Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Karfe bakwai ta tashi amatu ta mata wanka sannan itama ta shiga tayi nata wankan,bayan ta fito ta shiryasu duka ita da amatun,dukkaninsu cikin african abaya wadda aka musu dinkin iri daya sak komai da komai,tun wani zuwa da anty zuhriyya tayi nigeria tayi musu tsarabarta dukka matan har ita kanta.


A falo suka samu anty zuhriyya abeed ya tadata yunwa yakeji,ta dubesu tana murmushi
"Yau wace rana ba'a mana gori ba bamu roqa ba za'a asibiti damu" murmushi bilkisu tayi don har yanzu bata jinta dai dai
"Qawa tayi patient a asibitin,su suka uzzuramin zanje da ita na huta da tambayata amatu da takeyi"
"Ai ya kamata.....amma fa ba qaramin kyau kukayi ba,ni sai naga abayar nan tafi kyau da jikinku,kamar yaya da qanwarta" murmushi bilkisu ta sakeyi har haqoranta na bayyana
"Kai ummi...,ai dama tana da kyau baki taba kula bane,bare wannan atamfar da suka ratsa mata ta dace da jikin abayar sosai"
"Gaskiya kam ai sun iya dinkata,ba kamar wadanda na saba gani,inajin idan muka koma saina sake siyan wasu"
"Nima suna burgeni,zan qara wasu kodon fita aiki ma" suna wannan hirar suna karyawa ita da amatun,duk daba wani abun kari na azo a gani bane,saboda dama ba kasafai take jiran abincin break ba na duka gida duk randa zata aiki,musamman idan babu 'yan makaranta ita kadai zatayi fitar sassafe.


Wayarta ce ta dauki tsuwwa,ta janyo 'yar mitsitsiyar jakar hannunta me kyau ta fiddo wayar tana duba me kiran,sai taga daga asibiti ne,cikin yana dake nuna gaggawa ta gaske akace da ita
"Dr bilkees....kiyi hanzarin isowa asibiti,akwai matsala mai girma" maganar ta tada mata hankali sosai,tasan tunda aka gaya mata hakan akwai matsalar,don haka ta dire nata cup din ba tare data ida shanyewa ba,ta azalzali amatu ta wuce su tafi.


Gudu tayi sosai ba irin wanda ta saba ba,duk sanda take sake kusantar asibitin gabanta na qara faduwa,har gumi takejin yana tsatstsafowa a goshinta,idan matsala ce ya saba ganinta kala kala,amma batasan me yasa yau din take a birkice ba hankalinta a tashe fiye da yadda ta saba.


Tana aje motar a muhallin ajiyar motoci ta fito ba tare da bata lok
Uaci ba,ta kulle motar kana ta soma takawa zuwa cikin asibitin gabanta na dukan uku uku,sam batau lura da surutun da amatu keta faman zuba mata,data gajima saita dubeta cikin daurewar fuska
"Kimin shuru amatu,tun bansa an maidaki gida ba yanzun nan" gum tayi da bakin nata kuwa,saboda tasan kadan daga aikin ammin tata.


Tun daga nesa take iya hango dakin da suhaima ke kwance,kamar akwai mutanr dai daiku tsaye qofar dakin,sabanin da da bazaka samu kowa ba,data sake wasu taku zuwa wajen saitake jin sauti kamar na sheshsheqar kuka duk da batasan muryar wace ba hakanan batasan wace me kukan ba,amma hakan yayi matuqar fadar mata da gaba,sa'annan ya sake sanyata qara saurinta ta durfafi dakin kai tsaye saboda wani abu da zuciyarta ta soma raya mata,harta saki hannun amatu dake cikin nata ba tare data sani ba,burinta shine kawai ta isa dakin taga abinda yake faruwa.
7/11/21, 4:34 PM - My Mtn Number: 53
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070

Babu inda idanunta ke kalla a dakin sai gadon da suhaima ke kwance,a miqe take sosai ba kamar yadda ta saba zuwa ta taddata yawancin lokuta tana zaune suna hira da wani ba,likitoci da nurses shida ta taras a kanta,saidai dukkaninsu suna tsaye ne,akwai alamun alhini saman fuskarsu.


Saita kutsa tsakiyarsu ba tare da tace da kowa komai ba,ta isa ga suhaima da idanunta na ke a rufe,jikinta ne gaba daya taji ya hau rawa,guri daya ta taba a jikinta gaba daya taji wani rauni yazo mata,ba wani ba wata yarinyar ta rasu,ta koma ga mahaliccinta,saitaji tana son daina gane komai,ba zata iya ci gaba da tsaiwa ba saboda yadda taji qafafunta na rawa,saita samu jikin bango ya jingina kawai tana son daidaita numfashinta,sai a sannan ta lura da wani mutum fuskarsa kife jikin gadon saitin kan suhaimar,kamar wanda bai dakin baisan me akeyi ba.


Idanunta ta runtse tana jiyo sautin koke koke daga wajen dakin,wanda ta tabbatar da cewa wasu ne da suka jibanci yarinyar,batasan ya zata iya buda baki ba tace musu ta mutu,ita kadai tasan me takeji a zuciyarta,sosai qirjinta yake suya,tana jin tunda ta kama aikinta bata taba mara lafiyar data shiga zuciyarta ba kamar suhaima,bata taba jin qaunar patient dinta ba kamar yadda taji tana son yarinyar sosai har cikin zuciyarta,amma sarkin dake da iko da kowa ya amshi abarsa,saita soma jan qafa ta durfafi qofar fita daga dakin.


Suna nan tsaitsaye kamar yadda ta barsu,saidai bata iya gane fuskar kowa a ciki saboda idanunta cike suke taf da qwalla,riqeta taji anyi
"Likita ke ake jira....bata mutu ba ko?" Dubanta ta maida kan matar dake riqe da ita tana kuka,kuma ita ta jefa mata tambayar
"Saidai muyi haquri,Allahnmu yafimu sonta" abinda ta iya gaya mata kenan matar ta zame a wajen tana sake fashewa da kuka,tabbas da zata iya data tsaya ta bata baki,saidai itama tata zuciyar cike take fak da rauni da kuma alhini,don haka ta wuce zuwa office dinta.


Dai dai lokacin da mama sodangi dake tsaye gefe guda tana matse hawaye tayi toxali da ita sanda take wucewa zuwa office din nata,daurewa kanta yayi,ta shi kokwanton bilkisu ce koba ita bace?,idan itace ya akayi tazo nan?,yaushe ta zama likita?,to amma bilkisu batakai cikar wannan ba,batakai wayewar wannan ba,bata kai gatan wannan ba......saidai kuma batajin akwai lokacin da xaixo ta kasa gane bilkisun,yarinyar da kullum take kwana da ita ta kuma tashi da ita,yarinyar da har yau ta kasa barin kwanyarta,ta kasa mancewa da ita,tausayinta yaqi raguwa daga ranta bare ta manta da ita,amma ga akayi tazo nan?.


Tunaninta yazo dai dai dana afnan,wadda tunda ta fito ta zuba mata idanu,duk da cewa tana cikin alhinin rasuwar yarinyar,amma sai zuciyarta ke gaya mata classmate dinta ce,qawarta ce kuma abokiyar fadanta,wato bilkisu bilyamin,amma ya akayi bilkisun ta zama likita?,bayan tafi kowa sanin auren dole akayi mata,auren dolen da yayi silar tsigeta daga karatun da tafiso fiye da komai,ya akayi ta tsinci kanta a brasil bayan tasan cewa basu da qarfin da zata iya zuwa wannan qasar?,anya ko bilkisu ce?,amma ta yaya zata mantata,bayan kullum saita tunata,kullum da tausayinta take kwana take tashi,da kuma burin son sanin ina take?,ya rayuwa ta kaya mata?,indai ko bilkisu ce to zataso tabbatar da hakan.


Tana isa office dinta ta zare rolling din kanta ta zauna saman kujerar hutawa dake office din,dafe da hannayenta guda biyu ta saki wani irin kuka,hakanan mutuwar ke ci mata rai,tana tuno yarinyar a sanda take raye,tana tuna hirarrakinsu da amatu,zancanta daya biyu abbinta,ba kasafai take maganar mahaifiyarta ba kamar mahaifinta,bata tsammanin kuma duk yadda yarinyar ta damu da iyayen nata sunzo sun ganta har ta koma ga Allah,ranta na mata suya idan ta tuna yadda tazo jiyya qasar babu dumin uwa ko uba a tare da ita,duk da cewa a sannan take da buqatarsu cikin rayuwarta fiye da kowanne lokaci,tunda duka duka shekarunta shekarune qanana qwarai,sosai tayi kuka wanda ta jima batayi irinsa ba,sai mutuwar ta tada mata tabon rasuwar mahaifiyarta.


Tunda ya kifa kanshi ko sau daya bai dago ba,shi ba qaramin yaro bane abinda tayi a gabanshi kadai ya tabbatar masa tun daxun suhaiman ta tafi,jarumi ne na gaske a zuci da fili,ganin kukansa ba kowanne mutum bane ya taba katari dashi ba,uwa uba kuma ya tabbatar hawayensa zai zama silar rasa jarumtar mutane da yawa,hakan ya sanya ya zabi kasancewa a haka har zuwa lokacin da yaji an taba kafadarsa.


Abdulrashid ne tsaye a kansa,ya daga kai ya dubeshi da idanunsa da suka kada sukayi jaa sosai,abdulrashid din yadan matsa kafadarsa alamun lallashi,saiya dauke idanunsa ya maida ga gawar suhaima dake lullube.


Addu'a yayi mata sosai wadda tadan saukar da nutsuwa a zuciyar yarima,kana ya juya ya fice ya sake barin azeez dake zaune a wajen,yana iya jiyo muryoyin 'yan uwanshi daga waje,ciki harda sautin kukan safwa wadda aketa baiwa baki.


Tsahon wasu mintuna abdulrashid ya sake dawowa,still hannunshi saman kafadar azeez,muryarshi a tausashe yace
"Sunce mahaifi ko mahaifiya ake baiwa certificate of death....likitar kuma ita ke bayarwa,so saidai dana bincika likitar ta fita,saidai xuwa gobe idan Allah ya kaimu,sun rubuta duk wata takarda,ya kamata mu wuce da ita gida,idan anan za'a binneta to,idan ma saimun koma gidane ya kamata asan abunyi" kai kawai azeez ya iya gyadawa,ya miqe cikin qwararawa kanshi gwiwa ya isa inda gawar suhaima take.


Duk da nauyi irin na gawa haka ya dagata ya aza a kafadarshi,ba yadda abdulrashid baiyi ya ajeta a samo abun dauka su dauketa ba amma yaqi ya wuce gaba.


Fitowarsa ta sake rura koke koken da sukeyi,hakanan suka dunguma gaba daya suka wuce zuwa harabar asibitin don su wuce gida a motocin hayar qasar.


Fulani ce qarshe wadda take riqe da safwa tunda ta soma kuka,bata saketa ba kuma sai a yanzun data qara sauri tabi bayan azeez din,ita kanta cike take da alhini sosai,zuciyarta sam babu dadi,hakanan idanunta sun dan tasa saboda kukan datayi na rasuwar yarinyar.


Tayi nisa a tunani taji an bugi qafafunta,ta dawo da hankalinta da sauri gabanta taba furta
"Subha....." Saidai batakai ga qarasa maganar tata ba ta tsaya saman harshenta,sakamakon ganin da idanunta suka mata na yarinyar da tunu ta miqe ta kwasa da gudu abinta cike da quruciya tayi cikin asibitin abinta,da alama babu abinda ya shalleta da bugewar da tayi dama wanda ta buge din.


Tamkar idanunta zasu fado haka ta bita da kallo,zuciyarta na wani irin bugawa,tunda take bata taba ganin kama ta zahiri ba irin yau,bata taba ganin,to amma shin idanunta ne da suka soma samun damuwa ko kuwa gaskene?,zahiri ne?.


Tana tsaye tana wannan saqa da warwarar har yarinyar ta gama bacewa idanunta gaba daya ba tare data sani ba
"Ammi....ke ake jira,zamu tafi" ta tsinci muryar afnan,wadda ke tsaye bayanta,cikin mamaki kuma tana bin inda taga fulani aishan nabi da kallo tana tunanin me take kallo haka?,me kuma ya tsaidata?,saidai bata ga komai ba.


Ajiyar zuciya fulanin ta saki kana ta soma takawa afnan na biye da ita,hakanan takejin fuskar yarinyar na mata yawo cikin idanu har suka isa bakin motar aka bude mata ta shige.


Hukumar asibitin tuni ta bada ambulance an dauki gawar suhaiman,wanda acikin ambulance din azeez ya tafi.


Mai martaba da yayo waya kawai ya bada umarnin a mata suttura abunneta a nan din,Allah yayi anan qasarta take,kuma akwai musulmai a qasar,hakan kuwa akayi,isu isu suka zauna zaman jimamin rashin yarinyar,saboda ta shiga ran da yawa daga cikinsu,musamman kasantuwarta ta fito daga tsatson mutum mafi soyuwa a zukatan al'umma cikin masarautar,sai waya da suke amsa daga 'yan uwa da abokan arziqi dake nigeria ta tayasu ta'aziyya.


Ta bangaren bilkisu kuwa kukan data sha yasaukar mata da ciwon kai sosai,hakan ya sanya ta tattara ya nata ya nata ta wuce gida kawai,ba tare data tsaya cike takaddun da tasan dole zatayi ba saboda patient dinta ce ta rasu,amma tunda taga office din dr adam na nuna alamun yana nan,saita wuce din kawai,yasan zaiji da komai,a harabar asibitin ta samu amatu ita da wata nurse da tasu tazo daya,ta amsheta suka wuce zuwa gida.


A hanya amatun keta mata surutun ya zasu koma bata ga suhaima ba?,batace da ita komai ba,donta fuskanci batasan ta rasu ba,batasan kuma ta yadda zata gaya mata ta fahimta ba,haka yarinyar ta haqura tayi shuru,don tasan halin maman natasa sarai,aduk sanda suke mata surutu irin wannan indai sukaga shuru taqi amsasu to batason magana ne.

¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶


Misalin qarfe tara ne na dare agogon qasar brasil din,dai dai lokacin da yarima ke fitowa daga wanka,jikinsa sanye da rigar wanka wadda iyakacinta qauri.


A hankali yake takowa tsakiyar dakin,jikinsa na fidda sassanyan qamshin turarukan wankanshi,akwai qaramin towel a hannunshi yana goge ruwan jikinsa.


A yau yana jin sauqi cikin zuciyarsa fiye da kullum,yana jin haquri da danganar rashin tilon diyarsa yana shigarsa,saidai abune da yasan cewa bazai taba mantawa dashi ba.


Har ya isa gaban mudubi ya soma shafawa lallausar fatarshi mai saiya jiyo sheshsheqar kukanta,sam yama mance da ita cikin dakin,saboda yadda a kwanakin gaba daya ya sake dauke mata wuta fiye da yadda ta sanshi,saiya waiwaya sashen daya jiyo kukan yana kallonta.


Tana zaune takure waje daya,ta rungume gwiwoyinya a qirjinta,jikin gwiwar tata ta kifa hoton da yake da tabbacin na suhaima ne,saiya waiwayo gaba daya ya jingina da madubin gami da rungume hannayensa a qirjinsa gami da xuba mata idanu yana kallonta.


Cikin kwana uku ta fige ta rame,idan ka ganta saika zaci takaba take,zuciyarsa takanyi zafi a duk sa'ilin daya tuna yadda tayi watsi da rayuwar suhaima,tamkar bata damu da ita ba,koma na itace ta haifeta ba,hakanan yakanji zafi sosai idan ya tuna tahowar yarinyar wata qasa ba tare da mahaifiyarta ba,yaci alwashin hukuntata fiye da tunaninta kan abubuwan da take aikatawa harsai ta gane kuskurenta,to amma yanayin da yaga ta shiga yanzun yasa dukka wasu makamanshi suka zube,tausayinta ya soma kamashi,yasan cewa duk yadda uwa takai ga nuna halin ko in kula ga danta,ba qaramin dukanta zaiyi ba aduk randa akace yau babu shi a duniya,sai tafi kowa girgixa da jin xafi,kamar yadda a yanzun ya bayyana qarara kan safwa din,wannan dalilin ne kawai ya sanya yaji ya kamata yadan kawo sassauci cikin yadda yake matan,koda ba duka ba.


A hankali yake takawa har zuwa inda take zaunen,saiya zauna daga gefanta,ya saka hannunshi ya zare hoton ya aje gefe,sannan ya janyota zuwa cikin jikinsa.


Gaba daya ta shige ingarman qirjinsa tana sake sakin wani sabon kukan,wanda ke nuna dama tallafinsa take da buqata,ta cukuikuye gaban rigarshi sosai tana sakin kukan.


Baice mata komai ba sai hannunshi ɗaya daya saka yana shafan saman kanta,idanunshi na kallon wani waje daban,yayin da launin qwayar idanunsa ke soma canzawa,yana tuna abubuwa da yawa,wanda bai tsammaci zasu zo mishi ba a wannan lokacin.


Ya tuna sanda wata ke masa kuka mai bayyana pain da zuciya ke ciki shigen wannan,amma a lokacin bai tsaya ya mata wani dogon lallashi ba,hakanan yakan tuna wataqila har yanzu a doron duniya akwai wata halitta dake dauke da ciwo mai daci shigen wannan a zuciyarta tana rayuwa a haka,me yasa?,anya kuwa lokaci baizo ba da zaibi diddigin tsohuwar alaqa ba?,anya kuwa lokaci baiyi da zai bazama ya tono wannan alaqar da take da buqatar abincikata ba?,yana ji a jikinsa zuwa yanzun koda ya bijirema ammi baida laifi,Allah ba zaya kamashi ba,saboda ya cika mata dukkan wani burinta data qudirta akansa,ya cika mata dukkan wani qudirinta?,to me yayi saura?,ya nemota ya sauke haqqin dake wuyanshi,ya nemota duk inda take.


Tsahon wani lokaci kowannensu yana fama da tabo da ciwon dake cikin zuciyarsa kafin ya sauke ajiyar zuciya mai qarfi har qirjinsa yana dagawa,safwa dake kwance saman qirjin tayi luf bayan ta gama kukanta tana shaqar daddadan qamshin da jikinsa ke fiddawa duk da bai shafa kowanne turare ba,amma qamshi yabi jikinsa,ya kuma zauna masa sosai saboda tsabar yawan tu'ammali dashi da yakeyi kowanne lokaci
"Shikenan ta tafi my prince?,ta tafi ta barmu?" Saiya dagata daga qirjinsa,hannayenshi saman kafadunta yana kallonta
"Haka Allah ya tsara,kuma yadda yakeso haka za'ayi,koda mu ya kira dolenmu muje,bamu da wani sauran uzuri....idan bawa yayi haquri mai kyau sai hakan ya zame masa alkhairi nan gaba" kalamai ya gaya mata masu kwantar da hankali da sanya nutsuwa,sannan daga qarshe ya sanyata ta shiga tayi wanka ko zataji sanyi cikin ranta.


Shiryawa yayi shima ya sanya kaya sannan ya bude qofar dakin ya fita.


Falon gidan ya bulla,wanda yake dauke da dakunan da fulani mama sodangi,afnan da sauran barorinta suka sauka,don mom din safwa kwana biyu sukayi suka koma,don haka gidan saisu yasu.


Kitchen ya shiga da kanshi,yunwa yakeji amma kwana biyun nan baya iya cin wani abincin kirki,har ita safwan ya lura da haka,don kafin tafiyar mom dinta yasha jin tana artabu da ita.


Fresh milk mai sanyi ya ciro kwali biyu manya,saboda sosai yakejin cikinsa a fafake,mutumin daya saba baya wasa da cikinsa sam,ya dauki cups guda biyu sannan ya juya ya fice daga kitchen din.


Yana fitowa fulani itama na fitowa daga nata dakin sukayi kacibus,cikin kulawa take dubanshi da kwalin madarar hannunsa
"Da kayi magana idan kana da buqatar wani abun,basai ka shiga kitchen da kanka ba" duban kwalin madarar yayi shima sannan yace
"Ba wani abu,ita zan dauko kawai dama"
"Kana nufin madara kawai zakusha a abincin dare?" Tayi maganar tana juyawa gami da samawa kanta wajen zama,ganin haka shima saiya isa daura da ita ya zauna yana amsa mata
"Ta ishemu,ba wata babbar yunwa bace" kai ta girgiza
"Ban aminta ba,kwana nawa rabonka dakaci abinci,ina sane fa...." Kafin yace komai ta qwalawa afnan dake daki kira,a sannan tana waya ta sauko daga gadonta ta qaraso cikin falon da wayar a hannunta,don bata tsammaci harshi yana wajen ba.


Ganinsa awajen ya sanyata saurin katse wayar,ta soma qwaqule earpiece din dake kunnenta kana ta qaraso tana hardewa,saboda yadda ya kafeta da idanunsa masu dan banzan kwarjinin nan
"Gani ammi"
"Shiga kitchen ki samawa yayanku wani abuncin mara nauyi haka wanda bazai dauki lokaci ba" amsawa tayi da to sannan ta wuce ciki da sauri,ta sanya afnan ne saboda tasan duk wanda ta saka ya masa ba lallai yaci ba.


"A ina maganar yarinyar nan ta tsaya ammi?" Yarima yayi magana yana duban ammin tasu,fuskarta ta nuna alamun alhini kafin ta amsa mishi
"To....ana nan dai ana addu'a,ina kyautata zaton mijin auren ne har yanzu baizo ba,tunda koda yaushe addu'a ake,hakanan duk wanda yaxo ba korarsa take ba,ana bashi dama,Allah ne kawai baiyi ba" shuru yayi kawai yana dan tunani a ranshi,dukka yaran gidan banda 'yar wajen fulanin masanawa afnan ce kawai ta rage gaban ammin,wani lokaci yakan qalubalanci mace ta zurfafa karatunta yayi zurfi da yawa ba tare da wani tsayayye ko gamsashshiyar magana a kanta ba,wasu mazan sai su dinga mata kallon tayi girman datafi qarfinsu koda ba yawan shekar gareta ba,misali ga afnan din da karatunta yake zurfi a yanzu,uwa uba kuma ta fito daga babban gidan sarauta dayake da dumbin arziqi tarihi da nasaba,ba kowane zai iya fuskantarta yace yana so ba,duk da bata rasa komai ba daya danganci kyau kyakkyawan hali nasaba da tarbiyya ba
"Allah ya zaba abunda yafi alkhairi"
"Ameen" ammin ta amsa tanajin babu dadi a ranta.


Dukkan abinda ta burata a duniya babu wanda Allah bai mata ba,amma saiya zamana afnan din ta zama ta takashin baya ta fannin aurarwa cikin gidan,wannan shine abu qwaya daya tilo dake damunta a yanzu,bata kuma ta hanyar da zata maganceshi kota kawo qarshensa,wanda har abokan zamanta manyan abokan adawarta ke samun abun goranta mata da yada mata magana a yawancin lokuta,sauqinta ma duka yayyenta aka aurar babu sa'anninta da aka aurar bare abun ya ta'azzara,itace auta.


Tunaninta ya sake nisa,fuskar yarinyar da yadda ta bugeta kana taci gaba da tafiya abinta cike da quruciya,abun yakan yi mata yawo aka,yana kuma dawo mata akai akai,saidai tunani guda daya dake sanya mata relief kan wani hasashe da zuciyarta ta soma mata,hasashen data kira da banzan hasashe mara tushe bare makama shine,bata ga hanya ba ko,hakanan bataga hadinsu da wannan qasar ba,bare tace hasashen da zuciyarta ke mata ne ya tabbata,babubta wata hanya da hasashenta zai iya zama gaskiya,saita saki ajiyar zuciya tana jin nutsuwa kadan kan tabbacin da daya sashen na zuciyarta ya bata.

*_da sannu sannu dai kunkuru zaije inda jirgin sama yaje wata rana,kada ku damu,ku zama masu bibiya cikin nutsuwa ba tare da gaggawa ba😊😊_*
7/11/21, 4:34 PM - My Mtn Number: 54

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________

*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070



Mintina qalilan afnan ta dawo ta kammala,ta miqa masa plate din dake a rufe,da idanu ya mata alama takai mishi daki,saita juya zuwa dakin,cikin ranta tana mita da qunqunin rashin ganin amfanin matarsa,da ba zata iya tsaya masa kan cikinsa ba,da sun hada muhalli saidai su suyita hidima dashi,komai tafison a mata tana daga zaune yadda take tun daga gidansu.


"Munyi waya da mai martaba,yace ya kamata mu dawo gida hakanan,saboda jama'ar dakeson yi muku gaisuwa" kai ya jinjina sannan yace
"Kamar yaushe ya kamata kenan mu tafi,tunda ticket kawai zamu siya" dan shuru tayi kadan sa'an nan ta dora
"Idan ba damuwa nan da jibi ya kamata mu wuce" ya sake jinjina kanshi
"Shikenan,babu damuwa,gobe zanje na karbo certificate din mutuwar suhaima,jibin saimu wuce in sha Alla" ajiyar zuciya fulani ta sauke mai nauyi sannan tace
"Allah yayi mata rahama"
"Ameen ameen ya Allah" ya fada yana sadda kanshi qasa,shuru ya ratsa falon na wasu mintuna,sa'annan ya miqe yana yiwa fulanin sallama ya wuce xuwa cikin dakin.


Ya tars safwan tayi wankan tana zaune gefan kujera shuru ba tare da tana yin komai na,idanunta a kode suke sosai,ya qaraso ciki yana dauke idanunshi daga kanta,dab da ita ya zauna ya aje kwalin madarar saman wani dan qaramin tebur,sannan ya bude ya cika cup ya miqa mata,shuru tayi kamar ba zata amsa ba,amma ganin yadda ya tsareta da idanu ya sanyata tilas ta miqa hannu ta karba,ta soma kurba a hankali shi kuma yana ci gaba da kallonta,har sai data sha fiye da rabi sannan ta ajjiye masa tace ta qoshi.


Baice komai ba shima ya bude kwali guda ya soma kurba shima a hankali,sai daya sha kusan rabi sa'annan ya lumshe idanu yana aje numfashi bayan ya jingina jikinsa da kujerar.

¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶



Fashin da tayi na kwana biyu saboda ciwon kan data dawo dashi tun ranar mutuwar suhaima ya sanya a ranar larabar ta shirya da wuri don tafiya asibitin,a kwanaki biyun tayita fama da wayar dr adam kamar zaya zo ya dauketa,yayi mita yayi qorafi kan rashin bashi adress na gidansu yafi sau shurin masaki,amma yaci mata alwashin kome zatayi bazaya janye ba,ta kuma rubuta ta jjiye,saiya lalubo gidansu duk inda yake,hakan daya fada ya bata dariya,don haka saita saki murmushi kawai ba tare data ce masa komai ba.


Yau kam free take tasan amatu ba xata takurata kan zata bita

Please Login or Register in order to submit comment