Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abincin da yakeso,baya son qazanta ko kadan,shi yasa zakiga kamar baicin abinci,yana da zabi,ba kowanne yake ci ba"dukkaninsu babu wanda yalura da yanayin da bilkisu ke ciki ba.


Hannayenta ta zare daga cikin flour sannan ta yayibi after dinta da dankwalinta,tanason fita tana kuma tsoron kada ta samesu a falo,idanunta ta runtse kana ta saka kai,saidai cikin sa'a babu kowa a falon,hakan shi ya bata damar wucewa da sassarfa zuwa dakinta.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 28
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*
*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070
_________________________
*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*

*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*

*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸ™ŽðŸ½â€â™€ï¸

*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaÉ—a ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯ðŸ½â€â™€ï¸ðŸ‘¯ðŸ½â€â™€ï¸

*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*
*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*

*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*

*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞ðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾





Siyayya sosai azeez din yayiwa safwa,bawai don bata dashi ko tana buqata ba,a'ah,sai don kyautatawa dakuma amminsa daya tabbatar da cewa zataji dadin hakan,don ya fuskanci a rayuwa tana matuqar qaunar tarayyarsu da safwa din.


Shi da kanshi ya kaita airphort bayan ya siya mata ticket,sukayi sallama,sai a sannan hankalinsa yakwanta,saidai ta tafi ta barshi da tarin ciwukan da baisan lokacin warkewarsu ba.

******* ****** ********


Karo na uku kenan data kawo mata wani abu cikin cup tace ta shanye,kuma wai ita kadai,don bata bari ko a gaban idon rakiya tabata,akwai yarda da aminci tsakaninsu,don haka babu wani zato ko kokwanto,barema dukkan abinda take batan akwai dandanon madara sosai da garÉ—in wasu abubuwa da batasan meye ba.


Tana tsaye saman kanta tana dubanta,har ga Allah tanayine saboda taimakon bilkisun,tana kuma yine cike da fata da kuma saka ran kome zaya faru bilkisun taci gaba da zama a matsayin da take dashi yanzu,wannan shine babban fata da burinta na komai ya canza.


Jikinta yana bata komai yana iya faruwa sa bilkisun cikin kwanakin,hakan yasanya hatta da ruwan wanka sabulu da turare nata na dabanne,wanda hakan yasake tsumata da sauya mata fata da odour na jikinta zuwa wani yanayi na musamman,duk da batasan manufar mama sodangin ba,amma canje canjen data qara gani akan nada yabata mamaki,saidai batayi magana ba,tayi shuru tana kallo.


Sai data shanye sannan mama sodangin tazauna a gefanta tana dubanta,cikin tausasawa tace da ita
"Ina fatan baki manta matsayinki cikin gidan nan ba,dakuma abinda yayi silar barowarki qasarki" wani mummunan faduwa gabanta yayi,kana ta daga kai tayi ta dubi mama sodangi cikin mamakin jin furucinta,ta tuna mata da wani babban abu da ita ta manta dashi ko tace ta shagala,wanda tasan yin hakan tamkar yaudarar ce tayiwa kanta,saita gyada mata kai a sanyaye
"Kome zaya faru bilkisu ki tareshi da kyakkyawan fatan zai sauya dukkan zuciyoyi da tunani zuwa bigiren alkhairi a taki rayuwar,kiyi haquri da dukkan.abinda ka iya faruwa,kome zanyi zanyine dominki bilkisu,zanyine don hakan yazama sila na wanzuwar abinda ba'a taba kawoshi cikin tsari da tunani ba" saita miqe ba tare data iya kallon idanuwan bilkisun ba,itama saita bita da kallo harta fice,bata iya gane komai cikin kalamanta ba,bata sani ba ko qwaqwalwarta ce tayi qanqanta da kalaman sun mata girman da bazata iya fasasu ba,daga bisani data gaji da qoqarin fassara komai saita watsar tashiga sabgarta.


Cikin kwana daya tal mama sodangin tasauya mata dukka kayan baccinta da nau'in wasu kaloli masu kyau tsada da daukan hankali,duk da basuyi mata ba ita a yadda takeso amma haka ta haqura,saboda tunawa kanta da tayi wacece ita?,karta zarme da yawa,itadin tamkar aikin kwangila ne ya kawota gidan,so zabe ko nuna ra'ayi duka ba nata bane.


Abu na biyu data lura dashi shine yadda mama sodangi ta maida musu lokuttan kwanciyarsu daga qarfe takwas na dare,sabanin da dasai tatafi daki ta kwanta ma tabarsu,musamman alokuttan datasan cewa yarima yana iya shigowa,shima duka bata damu ba,idan ta koma dakin taji batajin bacci sai ta dauki wayarta ta rage dare da ita har zuwa sanda zataji bacci,kusan kwanaki uku kenan hakan ma faruwa kafin mai afkuwa ta afku,mai afkuwar data sanya ta gane dalilin samun dukkan sauye sauyen data gani.



*12:30 am*


Tun sanda tabar falon takoma dakinsu take kwance tana juyi daga farkon gadon zuwa qarshensa da wayarta a hannu tana browsing abubuwan da tasan zasu amfaneta,tun tanayi cikin marmari harta gaji bayanta ya qage,don haka ta aje wayar ta sauka daga gadon,mintuna wajen biyar takashe tsaye gaban ma'ajiyar kayanta dake lafke da kaya,wanda ita kanta batasan sanda ta tarasu ba,dukka mallakinta ne,hakanan lokaci lokaci takanji mama sodangi na waya da wata mace da take kira da fulani,wadda har yanzu batasan matsayin matar ba,duk da tajima tanajin sunanta bakin umma luba kafin mama sodangin,saidai tafi zargin ita ta asassasa dukkan wani abu dake gudana a yanzu cikin rayuwarta.


Takanji tana tambayarta me suke da buqata?,yaya zamansu yake,takanji ta aiko mata da kudi tace ayi siyayya,sukan aje mata sabulai mayuka suturu da taruruka masu dan karen tsada kyau da gyara jiki duk bayan wasu lokutta,saidai bata sani ba,ita fulanin ce ke bada umarnin ko a'ah,amma tafi tunanin ita dince,tunda sauyin bai faruwa yawancin lokaci sai bayan mama sodangi tayi waya da ita.


Bakinta ta tabe,ita sam a rayuwarta a baya bata san wani sanya kayan bacci ba,sai gashi lokaci daya an mata sabo dasu,hakanan ta zari daya daga cikinsu da takejin tafi kwanta mata,mai wani irin taushi da sulbi,ta cire kayan jikinta sannan ta sanyata,ta daure madaurin dake jikinta kana ta daga kai tana duban agogo.


Idanu ta zaro tana mamakin lokuttan data bata har haka akan waya,bacci takeson tayi amma qishirwa takeji sosai data sanya maqogaranta bushewa,dole tana da buqatar ruwa,don haka ta zura slipper mahadin kayan data gani a jiki,tabude qofar dakin a hankali ta durfafi kitchen,don tasan a canne kawai zata samu ruwa mai irin sanyin da takeso.



Zaune yake a daya daga cikin corner din kitchen din,idanunsa aruntse,hannunsa daya riqe da cup na ruwa,yayin da dayan yafin hannunsa ya runtse qwayoyin yana tantama da tunanin yiwuwar shansu ko a'ah,yayima kanshi alqawarin yadaina sha tun a wancan lokacin,to amma yanayin daya samu kan nashi a yanzun bashi da wani solution idan ba shan zaiyi ba,hakanan rashin shan nasa baisan wanne irin sakamako zai haifar masa ba,wala'alla sai yafi nashan tablet din muni.


Takun daya soma ji yasanyashi bude idanunsa da suka kada suka canza launi zuwa bakin qofar,karon farko da yaga fuskarta sosai fiye da gani guda biyun da yayi mata a baya,a hankali take takawa zuwa inda fridge din yake,alamu sun nuna kamar tana tsoron wani abu ne,wala'alla daren daya soma yine,ci gaba yayi da qare mata kallo har zuwa sanda ta dauki ruwan taci gaba da takawa cikin sanda wanda tafi kama da yanga tabar kitchen din ba tare data lura da wanzuwarsa a wajen ba.


Sosai yasake rintse idanunsa kamar zai shigar dasu ciki,wani abu yana yawo sosai a jikinsa,ganin da yayi mata tamkar wani fami yasake zame masa,saiya kasa ci gaba da riqe kofin hannunsa,ya ajeshi gefansa hannunsa na rawa.


Ya kusa mintuna biyar kana yamiqe yana qoqarin daidaita kanshi yafice daga kitchen din,sanda ya iske falo saiya kasa ci gaba da tafiya zuwa samanshi
"Halal dinka ce,halal dinka ce" yaji wani sashe daga qwaqwalwarsa yana gaya masa tamkar wanda akewa magana atsakiyar kanshi.


Tabbas bashi da wata mafita,yakai irin stage din da idan ba allura zaiwa kanshi ba zaiyi wuya ya iya controlling kansa,ya riga da ya yiwa ammi alqawarin barin allurar dama magani gaba daya,kamar wanda mayen qarfe yake ja haka yadinga jinsa kamar ana fusgarsa zuwa cikin dakin,sannu a hankali har ya isa bakin qofar,yasa hannunshi saman handle din yamurza tabude ya sanya kanshi ciki.


Dai dai sanda qofar tabude bilkisu dake kwance tsakiyar gadonta tana sauraren bacci ya sureta tabude dukkanin idanunta cikin sauri da wata irin matsananciyar faduwar gaba,saidai bata iya ganin komai ba sakamakon duhun dake mamaye a dakin,wanda tuni dama takashe duk wata fitila ta dakin don tagama shirin baccinta.


"Waw.....waye?" Ta tambaya cikin tsananin tsoro,bai amsa mata ba yaci gaba da nufar direction din da yasan zai kaishi zuwa inda fitilar gefan gadon take,a nutse yadora hannunshi ya kunnata,wani qaramin haske da baikai yakawo ba ya bayyana,hasken da bai iya nuna maka zahirin fuskar wanda kuke magana dashi.


"Way....waye?" Ta sake tambaya cikin kakkarwar murya karo na biyu
"Abdul'azee" ya bata amsa da wata iriyar gajiyayyar murya,abdul'azeez?,tasake furta sunan can qasan zuciyarta,sunan data jima da haddaceshi qyam a qwaqwalwarta,sautin muryarsa da qamshin turarensa suka qarasa bayyana mata wayeshi,gaba daya jikinta yasaki yamutu,ya lumshe idanunta tanaji a jikinta koma meye a yau komai ya qare yazo qarshe,damar da take tunanin ta samu ko zata samu ta qare mata,tasan qaryarta,bata da bakin wata magana ko yunquri,anzo wajen da zatayi bautar da take tunanin ita aka kawota tayi,wasu zafafan hawaye suka biyo kuncinta,ta cure waje daya tana jin kaduwa da tsoro har cikin hanjinta,tanajin kamar ana mata bushara da cewar mala'ikan mutuwa ke isowa gareta.


Ba zata iya cewa ga yadda akayi ya kawo kanshi gareta ba,kamar yadda ba zata iya adar da yadda komai yasoma wakana ba saboda tsantsar tashin hankalin data shiga,yau cikin wata qasa cikin wani dare a cikin wani irin yanayi zata rasa 'yancinta da alfaharinta na diya mace,wanda tasan dama kamar an riga da anyi cinikinsa tun ba yau ba an biya iyayenta.


Abu uku xuwa hudu kawai zata iya tunawa,yanayin qamshinsa,addu'ar dataji yanayi tun afarko,muryarsa da bata tantance me yake fada ba,da kuma 'yar banzar azabar data ci,wanda shine abu na qarshe da bata sake sanin meke faruwa da ita ba harsai bayan wasu awanni data farka,ta fuskanci azabar data sha da kuma zallar tsoro da baqinciki suka hadu suka sumar da ita.


Lokacin data farka ta fuskanci akwai mutum kusa da ita,ta qanqanuwar fitilar gefan gadon take iya hango inuwarshi,saidai bata iya ganin fuskarshu,xaune daura da ita,da 'yar qaramar tazara a tsakaninsu,da alamu babu wani bacci daya iya daukanshi,idanunta ta maida ta rufe,saita fashe da kuka,kukan daya sanya abdul'azeez ya fahimci cewa ta farka bayan dukka taimakon gaggawar daya bata
"Am really sorry" ya furta a hankali yana jin zuciyarsa sam babu dadi,taji sarai abinda yafurta din da qaramar murya can qasa,tana jin sanda tamiqe ya soma takawa sannu a hankali yafice daga dakin ba tare da ya waiwayo ba.


Bai rufa minti biyar da fitar ba taji an kuma turo qofar,kana aka kunna makunni qwan dakin,haske ya mamayeshi,ta tsammaci shine don haka bata bude idanunta ba,hakanan bata fasa kukan da take ba
"Bilkisu" aka kira sunanta,a sannan ta fuskanci mama sodangi ce,saita bude idanun nata da suka kumbura suka mata nauyi ta dubi maman,fuskarta sam babu wata walwala ko digon fara'a,tasoma takowa inda bilkisun ke kwance,ita kuma tasake maida idanun nata tarufe,takuma dora kukanta daga inda ta tsaya.


Mama sodangin kusan ita ta gyarata tayi mata komai kana ta kakkabe mata dakin tacire zanin gadon ta sauya wani,ta barta tana sallah daga xaune itakuma tasake ficewa,daga yanayin yadda take aikin xaka tabbatar jikinta itama a mugun sanyaye yake,ga bilkisu kuwa hawaye sunqi barin idanuwanta,tana daga xaune take sallar don ba xata iya tsaiwa ba,koda ta idarma saita hada kanta da gwiwa tana kuma sakin wani tsumammen kukan,dukkan abinda yafaru da ita a daren jiyan yadinga tariyar kansa da kansa a kwanyarta.


Shi kadai yadinga sakin ajiyar zuciya qasan shower din idanunsa a rufe lokacin da ruwan ke sauka yana ratsa kowanne sashe na jikinsa,yana tuna dukkan abinda yafarun,wanda yake jinsa tamkar a mafarki,kamar ba shine abdul'azeez ba,yana feeling guilty ta wani sashe na zuciyarsa,yayin da wani sashen kuma yakejin he is innocence,matarsa ce,abinda yayin akwai tarin bambanci tsakaninsa da wanda shedan yakeso yayi,koma meye dai aure aurene,kuma matarsa ce,duk da har yanzu gulitiness din da yakeji a zuciyarsa yana nan,amma yanajin wani yanayi na daban a gangar jikin nasa da zuciyarsa gaba daya,duk wani nauyi daya dade saman zuciyarsa da gabbansa yanajin babu shi,yanajin kansa fresh,tamkar ranar amminsa ta haifeshi,yayin da wani irin happiness ke kutso yanayin da yake ji yana ratsashi,kallo daya zakawa fuskarsa ka karanci hakan,duk da cewa baisan hakan yana bayyana ba,da ire iren wadan nan tunane tunanen ya kammala tsarkake jikinsa sa'annan yayi wanka yafito.


Mama sodangin ce tasake shigowa dakin karo na biyu,dauke da kofi me cike da kakkauran tea sai zuba qamshin ganyan shayin ahmad tea yake,yana fidda turari,tayi sallama duk da bilkisu bata amsa ba,tasamu gefanta tazauna tana riqe da kofin,saita ajeshi gabanta sannan tace
"Ki daure ki saka wani abu cikin cikinki,likita nakan hanya,zata dubaki" ko motsawa bata iyayi ba bare ta daga kanta,lallashin duniya mama sodangi tayi mata amma bata iya motsi ba,ta sani koda ta kurba abune mawuyaci ya iya wucewa maqogoranta,a haka sukaci gaba da zama har sanda rakiya taturo qofar dakin ta shaida mata zuwan likita.


Dr huda,matashiyar likita,wadda qalla ta doshi shekara ashirin da bakwai,mutum mai haba haba da son jama'a,uwa uba fara'a,kusan ita ta hilaci bilkisu tasha shayin dakyau kafin tafara dubata,tanayi tana tsokanarta,saidai hakan bai rage komai cikin abinda take ji a zuciyarta ba,daga qarshe saita lumshe idanunta kawai tadaina ganin kowa saijin zantukansu.


Tayi mata dukkan abinda yadace,ta dubata dakyau ta bata magunguna,takuma fadiwa mama sodangi yadda zata mata treating wajen tawarke da wuri,baqinciki da kunya suka cikata,yanzu kowa ma sai yasan abinda yayi mata?,daga bisani tasa mama sodangi ta bata waje tace zasuyi magana da bilkisu
"Yi haquri ki bude idon ki kalleni" kasa yin yadda tace tayin tayi,saita zauna dab da ita ta kamo hannayenta
"Don Allah badon ni ba" dole ta budesu tana duban dr huda,saita sakar mata murmushi
"Hala kinwa ango gaddama ko?...." Bata da amsar bata illa shuru,saita sake murmushi tana dubanta
"Ba'a haka qanwata.....miji irin azeez kike jawa aji?" Da kallo dai tasake dubanta tana kuma sauraren maganganunta harta gama,ta dora da bata shawarwari,wadanda su da babu duka dayane a wajenta.


Saidai yadda ta jata a jiki da yadda tasan aikinta ya burge bilkisu,har taji tadan burgeta,taji inama ace itace dr huda,inama ace itace tasamu cikakkiyar damar kammala karatunta,tana sha'awar ta zama wata,saidai almakashin qaddara yasa kaifinsa yana daddatsa rayuwarta in to pieces,wannan abun daya faru yasanya take dukkan wata dama tata a rayuwa ta qare,duk wani buri nata ya rushe,babu wani sauran abinda yarage mata kuma.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 30
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070





Tun daga ranar da abun yafaru tasake zama so silent,takoma dabi'arta tada koma fiye da da,yawan shuru shuru,zaman kadaici dakuma tunane tunane,ta sanyawa daren suna da baqin dare a wajenta,duk da cewa mama sodangi na iyakar qoqarinta na ganin ta daidaita lamuranta,abinda bilkisu ta lura dashi shine,maman tasanya wani distance na daban tsakaninta da rukiya,bata fiya barinsu xama tare ba,hakanan rakiyan ta sauya mu'amalarta da ita,wani girma take bata kamar yadda suke a baya,kwatankwacin kuyanga da uwar gijiyarta.


Sai yanzu take ganin wautar data tafka da har tasaki jiki,ta manta silar zuwanta mexico,ta manta abinda ya kawota,takuma manta wacece ita,sa'an nan ta manta dukkan qalubalen da takan iya fuskanta har sai daya zo ya cimmata.


Duk yadda mama sodangi taso.dai daita komai abun yaci tura,abun yana damunta yana kuma taba ranta sosai,bata gane ba qaramin sabo sukayi da bilkisun ba har sai data maida kanta wannan yanayin nata na baya sa'an nan tagane sun shaqu da juna,ganin tana neman illata kanta yasanya tazauna da ita,maganganun da tayiwa bikisun suka sauketa daga matakin da take kai daga kaso cikin kaso dari zuwa suka kwashe kaso saba'in suka barta da talatin,sannu a hankali lokaci dakuma juyawar zamani tsawaitarsa da abubuwan da yakanzo dasu ya sanya ta kuma saki kamar baya,saidai duk da haka bata bar É—ari É—ari tsoro dakuma fargaba ba,duk da cewa daga baya itama ta ragu,saboda rashin jin duriya motsi ko sautin muryarshi tun daga ranar da abun yafaru.


*_BAYAN WANI LOKACI_*



Nannauyar ajiyar zuciya yasaki bayan shigowarsa dakin nasa wanda a baya yake zaune a ciki kafin ammin tasa tayi masa sauyin gida tare dasu mama sodangi,tafin hannunshi ya sanya yana murza fuskarshi gamida fuskar da iska daga bakinsa,tsabar gajiya ce ta taru tayi masa yawa,uwa uba kuma da yanayin da yake ciki wanda yana tsammanin wanzuwar al'amarin zai kawo qarshen duk wani abu dake damunsa,saidai ga mamakinsa ko sau daya lamarin yaqi barin kwanyarsa ta huta,tamkar wani famine yayiwa ciwonsa,kullum kwanan duniya rana bata taba fitowa ta fadi na tare daya tuna da daren ba,daren dako yaqi ko yaso dole ya sanyashi cikin jerin dararen da zai dinga tunawa tsahon rayuwarsa,saidai baisan a wnne bigire zai saka shi ba?,na farinciki ko na baqinciki ne?,har yanzu ya kasa tantancewa.


Abinda kawai zai iya tunawa shine,zuciyarsa ta kasu gida biyu,yana da tabbacin cewa a ranar yasamu sauqi daga nauyin zuciya,yasamu wani irin inner peace da baisan akwaishi ba a duniya,yaji kansa tamkar jaririn da aka.haifa yau,yayin da wani sashen na zuciyarsa yake iya tuna mishi sautin kukanta,muruyart da taketa magana wdda bai fuskantar me take cewa,amma yana da tabbacin bazai wuce roqo na,zuciyarsa na yawan tambayarsa kayi dai dai?,yakan amsawa kanshi da eh duk da bada wani cikakken qwarin gwiwa ba,amma.yana da hujjar cewa matarshi ce.


Bai fiya son abinda zai dameshi ba,don haka tun daga ranar yayiwa gidan qaura,yakan iya kwana daya zuwa biyu a wannan gidan nasu kafin yaje wancan gidan,wanda yawanci idan yaje din kwana daya biyune shima yabarshi yasauya muhalli.



Kamar yau din dai a gidan nasu ya kwana,wanda wani lokaci hirarrkin su mustapha suna debe masa kewa,koda bazai tofa komai ba,amma.yakan zauna cikinsu yana sabgar gabanshi yana kuma jinsu.


Wani dogon tsaki yaja kana ya miqe,ya rasa tunanin me yake daya sanyashi ya zauna har haka,baisan mene yake dagula lissafinsa ba,karatunsa ne daya dauki zafi saboda watanni qalilan da suka rage masa ya kammala ko kuwa a'ah,iya saninsa ba kasafai karatu ke damunshi ba,saboda baiwar qwaqwalwa da fikirar da Allah ya bashi,bai sani ba wannan karon....kodon hausawa sunce idan aski yazo gaban goshi yafi zafi?.....



Wanka yayi yashirya cikin wasu qananun kaya da suka fidda sigar kyan da Allah yayi masa,mai cakude da kwarjini izza da jinin sarauta,yadauki maqullin motarshi bayan ya gama feshe jikinsa da turaruka kana yayo hanyar waje yana qoqarin kunna wayarshi dake kashe tun dazun,saboda baison yawan kira hakanan yakeji.


Kusan dukansu yanzu suna falon,sabanin daxu da mustapha ne kawai a zaune,yanzun kamal da jabir hadi da wani abokinsu mudassir dukka suna zaune,jabir dai kallo yake na wani wasan qwallon raga da ake haskawa live,kamal da mudassir hirarsu data shafesu suke,yayin da mustapha yamaida hankalinsa kacokam kan allon computer din dake saman cinyarsa,da alama karatu yake dubawa.


Fitowarsa tadan ja hankalinsu gaba daya,idanuwan kamal dake cike da hassada dukka suna kan azeez,yana jin inama yana da iko da a daren yau saiya qwace dukkan abinda azeez din yake taqama ya mallakeshi,saiya qwace duk wani abu da xai dinga nuna fifiko da daukakarshi a cikinsu,ciki kuwa harda kyau da kwarjininsa.


Mustapha ne ya daga kai ya dubeshi
"Zaka dawo ne koka tafi kenan?" Agogon hannunshi ya duba kana ya amsa mishi
"No,zan danyi wani uzuri ne nadawo" kamal daketa kallonshi wanda duk bibiyarsa ya gaxa cimma gacin inda azeez yake zuwa ko kuma yakoma,ya kasa haqurin yin shuru
"Wai yarima ya kake mana asha ruwan tsuntsaye ne kwana biyu?ina kakeyin layar zana?" Wani kallo ya jefawa kamal din wanda ya sanyashi shan jinin jikinsa,saiya janye idanunsa daga cikin na azeez din
"Ka sani shima ko yabi sahun 'yan morewa quruciya da rayuwarsu" jabir ya fada cikin tsokana yana qyalqyala dariyarshi harda buga qofa,don ya fadine shi har zuciyarshi ba tare da yasan meye a zuciyar kamal ba,harara zeez ya jefawa jabir din kana yasoma yin gaba zai fice ba tare daya amsawa kowa cikinsu ba
"Abinci fa?" Mustapha yadan daga murya yana fada
"Saina dawo" ya bashi amsa a taqaice yana qarasa ficewa daga falon.


Sannu a hankalin yake tuqinsa a nutse,harya shiga cikin unguwar,idan bai manta ba yau kwana biyu ko uku kenan rabonshi da ita,da wannan tunanin ya faka motar a qofar gidan yakasheta yafito,kana ya sanya muqullinsa ya bude gidan,ya tura falon yashiga.


Shuru yake babu kowa ciki,dama ya tsammaci hakan,don lokacin kwanciya barci ne ga duk mutumin da bashi da wani aikin da zaiyi,saboda dare daya soma yi,karaf idanunshi suka fada sashen da dakinta yake,saiya lumshe idanu yana dauke kanshi,kana ya durfafi samansa.


Dakin fes yake,kamar yadda ya zame masa dabi'a,baya barin dauda ko qura a duk muhallin da yasan zai zauna,ya buda duk inda yake da buqata yadauki abinda yake buqata din sannan yakuma rufe dakin ba tare daya zauna ba yafice a dakin.


Karo na biyu idanunshi suka sake sauka a qofar dakin sanda yake saukowa daga saman,tamkar wanda magnet yaja ganin nashi haka yaci gaba da kallon dakin,har ya gama saukowar,saiya durfafi qofar fita da sauri yanason daqile duk wani abu dakeson masa tasiri cikin ranshi.


Murus jikinsa ya mutu lokacin daya shigar motar da niyyar tada ta,saiya kasa tabuka komai,kasala da mutuwar jiki na baibayeshi,wani irin shauqi yana mamaye gabbansa,ya tabbatar da cewa bazai iya maida kanshi gida ba a yanayin da yake ciki ba,don haka saiya kashe motar yafito yakoma cikin gidan.


Tamkar wanda ake sauyawa direction,kamar wanda wani abu mai qarfi yake janshi saiya samu kansa da sauya akalarshi zuwa dakin nata.


A hankali ya tura qofar,duhune yasoma yi masa sallama bisa dukkan alamu tayi bacci,a nutse yanufi inda yasan zai samu haske bedlamp,ya sanya hannunshi ya kunna,qaramin haske mai duhu ya bayyana.


Tarwai fuskarta ta fito dab da fitilar,kamar wadda tasan da faruwar hakan,saitin fuskartata wayarta ce a yashe,da alama tana tsaka da dannata bacci yayi awon gaba da ita,saiya samu kanshi da xubawa fuskar tata idanu,karon farko daya fara aikata hakan tunda yasoma saninta,kamar ba bacci take ba,kamar idanunta biyu,idanunsa

Please Login or Register in order to submit comment