Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bai damu da hayaniya dukan qirji da qoqarin tureshin da taketa famanyi ba,duk sanda ya saki ajiyar zuciyar yanakanji qirjinsa ya rage nauyi,duk sanda ya tuna itace rungume a qirjinsa sai yaji kamar bashi da wani sauran matsala a rayuwarshi,saida yayi mai isarsa,har cikin ruhinshi yaji cewa ya gamsu sannan ya sassauta riqon da yayi matan yana duban tsakiyar qwayar idanunta.


"Sai yaushe princess,har sai yaushe sannan xaki bani dama?,dama guda daya da nake buqata daga gurinki,wadda zata iya bani lokaci da zan warware miki komai" ya fada da wata iriyar lallausar murya dake cike da bege wanda ya taba sassan jiki zuwa ruhi,cikin fusata dai da qoqarin qwace kanta har yanzu tace dashi
"Baka da wannan damar,ba kuma zaka samu ba,ka sakeni nace ka sakeni!" Ta fada a tsawace,sake riqonta yayi sosai fiye da dazun,kai kace ce masa tayi riqeni,sosai ta fahimci cewa da gaske yake bazai saketa din ba,saboda haka tace
"Ba yaranka kakeson gani ba?,su kazo gani?,to sakeni na turo maka su" ta fada a fadace sosai,saiya saki wani irin lallausan murmushi dakan wuce da zuciyar 'yammata lokaci guda,ya kuma girgixa kai
"Ba yarana kadai ba,harke ina da buqata,ina da buqatar ganinki,ina da buqatar zama dake,ina da buqatar rayuwa dake,kafin sannan kuma ina buqatar tattaunawa dake,wanda tattaunawar ita zata kawo makomar rayuwar yaranmu"
"Makoma!,makoma kace?,makomar banza da wofi?,ku baku tuna ba?,bakuyi tunanin cewa ina makomarsu ba?,yaya makomarsu zata kasance,su waye zasu zama,duka sai yanzu kake wannan maganar?,ni bakuyi tunanin tawa makomar ba,saboda ba uwace ta haifeni ba,nidin ba mutum bace?,me zan koma me zaya sameni dukka baku damu ba!,ka sakeni malam" ta qarashe maganar launin fuskarta yana sauyawa,hakanan fushinta na qara fitowa qarara har cikin idanunta.


Wani riqo yayi mata sosai yana dan girgizata
"Na yarda bilqess,na yarda da komai kika ce an miko an mikin,kuma ya cancan ci kiyi komai din matuqar zaki huce,amma ki fuskaceni da farko mana".


So take ya fuskanceta kamar yadda yakeso ta fuskanci shi,amma ta lura babu niyya ko alamun hakan tattare dashi,kuka kuma take da buqatar yi saboda yadda takeji zuciyarta na cunkushe mata tare da tuna mata wasu abubuwa masu nauyi da suka taba wanzuwa tsakaninsu,don haka saita sulale ta tsakanin hannayensa tayi qasa kawai,kana ta fice daga tsakiyarshi ta miqe kuma tayi gaba da sauri.


Tana fita daga dakin sukayi kacibus da yarinye
"Maman 'yan biyu,hajiya tace ya shigo su gaisa mana" bata tanka ta ba face gaba da tayi abinta,tana da tabbacin taje ta bawa hajiyan labarin cewa ga babansu amatu ne,don duk wanda ya ganshin basai ya tambayeta ba yake gane wayeshi.


Da kallo yarinye ta bita harta bace tana tunanin kodai bata jita ba,sai kawai ita din tayi gaba zuwa falon don ta sanar masa.


Yana tsaye idanunshi a rufe ya daga kanshi yana kallon sama,ya zuba hannayensa dukka cikin aljihunsa,da alama wani tunani yake me cin rai yaji sallamarta,saiya buda idanunsa a hankali ya zubesu akanta,ta duqa cikin girmamawa,kwarjininsa na dukanta
"Hajiya tace ka qaraso ciki ku gaisa" a nutse ya gyada kanshi,hakanan yaji abun ya masa dadi,don haka babu musu,tanayin gaba yabi bayanta.


*_ASHA HUTUN LAHADI LAFIYA_*🚢πŸΎβ€β™€οΈπŸšΆπŸΎβ€β™€οΈπŸšΆπŸΎβ€β™€οΈπŸ˜ŽπŸ˜ŽπŸ˜Ž
7/11/21, 4:35 PM - My Mtn Number: 67
https://youtu.be/NNr-vDOJzq8

*makaranta ce,mai wahalar samu,mai azabar tsada kuma,amma sai gata a KYAUTA!!!*

*CI KA ZAUNA LAFIYA youtube channel,ba tashar youtube kawai bace,face MAKARANTA GUDA garemu al'umma*

*makaranta ce da*

*ZATA GYARA MANA CIMARMU*
*MUSAN ME ZAMU DINGA CI*
*MUSAN ME ZAMU DINGA SHA*

*_DOMIN TSIRA DAGA CUTUTTUKA,DAMA SAMUN WARAKA DAGA GARESU IDAN AN RUGA AN SAMESU,KAMAR SU_*

_ciwon suger_
_ciwon hanta_
_ciwon qoda_
_cututtukan mafitsara_
_paralyse_
_H I V_
_Rashin gani_
_Rashin samun isashshen barci_
_ciwon cancer_
_matsalar fata kamarsu pimples quraje da sauransu_
_ciwon ciki_
_typhoid_
_malaria_
_rashin jini_
_siclier_
_asthma_
_limoniya_

*_dama dukka sauran cututtukan da suka addabi al'umma duk ta cikin ABINCINMU_*

Tare da

*DR KABIRU ABDULKARIM*
*_Likita kuma masani,wanda yayi karatu a qasar ISRA'ILA*

*_KASANCE DA TASHAR(CI KA ZAUNA LAFIYA)dake a YOUTUBE,kayi subscribing,ka kuma fara bin shirye shiryenta domin samun ƘARUWA da kuma WARAKA,BABBA DA YARO MATASA DA KUMA DATTAWA,MAZA DA MATA duk kuna da buqatarta_*

*ka dannan wannan shudin rubutun domin zuwa gareta kai tsaye*
https://youtu.be/NNr-vDOJzq8


*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903Β 234Β 5899
Ko
09033181070


A hankali yake takawa yana tattauna zancan cikin ranshi,baiga wasu alamu dake nuna sakkowarta ba ko kadan,yana jin zaiyi qundumbala ne kawai ya sake tunkarar mai martaba,yayi masa dukkan hukuncin da zaiyi masa matuqar zai gyaro lamarin ta dawo cikin rayuwarsa ita da yaransa.


A bakin sassan ya samesun kuwa suna wasansu,saidai amatu na langabe zaune waje daya tun ciwon dazu,dukkaninsu sun ganeshi,kusan tare suka nufoshi kamar yadda shima ya nufesu cikin farinciki,yana jin wani dadi yana ratsashi,gaba dayansu ya rungumesu cikin jikinsa yana kissing dinsu,yayin da kowannensu ya soma cikashi da surutu yana son mishi hira.


Ko daya baiji nauyin da suke dashi ba ya daukesu cak,daya a hannun dama daya a hannun hagu haka ya nufi sashen hajiya dasu amatu na nuna mishi ciwonta a shagwabe,ya kuwa biye mata yana sakw zuzuta ciwon,badon nuna gwaninta ko wani abuba,a'ah,har cikin ranshi yakejin ciwon shima kamar a jikinsa yake a haka suka qarasa sashen,yace bari su fito zaya kaita asibiti.

Cikin jin dadi hajiya ta tarbeshi,shima ya gaidata cikin girmamawa,kai bakace shine wannan azeez din ba d'a ga sarkin kaisa kuma shahararren dan kasuwa na duniya ba.


Babu yadda hajiyan batayi da bilkisu ba ta fito amma taqiya,data aika yarinye saita cema hajiyan kanta ke ciwo,shi yasan kwanan zancen,don haka bai tsawwala da yawa ba yace zai wuce yakai amatu clinic a wanke mata ciwo,kama baki hajiya tayi sannan tace
"Saboda taya bera bari wannan dan ciwon za'a kai ta ganin likita,rakine kawai irin nata,shi yasa kishinsu ya kasa daidaituwa da kishiyarta" wato mama mahaifiyar abbaa.


Murmushi kawai yayi,ya fuskanci tsohuwar tana da yawan barkwanci da raha,hakan sai yaji yayi masa
"Zamuje mu dawo hajiya,wataqil yana mata zugi ne" hajiyan na musu tsiya haka suka fice.


Suna fitowa harabar gidan abba da mahaifinsa dr maisara suna shigowa gidan,da qafa suka shigo da alama sun faka motarsu ne a wajen gidan,duk yadda akai kuma ba zasu jima ba zasu sake fita ne.


Dukkansu idanunsu akan azeez,ga abbaa tuni ya fahimci komai ganinsa dauke da yaran,ga kuma kama ta zahiri nan dake bayyana kanta,yayin da dr maisara ke kallonshi cikin mamakin kamannin da yake gani zahiri game dashi da kuma yaran.


Sun cimmashi don haka ya qarasa garesu suka gaisa kana ya koma inda yaran suke.


Dukkansu yaran ya zuba cikin lafiyayyar motarsa,ya tada ya fice daga gidan.


Yawo sukayi sosai dasu bayan anwakewa amatu ciwon,manyan wuraren shaqatawa dake garin,saida kowannensu ya gaji tubus sannan suka dawo gida.


Ciki dukkansu suka shiga harda su abdul din,don tuni amatu ta soma gyangyadi saboda gajiya,saiya haye saman motarshi kawai ya zauna shuru yana kallon sararin samaniya wadda ta cika da taurari da kuma farin wata daya kai rabi saboda tuni kwanakinsa sunyi nisa,sam sai yaji baison barin qofar gidan,kamar ya dawwama anan,har zuwa sanda zatace ta yafe masa.


Shuru anguwar,cikin layinma gaba daya shi daya ne zaune,har zuwa sanda wata mota ta shigo layin da full light dinta,amma data matso dab dashi sai aka rage hasken motar.


Saida suka giftashi sannan ya gane su waye a ciki,bai damu ba yaci gaba da zamanshi har suka shige cikin gidan.


"Wannan yaron waye?,kamar nasan fuskarshi" dr maisara ya tambayi abbaa sanda yake qoqarin faka motar
"Zaka iya saninsa,sanannen dan kasuwa ne,sannan kuma babansu amatu ne,tsohon mijin bilkisun zuhriyya"
"Eh qwarai,amma ina fata lafiya ko?"
"Nafi zaton bikon matarsa yake,saboda zuhriyya ta soma yimin maganar,to bamu gama ba wannan tafiyar ta taso"
"Haka ake bikon?" Dr maisara ya fada yana duban abbaa,shima abban saiya kalleshi don bai fahimci me yake nufi ba,duk da yasan mahaifin nasa baisan komai kan auren bilkisun na baya ba
"Eh...to ai banga wani support da kuke bashi ba,kada kacemin daga kai har zuhriyyan goyon bayan diyarku kuke?" Ya san mahaifin nasa sarai,yasan dattakonshi sak irin na mahaifiyarsa fatsima,babu abinda sukaqi jini irin lalacewar aure,dole ya yiwa mahaifin nasa bayani,idan ba haka ba yanzun dukkan laifin zai koma kansu.


A nutse yaw warwarewa mahaifin nasa bakin gwargwadon abinda yasani yakuma san zai fahimta,shuru dr maisara yayi yana jinjina lamarin,kana ya sauke nannauyar ajiyar zuciya
"Tabbas ko shakka bana yi,sarki abdallah baida masaniya kan faruwar hakan,bada kuma yawunsa aka aikata komai ba,na sanshi tun kafin ya zama sarki,nasan halayensa sarai,amma wannan magana ce dake da buqatar nazari....zamuyi magana in sha Allahu,bai kamata a qyale lamarin haka ba"
"To baba,Allah ya tashemu lafiya"
"Amin" ya amsa yana yunqurin fita.


Har ya sanya qafarsa waje sai kuma ya waiwayo
"Kar a kuma hanashi ganin yaranshi,domin su babu ruwansu dama duk abinda ya faru,kuma suna da haqqi saman wuyanshi na mahaifinsu"
"Tuni dama zuhriyya take turasu idan yazo,in sha Allah kuma za'a ci gaba da hakan" daga wannan dr maisara ya fice yana jujjuya batun cikin ranshi.


Koda abbaa yafito sashen hajiya ya nufa,don yau duka bai samu ya shiga ya gaidata ba.


Daidai lokacin da bilkisu anty zuhriyya da hajiya ke zaune dukka a falon hajiyar,amatu na kwance saman cinyar bilkisun.


.


Magana hajiyan take cikin siyasa akan abdul'azeez din,yadda take ka kirkinsa da cikar kamalarsa,saidai sam bilkisu jin maganar take kamar ta dora hannu aka tayita zunduma ihu,kamar tacewa hajiya tayi shuru,amma hakanan ta haqura ta rufe bakinta tayi mata kawaici.


Bayan sun gama gaisawa da abbaa ne yace
"Yaron nan yarima muka samu nida baba zaune qofar gida saman mota,baba ke fadan an hanashi ganin yara ne,daga yau yace kada a kuma hanashi ganinsu duk sadda yazo"
"Shine dai dai ai,ina ruwan yara da rigimarsu" hajiya ta cafe zancan
"Ai dama ba'a hanashi ba abbaa" anty zuhriyya ta amsa tana kallonshi
"Ni wallahi da zaku nuna halin dattako,da yazo koma meye an zauna an sulhunta,darajar mace fa dakin mijinta,darajar 'ya'ya gidan ubansu,sam agolanci baida dadi,duk yadda za'a kula da yaro kuwa".


Tsam bilkisu ta miqe tana saba amatu a kafadarta,sabida zancan bai zauna mata ba,sam sam ba irin aurenta akewa wannan gatan na zaman sulhu ba,hasalima batajin hajiya tasan ainihin yadda auren da rabuwar ta kasance,shi yasa ta fadi hakan,tadai san sanda aka sakota da cikinsu amatu,saita wuce kawai dakinta,hajiyan ta bita da kallo harta bace sannan ta dubi anty zuhriyya
"Kada su sake ku biyewa shirmenta,shi aure rai gareshi,koda kashe juna kukayi aka dawo idan da rabo sai an koma,mutuwar aure na jawo tozartar yara da tabarbarewar al'umma matuqar ba'a kwai wani qaqqwaqwaran dalili da zai janyo hakan ba"
"Hakane" abbaa ya fada daga nan ya mata sallama ya wuce,anty zuhriyya ta miqe ta biyo bayanshi.


ΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆ


Tun randa abun ya wakana tsakanin fulani adama fulani saratu da hajja fauziyya suka kasa zaune suka kasa tsaye,kowanne yanason sanin ainihin abinda ya wakana,yana son yasan ainihin labarin,shin da gaske matarshi ce?,idan matarshi ce yaushe akayi auren?,maimartaba ne ya daura masa auren yakuma boye ku kuwa?,dukka har yanzu babu wanda yasan taqamaimen asalin maganar,gashi mai martaba gaba daya ya musu dif,kai kace babu wani zance irin hakan daya taba faruwa cikin masarautar,gaba daya ya shiga sha'aninsa da sabgoginsa,ko a fuska basuga wata alama ta komai ba tattare dashi,har gwara fulani aisha sun samu labarin ta fada yanayin damuwa,amma banda wannan itama basu samu komai ba basu kuma samu wani bayani ba sabanin hakan.


Ta gefan kamal shima hankalinsa na a tashe ne,kalmar matata ce din da azeez ya fada na neman tarwatsa shirinsa,indai ya tabbata kenan tilas ya haqura da ita?,ya sake rasata kenan duk burin da yaci a kanta ya tarwatse?,wannan tunanin shima ya saka masa damuwa,ya kuma hanashi sakat.


ΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆ


Kamar yadda a cikin wadan nan lokuttan suka koma shi da ita kamar wasu baqin juna,misalin qarfe goma na safiya,tana tsaye daga gefansa yana shiryawa cikin irin suturar da yake sakawa idan zaiyi zaman fada.


A lokuttan baya itake tayashi shiryawa,ta qware tsaf ta wannan fannin fiye da kowacce mace cikin matanshi,wani lokaci har bai ganin kyan shigarshi idan ba ita ta tayashi shiryawar ba,saidai a yanzun dare daya ya soke wannan,duk lokacin data yunqura zata tallafa mishi yakan dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu,tun tana qoqarin gwadawa harta haqura,daya daga cikin horon da yake mata kenan wanda ke matuqar ci mata rai,shekaru kusan arba'in komai laifin da zata masa bai taba yi mata abu makamancin haka ba.


Yanzun ma tana tsaye ya gama shiryawa,da sauri ta dauki cup dinsa na tatacciyar madarar shanu data tafasa masa da citta da kununfari ta miqa masa,saidai kamar kullum yauma hannu ya daga mata kawai,kana ya soma takawa zai fice.


Kasa jurewa tayi,yau haqurinta da dakiyarta sun qare,saita saki kofin madarar ya tarwatse a nan wanda hakan ya sanyashi juyowa,har a jikinsa yaji fashewar abun da yadda take tsallakesu,amma saiya dake ya basar,itama bata damu da wannan ba ta tsallake cikin hanzari ta isa inda yake.


Hannayensa ta kama gam cikin nata,sai kawai ta fashe da kuka,baice mata uffan ba,kamar yadda bai dakatar da ita ba har sai datayi mai isarta
"Duk hukuncin da zakayimin ka yimin don Allah,amma banason wannan shurun,wannan halin ko inkula din don Allah" a shashance yace
"Wanne laifi kikayi kuma?,kinyi wani abune dama?" Kuka ta kuma saki tana girgiza kai
"Kada kace haka don Allah,kada kace haka".


Duk yadda yaso ture tausayinta daga ranshi amma hakan yaci tura,bazai iya tuna sanda ya ganta tana kuka haka ba,duk da hakan ya riga ya qudirta dole ya hukuntata yadda zataji a jikinta,bai taba tunanin zata tafka ta'asa mai girma haka ba,don bashi ba ba yarima ba,yarinyar data aikatawa abun,yanason ta gamsu a karan kanta ta cutar da ita,yanason ta gamsu cewa ya kamata ta nemeta,ya kamata ta nemi afuwarta,shi kansa yariman yana da laifi cikin abun,kuma koshi din bazai qyaleshi ba,saiya hukuntashi daidai da laifinsa
"a'ah,meye na damuwa kuma?,bayan kin aikata abinda ya dace ne?,kin isa kiyi shawara da kanki fa kuma ki yanke hukunci tunda shekarunki sunkai,kuma komai ya tafi daidai,meye na damuwa kuma?".


Shuru tayi tana sheshsheqar kuka,sai ya zame hannunsa kawai yayi gaba yana juyo sautin kukanta,duk da yadda zuciyarsa ke masa nauyi dajin kukan nata.


Yana saka qafarshi falonshi ya tadda fulani adama zaune gefen kujera,ta caba ado sosai har abun yaso bashi mamaki.


Tana ganin fitowarsa ta miqe cikin girmamawa tana sakin murmushi
"Allah ya baka yawan rai,Allah ya tsare mana kai,ya qara lafiya da nisan kwana,barka da fitowa takawa" ta fada cikin daga murya,don tana da masaniyar aisha na cikin dakin,murmushi ya saka cikin sarauta,yana daga tsaye don baison ya zauna ta bata mishi lokaci
"Ya akayi adama?"
"Barka da warhaka"
"Barka kadai,kun tashi lafiya?"
"Lafiya qalau ranka ya dade,zuwa nayi dama in gaisheka,jiya da yau duka bamu samu ganinka ba,gashi ka barmu cikin alhini kwana biyu"
"Lafiya alhmdlh....alhinin me fa?" Sosai ta sauya fuskarta ta maida kalar jimami,kanta a qasa ta girgizashi
"Abinda ya faru da yarimanmu,kullum cikin zullumi muke kwana,muna fata Allah yasa ba wani abu mara kyau ya aikata ba,gashi babu wanda ka yiwa cikakken bayani a cikinmu Allah ya baka nasara" kanshi ya dauke don ya jima da soma karantar adaman,musamman lokacin daya matsa bincike kan daga wannw saqo hotunan suke fitowa,sai suka lura sunfi fitowa daga nahiyar da fulani adaman take,saiya soma takawa yana yin gaba kafin ya bata amsa
"Awwnnn....ashe....na mance ma wani abu ya faru,kuyu baccinku dakyau ku daina tunani,ba wani big issue bane ba,kusa a ranku kaman ba'ayi ba"
"Amma muna buqatar qarin bayanin da zai kwantar mana da hankali,ko 'yar uwarka bakaga yadda ta damu ba" saiya juyo yana dubanta
"Kije ki musu bayanin dana miki,inaga ga ishi kowa a cikinsu"
"In sha Allahu ranka ya dade" ta fada tana sunkui da idanunta ganin yadda ya tsareta da ido,daga haka ya juya ya fita cikin jama'arsa.


Da baya da baya fulani aisha ta koma ta zauna bayan ta gama jin duk abinda ya wakana tsakanin fulani adama da me martaba,hannunta tasa tana toshe bakinta da kuka keson qwace mata karo na biyu a ranar yau,duk da taurin rai da dakiyarta,a haka kamar yayi fushi da ita,amma kuma a fakaice ta wani bangaren yana qoqarin lulluba asirinta,tabbas ta sani tsakaninta dashi wata irin soyayya ce min indillahi tun quruciya,bata taba kuma zaton qiyayyar su adaman a kanta takai har hakan ba,tasan suna sone suji komai,su samu abunda zasu qarasa tarwatsa ta,saita dafe kanta da hannu biyu tana ambaton sunan Allah.
7/11/21, 4:35 PM - My Mtn Number: 68
https://youtu.be/-kbsWo6IjOo

*_yadda zaku sarrafa albasa ke da mai gida/kai da uwargida,domin samun ingantacciyar lafiya da gyara xamantakewar aurenku,ta kuma rabaku da shaye shayen magunguna barkatai marasa fa'ida da amfani,da kuma illata lafiyar dan adam_*

*Tare da*

*DR KABIRU ABDULKARIM*

*_dannan shudin rubutun nan,bayan ka shiga ka saurara kuma kayi subscribe,share da kuma like_*
________________________________

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903Β 234Β 5899
Ko
09033181070






Ranar ya jima sosai a fada,wanda kafin ya tashi yasa aka shaidawa mama sodangi yana buqatar ganinta bayan zaman fada.


Zama sukayi daga shi sai ita,ba tare da sanin kowa ba,ya samu dukkan bayanan da yake da buqata kafin ya sallameta,yayi shuru abun na sake qona mishi rai,aisha ta mishi ba zata,ta kuma bashi mamaki,badon Allah ya tsare ba shi kadai yasan yawa da girman abinda zai faru,a hakanma yana ji a jikinsa tsarewarsa ce ta kawo lamarin ya tsaya iya haka,ya miqe ya shige ciki yana sake wassafa hukunci da qarshe da zai yanke kan lamarin.


ΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆΒΆ


Bayan ya tabbatar da tahowarta qasar kaisa a ranar,saiya sauya akalar motarshi zuwa masaukinsa,ya dauki dukkan abinda zai dauka shima ya nufi qasar kaisa,ya nufeta da qarfin gwiwa da tarin karsashin zuwa ya samu mai martaba kanshi tsaye,ya gaji da wannan walagigin haka,ya gaji da yadda take wajigashi tana wasa da hankalinsa duk yadda taso,yana da buqatar ayita ta qare kawai.


Sanda ya isa bai nemi kowa ba,hakanan bai shiga masarauta ba kai tsaye,hakanan ya samu kanshi da ra'ayin sauka a village(wani gida ne nashi da aka yiwa gini na musamman,gini irin na qauye na gargajiya saidai kuma a zamanance,dukkan abinda ke cikin gidan na gargajiya ne,hatta da dakuna na bukka ne,saidai kuma ciyawar da turakunan da akayi amfani dasu a zamanance ne,hakanan katangun duka na qasa ne bulon qasa ne,saidai lailayayye sosai wanda kana gani kasan an zamanantar dashi,hakan kitchen din dake cikin gidan,kwanukan girki na qasa,kwanukan abunci na akushi ne,gadon qarfe mai rumfa amma na zamani,kawai qoramu da aka gyara wajen,kai kace ire iren na qauye ne,akwai randuna na qasa na ruwa mafitai tabarmin kaba da sauransu,duk da awani wajen tiles akayi aka saka carfet,sannan dole ta sanya aka saka ac saboda sake qawata wajen da bada nishadin xama.


Gidane daya dauki hankali matuqa saboda yadda aka tsarashi,afnan na bala'in son gidan tun lokacin da aka kammalashi,saidai tasan babu fuska bare tace zataje,gidane na musamman a wajen maishi shi karan kanshi,yanayin wajen na qawatar dashi,saboda yadda ya cika da tsirrai da shuke shuke da ko yaushe sukan sanya gidan ya kasance luf luf cikin sanyi da qamshin qasa mai dadi,yawan tsirran ya gayyato tsuntsaye kala kala,wadanda suka kama bishiyoyin gidan kowacce na rera salon nata kukan ko waqar,idan ka shiga gidan kaida kanka kasan na musamman ne.


Ya jima zaune a daya daga cikin falukan gidan bayan ya rage kayan jikinsa,saiya jawo wayarsa ya soma neman layin safwa,saboda kwana biyu gaba daya baida nutsuwar kiranta,hakanan itama baiga nata kiran ba,bai sani ba tana kaisa din ko ta qara gaba yadda ta saba,a halin yanzun yana da buqarta kusa dashi koda ba zata tsinana masa komai ba,amma a qalla zai dinga jin motsin mutum.


Sam sam sai wayar tata taqi shiga,ya gwada kusan sau uku amma ana gaya mishi layin a kashe yake,yayi mamaki qwarai,saiya gwada ta mamanta itama taqi tafiya,don haka ya sauya shawara yayi kiran afnan.


"Barka da warhaka yaya...." Ta fada cikin nuna girmamawa
"Yauwa....ko safwa tayi magana daku zata wani wajene?" Mamaki saiya cikata,itakam tana mamakin aure irin nasu,safwa ko yaushe jinta take kamar qaramar yarinya,ta kasa gane ainihin ma'anar aure,ta kasa gane cewa ta girma,saita yita yin abu kamar yau aka haifeta,shima ta nashi fannin ya rungumi kasuwancinsa gaban komai,ibadarsa ce kawai yake sakawa gaban kasuwanci,sam kamar zaman auren nasu bai dameshi ba
"Am asking you kinma mutane shuru?" Ya fada a dan fadace,da alama ranshin a bace yake
"Bandai sani ba,amma dai ganina na qarshe da ita....tazo wajen ammi bata sami ganinta ba,tace na gaya mata zata yiwa daddynta rakiya zashi yearly cheakup dinsa" daga haka bai sake jiran jin komai daga bakinta ba ya katse kiran.


Sai yaji ranshi ya baci sosai wannan karon,ya kamata ya dauki mataki hakanan,aure ba abun wasa bane,hakanan shiba lusarin namiji bane,bazai zauna mace ta soma haihuwa dashi ba amma har yau sakarya bace,batasan ciwon kanta batasan ma'anar zaman aure ba,atleast koda zata bai kamata ta wuce haka ziqau kaman ita ke zaman kanta ba,tunda matsalolin nan suka sanyashi gaba bai sakata a idonshi ba,amma yasan ya tsare dukkan wani haqqinta.


Idanunsa na alumshe yana wassafa matsalolinsa guda biyu wata sassanyar busar sarewar sarauta ta ratsa falon,alamun anason magana dashi,idanunsa na a rufen ya bada umarni a shigo din,daya daga cikin amintattun bahi na musamman da ya saka aka turo mishi suke kula da gida ya bayyana,cikin shiga ta musamman,kaman yadda yake kamar sutura ga duk wanda ke aiki cikin village
"Allah ya taimakeka,ya baka yawan rai.....yallabai abdulrashid ne yake neman iso" da hannu still dai ba tare daya buda idanunsa ba ya mishi nuni daya barshi ya shigo.


Sallamar abdulrashid ita ta sanyashi bude idanunsa,ya zuba mishi idanu kamar yadda shima ya zuba masa nasa idanun yana kallonshi harya samu waje ya zauna.


Tashi abdul'azeez yayi sosai ya zauna har yanzun idanunsa kan abdulrashid daya lura yana masa kallon qurilla,ya buda baki zaiyi magana dariyar da abdulrashid ya sanya ita ta katseshi daga fadin abinda yayi niyya,cikin mamaki yake duban abdulrashid,daga baya daya lura akwai shaqiyanci cikin dariyar tasa,sai kawai ya sake maida idanunsa ya kulle,ya kuma koma ya kwanta kamar yadda yake a dazun,har yayi dariyarsa ya qoshi don kansa sannan ya soma magana
"Mai firgitarwa yau shi ake firgitarwa?,lallai dara taci gida,inama zanga dukka matan da kake zame musu xaki idan sun ganka,jikinsu ke tsuma saboda kwarjininka,soyayyarka ke hanasu bacci da sukuni,suke kasa kallon fuskarka,yau suzo....ga wata yarinya guda daya ta birkita maka tunani...ta hana rayuwarka sukuni,ta hanaka sakat....ban taba zaton kai rago bane yarima sai yanzu,ban tsammaci cewa kai rago bane sai akan bilkisu,kaga yadda ka birkice ka hautsine?,idan na gani da kyau ma kamar ramewa naga kayi hakane?",ya qarashe ta sigar

Please Login or Register in order to submit comment