Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.

Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.

______________________




Duk taku daya da zatayi na kusantar dakinsa sai taji wani matsananciyar faduwar gaba ta sameta,karon farko a rayuwarta tunda tafara irin wannan harkar data taba samun haka,sanda ta isa qofar dakin tsaiwa tayi cak bayan ta dora hannunta a handle na qofar,tanajin yadda zuciyarta ke bugawa sosai,ta lumshe idanunta tana son baiwa kanta qwarin gwiwa gamida hasashen nasara,kana tatura qofar cikin sauri kawai tashige.


Daga can sashen kamal yasaki ajiyar zuciya sanda minal ta bayyana cikin dakin,yana sake gyara zamanshi sosai tare da sake saita komai tare da bada hankalinsa gaba daya.


Yaji bude qofar amma bai damu yadago ba,saboda yana zato da tsammanin daya daga cikinsu mustpha ne yadawo,baiso kuma kowa ya fahimci yanayin da yake ciki,infact ma baison takura,baisan ya akayi ya manya bai rufe dakin da muqulli ba.


Tsaiwa tayi tana dan qarewa dakin kallo,yadda ya hadu haka komai nashi yake hadadde,yadda ya tsaru haka komai nashi yaje a tsare,yadda yake maikyau haka komai nashi yake me kyau,ta sake gasgata yarima azeez din na dabanne,saita sauya shawara,gwara tayi maaa shigar gaba daya,tana da yaqinin a yadda taga jikinsa na wani irin rawa bazaiqi karbarta ba,hakan shiya baiwa minal damar soma raba jikinta da duk wata sutura data shigo da ita,kana ahankali tasoma takawa zuwa gadon da yake zaune akai.


Kamar a mafarki yasoma yin wasu abubuwa da suka sake birkitashi,cikin qanqanin lokaci tasoma cin galaba akanshi,wani irin bugu zuciyarsa take masa kamar zata tsaga qirjinsa tafito,yana kallonta,yana kuma son hanata amma ya gaza,abinda yake ji cikin jikinsa yanason yafi qarfinsa,tsahon wasu mintuna tana neman qarasa gusar mishi da hankali don tacimma burinta dana kamal,tamkar qiftawar idanu taji an harbota daga saman gadon zuwa tiles din dake shimfide qasan dakin
"Hasbiyallahu la'ilaha illa huwa,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim" daya soma fadi tundaga zuciyarsa harta fito saman bakinsa yaci gaba da maimaitawa muraran a fili,ya rarrafa yasauko daga saman gadon yanaci gaba da maimaita addu'ar.


"Kut!" Kamal dake jiran komai yasoma wakana yafara recording yafada yana miqewa zumbur daga kashingidar da yayi zuwa zama dafa'an,cike da mamakin ta yaya yayi escaping?,duk wata jijiya ta jikinsa sai data tsinke,ya hade hannayensa yana murza tafin hannayen nasa waje daya.


zuciyarsa na wani irin tafasa,bacin rai yafito mishi muraran saman fuskarshi,kauda kanshi yayi sam ba tare daya dubeta ba tunda ya fuskanci babu suttura a jikinta,saiya sanya qafa ya tura mata kayanta,cikin rawar jiki dakuma tsoron yanayin da taga fuskarshi ta koma tasoma maida sutturarta,tana gamawa tasoma laluben qofar fita,tsawa ya daka mata mai qarfi
"Wacece ke?,daga ina kike?,ta yaya kika iya shigowa har inda nake?" Cak ta tsaya numfashin tsoro na fita da gudu daga qirjinta,lallai duk a baya yunqurin banza tayi tunda baima gane wacece ita ba,wani gumi ya karyo mata sanda taji yana takowa inda take tsaye saita kasa waiwayowa.


Hannu ya sanya kamar zai shaqeta saiya fasa,yakuma fasa mata wata tsawar data sanya gumi yanko mata,daidai lokacin da mararsa tariqe saiya duqa riqe da marar tasa,da wannan damar tayi amfani tayi wuf ta bude qofar tafice kamar zataci da baka.


Bai kuma bi ta kanta ba saboda yanayin dayake ciki,yaja jikinsa daqyar yaisa inda yake aje magungunanshi ya lalubosu,qara yawansu yayi akan qa'idar yadda akesha,saboda a yanayin da yake ciki baya jin idan yabi qa'idarsu ba zasuyi masa aiki ba.


Minti biyu yaji kamar baisha komai ba,saiya sake jawo satches din yakuma ballan adadin na dazu yasake sha,cikin gaggawa dason tsaida halin da yake ciki ba tare da yasan silar shan wani abu bane yasa yatsinci kansa a yanayin ba,yadinga ballar maganin cikin fitar hayyaci yana sha har suka danganashi da ficewa daga hayyacinsa gaba daya,bai iya gane waye kusa dashi ko abinda ke faruwa a inda yake ba.


Tun lokacin da kamal ya fuskanci abu ya kwabe yayi hanzarin tattara laptop dinsa yafice daga falon kada azeez yafito ya taddashi,don haka sanda minal tafito bata taddashi ba,itama bata wannan take ba,don haka bata tsaya nemanshi ba tafice itama tatari taxi tafada sai gida.


Sai daya bada minti ashirin qwarara yasake dawowa cikin gidan,jin shuru babu alamu ko motsin azeez yasa yanufi dakinsa,sosai ya rikice ganinsa cikin wannan yanayin,ba ranshi suke so ba,sunanshi suke so su bata,darajarshi da matsayinsa kadai sukeso su amsa,cikin rudewa yakira number asibiti mafi kusa dasu,babu bata lokaci suka iso da motar asibiti suka daukeshi.

*****************


Madaidaicin filine na musamman daga wanu sashe na sasasanta wanda aka qawatashi da abubuwan daukan hankali da more rayuwa iri daban daban saboda hutawar fulani aisha.


Kamar yawanci lokuta haka yauma,tana kashingide cikin filin saman wani tattausan kilishi wanda aka zagayeshi aka kuma qawatashi da wasu irin manya da qananun filalluka wadanda ke dauke da zane da tambarin gidan sarautar kaisa,daga dama da hagunta kuwa barorinta ne wadanda suke amintattu a wajenta,wanda sukan zauna lokaci lokaci ayi hira sukuma bata labarai dakan debe mata kewa.


Yauma hakance ta kasance,shugabar zaman wadda koda yaushe baka rabata da labarai a bakinta umma luba ce,murmushi kawai fulani aisha ke fitarwa,da alamu labarin da umma lubar take bata ya qayatar da ita matuqa.


Daya daga cikin wayoyinta dake aje gabanta suka dauki qara,daya daga cikin barorinta data fi kusa da ita ta miqa hannu ta dauko kana ta rusuna cikin girmamawa tamiqa mata,hannu tasaka ta amsa tana duba mai kiran,abdulrashid ne,dan waziri musa adamu,hakanan tasamu kanta da miqewa tazauna sosai,barorinta suka dau kirari
"Allah ya taimaki uwar yarima,magajin maimartaba qwaya daya tilo" hannu ta daga musu alamun tana buqatar shirunsu,ta kara wayar a kunnenta bayan ta daga.


"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" fulani aysha tafada tana miqewa tsaye kamar wadda aka tsirawa allura,take suma dukka sauran barorin suka miqe suka tsaitsaya,donsu tabbatar tunda sukaga haka sun tabbata babu lafiya
"Allah yayi miki jagora yakula da lamarinki" umma luba tafada cikin nuna tsantsar kulawa da damuwa,saita sauke wayar daga kunneta tanajin zafi yana ratsata duk da iskar dake kadawa a wajen,a hankali takoma tana zama a inda tatashi bakinta yana furta
"Ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagisu"
"Amin ya Allah.....amin" suka kusan hada baki wajen fadar haka.


Shuru ya ratsa wajen na wasu mintuna kanta a qasa tana maimaita maganar da abdulrashid ya gaya mata,shudewar wasu mintuna kana ta daga kanta a hankali tace
"Ina laure?...." Da hanzari ta matso tana zubewa a gabanta
"Gani ranki shi dade..."
"Ki gaggauta zuwa ki shaidawa jakadiyar mai martaba,a shaidawa maimartaba,akuma yimin iso inason ganinsa da gaggawa yanxu yanzu"
"An gama ranki ya dade....Allah ya huci zuciyarki" tafada tana miqewa da matuqar hanzari tasauka daga wajen tayi dan nesa kadan tadauki takalmanta tabace daga filin.


Shurune yaci gaba da wanzuwa a wajen,kowa yashiga cikin nutsuwa da taitayinsa,umma luba ta matso gefanta,cikin salo da dabara tasoma magana cikin kalaman kwantar da hankali da sanya nutsuwa
"Na gode" fulani ta ambata tana dagawa umma luba hannu,da alamu taji dadin furucinta,saidai a yanayin datake ciki bata buqatar dogon xance.


*_fulani adama_*



A daidai wannan lokacin daga can cikin quryar dakin gadon wanda babu mai shiga ciki sai ahalinta ko yaran cikinta,a lokacin da take yunqurin amsa kiran koda gittawar tsuntsu bata amincewa barorinta abarshi yawuce ba bare bil'adama.


Kirane daga qanwar maimartaba mahaifiyar kamal fauziyya mu'az kaisa,qaramin murmushi fulani adama tasaki,tun jiya taje jira taji daga gareta,kuma jikinta yana bata aiki yayi nasara,wanda indai hakan tafaru rabi cikin burinkanta sun soma cika,a duniya babu wadda ta tsare mata gaba da baya irin aisha da dukka abinda suka fito daga tsatsonta,har yaranta mata gani take suna samun soyayya daga wajen maimartaba fiye da nasu yaran
"Ya ake ciki?,ina fatan komai ya kammala" ta tambaya muryarta na nuna tsantsar jin dadi
"Inafa!,komai yana shirin kwabewa,yanzu haka yarima yana kwance gadon asibiti unconsciouse" tsaki taja tana jin sam wannan bai dameta ba,inda zai mutu ma salin alin da tafi kowa farinciki a duniya
"Ba wannan bane ya dameni,an samu nasara?"
"Ta ina fulani?,ya tsallake duk wani tarko" take fuskarta ta sauya,bacin rai ya mamaye zuciyarta,ta yaya?,wannan wanne irin yaro ne,dogon tsaki taja takatse wayar kawai ba tare data iya sake furta komai ba,saita kasa zama,tahau safa da marwa cikin dakin tanason baiwa kanta damar yin tunanin abinda yadace tayi.


"Allah ya taimakeki,Allah yabaki yawan rai,zaishiga sallar la'asar,idan yafito ki taddashi a sassansa" miqewa tayi ba tare data ce komai ba,tanajin ba zata iya zama a nata sassan ba har zuwa sanda zaiyi sallar yafito.


Daga nan bata sake tsayawa ba saidata dangana da ainihin bedroom dinta,ta canza shigarta,cikin qaramin lokaci tafito a fulaninta sak,ta wani sashen kuma gimbiya diya ga sarkin mali,a gaggauce tafito tabaro sashen nata zuwa sassan maimartaba qarqashin rakiyar mutum uku rak,suma suna zuwa wani shinge da babu mai shiga sai iyalan nasa suka juya suka koma suka barta.


Kasa zama tayi cikin tashin hankali take kaiwa tana kawowa,ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta qasar mexico,hankalinta a tashe yake qwarai,tana tsoron wani mummunan abun yasamu abdul'azeez din,abdulrashid yaqi mata cikakken bayani bare ta fahimci silar ciwon nashi.


Tana jin takun shigowar maimartaba tayi hanzarin juyowa tana dubanshi,itama shi take kallo,dukkanin rauninta ya bayyana,har kamar idanunta ma sun tara ruwan hawaye,duk da basu kai ga zubowa ba.


Yasan meke faruwa,hakanan yasan rauninta,dukkanin rauninta abdul'azeez ne,bata iya jurewa idan wani abu ya sameshi,saita nufeshi da sassarfa kuka yanason qwace mata,ganin haka shima yaqara sauri yatareta,tafada jikinsa saita saki kuka mara sauti,bayanta yake shafawa a hankali cikin sigar lallashi ba tare da yace komai ba,tsawon wasu daqiqu sannan yace
"Duka ina jarumatar dana sanki da ita ayusher?,ummm..." Muryarta can qasa saidai duk da haka zaka fuskanci tana kuka ne tace
"Ina tsoron ko wani keson cutar min dashi ranka yadade,bisa alamu azeez baida lafiya sosai" saiya dagata daga jikinsa yana duban fuskarta gamida girgixa mata kai
"Um um,ko kadan aysha,nace kidaina kawo ire iren wadan nan tunanin a ranki kan abdul'azeez,yanzu dubi fuskarki....sam.hawaye bai dace da fuskar saraki irinki ba" dole yanayin yadda yayi maganar ya sanya murmushi yakubce mata,kai kace ba shine qasaitaccen sarkin nan bane ma'abocin kwarjini da izza,sai tasa tafin hannunta tana share hawayen daya bata mata fuskar,kana yajata saman daya daga cikin kujerun ya zaunar da ita
"Yanzu me kikeso ayi uwar abdul'azeez?"murmushin yasake kubce mata karo na biyu,yasan takanta sosai,saita duqar da kanta tana murmushi ba tare datace komai ba
"Anaso aje wajen yarima azeez aga halin da yake ciki ko?" Ya bata amsar tambayar da kanshi yana dage gira,kaita jijjiga da hanzari harsai da murmushin shima yakubce masa
"Ki shirya gobe ku wuce keda duk wanda kika zaba" hannayensa ta kama cikin murna tariqe qam
"Na gode your royal highness....Allah yaqara girma,yajiqan magabata" cikin lumshe idanu dajin dadin addu'arta yace
"Ameen"
"Sai alfarma daya da nakeso ayimin" tafada tana wasa da hannunshi da har yanzu bata saka ba
"Uhmm,inajinki" shuru tadanyi na wasu sakanni sannan tace
"Inason maganar rashin lafiyan azeez yazama asirtaccen zance Allah ya taimakeka ina neman alfarma" shuru yayi nawasu sakkani yana kallonta murmushi nafita saman fuskarshi ba tare data sani ba saboda idanunta suna qasa,yadade da sanin nata yarda da kowa ba indai akan Abdul'azeez ne
"Wai...dani da abdul'azeez wa akafi sone" da sauri ta daga kai tana ware idanu,dariya nason qwace mata,saiya ci gaba da kallonta yana cewa
"Yes,inaso inji" hannu tasa kamar zata rufe bakinta saita fasa tasoma magana
"Kaine maqyanqyshin abdul'azeez fa,kaga dole taka soyayyar ta dara tashi,albarkacin soyayyarka shi kansa yake ci" murmushi ya fidda,aysha badai iya nunawa miji qauna ba
"Um um....kadda nasaki jiki fa,ki gadi gaskiya anya abun cikin qwai baifi qwan dadi ba" kanta tadora saman kafadarsa tana dariya
"Ko kadan qwan gaba dayanshi yafi dadi" ana tsaka da wannan aka nemi izinin shigowa falon da suke,yasan koma waye wanda yashafi iyalinsa ne don haka yabada izinin shigowar.


Fulani saratu ce,cikin shiga ta alfarma ita dinma,amma haske aysha saiya dusashe fiye da nata rabin adon,ganin aysha a wajen saita tsuke fuska ta qarasa shigowa da sallama,daga shi har ayshan kowa na mazauninsa daban saboda jin anason shigowa,ya amsa sallamar yana marabtarta kamar yadda yasaba yima matanshi,ta amsa masa amma sam fuskarta babu wani walwala ko fara'a,abu daya ne dataji dadi shine tadda aishan datayi a wajen,hakan yayi mata daidai,zatayi maganganunta son ranta,tunda dama ganawar ta nemi yinta ne saboda yaron aishan
"Magana nazo muyi dakai Allah ya taimakeka"
"Ina saurarenki saratu,Allah yasa lafiya".


Gyara zamanta tayi tana sake hade fuskarta,kana a fakaice ta watsawa aisha harara wadda batama san tanayi ba
"A gafarceni ranka yadade,magana ta gaskiya ce nazo na gaya maka,duk da hausawa sunce daci gareta,tuba nake ranka ya dade kan maganar walida ce..." Saita danyi shuru tana maida numfashi,yayin dashi kuma yaci gaba da kallonta dakuma saurarenta ba tare daya ce komai ba
"Da yarana,dana adama dana aisha ina tsammani dukkansu Æ´aÆ´anka ne,hakanan kowanne yana da haqqi akanka,koda wanne irin jinsine,bayan haqqi da suke dashi suna buqatar a daidaita su dayi musu adalci kan komai a cikin gidan nan....zancan tafiyarta makaranta,ranka yadade da farko baka wani tsaurara ba kace zaka yi tunani da shawara,amma tunda abdul'azeez yazo yatafi kace fau fau babu wadda zatabar qasar kaisa da maqotanta tafita a nijeria zuwa baquwar qasa karatu,Allah yabaka yawan rai,caa nake shi wanda aka nema shawarar yabayar a yanzu haka zancan da mukeyi baya qasar nan,sai daya zaba qasar da yakeso sannan yatafi,a irin wannan ranka yadade yaran zasu dinga ganin kamar ba'a musu adalci saboda su yara matane,idan batun jinsine babu jinsin da bazai lalace ba idan yaso,shi kansa akasan me yakeyi a can din......" Da sauri aysha tamiqe jin tazo inda ba zata iya jurewa ba,kuma batason sanya baki cikin maganar ko digo saboda girmamawa gashi maimartaba,don haka tasoma takawa zata fice daidai sanda sarki abdallah ya dagawa saratu hannu yana dakatar da ita,bataji me yake ce mata ba itadai ta sanya kai tayi gaba abinta.


Tana tafe a hanya tana mamakin abinda ta tsarema matan,ta tabbata banda kariyar Allah,da kaifin wayo da basira da Allah yabata da tuni sun gama batar da ita itada irinta a tarihin masarautar kaisa,tasan tana takatsantsan da bata duk wani shirinsu sun sani ko basu sani ba,amma ko sau daya bata taba yarda ta jefi yaransu da wata mummunar kalma ta batanci ba,tunda tasan duk inda za'aje azo yayyene ga nata yaran,kuma jinin abdallanta ne.


A ranar tagama tsara komai na tafiyarta,takuma zabi mutanen da zatayi tafiyar dasu,ta basu umarnin kowa yashirya,don a sassanta duk wanda zasuyi tafiyar zasu kwana,duk da amintattunta ne bata yarda su kwana akowanne guri ba sai a nan,cikin murna da zumudi kowanne yasoma shirinsa a sirrance ba tare da kowa yasan meke faruwa ba bare susan inda za'a din.


**************


"Alhamdulillah" bilkisu ta fada tana sauke ajiyar zuciya lokacin data shiga soron gidan nasu,don bata tsammaci zata ita kawo kanta gida ba daga makaranta,duba da irin doguwar tafiya da tazarar dake tsakanin gidan nasu da makarantar saboda azababbiyar yunwar dake sakadar cikinta,wanda rabonta da abinci tun daren jiya wanda shima wanda tasamo ne daga gidan umma luba suna yanyana sukaci ita da qannen nata.


Sosai ta ware hancinta tashaqi qamshin soyayyar miyar dake tashi har soron gidan nasu,wanda kanaji ko ba'a gaya maka ba ta wadatu da nama,qamshin na shiga har cikin hanjinta taja qafafunta ta shige tsakar gidansu.


Sauka idanunta sukayi kan varender dake qofar dakin amaryar baban nasu wadda ake kira da jummai,itace zaune kan kujera 'yar tsuguno,tasha kwalliya da wata atamfa tata koriya shar,fuskar nan tasha jar hoda da jan jambaki wanda ada ake kira da kanta kile,idanun nan badau da kwalli ga jagira data ja layi daya a kan gashin girarta,idan gidan karuwai kashigo saika rantse magajiyar karuwai ce,gabanta rishonta ne tanata juya miyar data budade hancin kowa dake cikin gidan.


Dagakai tayi tana duban bilkisu ba tare data amsa sallamar da takeyi ba,zata iya cewa tun zuwanta gidan babu wani abu qwaqwqwara daya taba hadata da ita,tundai ita bilkisun ba mazauniyar gida bace,koda ace mazauniyar ce sam bata da kwarafniya,saika wuni a gidan bakaji muryarta ba,koda kajinma to fada takewa qannenta kan wani abu da sukayi wanda ba dai dai ba,saika taka mata ka zubar mata bata daga kai ta kalleka ba bare ta nuna damuwarta,duk da ta tsani raini da wulaqanci abu biyu da ba kasafai take iya juresu ba,hakan yasa takan qauracewa sabgar jama'a ainun sai idan ta kama.


Sai data leqa rumfar umma katti tashaida mata ta dawo yadda tasaba,duk da cewa ba wani magana mai dadi take gaya mata ba,wani lokacima takan hantareta ne kota jefeta da baqar magana
"Ke da'alla can,naji kin dawo saime?,wata uwar kike tsinanamin da zaki damweni dakin dawo?,'yar wahala wadda kullum take qarewa a gantalin neman boko,bokon da nake da yaqinin bazai tsinana miki komai ba,idan kinso in kika tafi makarantar karki dawo,amiki daki acan,ina nan ina fama da baqincikin ubanku daci dakai da tufatar dakai amma kin dameni da wani umma nadawo,mtseeww" haka take balbaleta da masifa dakuma mita duk sanda 'yan wulaqancin ke kusa,ko kuma wani abu ya hadosu da babansu,itakam takan cika da mamaki a kullu yaumin,yau koda ace umma kattin bata zauna da mahaifiyarta sunsan juna ba bai kyautu tadinga mata haka ba,ta tsammaci yadda suka zauna da mahaifiyarta takuma yi haquri da ita itadin me riqeta ce?,bata mantawa sanda mahaifiyarta keda rai,yaran babansu da iyayensu suka fita suka barsu sun kusa biyar a sannan,mamanta itake musu komai cikin kudin da ake aiko mata daga gidansu,yadda take kula da bilkisu haka take kula dasu,bata barsu sunyi kukan rashin komai ba harsai data koma ga mahaliccinta,shi yasa har yanzu duk da basa zaune qarqashin mahaifinsu duk wanda Allah yakawo gidan zai mata alkhairi komai qanqantarsa,saboda tunawa da abinda mahaifiyarta maimunatu tayi musu.

Babu wanda yatankawa wani tsakaninta da lami bayab sallamar datayi har bilkisun tawuce dakinsu,dakin babu kowa yadda ta tsammata sun wuce islamiyya,ta soma rarraba idanu tanason taga me sukaci,data daga kwanukansu saitaga burbushin garin kwaki,aje kwanukan tayi tasaki ajiyar zuciya,duk da tasan shita bar musu tayi tunanin basuci ba sun aje mata,tunda idan suka fuskanci bataci abinci ba saisuqi ci su aje mata su su haqura.


Tana fidda kayan makarantar tana tunanin kudin extra lesson da za'a soma yi musu saboda shirye shiryen zana jarabawar waec da neco,komai da zata buqata an riga da an biya amma babu kudin extra lesson,wanda tasan cewa anty zuhriyya batasan zai taso ba,da babu shakka saita bayar,wasu qwalla masu dumi suka taru a idanunta,wanda bata iya dannesu kulli yaumin idan tatuna da qanwar mahaifiyartata wadda ita ta maye mata gurbin mahaifiya,kullum tatashi daga shimfidarta da safe tana tashi ne da begenta,haka nan tana kwanciya ne da tsananin kewarta da burin ganin shekarun sun cika ta dawo zuwa gareta.


Hakanan jiki a sanyaye ta daura zani tafita ta watsa ruwa,tadawo ta shirya duk da yadda yunwa ke sassaqarta,amma dole taje gidan aikinta.



*_Shin kina ko kana sa sha'awar koyon ilimin ICT?_*

*_Ko kuna da sha'awar yadda ake hada cartoon?_*

*_Ko kana da sha'awar yadda zaka bunqasa kasuwancinka ta hanyar online?_*

*_Matsalarki ko matsalarka rashin makarantun da zasu koyar dake/kai ilimin computer ta fannnin larabci?_*

*ALBISHIRINKU KANAWA*

*_Kukanku ya qare,matsalarku tazo qarshe,shahararren kantin nan na yanar gizo wato RAHAMALLS yazo muku da makarantar koyon sarrafa computer a sauqaqe wato RAHA COMPUTER INSTITUTE(RACI)_*


_Sun tanadarmuku qwararrun malamai wanda zasu koyar daku bisa tsarin da kuma cikakkiyar qwarewa ta yadda zaki fahimta fiye da yadda kuke zato_



*ga masu buqatar aji na musamman har cikin gidajensu,makarantar ta shirya tsaf don baku darussa har cikin gida*

*sannan akwai tsarin ajujuwa na musamman bisa yanar gizo wato(online classes)*

*kaidai maza garxaya ka tuntubesu akan wanannan lambar waya*

08033990209


*_akwai ragin kaso hamsin cikin dari na kudin registration ga kowanne dalibi_*👌ðŸ½ðŸ‘ŒðŸ½ðŸ‘ŒðŸ½ðŸ‘ŒðŸ½ðŸ‘ŒðŸ½ðŸ‘ŒðŸ½
7/11/21, 4:31 PM - My Mtn Number: *S R B*

*_wannan littafin na kudine,kuma amanace a hannun duk wanda yasiya,gamai buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadan nan lambobin kai tsaye_*

0903 234 5899
Ko
09033181070


15



Har zata fice taga alamun baban nata yana dakin amaryartashi,wanda dama yawancin lokuta anan yake wuni abinsa akwance,sai yamma zuwa dare zai fita nemo mata na cefanen gobe,don sudin tamkar masu haya a gidan suke,wadanda babu wani haqqinsu dake rataye saman wuyanshi,bai damu da cinsu shansu suturarsu ko lafiyarsu ba,yabasu muhallin zama ne kawai,wanda shima yakan yanka lokaci zuwa lokaci duk sanda yatashi wani zarafi na aurensa.


Shawartarta zuciyarta tayi,yaudau karon farko a rayuwarta,lokaci na farko tunda tayi wayo tsakaninta da mahaifinta,ta waiwaya ta duqa gabanshi ta roqeshi ya mata wata hidima qwaya daya cikin rayuwarta mana,takai minti goma tana shawara da zuciyarta daga qarshe tayi qundun bala takoma tataka zuwa varender da tunda aka ginata bata taba koda gogar gininta bare akai ga takawa.


Bakin qofar dakin ta tsaya tayi sallama a nutse,yana daga ciki tajishi yana amsawa
"Waye ne?,waye a nan?" Yasake fada
"Bilkisu ce" ta amsa a sanyaye,tanajin alamun tashinsa daga kwanciya da alama akwance yake
"Mai gado,shigo mana,yaukin gama baqin ran naki kenan zaki shigo kiga dakin uwartaki" yafada yana kakkabe shimfidarsa,batabi ta wannan ba tacire takalmanta dasukayi qasa sosai saboda dadewa dakuma tafiya tasanya kai falon.


Yana zaune saman kujerar da aka qarawa laushi da bargo,yayin da lami ke zaune gefansa tana kallon bilkisun harta shigo,kai tsaye ta isa gabanshi ta duqa tana gaidashi ya amsa yana jiran jin me zatace,cikin sanyinta da nutsuwarta tace
"Baba....zuwa nayi na roqi alfarma wajenka,karatunmu yazo gangara,zamu zana jarrabobi guda biyu,to kowacce tana da muhimmanci wajen dalibi,hakan yasanya aka ware mana lokaci daban wanda za'a dinga mana wani karatun bayan wanda muke a marantar,to akwai kudi da kowanne dalibi zai bada saboda malamai zasu dauko qwararru wadanda zasu dinga mana wannan karatun,za'a dinga biyansu ne...." Saita tsagaita tana tunanin qarasa gaya mishin,zamansa yagyara yana washe baki
"To yanzu cewa akayi nazo za'a daukeni kenan nima a dinga biyana?" Da mamaki ta daga kai ta dubeshi,amma saita sadda kai tana girgiza kai
"A'ah,cikin kudaden da anty zuhriyya tabiya babu kudin wannan,shine nace don Allah ko zaka taimaka ka biyamin".


Tsaf ya hade girarsa yana dubanta
"Kai,amma maigado bansan baki imani ba saiyau,yanzu don Allah keda kike fita aiki kullum yaumin nida kowa yasan kasuwanci yanzu ya durqushe sai lahaula wala qawwata illa billah nizaki duba kice nabaki wasu kudade?,yo aini da kikayi sallama na zaci anmiki albashi kika dubi halin da nake ciki kikazo kibani wani abu a ciki nima,gaskiya maigado kin bani mamaki,hankalinki ashe a qauri yake....to bari na gaya miki zance na gaskiya,ni yanzu bana maganin kome,kinganta nan lami baiwar Allah couse couse takeson ci amma haka na bata haquri shinkafa take dafawa yanzu....shawarar dazan baki idan kin samu ki biya,idan bakisamu ba ki tattara ki haqura da karatun,dama ni ya isheni" tabe baki lami tayi tana dora qafarta daya kan daya
"Uhmmm....ni bilya ma baikenka nagani,kana da zuqeqiyar yarinya kamar wannan amma ka sakata a gaba kanata ciyar da ita babu gaira babu dalili,tun farko aida kudin makarantar ka karba kayi mata kayan daki kasamu wani mai damshi damshin ka aurawa,qila da tuni yanzu yanzu ya biya maka hajji ana kiranka da

Please Login or Register in order to submit comment