Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Cikin madaukakin farinciki take takowa zuwa inda yake tsaye a filin sauka da tashin jiragen sama dake mexico,jinta take cikin wata duniya ta musamman,yau da kanta ta kawowa azeez din ziyara,abinda ta dade tana so tana kuma sanya rai.


Murmushine sosai kan fuskarta tana kallonshi,yayin da shima ita yake kallo,fuskarsa ta washe alamun akwai fara'a sosai shima bisa tashi fuskar,dab da zata qaraso inda yake tasoma sassarfa saboda yadda fa qagu ta ganshi,ji take kamar ta shekara bata ganshi din ba,ta taho da sauri da niyyar fadawa jikinsa,da hanzari yakauce yana mata murmushi kana ya kada dan yatsanshi manuni
"Nooo...." Saiya mata nuni da mutanen dake zirga zirga a wajen da idanunsa,kafadunta ta daga tana tabe baki gami da bata rai,cikin idn't care manner,baisan me yasa take daukan wasu abubuwan ba'a bakin komai ba,tsabar wayewa ce ko boko ne ya mata yawa oho bai sani ba,ko kuma sangarta ce da gata?,ita ba rayuwar waje tayi mai yawa ba bare yace abunne yashigeta,sam tana ganin don yayi hugging dinta ba wani komai bane,hakanan bata dauki kisses a tsakaninsu a bakin komai ba inda yana biye mata,tana ganin ai suna son juna kuma auren juna zasuyi,so ba wani abu bane don suna body contact,tunda ba maj gaba daya suke ba sun kame kansu,saidai sam shi bai yarda da wannan tsarin ba,tunda yasan kanshi,yasan matsalarsa yasan kuma yaya jikinsa yake,ko baya ga hakama shi abun baya burgeshi,yafison komai yazo a lokacin daya kamata yakuma dace,sai yafi bada armashi da ma'ana.


Har yabude mata motar tashiga tana zumburo baki,yasan don ya hanata ta rungumeshine yasa take wannan kumbure kumburen,saiya basar kamar bai lura ba,yasoma tunanin inda zai ajeta,daga bisani ya yanke ya tambayeta
"Ina madam takeso ayi mata masauki?" Cikin muryar dake nuna fushi tace
"Inda yallabai yake zaune mana" ya gane sarai inda take nufi,gidan da suke zaune shi dasu kamal da mutspha harma da jabir,bazai soma wannan gangancin ba,yaje yakaita cikinsu ya aje,ita kanta ziyarar tata banda tare da antynta sukazo qasar ta sauka a wani gari ita kuma tace zata qaraso ta kwanan musu ko dayane da yace ya yafe,baison yafadiwa antyn haka taga kamar ya gwasale mata 'yar 'yaruwarta ne,duk dashi wannan ba damuwarsa bane koda zata ji haushin,amma ita safwan a karan kanta ta jima tana masa nacin xata zo takanas daga nijeria zuwa mexico,shike dakatar da ita,sannan uwa uba yasan baya bata attention dinsa kan soyayyarsu yadda takeso saboda dalilansa da suka ta'allaqa da yanayinsa,dakuma yadda ita a karan kanta take mu'amalantarsa yana masa tsauri da yawa,dakuma jefashi cikin yanayi.


"Zabi wani wajen dai" saita dage kafada
"To daya gidan" kafadanshi yadaga,yana ganin can din babu matsala sai yace
"Alright". Ko kafin su isa gidan tuni ta warware daga fushin da takeyi dashi,don dama bata iya wani dogon fushi dashi.


Tana zaune gefan gadonta tana warware kalbar dake kanta,wadda rakiya tayi mata bayan tsefaffaen kan ya dameta,sallama cikin wata lallausar murya ta ratsa falon kana ta isketa har dakinta,sai tabar duk abinda take tana saurare ko zata sake jin wani abun bayan sallamar,bata sake jin komai ba face muryar rakiya cikin tsananin girmamawa tana fadin
"Barka da zuwa Allah ya taimakeka....barka da warhaka yarima"
"Yarima?" Ta tambayi kanta gabanta na wani mummunan faduwa da batasan dalili ba,indai zata san cewa yana gidan,indai kuma za'a ambaceshi ko yaya sai taji wannan fargabar da faduwar gaban,tamkar wadda akace gashinan shigowa saita rarumi dankwalinta tana rufe tsefaffen kanta,kana ta rarraba idanu cikin dakin,gabanta naci gaba da faduwa,zuciyarta na mata saqe saqe gamida raya mata abubuwa masu yawa.


"Tana madafa....bari nayi kiranta" tasake jiyo muryar ruqayya tana fada cikin sauri,duk da bataji me yace daga can sashen ba,amma tabbas mama sodangi ya buqaci gani,hakanan tasamu kanta da tashi cikin sanda ta isa bakin qofar dakin nata,ta sanya hannu da niyyar murza muqulli,wata zuciyar tace zai iya yiwuwa ajiyo qarar taba qofa,tunda cikin falon babu kowa
"Wow swerry,gidan nan yayimun fa" muryar safwa ta katse shurun da falon yadauka bayan wucewar rakiya
"Am so glad to hear this" ta sake jiyo lallausan muryar tana fada a taqaice,ci gaba tayi da tsaiwa hakanan ba tare da tasan dalili ba harta jiyo muryar mama sodangi na fitowa daga kitchen.


"Barka da dawowa" ta fada itama akwai alamu na ban girma a muryarsa,manyan idanunshi ya lumshe yana gyada kai kawai,yanayin yadda yake maganarshi idan baka sanshi ba zaka tsammaci yanga ce yakeyi,saidai hakanan yanayin halittarsa take
"Yauwa sodangi....ga baquwa nan,sunanta safwa,zatayi kwana biyu" cikin girmamawa tace
"Fulani ta shaidamin.....Allah ya baki nasara barka da zuwa" dan murmushi safwa tasaki dadi yana ratsata,tanason harkar da za'a dinga bata girmanta ana kuma kambamata,tunda tasan takai ayimata hakan,saita gyada kai kawai tana cewa
"Barka kadai sodangi,mun sameku lafiya?"
"Lafiya qalau gimbiya safwa" sunan yasake faranta mata rai,hakan yasa lokaci daya taji mama sodangi tayi mata a ranta.


Miqewa yayi don dama a hannun kujerar yake a zaune,sai safwan ta dubeshi da shagwabar nan tata
"Ina zuwa kuma?" Cikin sanyin muryar kamar yadda yasaba,kai bakace ya iya hargowa ba,shi yasa duk wanda yaganshi a sa'ilin da yake fada take daban mamaki,bazakace shi bane
"Zan qarasa schedules dina nayau" kafada ta maqe tana dubanshi
"Sam ba yarda ba,kamata yayi kayi cancel duk wani schedules naka har sai na koma,tunda kasani saboda kai nazo ai" tuni mama sodangi tajuya don komawa kitchen,don abun yadan mata nauyi,tunda bata taba ganin hakan ba,hasalima duk fadar safwa da ake yau tasoma ganinta.


Girarshi yadage sannan yace
"Really?"kawai saita sake mishi kukan shagwaba,kusan bataji me yace mata ba,amma taji takun hawanshi sama,kasa barin wajen tayi har zuwa sanda aka gyarawa safwa dakin da zata zauna,daganan bata sake jin komai ba,saita saki qofar takoma bakin gado tana sakin ajiyar zuciya a jejjere.


Dai dai lokacin karatunsu harda wasu mintuna akai taji anyi knocking qofar dakin,saita sake yin wuri wuri,duk da kusan awa biyu cif bata sake jin wannan muryar da take da yaqinin tashi bace,sai muryoyinsu rakiya da mama sodangi wani lokaci dana baquwarsu wadda da alama tacika tambaya dakuma surutu.


Shahadar quda kawai tayi tabada daman shigowa,rakiya ce a shirye tsaf riqe da litattafansu a hannunta,fuskarta qunshe da murmushi take duban bilkisu,zamansun tare dakuma shaquwarsu yasanya daga ita har rakiyan kowanne yake mance matsayin dan uwanshi a tsakaninsu,sukan kalli juna ne tamkar qawaye,sau tari mama sodangi ce kan jawa ma rakiya kunne kada ta mance matsayim bikisun,itakuma bilkisu sam hakan bai mata dadi,don ita bataga wani matsayi daban dake gareta ba,uwa uba ma ita tafi jin dadin mu'amalarsu a hakan dari bisa dari,rakiya a matsayin qawa kuma 'yaruwa,mama sodangi a matsayin uwa,hakan yafi gamsar da ita,tun suna takatsantsan da kiyayewa har suma suka saki,suka kuma dauketa a yadda takeso su dauketan
"Akramakillah.....hala yau bazamu samu darasi ko guda daya ba?" Wayarta da take browsing da ita ta sauke bayan ta kashe datar,baya ga kiran 'yan uwanta tana jin dadin wayar sosai,duk da cewa bata charting ko guda daya,amma ta zame mata wani dandali na daukar karatu,tasan ingantattun link na manyan malamai da take shiga tadauki karatu sannan tafito,ta qaru fiye da zatonta,takuma sake imani da cewa,ita waya yadda ka dauketa hakan take,kamar kwalba ce,asali a tsaftace take,idan kaso kazuba ruwa ko lemo,idan kaso kazuba giya,wannan kai ka gurbatata.


Cikin sanyin murya tace
"Rakiya bamu kadai bane bafa a gidan" murmushi ya subuce mata,tana mamakin yadda bilkisun take bala'in tsoron gamuwarta da yarima abdul'azeez,ko ita da take hidima cikin gidansu,take kuma qarqashin ikonsu tsoronta baikai wannan ba,abun nasu yana da matuqar daure kai,ance mata aure aka musu,amma dagashi har ita babu wanda yataba ganin wani?,batasan koshi ya taba ganinta ba(eh ya taba ganinta amma rakiyan bata sani ba),babu wanda ya taba hada inuwa da dan uwanshi,duk da batasan ainihin rayuwar aure gaba daya ba,amma ta tabbatar wannan ba shine aure ba.


"Dodon yafita tun dazu,babu kowa cikin gidan saimu" harararta tayi kadan kana tayi shuru kamar bata yarda ba,sai kuma ta sauke ajiyar zuciya
"Muje" ta furta tana saukowa daga saman gadon,tazura slippers dinta tana ware dankwalin kanta tayi rolling dashi tabi bayan rakiya suka fice tare.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 25
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*
*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070
____________________________
*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*

*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*

*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸ™ŽðŸ½â€â™€ï¸

*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaÉ—a ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯ðŸ½â€â™€ï¸ðŸ‘¯ðŸ½â€â™€ï¸

*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*
*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*

*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*

*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞ðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾



Lokacin daya dawo dare yayi,saidai bawani dare can ba,a sannan sha biyu ne harda rabi,da muqullanshi daya saba amfani yabude gidan yabude yashigo,falon tsit babu kowa kamar yadda yakan tarar kullum idan yadawo,kai tsaye ya haura zuwa sama inda dakinshi yake.


Alwala yasoma yi kamar yadda yasaba zama da alwala akai akai haka ammi takoya mishi tun ba yanzun ba,yakuma saba yatashi da dabi'ar,alqawarin daya yiwa safwa yana cikin ranshi,mutum ne shi mai.matuqar kiyaye alqawari dakuma qoqarin cikashi,don haka yaja laptop dinshi yakunna.


Kiran safwa yasoma yi,wadda tajima gaban system din nata tana tsammanin kiranshi,harta soma kumbura jin shuru har yanzun bai kira ba,saidai idan ta tuna yana da cika alqawari sai kuma fushin nata ya sassauta,don haka yana kira ta daga.


Tarwai ta bayyana cikin screen din nashi,ta cika screen din gaba daya,tana kwance rub da ciki saman gadonta,sanye da wata lafiyayyar baqar riga ta wani yadi wadda ta haska fara tas din fatarta,gashinta na reto a kafadarta guda,fuskarta fes da madaidaiciyar kwalliya,labbanta sunata qyallin lipstick ta hasken screen system din.


Murmushi ta sakar masa tana kashe masa idanu daya,saiya lumshe idon nashi yana jin tsigar jikinsa na tashi,uwa uba yanayin kwanciyar da tayi din batayi masa ba,saboda ana ganin wuyanta zuwa qirjinta sosai,duk da basu bayyana ba gaba dayansu amma kana iya hango tudunsu
"Tashi sosai ki zauna" ya fada qasa qasa yana lashe busassun labbansa,murmushi takuma sakar masa,taji dadi ta sanyashi a yanayi,tana son taga yasauya saboda ita,anata ganin wannan kawai shine xai nuna ma'aunin qaunar da yake mata,hakanan zai bayyana adadin yadda ya matsu su zama mallakin juna kamar yadda itama ta matsu,tunda tasan bazai taba buda baki ya gaya mata yadda take da buqatar ji ba
"Meya faru da kwanciyata kuma?"
"Ki gyara kawai ko nayi cutting up kiran" tasanshi sarai zai aikata,don haka ta miqe zumbur tazauna tana tura baki gaba,saiya saki wani qaramin murmushi wanda iyakacinsa labbansa.


Bata iya wani dogon fushi da shi,don haka ba bata lokaci tasauko suka soma hirarsu,anan yayi realising lallai safwa batasan da zancan plan da ammi tayi na,saboda kusan rabin hirar tasu tayau tana nuna mishi yadda take bala'in kishinsa,daga qarshe ma ita yabarwa fagen yaxuba mata idanu yana kallon yadda labbanta da sukasha man lebe suke motsi.


Cikin jikinsa yaji tabbas akwai matsala idan sukaci gaba da zama a haka,don haka ya yanke shawarar samun abun mai zafi da zai rage masa abinda yasoma ji

Yasake kallon agogon dake aiki qasan system din,dare ya riga da yayi,bai kyautu ya tashi sodangi ba yanzu,don haka ya sanya laptop din a sleep bayan ya nemi uzuri wajen safwa ya dantse kiran,yamiqe ya zura slippers dinshi yasauko qasan.


Dai dai lokacin da yunwa ta hanata sakat sakamakon qin fitowa da tayi taci abincin dare,har suka gama abinda suke suka tafi suka kwanta.


Don dole ta tashi da hanzari jin yadda hanjinta ke curewa waje daya,slippers dinta itama kawai ta zura tana tattare hannun rigar baccin jikinta,wadda take riga ce iya cinya mai dogon hannu da wandonta dogo na wani lallausan yadi ruwan hoda,kanta babu dankwali,sai gashinta jelarsa ke reto a bayanta yana kuma qyalli saboda mai da gyara da yasha,ta bude qofar dakin nata a hankali kamar wata barauniya,ta tsaya ta kasa kunne,sai data tabbatar bataji motsin komai ba sannan tasoma takawa a hankali zuwa kitchen din.


Cikin qaramin plate tazubo abincin kana ta dawo falo,tvn dake aikia falon wadda sun manta basu kashe ta ba taja hankalinta suna nuna wani shirin girke gike,saita tsaya gaban tvn da plate din a hannunta tana yafitar abincin kadan kadan tana ci,idanunta da dukka hankalinta yana kan tvn.


Taku biyu rak yayi ya hangi mutum gaban tv,abun sai yaso daure mishi kai gamida bashi mamaki,a hankali yake qarewa bayanta kallo,a jikinsa yakejin baquwa ce,don sam batayi yanayi ko zubin rakiya ba bare yace itace,duk da ba wani kallonta yake ba amma yasan ba ita bace
"Wow" bilkisu tadan fada cikin birgewa,saboda abinda cook din ta hada yayi matuqar burgeta yakuma bata sha'awa.


Sautin muryarta yasake tabbatar masa da zarginsa,saiya ci gaba da saukowa idanunshi a kanta.


Jin takun saukowa daga step ya sanya gabanta mummunar faduwa,ta soma zazzare idanu,babu abinda yazo ranta illa
"SHINE!" zuciyarta ta gaya mata da qarfi
"Wala'alla ma dakinki zashi" zuciyarta ta sake gaya mata,sakin kwanon hannun nata tayi da hanzari ba tare data shirya ba,a miliyan tayi dakinta kamar zata tashi sama batare datako waiwayo ba bare taga waye,wanda hakan ya baiwa sassan jikinta damar motsawa dakyau,bataci biriki ba sai data tabbatar ta isa dakin,kana ta sanya muqulli tarufe qofartata gam.


Mamaki ne yasanyashi tsaiwa yana kallonta gamida mamakin wacece wannan?,ganin baida amsa saiya tabe baki gamida dage kafadunsa yawuce zuwa kitchen donyin abinda yafito dashi.


Koda yakoma dimma hirar kadan suka qara ya bata haquri,ya qarasa shanye coffe dinsa kana yayi shirin kwanciya yakwanta,kafin bacci yadaukeshi yatuna abinda yafaru mintunan da suka wuce,saiya tabe baki gamida jan qaramin tsaki,idan bamai matsalar qwaqwalwa ba wazaiyi haka?,kawai daga jin taku saika yar da kwanon hannunka kahau gudu,sake gyara kwanciyarsa yayi yana jan tsaki gamida rufe idanunsa,ya aje komai gefe yanason bacci ya daukeshi.


****** ****** ****** ****


Kimanin qarfe sha daya ne na safiyar ranar,su ukune zaune a falon nata saman dining suna karyawa,fulani aisha da yaranta uswa da sumaira.


Diyar uswa ce akan cinyarta tana bata farfesun nama a hankali yayin da suke taba hira wadda ta shafesu,daidai lokacin jakadiya ta qaraso,ta zube tana shaida mata saqon son ganinta da saudat(qanwar maimartaba mahaifiyar kamal) keson yi.


Kai ta gyada kana ta bada izinin ganinta,ta dauke idanunta ta maida kan yaran nata,sai ta yiwa sumaira inkiya data dauki sahla dake saman cinyarta,ita kuma ta miqe tana goge hannunta da tissue.


Cikin nutsuwa qasaita take saukowa daga wajen dining din zuwa ainihin falon,tana sane da zuwan saudat din gidan kimanin kwanaki hudu,amma bata nemeta ba kamar yadda ta nemi sauran abokan zamanta.


Tuntuni tasoma shaqar wani abu dangane kan saudatun,hakanan takejin sam takunta bai mata ba,tun kafin yau dama ba wani alaqa mai kyau bace can can tsakaninta da saudatun tunda aka aurota,hakanan jininsu bai hadu ba,hakan kuma baya rasa nasaba da aurotan da yayi a wata qasa,wanda a lokacin saudat din sam bataso hakan ba,akwai qawarta dataso hadashi da ita kamar kamar me,taji ba dadi sosai,don a sannan ita dayace ta rage mishi qanwa kuma abokiyar shawara,dama duka duka su ukune Allah ya baiwa sarki mu'az,Allah ya yiwa babbar yayarsun rasuwa,tabar yaro daya wanda yake hannun saudat din tana riqo.


Cikin qasaita shigo shan qamshi da kallon komai É—ai É—ai tashigo falon,don dukka cikin gidan babu sassan da yakai na fulani aisha kyau da tsaruwa da kayan ado na alfarma dake sake nusashe dakai cewa nan fa akeyin sarautar,don ita gada tayi daga fannin mahaifi dakuma miji,sarauta saidai ta nunawa wasu
"Bismillah" ammi tafada tana nuna mata daya daga cikin kujerun cikin nata salon qasaitar da isa,saida saudatun tazauna kana itama tayiwa kanta mazauni kan kujera maicin mutum biyu,kana ta dora qafarta daya saman daya idanunta kan saudat
"Matar dan uwana" ta fada kamar yadda ta saba kiranta dashi
"Maman kamal....yaushe a gari?" Ta fada a dake,saita dan yatsina fuska
"A qalla yau kwanana hudu cikin gidan nan,amma da mamaki idan kikace bakisan da zuwa na ba" hannayenta ta watsa kafin ta hadesu waje guda
"Ba abun mamaki bane,saboda kowanne mutum akwai irinsa,ba kasafai na fiya damuwa ko bibiyar al'amuran dake wakana cikin gida ba,indai lamarin bawai yajibanceni bane" wani duba ta mata tanason fahimtar meta fada din,magana ce cikin magana ko kuma magana tayi kanta tsaye ba tare da kowanne nufi ba?,saita gyada kai sa'an nan tace
"Haka ne" daidai lokacin da sumaira ke saukowa rungume da sahla,kana ta qaraso cikin girmamawa,fuskarta a sake kasancewarta maison jama'a fiye da kowa cikin 'ya'yanta,tazauna saman daya daga cikin kujerar tana gaida saudatu da suke kira da mom,gami da tambayarta 'yan uwanta yaran saudatun wato safna da safina
"Qalau" ta amsa a taqaice,daga bisani uswa ta sauko itama ta gaidata,saidai ita daga gaisuwar bata qara komai akai ba saima qoqarin miqewa da take don barin wajen,kasancewarta gwanar miskilanci ce itama kamar dan uwan nata abdul'azeez,dukka fulani aisha na ankare da yadda take amsa gaisuwar tasu,wanda tasha bamban da yadda take treating su walida qwarai
"Ke zonan,don uwarki me yasa ne baki da hali,kodon kinga mun aurar dake ne yasa kike ganin kanmu daya" ta fada cikin zafi zafi,kamar da biyu take maganar.


Uswa dake tafiya ta waiwayo kana tace
"Wa wai?,ni?" Wanda ita harga Allah bada wani abu tayi maganar ba,kusan nature dinta kenan
"Ban sani ba" ta amsa mata a gadarance.


Batace komai ba ta dawo din tasamu waje taxauna,saita soma fada mara dalili,ta inda take hawa bata nan take sauka ba,waita yaye kowa bata neman kowa.


Dukkan wani takunta da abinda fulani aisha ke nema ya gama bayyana kanshi,don haka saita shareta yadaga waya tasoma amsa kira,bata tsagaita ba har sai data gama taga yaran suna tashi suna wucewa ciki kana ta ajjiye.


"ƴan mexico ana can dai,ƙiri kiri an hana abdul'azeez dai rayuwa cikin ahalinsa,bayan bashi da wadanda suka fisu" saudatun ta fada kamar meyin fada,murmushi fulani aisha tasaki cikin nutsuwa tana aje wayar hannunta,kana ta daga idanun nata ta zubawa saudatu su.


👑 *SIRAƊIN RAYUWATA*👑


*_wannan littafin na siyarwa ne,kuma amana ne a hannun duk wanda yasiya,idan kina buqatar siyan naki ki tuntubi wadannan lambobin_*

09032345899


25



Lokacin daya dawo dare yayi,saidai bawani dare can ba,a sannan sha biyu ne harda rabi,da muqullanshi daya saba amfani yabude gidan yabude yashigo,falon tsit babu kowa kamar yadda yakan tarar kullum idan yadawo,kai tsaye ya haura zuwa sama inda dakinshi yake.


Alwala yasoma yi kamar yadda yasaba zama da alwala akai akai haka ammi takoya mishi tun ba yanzun ba,yakuma saba yatashi da dabi'ar,alqawarin daya yiwa safwa yana cikin ranshi,mutum ne shi mai.matuqar kiyaye alqawari dakuma qoqarin cikashi,don haka yaja laptop dinshi yakunna.


Kiran safwa yasoma yi,wadda tajima gaban system din nata tana tsammanin kiranshi,harta soma kumbura jin shuru har yanzun bai kira ba,saidai idan ta tuna yana da cika alqawari sai kuma fushin nata ya sassauta,don haka yana kira ta daga.


Tarwai ta bayyana cikin screen din nashi,ta cika screen din gaba daya,tana kwance rub da ciki saman gadonta,sanye da wata lafiyayyar baqar riga ta wani yadi wadda ta haska fara tas din fatarta,gashinta na reto a kafadarta guda,fuskarta fes da madaidaiciyar kwalliya,labbanta sunata qyallin lipstick ta hasken screen system din.


Murmushi ta sakar masa tana kashe masa idanu daya,saiya lumshe idon nashi yana jin tsigar jikinsa na tashi,uwa uba yanayin kwanciyar da tayi din batayi masa ba,saboda ana ganin wuyanta zuwa qirjinta sosai,duk da basu bayyana ba gaba dayansu amma kana iya hango tudunsu
"Tashi sosai ki zauna" ya fada qasa qasa yana lashe busassun labbansa,murmushi takuma sakar masa,taji dadi ta sanyashi a yanayi,tana son taga yasauya saboda ita,anata ganin wannan kawai shine xai nuna ma'aunin qaunar da yake mata,hakanan zai bayyana adadin yadda ya matsu su zama mallakin juna kamar yadda itama ta matsu,tunda tasan bazai taba buda baki ya gaya mata yadda take da buqatar ji ba
"Meya faru da kwanciyata kuma?"
"Ki gyara kawai ko nayi cutting up kiran" tasanshi sarai zai aikata,don haka ta miqe zumbur tazauna tana tura baki gaba,saiya saki wani qaramin murmushi wanda iyakacinsa labbansa.


Bata iya wani dogon fushi da shi,don haka ba bata lokaci tasauko suka soma hirarsu,anan yayi realising lallai safwa batasan da zancan plan da ammi tayi na,saboda kusan rabin hirar tasu tayau tana nuna mishi yadda take bala'in kishinsa,daga qarshe ma ita yabarwa fagen yaxuba mata idanu yana kallon yadda labbanta da sukasha man lebe suke motsi.


Cikin jikinsa yaji tabbas akwai matsala idan sukaci gaba da zama a haka,don haka ya yanke shawarar samun abun mai zafi da zai rage masa abinda yasoma ji

Yasake kallon agogon dake aiki qasan system din,dare ya riga da yayi,bai kyautu ya tashi sodangi ba yanzu,don haka ya sanya laptop din a sleep bayan ya nemi uzuri wajen safwa ya dantse kiran,yamiqe ya zura slippers dinshi yasauko qasan.


Dai dai lokacin da yunwa ta hanata sakat sakamakon qin fitowa da tayi taci abincin dare,har suka gama abinda suke suka tafi suka kwanta.


Don dole ta tashi da hanzari jin yadda hanjinta ke curewa waje daya,slippers dinta itama kawai ta zura tana tattare hannun rigar baccin jikinta,wadda take riga ce iya cinya mai dogon hannu da wandonta dogo na wani lallausan yadi ruwan hoda,kanta babu dankwali,sai gashinta jelarsa ke reto a bayanta yana kuma qyalli saboda mai da gyara da yasha,ta bude qofar dakin nata a hankali kamar wata barauniya,ta tsaya ta kasa kunne,sai data tabbatar bataji motsin komai ba sannan tasoma takawa a hankali zuwa kitchen din.


Cikin qaramin plate tazubo abincin kana ta dawo falo,tvn dake aikia falon wadda sun manta basu kashe ta ba taja hankalinta suna nuna wani shirin girke gike,saita tsaya gaban tvn da plate din a hannunta tana yafitar abincin kadan kadan tana ci,idanunta da dukka hankalinta yana kan tvn.


Taku biyu rak yayi ya hangi mutum gaban tv,abun sai yaso daure mishi kai gamida bashi mamaki,a hankali yake qarewa bayanta kallo,a jikinsa yakejin baquwa ce,don sam batayi yanayi ko zubin rakiya ba bare yace itace,duk da ba wani kallonta yake ba amma yasan ba ita bace
"Wow" bilkisu tadan fada cikin birgewa,saboda abinda cook din ta hada yayi matuqar burgeta yakuma bata sha'awa.


Sautin muryarta yasake tabbatar masa da zarginsa,saiya ci gaba da saukowa idanunshi a kanta.


Jin takun saukowa daga step ya sanya

Please Login or Register in order to submit comment