Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sanya qafa tayi fatali da ita?,meye abunyi a gareshi?,ya mata biyayya ya banzatar ya kuma sarayar da haqqunan rayukan da zuwa yanzu baisan guda nawa bane?,ko kuwa ya bijire mata ya shirya tunkarar dukkan wani abu da xai sameshi a rayuwa?.


Wannan tunanin shi ya kusa daskarar da qwaqwalwarsa,har baisan adadin lokutta daya shafe durqushe a wajen ba,sai daya ji jikinsa na fidda wani irin hucin zafi dake alamta masa tempurature din jikinsa ya hau sosai,sannan ya iya dafa abinda ke gefansa ya miqe tsaye da qyar,kamar wanda ya shekara a duqe,yakai kanshi dakinsa da qyar.


Bai damu da yanayin jikinsa ba bare yasha wani magani,tsahin daren kawai ya qarar dashi wajen yanke hukunci na qarshe a rayuwarsa,wanda wayewar garin ranar da sassafe ya isa gaban ammin,ya kuma shaida mata hukuncin daya karba cikin zabi biyun data bashi.


*_kaso na biyu cikin labarin kenan masu karatu,zamu shiga cikin kaso na uku,ku biyoni_*




*BAYAN SHEKARA BAKWAI*


Cikin nutsuwar 'yar madaidaiciyar motar mai azabar kyau fasali da tsari gami da daukan hankali take sako kai cikij katafaren asibitin dake zaman kanshi wanda keda mazauni cikin brasillia dake qasar brasil,bansan me ya sanya ba ban kuma san dalilin daya saka duk inda motar ta gifta saita dauki hankulan jama'a da dama dake kai kawo cikin asibitin,wasu kuma na zaune guraren da aka kebance saboda buqatuwar masu zuwa asibitin wanda a nan gida nigeria yafi kama da wajen shaqatawa ko shan iska,saboda yadda ya wadata da ababen zama masu kyau,korayen tsirrai da kuma iska mai dadi qwarai da kwantar da rai.


Bata gushe ba motar tana ci gaba da ratsawa cikin asibitin,har sai data isa muhallin da aka tanada a dokance saboda ajiyar ababen hawa,akayi mata parking me kyau kafin a kasheta,wanda zai gaya maka drivan dake sarrafa motar ba shakka yasan abinda yakeyi.


A qalla saida aka dauki kyawawan mintuna uku kafin qofar motar ta bude a hankali kuma cikin nutsuwa,wanda budewat motar yake dai dai da fitowar wani rantsatsen qamshi mai kwantar da zuciya da sanya nutsuwa,hadi da sanyin acn da aka kasheta a yanzu.


Idan kakai dubanka cikin motar sai kace tirqashi!,wata halitta ce mai cikar zati haiba da kwarjini,wadda kamala da nutsuwa suka sake qawata kyanta,kwarjininta kuma yake bayyana kansa.


Zaune take a sit din drivern da alama itace me tuqin kuma mamallakiyar motar,sanye cikin wani lallausan yadi mai azabar kyau da daukar idanu,wanda sam ba'a cika masa ado ko qawa ba,an masa dinkin riga wadda tsahonta ya kawo har gwiwa,sai kuma street skert mai matsakaiciyar tsaga wadda ba zata fidda halittar qafarta ba,tayi rolling da mayafi madaidaici wanda bata buqaci dankwali ba tunda ya rufe mata dukkan inda ake buqata,fuskarta sam babu kwalliya ko kadan idan ka dauke powder da man lebe masu taushi wanda yasa lebunan nata suka qara kyau da qyalli,sai jikinta dakw fidda wani irin sihirtaccen qamshe mai nuna tsada da ajin turaren da take amfani da shi.


hannunta dake sanye da wani kyakkyawan zobe qwaya daya,sai agogo a tsintsiyar hannunta daketa aikinsa ta sanya ta zare muqullin motar,sannan ta waiwaya sit din gefanta ta saka hannunta tana tattara kayayyakinta dake zube a wajen,wanda takardu ne cikin wasu folders,qaramar hand bag nata wayoyinta sai labcoat dinta dake rataye a fuskar kujerar.


Sai data gama tattare kayan tana shirin dorasu saman cinyarta don ta samu damar fita sai idanunta suka sauka kan wani qaramin lunch box da aka dan turashi qasan kujera da alama ana boyewa wani ne kada ya ganshi.


Idanu ta zubawa lunch box din kafin ta miqa hannu a hankali ta daukoshi,sannan ta dorashi saman cinyarta ta bude.


Komai da komai da ta zuba yana ciki,babu abinda aka taba ciki sai drinks din data zuba aka kwashe,choculets da biscuit.


Wani murmushi ne ya subuce mata bata shirya ba,ta dora yatsanta guda biyu saman labbanta tana girgiza kai
"Amatullah....amatullah,Allah ya shirya min ke" harta maida lunch box din sai kuma ta fasa ta hada da dukka kayayyakin nata ta zuro santala santalan qafafunta dake cikin hillshoes mai igoyiyi ta fito zuwa waje.


Nan take Dr Bilkees Bilyamin ta bayyana,kamanninta da suka dan sauya kadan sakamakon gishirin rayuwa wato ilimi daya ratsata,wayewa hutu jin dadi uwa uba nutsuwa da kwanciyar hankali data samu cikin wadan nan shekaru bakwai din.


Tana gama kulle motar ta soma takawa zuwa wata hanya da zata sadata kai tsaye da office dinta,tana mai sauya yanayin fuskarta,ta ragewa fuskarta fara'ar dake samanta a daxun,tadan daureta tana sake maida hankalinta ga inda take sanya qafafunta.


Daga yanayin yadda ma'aikatan asibitin ke gaidata cikin girmamawa kawai ya isa ya gaya maka ita din wata ce,ta dinga amsa musu bakin gwargwado cikin kulawa,har takai jerin inda office dinsu yake.


Office na kusa da qarshe ta saka card dinta wanda bayan ya gama duba bayanan jiki qofar ta bude mata,ta sanya kai cikin sauri ta shige.


Tana qoqarin maida qofar idanunta ya sauka kan wani office da yake opposition da nata office din,allon dake dauke da suna da matsayin me office din na mamallakin asibitin ya bayyana,tayi hanzari maida qofar ganin tana yunqurin budewa,bakinta cike fal da addu'ar Allah yasa ba zuwanta yaji ba ya fito,taja qaramin tsaki tana rage kayayyakin dake hannuntanta hanyar ajiyesu,donta hana kowa ya amsar mata kayan,matsayin da suke bata da girman da suke bata ita bata sonshi sam,batasan me yasa Dr adam yayi mata haka ba,ya fiya naci kafiya da kuma rashin zuciya,ta tabbata idan da wani ne da tuni ya tattara lamuranta ya watsar,amma shi ko a jikinsa wai an mintsini kakkausa,duk abinda takeyi din nunawa yake kamar ma bai fahimceta ba,sai sake shige mata ma da yakeyi.


Sai data gama duk abinda zatayin sannan ta soma amfani da kayan wutar dake gabanta,kama daga cellphone zuwa kwamfuta,ta soma da neman wanda ke kula da office dinta,taji ayyukanta na yau.


Akwai yaran data yiwa aiki jiya wanda dole yau zata shiga ta duba yadda suka kwana,sa'annan akwai wasu yaran da zata gani a yau din,duk da cewa sai yanzu ake gaya mata,don a qa'ida ba lallai ita zata gansun ba,amma iyayensu sun dage kan cewa ita din sukeso ta dubasu.


Tana cikin hada kayan da zata buqata idan ya fita round din,tana kuma jiran isowar nurses din da suke qarqashin kulawarta wadanda tare zasuyi round din qofar office din nata ya bude,wanda tun bata daga kanta ta kalla bakin qofar ba tasan ko waye.


Dr adam ne,shi kadai qofar ke budewa ba tare data bada izini ba,don haka bata daga kai ta kalli bakin qofar ba taci gaba da sabgarta.


Dogon matashi ne,ma'abocin tsaho da kuma fari,irin farin nan qal wanda kana kallonshi xaka san cewa ruwa biyu ne,a shekaru duka duka bai wuce shekara talatin da biyu ba,amma tsahonshi ya sanya akan bashi shekaru sama da haka,daga kallon farko xaka fahimci cewa shi din ruwa biyu ne kamar yadda na fada a baya,haka yake,mahaifiyarsa haifaffiyar qasar brasil din ce,yayin da mahaifinsa ya kasance dan asalin nigeria,bafulatanin jigawa,saidai dukka rayuwarsa yayita ne yana kuma yinta a qasar ta brasil,zai iya cewa tunda yake zuwanshi nigeria dangin mahaifinsa sau daya ne.


Cikakken likita wanda haihuwar mahaifiyarsa a qasar da haihuwarshi shima da akayi a qasar yasa ya samu damammaki masu tarin yawa,ya kuma zama shima halastaccen dan qasar,wanda hakan ya bashi damar mallakar fili da gina asibiti nashi na qashin kansa,babban asibiti na kudi wanda yayi shuhura cikin garin,yake kuma da kyakkyawan tarihi na qwarewa da iya kula da marasa lafiya,musamman mata da qananan yara,wanda a halin yanzu bilkisu take aiki a qarqashinsa,cikin asibiti bangaren cututtukan da suka shafi yara.


Ya fada soyayyar bilkisu tun bata gama karatunta ba,bayan ta gama kuma yasan yadda yayi ba tare da masaniyarta ba ya bata aiki a asibitinsa,wada farawarta aikin babu jimawa ya bayyana mata qudurinsa,saidai ko kadan ita bata dauki kalmar soyayya a bakin komai ba,face kalma mara ma'ana mara amfani a rayuwar mutum,kalmar da bata bata sha'awa kota burgeta,hasalima tana mata kallon azzalumar kalma mai cutar da duk wanda ya raɓa kanshi da ita.


Duk wani halin ko in kula da hannunka mai sanda bilkisu ta nunawa dr adam saboda ya shafa mata lafiya,ya barta ta rayu qalau cikin salama amma yayi funfurus,da fari ya dauka sonshi ne batayi,amma data gaya mishi ita bata taba soyayya bama saiya dauki tutsun da take masa ba'a bakin komai ba,yaci gaba da qoqarin kafa gwamnatinsa a wajenta,duk da yaji shakkun cewa da tayi bata taba soyayya ba,amma tunda daga bakinta yaji hakan,bashi da ikon musantawa,ya kauda kanshi daga duk wani zille zille nata,ya kafa dukka kayan aikinsa ,yaci alwashin saiya mallaketa a matsayin matar aurensa.


Tunda yake duniya bai taba ganin macen datayi masifar tafiya dashi ba,ta kuma kwanta mishi a rai irin bilkisun ba,ta hada dukkan wani abu da yake zata ga diya mace,harma ga wanda hankalinsa bai taba bashi mace kamar bilkisun zata mallaka ba,wata irin soyayya yake mata har cikin jininsa,hatta da mahaifiyarsa tasan da zaman soyayyar da yakewa bilkisu,yaci alwashin bazai sassauta ba har sai yaga abunda ya turewa buzu nadinsa.


Nannauyar ajiyar zuciya ya saki gami da murmushi kana ya sake hannayensa dake harde a qirjinsa tun daxun yana qare mata kallo,yayin da take zaune saman kujerarta tana ci gaba da duba wasu takaddu tana hadasu waje guda ba tare data dubeshi ba tunda ya shigo,ita ala dole bata ga shigowarsa ba,yasan kuma sarai ta gani,saidai shima yadda ta basar din yayi masa,tunda ko banza ya kalleta son ranshi,sai ya soma takowa zuwa bakin table din nata,yaja kujera ya zauna yana cewa cikin yaren nasara
"Kome kikayi kyau yake miki,kome kuma kikayi kin isa kiyishi"
"Assalamu alaikum warahmatullah" ta fada ba tare data dubeshi ba,saiya dan dafe bakinsa yana cewa
"Afwa,na sha'afa ne,kyakkyawar fuskarki ta shagaltar dani.....assalamu alaikum warahmtullah" a fakaice ta tabe baki kana ta amsa mishi ciki ciki,banu kaifi adam.din yana da dabi'u na gari,saidai hausawa sunce society da mutum ya rayu a ciki yana da matuqar tasiri cikin dabi'unsa da halayensa,dabi'unsa mafi yawa na turawa ne,wanda wasu abubuwan wajen cikakken bahaushe musulmi dan arewa abun kubya da qyamata ne,amma zaka samu su a wajensu ba komai bane,sabida tasirantuwa da sukayi da dabi'unsu,bare shi da aka haifeshi cikinsu,ya rayu dasu har yau kuma yake rayuwa a cikinsu,abubuwa da yawa na halyayyarsa tana cin gyaranshi akai,yana kuma gyarawar tare da qoqarin kiyayewa,don da wuya ya maimaita kuskure idan ta gyara mishi saboda zallar soyayyar da yakeyi mata,bata bashi dama ya sake cewa wani abu ba ta miqe tana riqe da wani file guda daya ta dubeshi
"Idan ka gama idan babu damuwa.....ka rufe min office din,zan fita round" fuskarshi babu alamun damuwa yace
"Me zanyi da office din da babu ke a ciki,wajenki nazo,ya kamata ko minti biyar a bani" saita gyara riqon takardun hannunta ta sake cewa
"Mubar aikin mu xauna hira kenan ko kuwa?"
"Da zakiyi hakan da nafi kowa murna" idanu ta dan fiddo,wanda hakan ya qara mata kyau a idanunsa
"Kafi kowa sanin cewa ba wannan nazo ba....sannan duk wani ganganci ko kuskure dazai faru a asibitinka,qasarka ba zata qyaleka ba zata hukuntaka ne,sannan waima.....shin ku turawa ba 'ance kunfi kowa kiyaye doka da qa'ida ba?" Dariya sosai yayi harta tsaya kallonshi,kana ya tsagaita ya bata amsa
"Baki fada dai dai ba,kin manta ni bahaushe ne dan nigeria?,kusan kullum saina gyara miki fa?" Kusan tunda ya soma sonta ya maida kanshi dan nigeria sosai,saboda yadda ya lura tana kishin qasarta,tana kuma yawan maganarta dason komawa can nan kusa,sabanin daa dabai damu ba,ka kirashi dan nigeria ko dan brasil duk daya ne a wajensa
"Banga alamu ba,tunda nidai a dan brasil na sanka...." Tana kaiwa nan qofar ta shaida mata akwai mutane dake tsaye a wajen,hakan ya nuna mata nurses din sun qaraso,don haka sai kawai tayi gaba abunta,batason ya sake tsaidata.
7/11/21, 4:33 PM - My Mtn Number: 48

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070





Tsayin wani lokaci tana round din tana duba dukan yaran da suke qarqashin kulawarta,cikin nishadi take komai gami da cikakkiyar qwarewa tare da kulawa ta musamman,lokaci daya Allah ya sanya mata son aikin nata duk da cewa a fari ba shine zabinta ba,amma a yanzun sai ya zama aiki mafi girma data fi so da qauna albarkacin yaran da take ceto rayuwarsu,hakanan Allah ya bata tarin farinjini wajen yaran,duk yaron data zama likitarsa saiya qaunaceta,babu banbancin yare kalar fata qasa ko addini,hakanan Allah yake sanya sabo da qauna tsakaninsu,don da yawa ma ko bayan sun bar asibitin sukanci gaba da hulda da ita da kuma zumunci.


Bayan ta gama dubasun ta soma ganin patient din nata suma cikin qwarewa da karsashi,ta samu sakewa don ba kasafai dr adam gake shigowa ba idan tana ganin marasa lafiya.


Ta dan dauki lokaci mai tsaho kafin ta gama dubasun,duk da cewa can din ba kamar qasarmu bane,babu cinkoson marasa lafiya da ake tilawa likitoci tarin aikin da yafi qarfinsu,saidai ita din qwarewarta ya sanya koda yaushe bata rabo da ganin marasa lafiya.


Ajiyar zuciya ta sauke tana duba agogon hannunta,lokacin dauko yara daga makaranta ya kusa,mintuna kadan suka rage,duk da cewa motar makaranta tana daukosu tun daga cikin makarantar har zuwa qofar gidajensu,amma yau ta musu alqawarin cewa zata zo da kanta ta daukesu,don lokacin tashinta yayi dai dai da lokacin tashinsu suma.


A nutse ta miqe ta soma warware rolling din kanta,idanunta nakan calender dake maqale a jikin bangon office din,tana lissafin kwanakin wata da kuma kwanakin da suka rage musu tafiya seminer din da aka turasu zuwa qasar dubai,ba kasafai ta fiya son irin wadan nan tafiye tafiyen ba saboda kare mutuncinta da kuma rage zargi a zukatan mutane,saidai duk sanda wani abu na samun qwarewa ya taso daga asibitin dr adam baya yin qasa a gwiwa wajen sanya sunanta a sahun farko farko,hakan na daya daga cikin mabudin nasararta,da kuma silar zamantowarta qwararriya kuma gogaggiya akan aikinta.


Gefe guda kuma tana samun dukkan wani qwarin gwiwa daga wajen anty zuhriyya da kuma abbaa,wanda batasan da wadanne kalmomi a kullum zata gode musu ba,hakanan batasan dame zata saka musu ba,sun bata dukkan wani taimako qwarin gwiwa da kuma goyon baya,har ta kawo matsayin da take kai a yanzun.


A nutse ta gama warware rolling din nata,kyakkyawan gashinta daya wadatu da gyara ya bayyana,yanata sheqi da fidda qamshi,ta nadeshi da band fari qal,ta zare agogon hannunta sannan ta shige bandaki ta daura alwala,wanda kusan sabonta ne,bayan ta fito ta ciro wani tattausan handkherchief wanda ke fidda wani qamshi mai sanyi ta goge ruwan jikinta,kana ta maida dukka nadinta da agogonta tsaf.


Lunch box din amatullah kawai ta dauka sai handbag dinta ta fita a office din,da saur i sauri ta wuce office din dr adam don kada ma ya fuskanci fitarta bare ya biyota,don tsaf zai iya shige maya mota yace sai sunje tare,abu na qarshe da tafi tsana kenan,don bata son yaranta su dinga ganinta da wani mutum na daban baquwar fuska,wanda hakan zai iya illawa tarbiyyarsu,hakanan batasan amsar da zata basu ba kan waye ne nasu,inda ma abun yazo mata da sauqi,duk da tarin wayo kaifin basira da fikira da Alla ya basu,Alla bai taba budar bakinsu sun tambayeta waye mahaifinsu ba,inda take godewa Allah kenan.


Sai data tada motar ta soma barin harabar asibitin sannan ta hangi dr adam ta madubin gaban motar,tsaye yake harde da hannayensa yana bin motar da kallo,hakan yayi mata dadi sosai,da alama yaso cimmata,saidai hakan bata samu ba,duk yadda akayi kuma aiki ya tsareshi ya manta actual lokacin tashinta ne sai daga baya ya farga,data tabbatar saiya mata katsalandan din daya saba mata.


Tun batayi nisa ba taji alamun shigowar saqo wayarta,bata raba dayan biyun shine,don haka ta share ba tare data duba ba taci gaba da tuqinta hankali kwance.


Minti ashirin da biyar kyawawa ta isa makarantar tasu,daga inda ake aje motoci tayi parking tana kallon yara nata ficewa zuwa motocin dake daukarsu zuwa gidanjensu,kusan dukkanin yaran yaran turawane masu jajayen fata,wasunsu 'yar qasar wasu kuma baqin haure kamar dai su.


Idanunta kan hanya har zuwa sanda ta hangi yaran suna nufota,kyawawan 'yan biyu masu masifar daukar hankali,duk da cewa ba jinsinsu daya ba wato mace ne da namiji amma kuma kamanninsu daya,kai daga gani basai an gaya maka ba kasan cewa 'yan biyu ne irin identical din nan,wadanda da ace jinsu guda n zaiyi wuya adinga banbance hassan da usaini ko hassana da usaina,sai Allah ya taqaita ya yosu jinsin daban daban.


Kallonsu take sosai kamar bata sansu ba,kallonsu take tana jin wata qaunar yaran nata tana ratsata,tanajin wata soyayya ta musamman dake tsakanin uwa da 'ya'yanta.


Murmushi ya subuce mata ita daya sanda taga sun tsaya sun danyi magana tsakaninsu,abdulrahman dake a mazaunin hassan ya hade rai yayo gaba abinsa,sau tari takan zauna ta jima ta kuma bata lokaci tana lalube tare da binciken dawa suke kama?,kaf danginta uwa da uba basu dauki kamar kowa ba,hakanan halaye da dabi'un abdur rahman sau tari suna bata mamaki,wata dabi'a ta daban kai kace babban mutum ne,dukkan tunani da hasashenta kan yanke ya kuma qare da bacin rai idan zuciyarta ta gaya mata
"Wala'alla dangin mahaifinsa ya dauko a kama,haka halayya da dabi'un ma" takan miqe cikin bacin rai kamar da wani take maganar,a sarari kuma ba'a boye ba ta furta
"Allah ya tsare,ya kiyashi 'ya'ya na"


Abdur rahman ne ya soma isowa,ta dubeshi fuskarta har yanzu dauke da murmushi
"Sarkin miskilanci sarkin fushi,me kuma akayi?" Ta fadi sanda yake shigowa sit din kusa da ita
"Abokina ne yace wai bamu da daddy...tunda bai taba ganin daddynmu ba,shi kuwa nashi daddyn ne yake kawoshi makaranta kullum,shine yace zai bamu daddynsu,amatu tace eh muna so" wani abu mai nauyi ne ya sauka a qirjinta,wanda har yayi tasiri wajen hanata cewa komai,a haka har amatu ta qaraso ta bude gidan baya ta shiga ta rufe,saita gaza cewa da yaron komai har zuwa sanda ta tashi motar,tana jin lokacin da amatu tayi hugging dinta tana murnar xuwa daukarsu da tayi,amma ta gaza waiwayawa ta dubeta ko tace wani abu,haka taci gaba da yin shuru,tana jin yaran na sabgarsu sama sama.


Wato komai nisan jifa qasa zai fado,sannu sannu ranar da take murnar bata zo ba takeson riskarta,wacce amsa ce zata dace da tarin tambayoyinsu da zasu ci gaba da zuwa mata dasu anan gaba kadan?,tunda koda yaushe wayo suke dada yi.


A hankali ta waiwaya tana duban sashen da abdurrahman yake xaune da litattafansa saman cinyarsa,saita lura da wata babbar takarda daya wareta yana kallo,ta sake duba karo na biyu,hoton wannan business tycoon din ne,wanda yayi wani irin shuhura da shahara a fadin duniya,qasashe iri daban daban,zata iya cewa a shekara gudan nan taga hotunanshi taji labarinsa babu adadi,saidai a duk sanda idanunta zasuga hotonshi saita hadu da wata mummunar faduwar gaba da fargaba da batasan dalili ba,wala'alla hakan baya rasa nasana da sunan da yake amfani dashi daya danganci sarauta,wadda batasan ta wacce qasa yanki ko nahiya bace *A M YARIMA*.


Tun abinda ya faru a wancan qarnin ta tsani duk wani abu da xai danganci sarauta,ko zai fito shafi sarauta,kama daga suna sutura da sauransu,hakan ya sanya take zaton dalilin faduwar gabanta kenan,harma ta soma tsanar ganin hotunan,wanda koda bata gansu a poster ba,takan ci karo dasu lokaci zuwa lokaci matuqar zata kalli labaran duniya a kowacce tasha,kuma zasu sako labaran kasuwanci,to abune mawuyaci suyi su qare basu sako shi ba
"Ina ka samu wannan hoton?" Ta tambayi abdul tana maida kanta ga tuqin da takeyi
"Uncle ne ya bani....mami...inason xama irin wannan mutumin idan na girma,uncle ya gayamin jajirtacce ne,inason na zama jajirtacce kamarsa" murmushi kawai tayi ganin yadda yake bayanin bilhaqqi daga zuciyarsa kamar wani babban mutum,ba tare data dubeshi ba ta sanya hannunta saman kanshi,ta shafi sumarsa sannan tace
"Allan yayi maka albarka,ina fatan ka fishi komai da komai,bakasan wayeshi ba,kullum kace kanason ka fishi ne ta hanyoyin alkhairinsa kaji?" Kai y gyada mata yana ci gaba da duban hoton daya bude din,da alama yana ji da takardar.


Sanda suka isa gida yaran sun rigata fita,kasancewar ta tsaya tattara duk abinda suka bari nasu a motar,ta gama ta fito tana shirin kulle motar ta hangi amatu datayi gaba kanta sanye da crown a kanta irin na yara.


Hakanan gabanta yayi mummunar faduwa,da hanzari ta gama rufe motar ta rufa mata baya,cikin taku qalilan ta cimmata sanda take dab da shiga falon gidan,ta jawota tana cire abun daga kanta,cikin fada ta soma magana
"Wannan abun fa daga ina?,ina kika samoshi?" A narke take duban ummin nata ganin yadda take fada tace
"Qawata ce ta bani" hakanan taji ranta yana baci ganinta da abun,ta zazzaro idanu tana dubanta
"Ashe baki da hankali amatu?,roqo kika koyo?,meye hadinki da wannan abun da zata baki shi?" Saita maqale kafada idanunta na cikowa da qwalla
"Ina sonshi mommy,yana bani sha'awa,shine tace tana dasu da yawa na birthday dinta,saita bani daya" wurgi bilkisu tayi da abun yana tuna mata wani abu,tana jin kamar masarautar kaisa ce a jikin abun,kamar ta bishi ta tattakeshi,ta maida dubanta ga amatu data fara qwalla,tana bin abun da idanu tana jin kamar taje ta dauko abunta
"Gargadi na qarshe zan miki,karki sake na sake ganinki dashi,bama shi ba,karna kuma ganin kin karbi wani abu daga hannun wani,idan ba haka ba saina yanka hannuwanki,kina jina?" Ta fada a tsawace tana dan murda kunneta,da sauri ta daga kai tana dafe kunnun nata da hannunta,hawaye yana sauko mata,sai kuma taji tausayinta ya ratsata,ta sakar mata kunnen tana cewa
"Oya...ku wuce ciki" dukka suka shige din da hanzari,ta maida dubanta inda tayi wurgi da abin na wasu sakanni sannna ta dauke kanta da zummar bin bayansu zuwa ciki itama,sai a sannan ta lura anty zuhriyya tana tsaye ashe tana kallon duk abinda ke faruwa,da suka hada ido saita dauke kai kawai ta matsa mata ta shige zuwa ciki.



A dakinta ta taddasu zaune babu wanda ya cire unifoarm dinsa bare yayi wanka koya sauya wasu kayan,tana shiga dukkansu suka taso suka rungumeta,amatu na kuka sai abdulrahman ne yace
"Kiyi haquri ummi,ba zata sake ba" wani irin tausayi da qaunarsu ta sake ratsata,wani irin so yaran suke mata,basason ganin bacin ranta ko yaya yake,yanzun zasu kasa sukuni gaba daya su addabi

Please Login or Register in order to submit comment