saqon kamar wani zunubi ne a rayuwa.


Tana tsaka da juya takardar aka turo qofar kitchen wanda yayi linking da backyard din,rakiya ce a gaba bilkisu na biye da ita,kallo daya zakawa fuskokinsu ka gane sam babu walwala,sabo turken wawa,kuma tasan dole suji babu dadi,don iya zaman da sukayi na shekarar sabo da shaquwa mai girma ya shiga tsakaninsu,sai ta aje takardar gefanta tana binsu da kallo.


Haka ta kwana da takardar har wayewar washegari da zasu bar qasar,sam ta kasa miqawa bilkisun,hakanan batayi wani isashen bacci ba a ranar,sanin cewa tafiyar safe zasuyi,hakan ya sanya tun bayan sallar asuba bata koma ba,ta sanya rakiya tasoma.shiri,sannan ta nufi dakin bilkisu da kanta da niyyar tadata,saidai ta sameta saman abun sallah,hannayenta a sama da alama kukanta take kaiwa ubangiji,don haka saita koma da baya tana ja mata qofar dakin yadda ta ganta,zuciyarta na karyewa itama,tanajin kamar ta saki kuka.


Sosai mama sodangin ta dinga sanyawa kanta dakiya da jarumta,hakanan ta hana rakiya shiga wajen bilkisun,don kada ta haifar mata da karyar zuciya da gazawa,ta tsareta da aiki a daki,ita kuma tashiga kitchen tana hada musu breakfas na qarshe,wanda bata da tabbacin cikin su ukun akwai wanda zai iya ci.


Tana tsaka da aikin rakiya ta kawo mata wayarta,takuma shaida mata fulani ce ke kira,cikin girmamawa ta amsa wayar,takuma gaidata,daga can bangarenta tadora da bayani
"Ina fata saqona ya iske ku ta hannun ahmad?"
"Eh Allah ya taimakeki"
"Da kyau.....qarfe sha biyu jirginku zai tashi,zan aiko driver ya daukeku yakaiku airphort,daga can idan kun sauka akwai motoci biyu....daya zata dauki yarinyar ta sadata da iyayenta,daya kuma zata maidaku gida,banason asamu wata matsala,ki tabbatar komai ya tafi yadda na gaya miki" wani nauyi da rashin dadi taji yana ratsa zuciyarta,da gaske kenan rabuwar zasuyi?,rabuwar da har ba'aso susan gida ko matsugunnin bilkisun?,bata da yadda zatayi,don ita din ba kowa bace,a qarqashin iko da mulkinta take,dolenta ta amsa da to,kuma ta tabbatar mata za'ayi dukkan yadda tace.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 35
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070

________________________________



Sosai ta ware idanunta da sukayi nauyi tana kallon qasar datayi shekara guda cif ba tare data rayu a ciki ba,ta cikin motar take bin ko ina da kallo,motar da take ciki ita qwal daya,daga ita sai wannan matar da taji an kira da ladingo,tun sanda suka sauko daga jirgi ba zata iya cewa ga inda su mama sodangi da rakiya sukayi ba,ta lura da haka,amma batace komai ba,hakanan bata buda baki da niyyar tambaya ba,wataqila yana cikin tsarinsu,wataqila dukka cikin irin nasu adalcin kenan.


Kamar wadda ta warke daga makanta haka ta dinga bin qofar gidan nasu da kallo,gidan da shigarta daya kwanakinta biyu tal a ciki,gidan da take da tabbacin kowanne irin daukan hankali xaiyi an samar dashi ne bisa cinikin mutuncinta da akayi
"Mun iso" muryar driver dake gaban motar ta ratsa dodon kunnenta,ba tare data waiwaya ta dubi kowa cikinsu,ko tabi takan kayanta dake cikin motar ba ta,ta sanya hannunta ta bude motar ta xura qafafunta tafito.


Duk da cewa dare ne,duk da cewa bata gama sanin kan gidan nasu ba,amma hakan bai hanata gane qofar shiga gidan ba,ta tura ta cikin qarfin hali ta bude ta kutsa kanta ciki.


Bata manta hanyar falon nasu ba don haka taci gaba da kutsa kai,bata dakata ba sai data isa qofar shiga falon,sai a sannan taji duk wani rauni nata ya dawo,sai a sannan fargabar yadda zata tadda 'yan uwanta ya fado mata,sai a sannan fargaba da tsoron irin rayuwar da zata gudanar ta dawo mata,ta sanya hannunta kamar wadda zata kama maciji ko qadangare ta yaye labulen nasu.


Hannatu tasoma hangowa zaune cikin falon qasan tiles din dake malale a falon,gefanta umaima ce da amina,hajara na kwance saman cinyar hannatun,da alamu kallo suke,don basu lura da labulen da aka daga ba.


Daga gefe saman kujera kuma wata matace zaune,itama.kallon take,a qalla zata doshi shekara talatin da takwas,qafarta daya saman daya,lokaci lokaci tana latsa wayar dake riqe a hannunta.


Wasu hawaye taji masu dumi sun ciko mata idanu,ko yaya suka rayu tsahon lokacin?,ko yaya sukaji lokacin da babu ita?,ko yaya rayuwa ta kasance musu?.


"Ta ina ake shiga?" Taji an fada daga bayanta,data waiwaya sai taga ladingo ce janye da akwatunanta,maida idanunta tayi cikin falon,ta qara taku ta saka qafafunta a ciki,bakinta dauke da sallama wadda take fitowa da qyar.


Dukkaninsu kamar an jona musu schoking suka daga kansu kusan lokaci guda,hakanan miqewarsu cikin tsananin mamaki wanda lokaci qanqani ya juye zuwa zallar farinciki,kana suka fara rige rigen isowa gareta,duqawa tayi a gabansu ta hadesu gaba daya zuwa jikinta,suka saki kuka kusan lokaci daya.


"Meye haka lafiya?" Matar dake zaune saman kujerar ta miqe tana tambaya gami da binsu da kallo,fuskarta akwai alamun rashin sanin wacece bilkisun,babu wanda ya iya tanka mata a cikinsu saboda kukan da sukeyi,ladingo ce ga dubeta ta soma gaidata,ta amsa tana son jin qarin bayani,kafin suce komai umma katti ta shigo falon
"Ke hannatu,kukan me kukeyi haka?,kuda waye kuma?" Cak ta tsaya ganin bilkisu duqe a gabansu,ta waro ido tana cewa
"Mai gado?,saukar yaushe?,yaushe kika zo?" Kai kawai ta daga ta kalli umma kattin,sai taga ta sauya sosai,ba kamar lokacin data barsu ba,maganar ladingo ce tayi kutse cikin tambayoyin da take jerowa bilkisun
"Ko xamu samu damar ganin mai gidan?" Tace da umma katti,don ta fuskanci kamar ita tafi wayewa da gidan akan wadda ta taras a falon.


Duban ladingo tayi ta gyada kai
"Eh bari ayi masa magana" daga haka ta juya zuwa wata qofa,tana tafe tana waiwayowa tana sake duban bilkisun harta shige.


A falonsa ta sameshi yana zaune yana zuba lomar tuwon shinkafar da ladi tayi da take girkinta ne umma kattin tashiga,har ladin ta daga kai xatayi masifa sai kuma saqon datazo dashi ya sanyata yin shuru
"Kazo ga maigado ta dawo" hakanan yaji wani faduwar gaba ta saukar masa,taste din abincin ya canza masa
"Na shiga uku,tofa" ya furta a sarari kuma a hankali,itadai umma kattin gaba tayi takoma zuwa falon don ta kashe qwarqwatar idanunta,taga meye zai faru,cikin yatsina fuska ladi tace
"Wai dama da gaske shekara dayar zatayi su dawo da ita?" Waiwayawa yayi.ya dubeta ba tare daya gane ma'anar tambayar tata ba,sannan ya miqe kawai yana goge hannunsa ya dauki hularsa dake gefe yadurfafi falon.


Yana shiga sautin kukansu yasoma sauka a kunnensa,saiya hada rai ya tsaya a kansu yana dubansu
"Wanne irin shashashanci ne wannan?,meye haka ke me gado?,ba zaku godewa Allah ba daya hada fuskokinku saiku xauna kuna kukan banxa dana wofi?" Janye jikinsu suka fara suna qoqarin tsaida kukan nasu,saidai ita bilkisun nata hawayen sunqi daina zuba.


Cikin girmamawa ladingo ta gaidashi sannan tasoma magana
"An umarceni dana danaganata da mahaifinta,kamar yadda akayi yarjejeniya bayan shekaru guda,to lokaci yayi,saboda haka gata nan kamar yadda fulani ta umarceni,shaidarta tana hannunta,dukkan abinda suka mallaka mata gasunan sun zama nata,tun daga lefe dukiyar aure dama komai da komai,hakanan sun bata dama,daga nan zuwa shekara guda duk abinda take da buqata a matsayin sallamarta ta qarshe ta fadi dukka adadin za'a bata....saidai fulani tace na tunasar daku yankewar alaqa ta har abada....." Wani abu ya soki zuciyar bilkisun da har ta gaza daurewa ta dubi ladingo,duban da yasa bata iya qarashe bayaninta ba,har abada kuma komai lalacewa ubanta ubanta ne,wato xallar rashin adalci,wulaqanci da kuma qarfa qarfan har yakai matakin da za'a dinga aikama mahaifinta gargadi ta hanyar 'yar aike kuma baiwa?,duk da cewa shiya siyama kansa koma meye,amma abun yasoma yiwa kunnuwanta muni.


Tsam ta miqe tana riqe da hannun aminatu da umaima,qasa qasa tace
"Kaini dakinku" da saurinsu sukayi gaba tana biye dasu,har zuwa dakin data zauna wancan karon lokacin da ake yinin bikinta,shine babu abinda ya sauya a ciki,saidai atsaftace yake hakanan komai yana shirye bisa tsari da doka,tasan za'a rina,dama bata taba tsammatar qazanta daga wajensu ba,saboda ta yadda da irin hoton data yi musu ma zallar tsafta da nutsuwa,saita qarasa zubewa anan tana sakin wani sabon kukan suna tayata,don suma bai ishesu ba,hannatu ce kawai bata biyi bayansu ba,wanda bata lura ba,har sai zuwa lokacin da zuciyarta ta gaya mata kukan ya isa haka,don bashi da wanu magani,face sake sanya qannan nata da zaiyi suma cikin wata damuwar,dole ta yiwa kanta waigi,ta goge nata hawayen ta lallashesu,kana ta shiga bandakinsu ta daura alwala ko zataji sanyi cikin zuciyarta.


Tana fitowa daga bandakin hannatun na shigowa janye da akwatunanta,saita dauke kanta don ko ganin akwatunan su kansu batason yi takoma kusa da amintu ta zauna tana kallon yarinyar tana dan murmushi duk cikin qarfin hali,tadan qara girma da wayo sabanin sanda ta tafi.


Hannatu ce ta qaraso ta dora mata wani abu dake nannade saman cinyarta tare da qaramar jakarta,saita kalli abun da alamun tambaya
"Kudinki ne da suka baki daga can,matar da kuka shigo tare ta baiwa baba,yace nakine bazai karba ba,baba ladi nata qoqarin sanyashi ya karba har tana yunqurin amsa nina karbo....karkiqi amsa don Allah yaaya,haqqinki ne,nakine bana wani ba,wanda akaci a baya ya isa,Allah ya amfana,idan ma kikace ba zaki karba ba babu abinda zai sauya,su zasu amsa su kuma murqushesu suci gaba da rayuwarsu ba tare da komai ya faru ba" idanunta taf da qwallar data samu ta tsayar take duban hannatun,tun daga yanayin jiki da kalamanta sun nuna hannatun bata da bace,hankali ya soma gameta,ba shakka ta sauya qwarai,ko nauyin daya hau wuyanta bayan tata tafiyar ne yasa hankalin yayi hanzarin zuwa mata haka lokaci guda?duk da dama tazarar shekara biyu rak ta bata,roqon datayi mata da qoqarin amso saqon da tayi tun daga falon,idan tace ba zata karba ba kamar ta watsa mata qasa a ido ne,don haka cikin hikima tace da ita
"Ganinsu ne banason yi hannatu" da sauri ta daukesu daga kan cinyarta
"Bazan takura miki ba yaaya,amma zanta ajjiye miki su har sanda kike da buqatarsu" ta qarashe maganar tana miqewa zuwa cupboard dinsu ta bude can sama ma'ajiyar kayanta ta cusa su sosai.


sai a sannan ta soma duban dakin loko da saqo,karon farko hauwa'u ta fado mata
"Ina kulu ta,ita kadai ce ban gani ba?" Ta ai qarshen tambayar tana maida idanunta ga hannatu,sai taga yanayin fuskarta ya sauya sanda take dawowa mazauninta data tashi,jin bata amsa mata ba saita sake duban sauran,suma dai kamar hannatun kowa fuskarsa ta nuna zallar damuwa,gabanta yayi mummunar faduwa,zuciyarta ta qiyasta mata wani mummunan abun ya samu hauwa'un suka boye basu gaya mata ba,cikin rawar murya tace da hannatu
"Hannatu,meya sameta baku gayamin ba?" Kai ta girgiza tana duban bilkisu
"Yan uwan mamanta sunxo sun tafi da ita"
"Ya Allahu" ta fada tana dafe kanta,wataqila rabuwarsu da hauwa'u kenan har abada taxo?,yan uwan mamanta?,yan uwan maman nata da sai afi shekara biyar ba'asan inda suke ba?
"Yaaya,hauwau na kuka tana cewa ba zata bisu ba sai yaaya maigado ta dawo,sai kin dawo kin sata a makaranta yadda kika ce,saikin dawo ta ganki amma haka suka dauketa,sunyi dauki ba dadi da baba,amma suka nuna mishi halinsu na fulani,saboda da zafinsu da shirinsu sukazo,tana kuka muna kuka haka suka jata suka tafi,kiran sunanki kawai take,munfi sati bama iya cin abinci,munfi sati muna mafarkinta,daga qarshe dole muka haqura saboda babu yadda zamuyi,amma kullum sai munyi zancanta,har yau muna kewarta,ko da kika ganmu xaune a falo ma zancanta muka gamayi kenan,sai gaki kin shigo".


Wani sabon tashin hankalin taji ya rufto mata,ji take kamar jininta ya hau,hauwa'unta,yarinyar da duk cikin qannenta taficin buri akan tazo ta ganta,saboda tasan tafi kowa qulafucinta,kukan dai da bataso tayi shiya sake dawo mata,don bata da wata hanya ta huce takaicinta da baqinciki idan ba kukan ba.

***** ***** ****** *****



Tun a mexico ammi fulani aisha ta shirya masa walima ta musamman,wanda tasamu halartar familynshi na kusa sosai,musamman dangin mamamshi daga mali,har safwa ma wannan karon sai data zo,da tarin kyaututtukanta na murnar tayashi karatunsa,wanda ita saura shekara guda ta rage mata ta kammala nata karatun,walima me kyau da qayatarwa akayi,kusan kwanakin duka cikin sabga yake,sai washegarin randa aka kammala walimar sannan yasamu huta,ya kulle kanshi a daki ya kashe dukka wayoyinshi.


Saidai tun baccin baiyi nisa ba yasoma mafarkai,hakan ya tilasta masa tashi,yayi addu'a ya gyara kwanciyarsa,saidai baccin ya gaza sake samuwa kwata kwata,haka dole yanaji yana gani yaci gaba da juyo saman gadon,daga qarshe ma wanka yayi yasake ficewa,duk da hutun da yake da buqata.

****** ***** ***** *****


Tana zaune daga gefan gadon hauwa'u wanda a yanzu ya zama nata tun bayan dawowarta gidan,saboda taqi nata dakin kamar dai wancan karon,sanye take da rigar bacci doguwa mai dan kauri,sai wani qaramin dan kwali data rufe kanta dashi.


Misalin bakwai da rabi ne na safe,dukka yaran na zaune a gabanta sanye da unifoarm suna karyawa,wanda ruwan tea ne da bread,zata iya cewa a yadda tasan rayuwar gidansu a da,yaran sun samu 'yanci da sauyi kaso sittin cikin dari maimakon daa,a yanzu akwai abinci a gidan dai dai gwargwado,safe rana da dare,babu zaman yunwa,hakanan baban nasu ya qoqarta sakasu a makarantar boko mai sauqin kudi,dama already ta barsu suna zuwa islamiyya,kuma basu fasa zuwa ba har kawo yau,basa yawo cikin tsumma kamar yadda sukeyi a baya,saidai kuma kusan babu mai kulawa da rayuwarsu,ba'a tsangwamesu ba tsangwama mai yawa kamar baya ba,hakanan babu mai tattalinsu kamar yadda suke dai a baya,umma katti ta kama yaranta sune a gabanta yadda dai rayuwar take a baya,mama ladi da amaryar da bilkisun tazo ta taras ya rangado wadda taji suna kira da anty sukam ta mijinsu suke ko ince ta kansu,domin a zahiri kowacce na nuna mishi tattali ne,yayin da kuma a badini kowaccen kanta da rayuwarta take qoqarin ginawa,suna hangen dan abun hannun malam bilyan,sannan kuma suna hasashe da lissafin basu haihu dashi ba,basu da kowa dashi,to ba shakka idan ta tashi barewa dasu zata bare.


Tana zaune tana dubansu suna 'yan hayaniyarsu har suka gama,hannatu ta kada kansu don wucewa makaranta,ta laluba jakarta don basu dan abun kashewa saidai babu komai a ciki,saita buraci inama ace tana da wani abu da zata basun dazai sake yawan farincikinsu,hakanan ta musu fatan dawowa lafiya suka amsa cikin cikin walwala suka fice,don wannan rayuwar da suke ciki gani suke sun samu dukkan komai,tunda basu saba irinta ba,a baya sun rayu babi ci sha suttura ko muhalli mai kyau daga mahaifinsu,a yanzu kuwa dukka sun samu,don haka a nasu ganin basu rasa komai ba.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 34

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070



Ajjiye wayar tayi tanajin wani daci da zallar rashin adalci cikin lamarin gaba daya,a iya sanin data yiwa fulani aishan macace mai tausayi jin qai da kuma kyan hali,batasan meya sauyata haka lokaci daya ba,tayi mamakin yadda tabari BURI gami da ALWASHIN watsa aniyar maqiya yakeson sauya halayya da dabi'arta,ta dauki buri mai tsaho da girma akan azeez fiye da yadda aka santa,duk da cewa dama can mutum ce mai son 'ya'ya,amma duk da haka tana da kyakkyawar halayya da dabi'a wadda ta siya mata soyayya mai girma a zukatan al'umma,sai gashi yanzun tana wasu abubuwa da suke baiwa sodangi mamaki,halayyar da sam tasan ba tata bace,rashin adalci,rashin tausayi da kuma nuna halin ko in kula akan kowa face diyoyin cikinta,indai hakane kuwa maqiya sun cucuta,dafin magauta ya ratsata,ya mata kuma tasiri da har yafidda kyakkyawar halayya daga cikin jininta ya sauya mata wata.


Kamar yadda ta zata din kuwa babu wanda ya kalla abincin ma a cikinsu har ita kanta,kusan kowa zuciyarsa babu dadi,duk da cewa wani abu yau ya bata mamaki,ta gaza karantar yanayin da zuciyar bilkisu ke ciki a yau,farinciki ko akasin haka?,wani irin emotion take gani kwance saman fuskarta data gaza tantance a wanne bigire zata ajjiyeshi?.


Kamar kazar sa qwai ya fashewa a ciki take shiryawa,ita kanta batasan a wanne matsayi ruhi da zuciyarta suke ciki ba,abinda ta sani kawai shine,ta tashi da qwarin gwiwa bayan ta raba dare tana tunani tare da qoqarin samarwa kanta mafita,ta sanyawa kanta wani yaqini da jarumtar amsar duk wani nau'in rayuwa da zata tunkareta.


Tana shiryawa idanuwanta na sauka sashe bisa sashe na dakin,tana tuna dukkan yadda rayuwarta ta wakana cikin gidan tsahon shekara guda,ta runtse idonta lokacin da tunaninta yakawo ranar daya amshi mutuncinta,take dukkan wani qwarin gwiwa data tattarowa kanta ta tarwatse,saita sulale a wajen saman gwiwoyinta tana rufe fuskarta da tafukan hannunta,tana jin wani irin abu yana tasowa daga qirjinta can cikin zuciyarta,ambaton sunan Allah tasoma yi,wanda hakan ya taimaka mata ta daidaita tunaninta,saita miqe a hankali,tazauna gefan gadon,ta nutsu nadan wani lokaci sannan taci gaba da shirinta.


Sanda take sanya kaya take kuma agogo wanda yake nuna mata mintuna ashirin kacal suka rage su fita daga gidan zuwa filin sauka da tashin jiragen sama don konawarta tushenta,qarar qararrawa taji da alama akwai mai buqatar shigowa gidan,dukka saita tattara hankalinta,har zuwa sanda taji.mama sodangi ta bude qofar,muryar wata mata taji wadda bata santa ba,saidai tana iya jiyo kiran sunanta da mama sodangi tayi da ladingo,daga haka bata kuma jin komai ba saita qara hanzari ta kammala shirinta gaba daya.


Sake duban agogo tayi,minti goma ya rage musu,tana dauke idanunta ana turo qofar dakin,mama sodangi ce,idanunta kan bilkisu,cikin wani irin yanayi daya dasawa bilkisu fargaba da faduwar gaba,wadda ta sanya ta gaza ci gaba da kallon maman,ta sadda kanta qasa,har zuwa sanda ta qaraso inda bilkisun ke tsaye.


Kamar wadda batasan meya shigo da ita dakin ba ta tsaya tana duban bilkisu,a hankali ta lalubo hannunta ta sanya takardar,hakan ya sanya ta daga kai tana dubanta,kai mama sodangi tasoma girgixa mata,idan ta lura dakyau ma kamar qwalla ce cike a idanunta,dukkansu babu wanda ya iya cewa da dan uwanshi komai aka sake shigowa dakin,sallamar ladingo ta karade dakin,maimakon mama sodangin ta amsa,sai kawai tasaki hannun bilkisun ta juya da sauri tafice daga dakin,ita kuma ta rakata da ido har ta bacewa ganinta,sai a lokacin ta ankara magana ladingo ke mata,ganin alamun bata ji ba yasanyata maimaitawa
"Idan babu damuwa zan soma debe kayanki na fita dasu,driver yazo za'a saka cikin mota" bata iya cewa da ita komai ba,don ji take kamar bakinta bai taba magana ba bare tasan ta yaya zata amsa mata,qafafunta tamkar lawashi saboda rashin qwari,tana jinta kamar mai tafiya a wata duniya ta daban tasoma nufar qofa don barin dakin ba tare data waiwaya tasake duban dakin ba,ba tare data tsaya ta duba ko akwai abinda ya kamata ta dauka ba,babu komai cikin hannunta sai takardar datake da tabbacin ko ba'a gaya mata ta meye ba tasan ta meye,har takai falo sannan taji kamar qafafun nata ba zasu iya qarasawa da ita waje ba,don haka ta lalubi kujera tazauna donta ragewa kanta nauyin da taji dukka gabban jikinta sun mata.


Kamar a inuwa

Please Login or Register in order to submit comment