Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

baqin ranta cike fal da wasi wasi.


*_PLEASE SUBECRIBE MH CHANNEL SAUTIN HIKIMA_*👇ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½

Watch
And
Share ðŸ™ðŸ½ðŸ™ðŸ½

https://youtu.be/p_fqPX2Ni9Y
7/11/21, 4:36 PM - My Mtn Number: 71
https://youtu.be/0PAxvmzE1Uw


*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070




A hankali ta shiga falon bakinta dauke da sallama,hakanan takejin wani irin nauyi ta kuma kasa daga idanunta ta kalli falon bare taga su waye a ciki har sai data iso ainihin falon.


Faduwar gaba taji saboda ganin fuskar dattijon wanda ke amsa sallamarta cikin sakin fuska dake cikin nadin farin rawani me ratsin gold,kwarjini da haibarsa sun cika falon gaba daya
"Maraba da 'yata bilkisu....maza qaraso nan" ya fada yana nuna mata daura dashi,ganin tana niyyar sulalewa ta zauna daga bakin qofar falon.


A hankali ta qaraso,sannan ta zame ta zauna a qasa kamar dazun kanta na kallon qasa,ta motsa labbanta da qyar wanda batasan me yasa tunda taga mutumin takejin wani irin nauyi ba tace
"Barka da warhaka"
"Barka kadai diyata,marhaban da surukata bilqisu" kasa amsa mishi tayi,sai gingirin da taji kanta yayi mata.


Shuru na wani sakanni sannan taji yayi gyaran murya sannan ya fara magana cike da dattako da kuma nutsuwa
"Sunana abdallah mu'az kaisa,mahaifi ga abdul'azeez...." Saiya dan dakata,yayin data sake daga kai a sace ta kalleshi,eh babu shakka,ga kama ta jini nan tsakaninsu,saita sake sadda kanta,yaci gaba da magana cikin hikima da nutsuwa
"Ya akaji da hidimar rayuwa,ina 'yan jikokina?" Gabanta yadan fadi,yasan dasu ne dama?,garin yaya?,waye ya gaya mishi gidan anty zuhriyya?
"Suna lafiya alhmdlh"
"Ma sha Allah"
"Amm....na samu labarin dukkan abinda ya faru tsakaninki da iyalina cikin satin daya gabata,a gaskiya ko a mafarki ban taba kawowa aisha ko abdul'azeez zasu aikata wani abu makamancin haka ba sam,sai gashi abun mamaki hakan ta faru,abun yayi matuqar girgizani da kuma daga min hankali,hakanan ya sakani cikin shakku da nazari..." Saiya dakata yana maida numfashi,da alamu abun yana tabashi sosai har yanzu cikin zuciyarsa
"Nazo da kaina wajenki diyata don na baki haquri,na kuma nemi gafararki.....karki dauka nazone a madadin abdul'azeez ko mahaifiyarsa,a'ah,nazo ne on behalf my self,nida kaina naga ya cancanci nima na baki haquri,saboda an cutatar da rayuwarki,an ruguxata ba bisa amincewa ko yardarki ba,an miki ta qarfi,kiyi haquri kiyi haquri ki kuma yafe ma masarautar kaisa gaba daya" wani irin kwarjini da nauyinsa takeji,da yake bata haqurin kamar zata nutse a wajen,indai har ta cika cikakkiyar yar adam,wadda ba butulu ba,ai bata da bakin magana sai godiya ga Allah,domin a yanzun ya mata komai,rashin cewa bata yafe din ba bataga me zai qareta dashi ba,don haka tace
"Ranka ya dade na yafe,Allah ya yafemu gaba daya" murmushi yadanyi sannan ya sake cewa
"Na gode qwarai da gaske....sannan akwai alfarma ta biyu da nakeso kiyimin,kada kice zaki duba wani abu ki tursasawa kanki wajen yin wannan alfarmar,a'ah....wannan zabinki ne,sai yadda kikace,ina mai neman alfarma a wajenki daki koma dakinki,kamar yadda abdul'azeez ya shaida min cewa ke matarsa ce,bayan ya maidaki gaban shaidu guda uku,mata biyu namiji daya,na kuma tabbatar da gaskiyar hakan....ina neman wannan alfarmar daga gareki ne domin kubutar da mutunciki da nasa da kuma na mahaifiyarsa da zaki taimaketa akan hakan" kanta ta daga da sauri ta kalleshi suka hada idanu,saitaji nauyi tayi maza ta sake duqad da kanta,alfarmar ta mata nauyi da yawa,har yaso ya fuskanci haka,saiya dora da cewa
"Kiyi haquri,ki kuma taimakemu,neman komawarki bawai yana nufin ki yafewa abdul'azeez ko aisha ba,kina iya ci gaba da hukuntasu ta yadda kikaso....sannan koda kin amince...zaki koma dakin nakine a duk sanda kikeso,igiyar aurenku ce banason a tsinkata kodon albarkacin albarkar yara har biyun da Allah ya baku,sa'annan shi kansa bazan shaida masa hakan ba,har sai kin gama hukuntashi son ranki,kin kuma gamsu a jiki da zuciyarki cewa hukuncin yayi miki.....don Allah diyata" ya furta yana dan zamowa kamar zai sauko qasa.


Sosai taji wani irin nauyi da kunya,da kuma tsoron kada fa ya sauko ya durqusa mata,mutumin da aqalla yama girmi mahaifinta bare ita,data tabbatar sa'ar autarsa afnan ce,don haka cikin firgici da sauri ta furta kalmar
"Na amince" ba tare data shiryawa fadar hakan ba.



Tana iya jiyo ajiyar zuciyarsa,ya saki murmushi wanda ya bayyana sannan yace
"Alhmdlh,alhmdlh,ba shakka kin cika 'ya ta gari,kuma nagartacciyar uwa ga jikokina,na gode miki sosai bilkisu,na gode qwarai da gaske,ubangiji ya albarkaci rayuwarku,yadda aka miki katsalandan a rayuwarki ina roqar sarki Allah ya sake miki juyi da sauyin rayuwa mafi alkhairi" addu'a sosai ya dinga jerowa tana amsawa da amin,har zuciyarta tayi wani irin taushi,hawaye ya soma sauka saman fuskarta.


Sanda ta fita sai data turo.masa su amatu,sun jima a wajensa kafin su dawo cike da kyautuka.


Batasan iya dadewar da sukayi ba,saboda tunda ta dawo tana dakinta a kulle,kwance saman gado tana rusgar kuka,tana kuma tuhumar kanta,anya batayi kuskuren amincewa zata koma rayuwa cikin wadan nan ahalin ba?,ta kuma amince babu neman shawara ko yarda antyn tata wadda take kamar mahaifiya a wajenta,wadda ta tsaya tsayin daka,kai da fata wajen inganta rayuwarta,harta kawo bigiren da take kai a yanzu,uwa uba kuma mahaifinta,duk da shi ya kasance sila kuma dalilim afkuwar komai,amma a yanxun ai ya canza,iri sauyin da bata taba zata ba,kuma kusan yama fita jin ciwo duk sanda ya tuna yadda al'amuran suka gudana.


Ta fannin anty zuhriyya tana ankare da ita,ta kuma san kwanan zancen,don haka ta hana kowa rabar dakin da take,ta bata lokaci,tasan nan da wasu lokutta zata sauko komai zai daidaita,saboda ko a yanzun itama tafi mata sha'awar takoma gidan uban 'ya'yanta,amma har yanzu akwai jiqaqqiya tsakaninta da fulani,batajin zata barta haka.


Ganin har sallar isha'i bata fito ba ya sanya anty zuhriyyan ta nufi dakin nata,inda tabar duka yaran suna cin abincin dare,tayi knocking qofar,a sannan bilkisun na saman abun sallah,wanda tun sallar magariba bata tashi daga kai ba,tayi istihara yakai sau goma duka a waje daya,tana neman zabin Allah,sai taji ta samu nutsuwa 'yar kadan cikin zuciyarta.


Tashi tayi ta bude mata,ta shigo idanuta a kanta,kana ta samu gefan gadon bilkisun ta zauna kana tace
"Tunda baqonki ya tafi baki fito ba,hala lafiya lau?" Kanta a qasa tana murza tafin hannunta,tana jin wani nauyin anty zuhriyyan kan hukuncin data yanke ba tare da shawartarta ba,ta rasa ta inda zata soma gaya mata,sai taji qwalla ta cika idanunta
"Na aikata wani ganganci na saurin amincewa da alfarmar daya nema a wajena ba tare dana shawarci uwa a wajena ba,saboda girma da shekarunsa...." Murmushi mai sauti anty zuhriyya ta saki wanda ya baiwa bilkisu mamaki
"Kada ki damu daughter....qarshe dai kice kin amince zaki komawa aurenki ne....alhmdlh....hakanma kamar wani tarnaqine ga maqiya da zaki musu,kada ki damu,duk hukuncin da kika yanke ina bayanki dari bisa dari,matuqar babu cutarwa ko keta dokar Allah" wani wawan ajiyar zuciya ta sauke mai sauti a sarari,anty zuhriyya ta kalleta,can qasan ranta cikin sigar tsokana
"Daughter.....irin wannan ajiyar zuciya haka?,haka dama kikeson yarima?" Da sauri ta dubeta tana gwalalo idanu cikin mamaki
"So ummi....don Allah kibar fada,wallahi naji dadine da ranki bai baci ba" kaitake gyadawa tana gumtse dariya
"A'aha,ga abu a sarari na gani,soyayyace zallah..."
"Wallahi ban taba jin sonshi a raina ba ummi" ta fada kamar zata saki kuka,anty zuhriyyan ta tarbi numfashinta
"Meye na saurin shiga masallaci haka?yo in banda soyayya meya hana 7yrs idonki ya qyasa wani harki aureshi?,saida kika jira yarimanki"
"Ki yarda dani ummi...kin manta ban taba sanin fuskarsa ba....Allah ba qaunarsa"
"Shshshs!!!!" Anty zuhriyya tace dariyar da take boyewa tana qwace mata
"Bansan sakarya bace ke sai yau,uban yaran naki kike cewa baki qaunarsa baki taba qaunarsa ba?,tome zobensa yakeyi a wajensa?" Idanu ta sake fiddawa,sam ta mance dashi,ya akayi antyn ta gani
"Su amatu na ajewa" dariya sosai ta saka sannan ta dubi bilkisun da kyau
"Kina sonsa,baki sonsa yanzu ba wannan zancan akeyi ba,abinda na sani kawai shine,zamu qona ran abokan adawa....zan kuma soma gyaran diyata tun yanzun,zan soma shiryata komawa gidan uban 'ya'yanta" sosai bilkisu ta narke,gabanta na faduwa ta kalaman anty zuhriyyan
"Nifa anty bazan koma yanzu ba,saiya gane kurenshi,kuma ma idan na koma ai kamar yaci galaba a kaina" idanun ta zaro itama
"Gane kure kuma na nawa daughter?,har abada kuma koda kin koma koda baki koma ba kece kikaci galaba a kansu,kin gama dasu,tunda kika haifa musu yara,gasunan,duk wanda ya kallesu yaga masarautarsa KAISA zammm....so ki aje kome gefe ki fara karbar gyara daga wajena" daga haka ta miqe tana niyyar fita,sai bilkisun tace
"Zanje gobe naga baba"
"Allah ya kaimu" ta amsa mata tana qarasa ficewa daga dakin.


¶¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶¶¶

Motoci biyu ta tanada domin yin mata rakiya,don tana da buqatar sirri,ba kowane takeson yasan inda zata da kuma abinda zai kaita ba,sai wasu motoci ukun da aka cika da kaya na alfarma iri iri,kayan qyale qyale na mata,saika rantse da Allah wani lefen 'yar gatan xa'a kai,kama daga tufafi,kayan kwalliya mayafai jakankuna takalma da sarqoqi harda gwalagwalai.


Cikin shiga ta alfarma ta nemi izinin fita wajen maimartaba,ya kuma bata izinin ba tare da yasan inda xata je ba,bare azeez wanda tun jiya daya dawo gidan yake kwance a sashensa cikin wani irin ciwo mara misaltuwa,ba tare da sanin kowa ba.


Tun safe data tashi ta kammala dukkan ayyukan da tasan tana yi cikin gidan,kana fa koma dakinta ta shirya tsaf cikin wata doguwar riga da aka mata dinki da shufom da duwatsun shuwarisky masu qyalqyali da daukar idanu,saita bada wani samfur na daban,ta kuma haskata sosai,hakanan tayi kyau kai bakace ita ta haife amatu da abdul ba,tsaf zaka mata kallon budurwa.


Tana fitowa falon tana lalubar atm dinta cikin jaka,don tana son ta yiwa babanta siyayya idan ta fitan kafin taje gidan,amatu ta kalleta
"Mami....nazo muje?"
"Babu da wanda xan fita,nima ba jimawa zanyi sosai ba,abinda ko wanka ma bakuyi ba,ku zauna bazan dade ba....,gidan daba baqonku bane,kusa ko yaushe kuna tafe.....ummi zan wuce"
"Saikin dawo,ki gaishesu,yauwa...,idan kin dawo ki tsaya don Allah ki tsaya a bawa road ki karbomin dinkunan nan wajen latif"
"In sha Allah" ta fada a gaggauce tana ficewa a falon.


Najwa anty zuhriyya ta kalla
"Yau kam da alama qazanta kukeji ko?" Najwan ta dubi anty zuhriyya
"Wlh yau bansan zubawa jikina ruwa"
"Kyaji dashi,tunda ke baki da niyya hada kan abeed amatu da abdul ki musu,duk sanda kikaso ke kyayi" waiwayawa tayi ta dubi abdul,kamar yadda ta zata din kuwa ya hade ranshi qyam,cikin dariya dariya tace
"Ummi kema kinsan ba'ayiwa abdul wanka tuntuni ya yaye kanshi" duban yaron tayi,yaro qarami sai manyance,shi Ala dole ba za'a jikinsa ba,shi yasa ya daina yarda ayi masa wanka
"Ku shiga tare idan kin gama musu ki hada masa nasa ruwan na daban yayi,ai babban mutum ne dama bai kamata anty najwa din ta dinga ganin jikinsa ba" dariya sukayi gaba daya,shima sai a sannan ya sassauta fuskarshi.


Ba'ayi minti biyar da shigar yaran ba mai gadi yayi knocking qofar falon,ta bashi izini ya tura qofar ya shigo,yana tsaye daga bakin qofar falon ya gaya mata saqon
"Hajiya....baqi kukayi cikin motoci,suna son a bude musu ne su shigo" tayi mamaki sosai,saboda iya saninta tasan basu da wani baqi,amma sai tace a bude musu su shigo din,ya amsa da to kana ya juya ya fice,saita miqe,ta isa window din dake can qarshe yana fuskantar harabar gidan,ta yaye labulen tana leqen masu shigowa.


Motocin da taga suna shigowa sai suka bata mamaki,saita saki labulen ta koma falo tana jiranjin su waye zasu shigo.


A hankali ta soma jin kamar banbadanci da kirari har zuwa qofar falonta,tana daga tsaye tana duban qofar falon,fulani ne akan gaba,sauran barorinta biye da ita.


Sosai anty zuhriyya ta zuba mata idanu,tana hango kamannin dake tsakaninta dasu amatu da kuma yarima azeez,cikin sakanni 'yan kadan kwanyarta ta gaya mata ko wacece matar.


Dukkan wani hade rai da bacin rai ta tattaro ta azawa fuskarta,ta kuma ci gaba da kallonsu har zuwa sanda suka gama shigowa
"Su waye ku?" Ta fada kanta tsaye idanunta cikin na fulani
"Mu baqi ne daga masarautar kaisa....muna tafe ne tare da uwar gijiyarmu,amarya ga sarkin kaisa,mahaifiyar yarima abdul'azeez magajin sarki,wanda ya taba auren diyarku" wani kallon banza ta watsawa mai bayanin,sannan ta kuma sake maida idanunta ga wata dake kusa da ita
"Ba wannan dogon bayanin na buqaci ji daga gareku ba,wa kuke nema?,saboda babu wata alaqa data taba hadamu da wata masarauta ma balle ta qasar nan a iya namu sanin"
"Uwargijiyarmu ce tazo ta gana da tsohuwar surukarta domin samun sasanci" kubra mafi kusanci da fulani cikin hadiman ta fada,sake watsawa mai bayani na gaba kallon banza tayi sannan tace
"Kece zakiga bilkisun?,ko kece uwar gijiyar da kiketa rattabo bayani haka?,mu duka ahalinmu babu wata data taba rabar masarautar kaisa bare tayi auratayya da waninku,so ina tsammanin kun samu buguwar qwaqwalwa" zata sake bada amsa fulani ta daga musu hannu,gami da nuni da cewa dukkansu su fice,ba'a rufa wasu sakanni ba duka suka fice din kuwa,falon ya zamana daga ita sai anty zuhriyya.


"Na tattako da kaina nazo ne domin samun maslaha,da kuma gyara barakar dake tsakanin maimartaba dani kaina da kuma yarona...inason a wannan karon idan so samu ne.....ta shiga masarauta ta bayyana yafiyarta ga abdul'azeez dani kaina,na mata alqawarin bata dukkan abinda takeso,na mata tanadin rayuwa mai inganci,hakanan ko a yanzun ma da tarin alkhairi nake tafe,idanma tana buqatar ta sake koma masa ne a matsayin matarsa,a shirye nake akan hakan,matuqar komai zasu daidaita".


A kaikaice anty zuhriyya ke mata wani kallo,zuciyarta taxo iya wuya,wannan damar take nema babu shakka kuma gata tazo mata,idan har bata amayar da dukka abinda ke zuciyarta ba,idan har bata hana idanun fulani bacci ayau da zafafan maganganu masu quna ba tabbas ita din bata haifu cikin uwarta da ubanta ba,hakanan bata da rana a wajen bilkisu.
7/11/21, 4:36 PM - My Mtn Number: 72

*Shiga tasharmu ta SAUTIN HIKIMA kayi subscribe,don samun da dadan litattafai*
👇ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½ðŸ‘‡ðŸ½
https://youtu.be/0PAxvmzE1Uw

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070




"Matsalar guda daya kenan....bakya ganewa....kuma ban saka ran zaki gane ba,tunda har yanzu baki gane din ba,amma bari na baki wasu alamomi ko zaki gane din" sai anty zuhriyya ta gyara tsaiwarta tana harde hannayenta a qirji,tana kuma yiwa fulani wani irin kallo
"Hala sanda kuka shigo gidan nan idanunki a kulle suke,koda a bude suke toba shakka girman da munin abinda ke zuciyarki ya rufe miki idanu.....ki kalla gidan nan da kyau,tun daga waje zuwa ciki....mun miki kama da mabuqata?....koda munyi zubin mabuqata,ba shakka Allah ne ya yisu,kuma ya yisu a hakanne bawai don baya sonsu ba,ya yisu ne saboda jarrabawa da sanya rayuwar kowanne bawa bisa mizanin jarrabawa,kuma ya yisu a hakane badon masu kudi mulki ko sarauta sun kasance mafiya soyuwa a wajen Allah fiye dasu ba"


"Naji kina wasu maganganu,duk da bani da tabbacin cikin hayyacinki kike,to idan ba'a hayyacinki kike ba gwara ki koma daidai,dukka tatsuniyar da kika lissafa dai dai take da dawowar matacce duniya,a yanzu bilkisu ya muku nisa,hakanan ta tsere muku,kwatankwacin yadda sama ta yiwa qasa nisan taraza mai tarin yawa"
"Koda ace xaki hada dukkan abinda kika mallaka keda ahalinki kaffffff......baku da abin maida bilkisu cikinku saboda girma ko martabar wannan abun,mu MUTUNCI muka zaba,MARTABARMU tafi gaban komai,hakanan KIMARMU babu wani abu da za'a mata farashi ko a daidaita ta dashi,KUDI ba shine arziqi ba,DUKIYA ba itace wadatar zuci ba,hakanan ƘYALE ƘYALEN RAYUWA ba shine samun nutsuwa da kwanciyar hankali na,saboda haka shawara guda daya xan baki.....sawunki a likkafa ki fita salin alin ki koma inda kika fito,ke da dukka wani tarkace naki da kike masa kallon arziqi ko kuma dukiya,koda sawun tayar motocinku bana buqatar tozali dasu bayan gushewarku bare wani abu daban".


Mamaki mai dimbin yawa,al'ajabi data dinga jinsa kamar a mafarki su suka dinga mamayarta,a iya tarihin rayuwarta,babu wani wanda ya yaba tsayawa haka ya gasa mata maga ganu makamantan wannan,ta tashi tsahon rayuwarta ana mata biyayya,ta tashi tsayin rayuwarta ana girmamata,ta tashi tsahon rayuwarta ana kiyaye dokokinta da bacin ranta,amma yau sai ga wata halitta tana gaya mata magangun da bata taba jinsu da kunnenta a kanta ba tsayin rayuwar tata,cike da zallar mamaki tace
"Kinsan me kike fada kuwa?,shin kin riqe kuqa dawa kike magana?" Murmushin takaici anty zuhriyya ta saki,kana ta tako dab da fulanin ta tsaya a gabanta
"Kinci sa'a ban riqe sunarki ba,amma dai nasan cewa ina magana ne da wata uwa kuma mata ga sarkin qasata,mace mai yawan dagawa alfahari da kuma zallar zalunci danne haqqin marayu da rashin sanin darajar dan adam.....ki fitamin a gida tun labarin zuwanki baikai kunnen sarki abdallah mu'az ba,tun ban wargaza shirinki da yayi saura ba" gaba daya ta gama daureta da jijiyoyin jikinta,siffofin data siffantata dasu sai suka tsaya mata a rai,koda yaushe jama'arta kallon mai kyauta tausayi haqqin na qasa da ita suke mata,amma yau sai gashi an siffantata da siffofi mafiya qyamata a awajenta.


"Ummi....ni wannan nakeso anty najwa yau ta sakamin"
"Nima wannan ummi don Allah...amma taqi wai saidai idan mami ta dawo" muryoyin amatu da abdurrahman da suka fito a guje a jere riqe da kayan a hannunsu ta karade falon kowa na saurin nunawa anty zuhriyya.


Cak idanunta suka sauka kan fuskokin da suka kusa sanyata shidewa,fuskoki guda biyu masu kama ta sak da sak da fuskar abdul'azeez dinta,ta wani sashen kuma tata fuskar take hange jikin tasun,sai take ganin kamar mafarki kamar almara,don haka ta soma matsawa gaba kadan don tagani abinda idanunta ke gane mata da gaske ne
"Kul!ahir dinki!" Ta tsinci muryar anty zuhriyya kamar mai bata umarni tana fadi
"Karki soma kusantar inda suke.....kamar yadda kika koresu tun suna gudan jini....,sun koru koruwa ta har abada,sun barranta daga kasancewa jininki,ina fata zaki hanzarta fita,don bamu buqatar gama nunfashinmu da naki" daga haka ta qarasa ta kama hannayensu zuwa ciki,suna waiwayen fulani tare da tunanin wacece ita?.


Wani irin gumi ne ya yanko mata,qafafunta taji sun matuqar sanyi kamar ba zasu iya daukar gangar jikinta ba,su waye wadan nan yaran masu tsananin kama da abdul'azeez
"Jikoki,yayan bilkisu da abdul'azeez" wani sashe na zuciyarta ya bata amsar tambayarta,mummunar faduwar gaba ga ziyarceta,tare da wani gumin da yafi na dazu dumi da jiqa sassan jiki,kada dai ace sune cikin data kore samuwarshi?,kada dai ace da gaskene,da gaskene abinda suka fadi,a sanda ta hana azeez ya mata bayani,a sanda ta kasa tsaiwa ta saurareshi?.


Wani irin mugun sarawa kanta yake,a matuqar salube jikinta taja qafafunta da qyar ta fice,tana jin sanda suka take mata baya suna binta da kirari harta isa bakin motar,ganin batace a sauke kayan ba ya sanya ba wanda yayi maganarsu,aka tada dukka motocin suka fice daga gidan.


Cikin motar riqe take da kanta,babu abinda ke mata kaikawo sai magangun anty zuhriyya,daga qarshe kuma fuskokin yaran su mata kutse cikin tunanin nata,gaba daya kwanyarta ta burkice,tana da buqatar qarin bayani,don haka ta shaidawa kubra,ta gayawa driver sassan yarima azeez zasu wuce kai tsaye,a kuma bincika a tabbatar mata yana nan kafin su isa din.


Har wani huci anty zuhriyya takeyi ita kadai,ranta a bace yake,wato yadda malam bilya ya zubda musu qima akan kudi har yanzu da wannan take kallonsu?,koda yake ko yanzun alhmdlh,ta fadi da yawa daga cikin abinda ke mata kaikawo a qirjinta,ko a yanzun ta rage wani nauyi da radadin.


Sam batayi niyyar shaidawa bilkisu ba,abbaa kawai tayi niyyar gayawa,don kada yaga jinkirin komawar bilkisu dakinta,don ta tabbatat ta gayawa bilkisu abinda ya faru za'a samu hutsancewarta ne kan komawar,ita kuma tafiso ta koma din,ko don yadda yarima yake binta,ta koma taga qarshen iko da iyawar aisha fulani!.


A hankali tayi sallama falon da yake mallakin mahaifin nata,ya daga kai yana amsa mata lokacin da yake shafawa qafafunsa man zafi,wadanda a yanzu kuma kusan suner rabin matsalarsa,don ko barcin kirki sai sunso suke barinsa yayi.


Murmushi dauke a fuskarsa yake maraba da bilkisun,kai bakace shine wannan malam bilya din ba,wanda a baya bai damu da kuka ko dariyarta ba.


Itama fuskarta dauke da murmushi ta qaraso cikin dakin,ta aje jakarta cikin sauri tana karbar kwalban man tana cewa
"Baba bari na samu ladan nima,naga hannunka bai kaiwa wani wajen" ta fada tana xama gabanshi ta soma shafa masa
"To ya zanyi,ita yanxu kaltume kafin ma ta samu damar zuwa ta shafamin na gaji da jira,hidima sun mata yawa,barin yanxun da take ita kadai" cikin salo tsokana bilkisun tace
"To kodai bazawarar da na gano a bayan layinmu xanwa magana?" Daquwa ya watsa mata
"Uwariyo....yauni na xama kakanki maigado?,ai ni yanzu mace dayace a duniya inda tana nan xan iya zama da ita,kuma nake marmarin zama da ita,nakejin inama zan ganta,saidai ta yimin nisan da babu damar sake haduwa har sai na cimmata,maimunatu,mace ta gari da banga irinta ba kaf rayuwata,salihar mace da nake yaqinin biyayyar miji zata sadata da aljanna in sha Allahu,ina miki fata maigado,duk da kin debi da yawa daga cikin halayenta,amma ina miki fatan biyayyar miji da haquri koda kwatankwacin na maimunatu ne" ya tuna da mahifiyarta,kuma sosai abun ya taba ranta,saita sadda kai qasa,maganar da yayi kamar yasan lamarin dake tafe da ita.


"Kamar akwai magana a bakinki mai gado" ya fada yana dubanta,shuru tayi na wasu sakanni sannan tace
"Kayi haquri baba,nayi wani hukunci ne ba tare da na baka dama ko naji ta bakinka ba" bata boye masa dukkan yadda sukayi da maimartaba ba ta shaida masa,murmushi ya saki,ya tabbatar batasan saida ya soma ganinsa ba kafin ita
"Baki kuskure ba maigado,abinda kikayin shine dai dai,kuma yanzun dukkanmu bamu da wani sauran hukunci a kanki,dukan hukunci naki ne.....duk yadda zan soki bilkisu kona kare miki haqqi ko martabarki bazaikai naso ganinki a dakinki ba,cikin martaba da rufin asirin aure,saidai idan harke din hakan bai miki ba" shuru tayi tana nazari.


Muryar mahaifin nata ta katseta,magana yake mata cikin sanyin murya da lalama,gami da nasiha da kuma sake neman afuwarta kan abinda ya aikata mata.


Ta jima a wajen shi,har zuwa sanda lokacin da ya tabbatar da cewa ta nutsu a xuciyarta sannan ya rabu da ita ta shiga cikin gidan wajen 'yan uwanta


A ladabce sunusi sarkin sassan yarime ke amsawa fulani ke amsa mata cewa yariman yana ciki,yanason mata bayanin cewa kwanakin duka da suka biyo baya suma basuga wulgi ko duriyarsa ba,amma basu samu damar hakan ba harta wuce zuwa ciki.


A mamakance take bin ko ina na falukanshi da kallo,babu wata alama dake nuna mata cewa yana nan din,dukkan alamu sun nuna cewa kamar an dauki wasu kwanaki ba'ayi amfani da bangaren nasa ma gaba daya ba,ko wanne qwan lantarki na a kashe,ba abinda keyi sai ac da keta fidda uban sanyi,tanayi tana kashe wasu,wasu kuma tana rabuwa dasu,cike zuciyarta fal da mamaki,ta tsammaci ma bai qasar,donko sanda sunusi yace mata yana nan tayi mamakin jin hakan.


Bedroom na qarshe tayi nasarar samu a bude,an kara qofarshi,ta tura da

Please Login or Register in order to submit comment