Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

saki jiki haka dashi,kamar dama can sun sanshi,sai kuma ya tuna cewa jini fa ba wasa bane,daga qarshe ya jasu qofar gidan cikin motarsa,ya dinga musu hotuna kamar dama ya siya wayar ne kawai saboda su.


Bilkisu kuwa a razane ta shiga dakin anty zuhriyya wadda ke tsaye tana linke hijabin jikinta,saita saki hijabin tana kallon bilkisun
"Kin gani ko anty,wallahi ya shigo yana falon,yana tare dasu amatu anty ya akayi ya shigo,kada ya debemin yara na" kafadarta ta kama
"Babu inda zashi dasu,ki kwantar da hankalinki" baki kawai antyn ta saka ta zubawa bilkisun idanu ganin yadda ta gaza nutsuwa,tana mamakin yadda take razana fiye da kima a duk sanda zata ganshi kamar haka,tabbas akwai dalili bayaga tsoron tafiya da yaran da take.


Sai daga baya ta fuskanci antyn ta zuba mata idone kawai tana kallonta,hakan yasa dole ta arowa kanta nutsuwa ta kuma zauna tana maida numfashi,ganin haka yasa ta juya taci gaba da ninkinta ba tare data ce da ita komai ba,ta barta tana qoqarin daidaita nutsuwarta.


Shikam daga can saiya kwashesu kawai zuwa shago mafi kusa dasu,ya dinga sanyasu suna zabar duk abinda sukeso,duk da basu rasa komai ba,haka ya dunga lodar musu siyayya harda ta banza da wofi,ya kashe musu kudi masu nauyi ba tare da yaji ko darr ba,saida suka cika motarshi da siyayya sai wajen zamansu kawai ya rage.


So yake yayi wani abu da zai iya zama madadi koya cike gibin da ya afku a rayuwarsu shekaru bakwai baya,yanajinsa wani babban mai zunubi kuma mai sabo idan ya tuna an raini cikinsu ba'a gabanshi ba,an haifesu ba'a gabanshi ba,an ciyar dasu abincij wani gidan ba nashi ba,basu taba sanya suttura tashi ba ko amfanuwa da wanu abu na mahaifinsu ba,duk tarin dukiyar da Allah yayi masa,yanajin ciwo da quncin hakan sosai cikin ranshi,amma yana fata nan da lokaci qanqani komai zai zama tarihi.


Sanda su ateeq suka gama shigo da siyayyar mamaki ya kama anty zuhriyya,tayi tsaye kawai riqe da baki da hannunta,sam yaran ma su basusan me ake ba,sai nunawa su ateeq kayan suke daya bayan daya,kowa na daukar nashi yana fadin wanda zai baiwa.



Bilkisu dake daki batasan me akeyi ba,sai data fito duka a sintirinta na ganin yaran sun dawo sannan tazo ta tadda kayan.


Sosai ranta ya baci,taji kamar ta tattara kayan ta cinna musu wuta,musamman data lura anty zuhriyya kamar bata nuna damuwa ba,kuma me yasa ma ta bari aka shigo da kayan cikin gidan
"Kun sanshi ne da kuka bishi kuka karbo kaya?,roqo kuka soma abdul?" Cikin tsoro suke kada kai,saboda basu taba ganin bacin ran mahaifiyar tasu irin haka ba,fada ta kama sosai duk idanunta sun rufe,har sai da anty zuhriyya tayi kiran sunanta kana ta tsagaita
"Ku tattara kayan kukai dakinku,najwa ki jera musu cikin kayansu,wanda zai lalace kuma ki sakasu cikin fridge"
"Amma ummi...."bilkisu tayi hanzarin fada
"Ya isa" ta dakatar da ita,ba wanda ya sake cewa komai cikinsu har sai da duka yaran suka bar falon.


"Zauna" antyn ta bata umarni cikin nutsuwa,ba musu tabi abunda tace ta zauna,antyn tayi shuru tana dubanta na wani lokaci kafin tace
"Lokacin da suka kore cikin jikinki,saninki ne cewa bashi ubansu bane da kanshi ya aikata hakan,mahaifiyarsa ce tayi gaban kanta ta aikata hakan,bilkisu,duk duniya bayan ke kanki babu wanda ya kaini jin zafin abinda ya faru dake,hakanan har yanzu inajin zafin hakan cikin raina...amma kinsan wani abu?,akwai wasu abubuwa da nayi nazarinsu cikin taqaitaccen lokaci,abu na farko..." Ta fada tana daga yatsanta
"Daga ni ke da duk wani mai qaunarki babu wanda zaiso ace yaran nan sun tashi ba tare da sunsan waye mahaifinsu ba,ba tare da sunsan asalinsu kuma tushensu ba,idan wasu sun musu kallon 'ya'yan halali saboda sunsan sanda aka daura aurenki,da yawa zasu musu kallon shegu ne,kalmar da sai ta kusa tarwatsa zuciyarki fiye da yadda zuciyar taki taso tarwatsewa a baya,duk yadda zanso daukan fansa nuna fushi ko jin zafi kan lamarin bilkisu,bazanso su abdul su rayu ba tare da sanin waye ubansu ba" shuru tayi tana kallon bilkisun kafin ta dora
"Abu na biyu kuma...dukka hasashena da abinda ya bayyana garemu....mahaifiyar yarima ita keda alhakin komai,ta shirya komai kuma ta tsara faruwarsa yadda taso saboda tana jin cewa qarfin izzarta isa iko da kuma mulkinta sun isa susa komai dai daita,ban sani ba koda goyon bayansa,ban sani ba ko babu,hakanan ban san ko tare suka shirya ba,amma abinda nafi gasgatawa shine ita ta shirya,zan iya cewa a yanzun kamar dama kika samu,dama kika samu da zaki nuna mata kurenta,dama kika samu da tana kallo zaki kasance da yaronta ba tare data tsara faruwar hakan ba" kamar wadda aka mintsina sai bilkisun ta miqe tana kada kai.


Murmushi anty zuhriyya ta saki tana nuna mata kujera da hannu
"Kwantar da hankalinki ki zauna,hasashena ne,kina iya yin dukka yadda kikaso a yanzun damarki ce" saita koma ta zauna din,anty zuhriyya ta dora
"Abu guda nakeso ki fahimta kuma ki gane,wannan dalilan nason yaran susan ainihin tsatso da mahaifinsu yasa na bashi damar shigowa gidan da kuma ganinsu bawai wani abu ba daban,abu daya kuma zuwa biyu nakeso na fahimtar dake,ki daina zafafa qiyayyar mahaifinsu gaban idanunsu,saboda shaquwa da qauna mai qarfi na iya shiga tsakaninsu,ta tadda zasu fara iya gano aibun abinda kikeyin,zasu kuma iya bin bayanshi nan gaba,sannan duk koma meye ya farun ba hurumin su sani bane,don haka ki dinga qoqarin dannewa,amma baya ga haka,babu abinda ya sauya game dasu a zuciyata,hakanan ba wani sassauci ko sauran dama a kanki,sai abinda kedin kika zaba"......


*_ABDUL_AZEEZ_*



Ranar yau din jinsa yake daban,jinsa yake kamar an sauyashi,wani irin farinciki ke ratsashi wanda ga duk wanda yasan shi,yasan ainihin zahirin fuskarshi zaiyi mamaki qwarai idan yaga wannan yanayin saman fuskar tashi.


Cikin nutsuwa da kuzari yake tuqin nasa,cikin zuciyarsa kuma yana wassafawa gami da ayyana yadda zai shawo kanta,yana ganin matuqar yaran suka shaqu dashi,shaquwar tasu zata taimaka qwarai wajen janyo nata hankalin.


Sassanyan murmushi ya subuce masa sanda ya gama hasaso kansa tare da bilkisun cikin wata duniya ta musamman wadda dagashi sai ita.


Komai ya katse masa sanda wayarsa ta soma ringing,yaja qaramin tsaki yana jin haushin yadda kiran ya katse masa daddadan tunaninsa,yanajin me yasa ma bai kashe wayar ba.



Dai dai lokacin da fulani kenan ke tsaye tsakiyar falonnata cikin tashin hankali,tana kuma sauraron mama sodangi dake mata kiran yariman.



Ganin ya kusa isa gida ya sanya baibi takan wayar ba,har sai daya isa wajen parking,yana tsaidata idanunsa yakai ga wayar wani kiran na shigowa,sunan mama sodangi daya gani ya sanyashi kashe motar kawai yayi,ya daga kiran ba tare daya fita a motar ba.


Ga mamakinsa muryar ammi ce ta soma shiga kunnensa a maimakon mama sodangi
"Barka da war....." Ya soma yunqurin gaidata
"Dakata yarima!" Ta dakatar dashi a matuqar tsawace,tsawar data ratsa kunnuwansa da kwanyarsa dakyau
"A yau na yarda da cewa nidin ba koman komai bace a wajenka,ni ba wata tsiya bace....sanna yaudarar daka jima kana min tsaho shekaru game da bilkisu a yau Allah ya bayyana min komai,na gani da idona,gani kuma na zahiri,saidai abinda nakeso ka sani,ka tafka kuskuren da zai jawo rushewar komai,qimarka da tawa,darajata da taka,martabarmu gaba daya,hotunanku ya fara yawo cikin masarauta kai da yarinyar cikin yanayi na abun tur da Allah wadai da bai kamata aga dan qwarai a haka ba.....bana so ka wuce satin sama ba tare da kazo ka sameni cikin kaisa ba,sa'anan daga yau a yanzun nan nake cewa.....idan ka sake rabar yarinyar ban yafe maka..."
"Ammiiiii" ya kira sunan nata cikin wani irin sauti na gigicewa da razana
"Kada kiyi haka,kada kuma kice haka,ina buqatar yin magana dake,akwai abubuwa da yawa da baki sani ba wanda ya kamata ace kin sani"
"Abdul'azeez!,ba kana magana bane da sa'arka ba,mahaifiyarka ce idan ka manta na gaya maka,bana buqatar sani ko jin komai,ruwanka kabi umarnina koka saba,furucina zai bika" daga haka ta katse kiran ta baiwa mama sodangi wayar,cikin tashin hankali da bacin rai ta soma magana
"Inason cikin barorina a zabo min amintattu mutun talatin da zasu shiga kowanne lungu da saqo na masarautar nan,su kuma zaqulo gami da fiddo hotunan a duk inda suke,hakanan suyi aiki ba dare ba rana,subi dare subi rana su tsince hotunan a duk inda sukaga an yar a qonasu,ba shakka wannan wani shirine da aka jima anayi ana bibiyar sawunmu don a tarwatsa mu,saidai kamar kowanne lokaci, a wannan lokacinma ina da babban zaton shirinsu ba zaiyi tasiri ba,amma fa.....sai munyi babban aiki,ta yadda hotunan ba zasu shiga hannun maqiyana abokan zamana ba,bare kuma....." Sai tayi jim tana tuna girman lamarin
"Mai gaba daya mai girma mai martaba,ayi gagggawar aiwatar da abinda nace cikin sirri,kada a samu kuskure"
"An gama" umma luba ta fada suka miqe tare da mama sodangi suka fice,yayin da mama sodangi tayi nisa cikin tunani gami da nazarin al'amarin,yadda zata kaya,da yadda zata kasance,meye qarshen abun?.

_kuyi manage,banson yin muku fashin posting,babu yawa,da babu gwara babu dadi ko?inji hausawa_ðŸ˜
7/11/21, 4:35 PM - My Mtn Number: 63

*_NAFISAKABDULLAHI_*

*_Mai karatu nasan zaka ce meye wannan?_*

*_shin kai/ke ma'abociyar hawa duniyar yanar gizo ce?,kina daga cikin masu shawagi a manhajar youtube?_*

*_to maza matso,GA SABUWAR CHANNEL 'YAR YAYI DAKE DA ZAMA A MANHAJAR YOUTUBE MALLAKIN MAWAQIYA NAFISA K ABDULLAHI_*

*_CHANNEL DIN DATA HADA dukkan wani sinqi sinqin abubuwan sanya ruhi nishadi,kama da_*

*waqoqi*
*fina finai*
*da bidiyoyi masu qayatarwa*


*_GARZAYA maza ka shiga wannan link din https://youtu.be/1VyZ6f1GTWg dannan maballin SUBSCRIBE don samun sabbin shirye shirye idan an dora,sannan ka danna LIKE kayi kuma SHARING_*

*_NAFISAKABDULLAHI YOUTUBE CHANNEL 'YAR YAYI_* 🥰🥰🥰

_ZAKU IYA MAGANA DASU KAI TSAYE A SHAFINSU NA FACEBOOK_
https://www.facebook.com/preetyfeenat.abdullahi


_KO KU TUNTUBESU TA WANNAN NUMBER WAYAR_
08071172003

*karku manta SUBSCRIBE,LIKE SHARE AND COMMENT*
*SAI KUNZO*🚶ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸš¶ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸš¶ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸš¶ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸš¶ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸš¶ðŸ¾â€â™€ï¸

__________________________
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070



Da qyar ya samu ya iya kai kanshi falonshi ya zube yana jin wani jiri jiri,astagfirullah kawai yake ambata a fili da boye,don wannan karon bayajin zai iya bin umarnin fulani kwata kwata,zaije ya tunkareta kamar yadda takeso,amma kuma bada lamarin da takeso din ba,a yanzun yana jin a shirye yake ya bayyanawa duniya bilkisu matarsa ce,a bayyane yake ya amshi matarsa da dukka yaransa,a yanzu ya sake shiryawa tunkarar duk wani qalubale daka iya fuskantoshi.


Yanaji wayar tana sake ringing,daya duba sai yaga safwa ce,baida kuzari ko sha'awar yin magana da kowa,a yanzun kadaici yake buqata fiye da kullum don ya shiryawa tunkarar abinda zai dososhi,don haka ya maida wayar silent gaba daya,harta qaraci burari da kiranta ta gaji ta ajjiye.


¶¶¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶¶


Idan tace tayi kyakkyawan bacci ko taci abinci ya tsirga mata kota zauna ta samu hutu da nutsuwa ba tare da fargaba ko tashin hankali baa kwanakin ta yiwa kanta qarya,koda yaushe cikin zulumi da aikin tsinto hotunan suke,abun yana neman ya gagari kundila saboda yadda kullum wayewar gari ake tsinto mata hotunan rututu,magana harta so ta zagaye kusan rabin masarautar,ya soma zama wani topic mai zaman kanshi da duk inda kaga mutane sama da biyu zaune suna hira kusan zancam da sukeyi kenan,don ma alkhairinsu cikin masarautar ya taimaka qwarai wajen rage yawan zargi da cecekuce.


Saidai kuma akace dan adam baka iya masa ba,dan halak shike rama halacci,wani duk yadda kakai ga kyautata masa akwai lokacin da zai rufe idanu ya shiga sahun masu cutarka ayi dashi,koda ka shekara dari kana masa alkhairi ne kuwa,shi yasa hausawa sukace dan halak shike rama halacci,to kusan hakanne,da yawa daga cikinsu da basu duba kyautayi kyauta gamida halaccin fulanin ba,sun gauraya da 'yan kora masu aiki qarqashin fulani adama suna sake hura wutar zancan lungu da saqo,wannan yakai har kunnan fulani yadda maganar ke yawo.


Tashi hankali sosai ta shiga,tana duba girman abinda ka iya zuwa ya dawo matuqar maganar taci gaba da wanzuwa har zuwa lokacin da baqi zasuci gaba da sauka masarautar domin halattar wannan gagarumin hawan daya tara al'umma da yawa,daren data masa barci,ta jima tana ta zirya gami da tunani da son hasaso wanda ya qulla dukkan wanna tuggun,duk da zarginta yafi ga mutum biyu,adama ko saratu,a binciken data saka aka mata kusan mutanen fulani adama su fi yawa cinin masu tofa albarkacin bakinsu game da lamarin,don haka zarginta yafi karkata a kanta.


Ta fannin fulani adama kuwa labarin dukkan yadda lamuran ke tafiya yadda takeso na zuwa mata kunnunta,abun ya mata dadi qwarai da gaske,tayi shewa tayi dara tana kuna jira da dakon ranar da zata isa gaban mai martaba fa miqa hotunan,ranar da zata samu dimbin shaidun al'umma na suma sunga hotunan na yawo a masarautar,ranar da zata tarwatsa farincikin fulani aishanta cusa mata kadan daga cikin baqincikin data jima itama tana cusa musu
"Allah ya baki yawan rai,ta qara yawan ma'aikatanta masu kwashe hitunan a duk inda muka sakesu"
"Ina umartarku daku qara yawan hotunan ninkin baninkin abinda aka saba bugawa da zubdawa,ku qara yawan sasannin da kuke ajjiyesu,so nake ya zamana hatta da maqasqanci mafi qarancun matsayin bawa a masarautar kaisa,babba da yaro ya tsinci hoton bawai labari kawai ba,ta yadda qimar abdul'azeez da mahaifiyarsa zata tafi daga masarautar nan,tafiya ta har abada" wannan shine umarnin da fulani adaman ta bayar.


Sannu sannu saiga hoton har a hannun fulani saratu,ta jima tana qarewa hotunan kallo cike da mamaki da jinjina lamarin,tana kuma sauraren bayanin da daa daga cikin bayinta keyi.


Murmushi ta saka daga qarshe tana ajjiye hoton a gefanta,ta zauna cikin nutsuwa tana fadin
"An hana yaranmu fita zuwa wata qasar karatu da zummar kada su lalace,lallai ya kamata nayi tattaki har zuwa sassan fulani na soma miqa jajena a qareta,tare da jiran ranar da labari da idanuwan mai.martaba zaikai kai wannan danyan aiki da yarima kaisa keyi a qasashen turawa" tana fadin maganar tana jin zuciyarta wasai,yanzun lokaci yayi da ko qaqa zata samu ta rama wani yanki daga haushi da takaicin aishan gami da kishi dake cin ranta.


¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶

Kamar kowanne lokaci yauma tana zaune cikin daya daga cikin falukanta da ayau ta zabi ta zauna,duk da zamane kusan na alhini da fargabar abinda kowannw second na awannin ranar zai iya haifarwa,zamane kamar na makoki take,zaman tattara dukkan wasu hotuna da aka zubar a ranar,wanda kafin ta koma ciki sukan tara hotuna masu yawa,wadanda a yanzu haka hotunan har sun ninka nada,hakan ke sake tabbatar mata lallai lallai akwai zagon qasa da kuma saran boye cikin lamarin.


Sanda aka nemi izi inta kan shigowar fulani saratu tayi mamaki qwarai,taso ta hana,sai kuma tayi tunanin idan har ta hanata din kamar tana basu isharar cewa tasan meke gudana,ko kuma haka abun yake,don haka tasa aka kwashe hotunan da ake tarawar zuwa inda kullum suke qonawa,kana ta bada umarnin ta shigo.


Cikin wani irin taku da take jin ranta fes ta shigi zuwa falon,ta daga kanta a fakaice tana kallon yadda aka narkawa falon dukiya da tsari gamida zubi irin na masarautar mali,falo ne da aka shirya nata shi takanas daga can masarautar iyayenta,kama daga ma'aikatan da sukayi aikin zuwa dukka kayan da aka zuba din,tana kishi sosai na yadda kullum gado na sarauta ke bayyana daga wajen aishan,tanajin da tana da iko ko qwanjin qwacewa da tuni ta qwace wannan nasabar.


Fulanin a yau tana lura da yadda take qarewa falon kallon,sabida kanta tsaye a yau takeyin hakan
"Bismillah mana" fulanin ta fada cikin qoqarinta dakiya gamida jarumta.


Sauke ganinta fulani saratu tayi saman fuskar fulani aisha sannan ta saki wani irin murmushi wanda ya haddasawa gaban fulani aishan faduwar gaban da tunda take bata taba jinta ba akan kishiya,sai saratun ta bude baki a nutse tace
"Haifaffiyar diya ga masarautar mali,mata ga sarkin yau,uwa ga sarkin gobe ko?" Ta qarashe maganar ta sigar tambaya,bata tabajin ta kasa magana ba tsahon rayuwarta don sun yada mata magana ba sai a yau,ta hadiye wani abu mai tauri idanunta tsakiyar na saratun kamar yadda itama take kallonta,tana kuma jin dadin sauyin tanayinta
"Shi jaje ai ba lallai sai a zaune akeyinsa ba,basai na zauna ba,don a duk yadda ta kama yinsa ake,fata dai a taya wanda akewa jajen alhini" saita soma takawa tana nufar qofa,sai kuma ta tsaya
"To uwar yarima....au a yanzun fa bai kamata ke daya a rinqa kiranki da wannan sunan ba,muma ya kamata mu shiga ciki,don da alamu damar zama hakan ta zama ta mutane da yawa,duk da bamu da cikin haifar diya maza,sai ya huwacewa yaran namu mata,kinga ko cikin jikoki a laluba,wala'alla a dace da kinin abdul'azeez,kinga shikenan.....baki alaikum" ta qarasa tana sake sakin murmushi
"Kinga dai na manta zan fita ban miqa saqon jajena ba,ina miki fatan nasarar tsallake wannan guguwar data kunno muku,duk da bawai har can qasan zucia ba,na tabbatar kina sane da dukka dokokin masarautar kaisa ko?,to Allah ya sanya iya kanta kawai yariman namu ya tsaya,kada aje allura ta tono garma kuma.....na barki lafiya" daga haka ta saka kanta ta fice tana jin wani nishadi da farinciki yana yawo da ita,don tunda take bata taba ganin damuwa firgici saman fuskar aisha ba sai yau,abinda suka jima suna son gani amma basu gani din ba sai yanzu,ba shakka ita duk wanda ya aiwatar da wannan shirin ya mata dai dai,tana kuma fatan abun ya tsawaita,ta yadda zaiyi wancakali da dukkan dama da dajarta harda martabar aishan da iyalanta..


Fulani saratun na fita itama ta miqe tana jin kamar saman allura take,jikinta ko ina zufa yake fitarwa,ba shakka maimartaba na gab da sanin wannan lamarin tunda har takai ga kunnuwan abokan zamanta,wani tsanar bilkisu ta darsu a ranta,yarinyar tana son zame mata tauraruwa mai wutsiya,anya kuwa ba komayya tayi suka hada hannu da abokan gabanta aka shirya dukkan wadan nan abubuwan ba sabida a rusata?,tunda yarinyar ta shiga cikin rayuwarsu komai yake tafiyar mata a hagunce,amma babu babban mai laifi irin azeez,lallai wannan karon zata ture dukkan wata soyayya ta hukuntashi yadda zaisha mamaki shi karan kansa.


Zaune yake saman daya daga cikin kujerun falon yana kurbar coffe mai zafin gaske kamar zai qona harshe,dagashi sai boxer wanda hakan yayi silar tonuwar asirin qaqqarfan jikinsa dake a murde,da kuma lallausar gargasar data yiwa jikin mashi qawanya,kama daga qirjinsa singalalin qafafunsa zuwa na hannayensa.


Fuskarsa a yamutse take qwarai,kamar yadda zuciyarsa take a yamutse,tun jiya yake lissafin yadda zai tafi nigeria ba ya barsu a brasil,ji yake kaman zaiyi wani nisa dasu mai yawa wanda kamar ba zasu sake haduwa ba kenan,kaman zasu bace masa bat.


Wayarsa dake gefe ta dauki ringing,saiya shareta kawai,tayita kida tana katsewa har sai daya gaji ya duba mai kiran nashi.


Daya daga cikin informers nashi ne daya dauka haya,tunda yaga sunan yasan cewa akwai labari,don haka babu jinkiri ya daga wayar ya kara a kunnensa
"Nigeria?....ok thanks" ta fada yana katse kiran.


Cilla wayar yayi saman kujera yana fidda nannauyan numfashi daga bakinsa tare da hancinsa,tabbas ta sauqaqe masa kewarsu da yakeji,tafiyar tata kuma zuwa nigeria tayi masa dai dai,hakan shi zai bashi cikakkiyar damar da zai daidaita dukkan al'amuran,yanajin zuwa yanzun shima babu wani abu daya rage masa ko ya masa saura a brasil,don haka ya aje cup din kai tsaye ya nufi daki bayan ya dauki wayarsa,ya kuma yi booking flight,wanda ya kama zai isa nigeria ne ranar da ake gabatar da hawan daba din.



*_ABUN BOYE........_*


Rana ce ta musamman ga dukkan jama'ar qasar kaisa bama masarautar kadai ba,saboda rana ce da akanyi hawa na musamman,sarkin kaisa yakan kewaya jama'arsa waje waje,sukan tattaru su miqa masa gaisuwa ga wanda baida zarafin ganinshi cikin fada,wanda kume keda zarafin ganin nasa kan riskeshi acan ya miqa tashi gaisuwar,yakan zauna har zuwa lokacin sallar la'asar,wanda daga sallar la'asar dinne kuma zai wuce cikin gida ya gana da 'ya'yansa gamida jikoki da kuma 'yan uwa da suka samu halartar bikin.


Kowanne sashe na gidan kan zamana cikin baqi,hakanan kowa kan kasance cikin ado kamar bikin sallah,yaudinma haka ta kasance,saidai ga fulani aisha,sam bata taba ganin birkitaccen bikin hawan daba da yazo mata a hagunce,a kuma yanayi mara dadi ba irin wannan,don gaba daya bata nutsuwa ko kwanciyar hankali,ta sake baza da linka masu duba mata hotunan fiye dana baya,wanda akaci gaba da tsintosun kuwa kamar ana ruwansu.


Abinda ya sake tada mata hankali kenan,duk da tarin kwalliya da adon daga caba da sutturu masu azabar tsada da daukar idanu,duk wani abu data saba yiwa mai martaba a irin wannan rana batayishi ba,donko zuwa da suke masa rakiya sanda xai hau doki bata samu zuwa ba,wannan ya faranta ran adama da saratu,musamman adama da tuni ta gama shiryar tashin bomb a yau wanda zai qarasa gille sauran dukkan wata nutsuwa data yiwa aishan saura.


Tsaye take a daya daga cikin bedroom dinta,tana duban tulin hotunan dake cikin wata babbar leda,yayin da guda daya ke riqe ahannunta ta tsura masa idanu,saika rantse da Allah kallonsu take,saidai tayi nisa ne a duniyar tunani da kuma neman mafita.


A nutse afnan data yi ado sosai cikin suttura ta alfarma wadda ke alamta inda ta fito,ta turo qofar dakin mahaifiyar tata gami dayin sallama,adan firgice fulanin ta dago tana amsawa gamida qoqarin kifa hotunan saman madubi.


Tuni afnan ta riga data fuskanci me take boyewar,wanda tuni ita ta ganshi tama mallaki wasu daga ciki,kamar yadda wasu daga cikin jama'ar masarautar suka mallaka.


Idanunta akan mahaifiyar tata ta qaraso dakin
"Lafiya afnan?....ya akayi?"
"Su yaaya sumaira ne ke jiran fitowarki tun daxun shuru" tayi maganar tana miqa mata hotunan data shigo da su.


Batabi takan maganar jiranta da yaran nata keyi ba,illa miqa hannu da tayi da hanzari tana karbar abinda afnan din ke miqo mata,cikin zuciyarta tana fatan Allah ya sanya ba wani mummunan saqon bane.


Hotunan nan ne dai da kullum idaniyarta ke kwana su wuni suna kalla,ta kuma kwanta ta tashi tana mafarkinsu,hotunan dake barazana da kwanciyar hankalinta nutsuwarta darajarta da martabarta,saidai abun yakai har afnan ta samu itama?,lallai nan da wanu dan lokaci zasu isa hannun mai martaba.


Muryar afnan itace ta katse mata dukkan tunanin da takeyi
"Ya azeez....da tsohuwar matarsa,qawata bilkisu bilyamin....yarinyar da aka tsigeta daga karatunta,aka rabata dashi,sannan akayi mata auren dole ba tare data shirya ba,aka katse duk wani buri da mafarkinta saboda laifin da bata aikata ba,saboda biyan buqatar wasu,yarinyar da nake kwana na tashi kullum.ina tunanin ko tana ina?,ko a wanne hali take yanzu?,ashe da zuriata kuma jinina wajen cutatar da rayuwarta" takai qarshen maganar da alamun abun yana mata daci a rai,hakanan idanunta nakan fulani,wadda itama ra kafeta da idanu tanason karanta da kuma fahimtar me afnan din ke cewa.


Tsaf qwaqwalwarta ta soma shirya mata kalaman,saita hade rai sosai tana duban afnan
"Ke....banason sakarci,ki barmu da yarfe da bata

Please Login or Register in order to submit comment