Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fushi
"Kina nufin na zura idanu?,kinaso ki cemin na qyaleshi yaci gaba da mu'amala da wannan 'yar talakawar wdda ba sa'ar aurensa ba?,na qyale ya maido rayuwasa baya bayan andade da wuce wajen?" Ta fuskanci ta dauki zafi sosai,hakanan tayi nisan da bata ko jin kira bare ta amsa,don haka saitayi shuru ba tare data sake tankawa ba.

Shuru ya sake ratsa falon,tsanar bilkisu da ada bata jita ba tana neman samun muhalli da gurbi cikin zuciyarta,qarin wasu mintuna suka sake shudewa kafin ta sake magana
"A kowanne lokaci yarinyar nan itake shiga tskaiyar lamurana da tsarina ta nemi wargazashi,koda yauahe saita zama dalili na bacin raina,tun daga sanda na shigo da ita k
Lamurana kawo yau,yau gashi zata zama sila na tarwastewar qima daraja da martabata data yarona a idanun duniya,abdul'azeez bai taba bujirewa ko saba umarni na ba tunda na haifeshi,koda kuwa bayaso,koda bai dace da ra'ayi ko zabinsa ba sai data shiga rayuwarsa,ta yaya zan dubeta da idanun tausayi ko qauna?,sam sam....matuqar kuma ta zama sila na bacin martabarmu ba shakka sai tayi nadamar sanin fulani aisha da zuria'arta....ku kiramin yarima a waya,ina da buqatar magana dashi" ta bada umarni kai tsaye,ba tare data damu da wanda zai kirashin tsakanin umma luba da mama sodangi ba,burinta kawai ta sameshi a waya taji muryarsa.


*YARIMA ABDUL'AZEEZ*


Tun randa ya koma din ya tabbatarwa da ranshi bazai iya zama ba ba tare daya risketa gidansu ba,bisa adreshin da yake gani nata a wayarshi.


Misalin bakwai na dare ya gama shirinsa cikin shigar sarauta dake nuna ainihin asali da tsatsonsa,dukkan wani cikar kwarjini haiba da kamala sun bayyana tattare dashi,ya dauki mota shi daya ya fita,bisa jagorancin wayarshi dake masa nuni da hanyoyi da kuma titunan da zaibi har ya sadashi da qofar gidan.


Kyawawan tafiya ta minti talatin da biyu ya tuqe a qofar gidan,cikin nutsuwa ya samu wajen daya dace yayi parking,ya kashe motar ya fito yana kallon wayarshi dake nuno mishi arrow na saitin gidan.


A hankali ya dauke fuskarshi da kan wayar,ya aza idanunsa ga qofar gidan da yake fuskanta.


Sosai ya zubama qofar idanu,yana jin wani abu na yawo cikin zuciyarshi da ruhinsa
"Yanzu nan ne 'ya'yanshi da matarsa suke?,yanzu haka suna ciki?" Saiya dinga jin kamar ya sanya kai kawai cikin gidan,ya shiga ya daukosu kana ya sakasu a mota suyi tafiyarsu,su tafi can da nisa inda zai koya musu sabo dashi,inda zai koya musu yadda zasu qaunaceshi,su rayu abunsu su kadai ba tare da kowa ya shiga ciki ko ya kawo musu cikas ba.


Yanke tunanin yayi da hanzari yana maida wayar aljihunsa,kana ya soma takawa yana durfafar gidan.
7/11/21, 4:34 PM - My Mtn Number: 61
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070



Dukkansu suna zaune a falo suna kallo,yayin da najwa kecin abinci daga gefe guda ita da abdurrahman a kwano daya,anty zuhriyya da bilkisu kuma na zaune saman kujera,kusan anty zuhriyya ke kallon sosai fiye da bilkisu,wadda ta kasa hankalinta gida biyu,rabi yana ga tv,rabi kuma yana ga chart da suke da hannatu tana sake tambayarta lamuran gidan nasu,da sauran sabbin abubuwa da batasan dasu ba.


Ajiyar zuciya ta saki,wadda ta saka anty zuhriyyan juyowa tana kallonta,suka hda idanu,sai bilkisun tace
"Hakanan zuciyata tayi nigeria ummi"
"Mun kusa in sha Allah,don ba lallai abba ya bari mu qara wata biyu bama.....amma tun jiya nakeson tambayarki.....wannan tafiyar nidai a idanuna sai naga sam bata amsheki ba,da kika dawo a birkice na ganki,kamar wadda taje jinya?" Shuru ta danyi zuciyarta tana raurawa,babu wanda ke saurin karantarta irin anty zuhriyyan,bata da wata uwa a yanzu sama da ita,don haka bata boye mata ba,ta karanta komai,duk wani abu daya faru daga zuwanta dubai zuwa dawowarta.


Shuru itama antyn tayi cikin nazari da tsantsar mamaki,koda zata lamunci komai ita dinma ba zata yarda da tatsuniyarshi na cewa da yayi bilkisun har yanzun matarsa bace,wannan zallar rainin wayone da kuma rainin hankali.


"Kamar yadda nace miki ne,banason ki sanya damuwa cikin ranki,babu wanda ya isa ya sake shiga rayuwarki kamar daa,babu kuma wanda a yanzu ya isa ya tilastaki ko yi miki dole a dukkan wani sha'ani daya shafi rayuwarki,ki rabu dashi yayita bibiyar,wala'alla lokacin sakayyarki ne ubangiji ya kawo miki,lokacin da zasu girba abinda suka shuka....".


Dire kalamanta na qarshe yayi dai dai da soma bugawa da qaraurawar ta somayi,da alama akwai mai neman shigowa ciki kenan.


Najwa anty zuhriyya ta yiwa umarni taje ta duba,suna ci gaba da tattaunawa da bilkisu,babu jimawa ta dawo fuskarta dauke da murmushi,saboda kalaman da baqon ya gaya mata,kada tace me kama da amatu ne,idan ba haka ba tun daga yau ganin farko zasu fara fada dashi,don tana budewar abinda ta soma gani kenan,bata kuma yi qasa a gwiwa ba ta fada mishi kanta tsaye,yana da tabbacin indai ta fadi hakan ga bilkisi,babu abinda zai sanyata fitowa,daga nan kuma an samu matsala,shi yasa ya buqaci tayi shuru,saidai duk da haka bakinta motsi yakeyi,neman wanda zata gayawa taga mai kama dasu abdul takeyi.


Cikin mamakin waye baqon nata ta ari hijabin anty zuhriyya da yafi kusa da ita ta saka bayan antyn tace mata
"Wataqila adam ne" sai ta gamsu da hakan,don tasan akwai maganganu masu yawa a bakinsa game da ita da kuma abinda ya faru a duba,saidai kuma ai bai gaya mata zaizo ba,duk da wannan bata fasa fita ba,saboda zarginta yafi qarfafa akan cewa shi dinne.


Yana tsayr harde da hannayensa a qirjinsa,ya juyawa qofa baya,don haka bata yadda zataga fuskarshi har sai ta iso inda yake tsaye.


Dab dashi ta soma jiyo qamshin nan da yake tambarinsa a wajenta,yayin da shi kuma jikinsa ya bashi tana dab dashi,ya waiwayo da hanzari lokacin da ita kuma zuciyarta ke gaya mata shine take shirin juyawa cikin gida cikin tsoro fargaba gami da mamakin ta yaya akayi yasan gidansu.


Cike da kuzari gami da karsashi yayi hanzari shan gabanta kamar zai shigr jikinta yana jifanta da wani irin kalo mai nauyi,sai tayi hanzarin ja baya cikin fushin nan nata dakan taso mata duk sanda sukayi face to face dashi
"Janyemin a hanya zan wuce" sassanyar murmushi ya saki kamar babu wani abun dake damunsa sannan yace
"A fuska kamar baki zubin masu fada ba,amma ga mamakina sai.naji kin iya,a qalla kyadan dagamin qafa kwana da kwanaki bamu hadu ba,banga alamun kinyi kewar koda takurata a gareki ba,bayan ni kuma mahaliccina ne kadai yasan ya na kasance a kwanakin,kin hanamin ganin fuskarki,hakanan ko sau daya baki bari uban daya shekara bakwai baiga fuskokin kyautar da Allah yayi masa ba,hakanan baki barsu su kansu sunji dumin mahaifinsu ba".


Zallar rainin wayo qarara ta hango cikin kalamansa,kamar ma ba wani abu bane mai girma tsakaninsu ba,kamar ma ba wani abu ya aikata ma rayuwarta ba,yanason maida komai wasa,yana son maida komai ba komai ba,yanason kuma ya nuna kamar ya manta dukkan abinda ya farun,tunda har gashi yana so yana kuma shauqin ganin yaran da sun suna ciki suna a matsayin gudan jini basu zama mutane ba,to amma sai taga shurunta kamar ma ta bashi dama ne,don haka ta motsa bakinta bayan itama ta harde hannayenta a qirji,ta kuma yi jarumtar saka nata idanun cikin nashi,duk da yadda kaifin nashi idanun ke barazanar dakusar da nata
"Au...don Allah?,amma nayi mamaki da har kake da qarfin gwiwar kiran korarrun yaran da yaranka,ka manta wai kun dade da baiwa uwarsu su?,ya kamata kayi gaggawar ciresu daga sahun yayanka".


Yadda take maganar cike da qwarin gwiwa fushi fushi da kuma dakiya ya burgeshi,hakanan ya sake bashi damar qarewa kyakkyawar fuskarta dake samun kulawa ta musamman kallo,jajayen labbanta masu kyawun zubi,baisan yakai hannu ba zai shafi gefan fuskartata ba sai daya kusa sannan ya ankara,yayi hanzarin janye hannun nashi,cikin laushin murya yace
"Calm down baby....fushin bai miki wani kyau,haramunne kuma mace ta dinga dagawa mijinta murya haka,mala'iku suna jinki...." Sai ya matso dab da ita har suna musayar numfashi,muryarsa na sake yin laushi da taushin daka iya kashewa duk wata lafiyayyar mace jiki yace
"Ban fada ba,hakanan har abada bazan taba cewa na barwa duniya ko uwar d'ana 'ya'yana ba....ni abdul azeez....ko cikin shege na yiwa mace bata isa na bar mata yarona ba,koda zuciyata bata taba sonta ba,mun hadune a rariya,bare ke da kike da wani babban matsayin da duk duniya babu meshi,bare yarana da suke na sunnnah,da kinsan waye azeez da bazaki fadi hakan bama,jinina yana da qima da martaba a idanuna,koda b'arin dana akayi zan girmama inda aka binneshi,pls,na roqeki da dukkan wani abu mai girma....ki barni naga yarana,ki barsu su rabeni,koda ke akaran kanki ba zaki saurareni ba,duk da koda baki saurarenin ba ina mai tabbatar miki da cewa azeez bazai taba qyaleki ko rabuwa dake ba,idan kinayin wadan nan abubuwan don na barki,ina mai farincikin shaida miki cewa....ban gaji ba,bazan kuma gaji ba....idan akwai wasu qarin hanyoyin ma ki dado dukka kiyimin,indai zaki huce,indai zaki sake bani chance na shiga rayuqarki karo na biyu".


Mamakin wanne irin mutum ne shi ta tsunduma,dukka kalamansa yanayinsa da yadda take furtasu kawai sun isa gaya maka da gasken gaske yake.


Baya ta janye ta daga kai zata kalleshi ta gaya masa maganar da zata hanashi barci a yau,sai taga hankalinsa ya raja'a ga bakin qofar gidan.


A hankali ta wawaya don ganin abunda yake kalla din,amatullah da abdurrahman ne ke kokawa akan bindigar ruwa ta wasa,kowa nason karba,saidai tuni abdur rahman din ya amshe da yake shi din namiji ne,amatu ta soma tattakowa cikin kuka ta nufota,da alamu qara zata kawo mata.


Bata taba tunanin akwai wani abu da zai sake sanyata gudu ba bayan wanda tayi na quruciya ba sai yau,tuni ta riga azeez din isa ga yaran ta cafki hannayensu,kana cikin mugu sauri ta jasu zuwa cikin gidan ta banko qofa.


Daidai lokacin da najwa ta kasa haquri take baiwa anty zuhriyya labarin mai kama sak dasu abdul ta gani,shiya aikota kiran anty bilkisu.


Shuru anty zuhriyya tayi tana dan gajeran nazari,ranta na raya mata waye,duk da cewa tasan shi baisan gidan ba.


Yanayin yadda bilkisu ta shigo da yaran yasanya ta fahimci inda amsarta take,ko ina na jikinta na rawa,hakanan kuka keson qwace mata
"Maza najwa ku wuce ciki gaba dayanku,oya" anty zuhriyya ta bata umarni,ba jinkiri ta kada kan dukka yaran suka wuce ciki,falon ya rage daga ita sai bilkisun,ta qarasa ta kama hannuwanta
"Meye?,meya faru?"
"Shine ummi,bansan ya akayi yasan gidan nan ba har yazo,yaga su abdul sanda suka fita,har ya taho wajensu,ummi banason ya shiga rayuwarsu,bana son ya qwacemin su,yanzu yasan inda nake zaune" tabe baki anty zuhriyya tayi
"Don yasan gidan nan shine me?,don yaga su abdul sai meye?,kefa bai isa yin komai cikin rayuwarki ba ina gaya miki sai idan kece kika bada qofa kika yarda kin fahimta,babu abinda zai faru kamar yadda na saba shaida miki".


Tana dire maganar taji ana bude qofar falon gidan,tasan kuma mutum dayane zai.haka wato abbaa,saidai kuma a yadda sukayi dashi zai dawo lokacin dawowarsa bai qarasa ba,don haka ta maida kallonta ga bakin qofar cikin mamaki harya gama budewa ya shigo.


Da sallama a bakinsa yashigo din,saidai kuma ya karanci kamar akwai abinda ke faruwa saman fuskokinsu
"Lafiya abbaa naga ka dawo tun yanzun?" Anty zuhriyya ta tambayeshi sanda yake zama saman daya daga cikin kujerun fuskarsa na nuna alamun damuwa da kuma rashin walwala
"Wallahi jikin hajiya ne ga motsa sosai,ina can malam ke sanar min,sai naga kawai gwara na dawo mu fara shirin tafiyar nan,a haqura da qarshen watan,cikin satin nan kawai mu wuce mu sauka ringim din gaba daya" cikin yanayi na nuna alhini da kulawa tace
"Subhanallah,amma koda na kirata batace min komai ba,da sauqi kawai ta bini dashi"
"Eh ai batason a fada,haka take cewa kowa"
"Allah ya tashi kafadunta" ta amsa tana barin wajen da suke tsaye da bilkisu,itama bilkisun cikin sanyin jiki gami da sanyin murya tace
"Allah sarki hajiya,Allah ya tashi kafadunta,ya bata lafiya"
"Amin amin" ya amsa kana yace
"Meke faruwa?na shigo na sameku a tsayr carko carko,banji kuma motsin kowa a gidan ba ina duka yaran?" Yanayin damuwar lalurar mahaifiyarsa yasa taga bai kyautu ta sake qara masa damuwa ba,don haka tace
"Babu komai,kawai muna tattaunawa ne,sai kuma ka riskemu a haka" ta qarasa fada tana buda fridge don dauko masa abun sanyi,tana kuma qwalawa yaran kira tana shaida musu dawowar abban nasu,bilkisu kuma ta juya ta shige ciki tana qoqarin daidaita yanayinta.


Mutuwar tsaye yayi na wucin gadi a wajen da suka shige gida suka barshi,yana jin wani abu yana zagaya qwaqwalwarsa yakuma tsaida tunaninsa na wasu mintuna.


Ya jima a haka kafin yaji qafafunsa sun soma gardama da tawayen qin karbarsa,hakan yasa ya yiwa kanaa qiyamullaili ya isa ga motarshi ya shiga kana ya rufe.


Kanshi kawai ya kifa saman sitiyari,fuskokin yaran na yawo cikin idanunsa,wata qauna mai tsanani tasu wadda ta nunka wadda yakeji a baya tana shiga zuciyarsa tana barazanar kekketata,tabbas banda uwa uwa ce,banda fulani mahaifiyarsa ce babu mahaluqin daya iaa yayi masa haka a duniya,saidai uwa ta zarta duk wani tunani dan adam,hakanan takanyi komai ne da sunan soyayya koda zai dawo daga baya ya cutar da rayuwar danta ba tare data ankara da hakan zai iya faruwa ba.


Har uncle abbaa yazo ya wuce ciki bai sani ba,shima bai lura ba saboda yana cikin mota ne,ya tsammaci maqotansu ne suke da baqi.

¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶

Kwanki uku ya kwashe yana jera zuwa gidan ya zauna bakin qofa,yayita jera mata kira ko saqo kan ta taimaka ta turo yaran ya gansu koda ba zasu iso inda yake ba,idan ba zata barsu ba to ita ta leqo ya ganta,baya damuwa da yawa ko adadin awannin da yake shafewa zaune a wajen ba,burinsa kawai taji tausayinsa ta kuma yi masa alfarma.


Zuwan nasa tamkar takura yake a wajenta,duk da bata ganin koda qyallinsa,amma duk da haka bata qaunar taji saqonshi na cewa yana zaune a waje,saidai ta sharema zuciyarta,tunda babu abinda zai sanya ta fita bare ya ganta koya tareta,hatta da aiki ta dauki excuse,kuma dr adam baiqi ba ya bata.


Tana ta kasa kunne ko dr adam din zaice wani abu?,baice ba,amma akwai sanyin jiki daga yadda ya saba waya da ita,saida aka kwana uku sannan yace ta gaya masa yaushe zaizo gida ya sameta,akwai muhimmar maganar da yakeso suyi.


Ta riga data sani,tasan qarshen labarin,don haka tace dashi
"Zamuje nigeria mu dawo,kayi haquri idan na dawo saimu tattauna kome zamu tattauna din" bai musanta mata ba ya amsa da to.


¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶


Kamar kullum,yauma yayi parking motarshi daga gaban gidan kadan,duk da yasan cewa babu lallai ya samu ganinta ita ko yaran,amma a yau yana jin cewa bazai iya jura ba,don haka yana kashe motar ya fito sannan ya kulleta.


Tsayin mintuna yana duban gidan kana ya durfafeshi kai tsaye cike da qwarin gwiwa da kuma tarin jarumta,ya gaji hakanan,koda zunubin na bisa wuyansa naqin amsar cikin aiya kamata a sassauta masa hakanan,a barshi yaga gudan jininsa.


A lokacin bilkisu na kitchen ta dora sanwar abincin dare,sanye cikin doguwar riga mai yankakken hannu A shape na wani material mara nauyi,dankwalinsa baida fadi,hakan ya baiwa kwantaccen baqin gashinta dayasha gyara daman bayyana.


Abdurrahman ne kawai a falon shi da ateeq,amaturrahman da najwa da abid suna backyard na gidan suna wankin undies dinsu,wanda tuni sun riga da sun saba,saidai najwan na tsayawa tare dasune tana gyara musu idan sunyi kuskure.


Sosai.hankalinsu ya tafi kan cartoon da suke kalla,hakan ya sanya daya daga cikinsu ya kasa tashi yaga waye a bakin qofa,duk da qararrawar dake kadawa,dai dai lokacin anty zuhriyya ke fitowa daga dakinta sanye da hijabin data idar da sallar la'asar tana waya da hajiya.


Ta gama wayar don haka ta sauketa daga kunnenta,tana qoqarin katsewa tace
"Saboda sakarci kuna jin ana magana a waje amma ku kasa tashi ku bude,koma waye kenan yayita tsaiwa ko?" Ta qarashe maganar tana dosar qofar don ta bude din
"Sorry mommy" a teeq ya fada yana sake gyara zamanshi,don shi kallon yayi masa suger.


A hankali ta buda qofar,idanunta suka sauka kan azeez dake tsaye sosai,irin tsaiwar dake nuna kuzari da cikakken qoshin lafiya gami da cikar halitta.


Bata buqatar neman qarin bayanin wayeshi,kallo daya zaka masa ka tabbatar da kamanni na zahiri tsakaninsa dasu amaturrahaman,iya kamar kawai ta isa ta gaya mata wayeshi.


"Barka da yamma anty" ya fada yana dan rusunar da kanshi alamun girmamawa,sosai ta hade ranta,fada takeso da masifa tayi masa sosai,amma baya ga hade ran saita kasa komai,tana jin kwarjininsa yana cika wajen yana kuma cika idanunta
"Yauwa....lafiya?" Bai zaci zata tambaya ba,amma kuma yana tunanin qila bata sanshi ba,don haka cikin dakiya yace
"Nazo ganin twince ne,idan babu damuwa ayimin alfarma na gansu" ya fada yana kallon fuskarta,cikin ranshi yana addu'ar samun nasara.


Shuru tayi tamkar mai wani tunanin,tana son tace masa aah ne,tana son gaya masa maganar dake yawo kan bakinta amma kwarjininsa nason rufeta,daga qarshe sai kawai ta samu kanta da juyawa zuwa ciki,muryarta ciki ciki tace
"Bismillah" kana ji kasan wani abu ya tilastata fadan haka din.


Nannauyar ajiyar zuciya ya saki,a hankali yana shafa qirjinsa da hannu daya gami da lumshe kyawawan idanunsa yace
"Alhamdulillahi rabbil Aalamin" a nutse yabi bayan nata zuwa ciki.


Tuni ita ta isa cikin falon,ta kuma aika ateeq ya kira amaturrahman,ya shiga kitchen ya samu lemo da ruwa ya kawo falon,daga haka tayi shigewarta ciki.


Da abdurrahman ya soma tozali,kasa zama yayi yaji zuciyarsa na wani irin bugawa kamar yaga abun tsoro,ya zubawa yaron idanu,wanda sam shi baisan me ake bama,kamar kuma ance kalli bayanka,saiya waiwayo,take suka hada ido dashi,tsaiwa yaron yayi shima kamar mai tunani ya zubawa azeez idanu na wasu sakanni,hakanan kuma saiya saki murmushi yana cewa
"Ina wuni uncle" murmushin shima ya sake sama,kana ya miqa masa hannunsa alamun ya taho,kamar me tunanin wani abu ya tsaya yana dubanshi,sai kuma ya taso a hankali yana takowa inda yake.


Yana zuwa azeez din ya janyoshi jikinsa,ya rungumeshi gam yana jin wani maganadisu cikin zuciyarsa,tarin qaunar yaron tana motsawa daga ainihin zuciyarsa,koda ba'a fada ba yasan photocopy dinsa ne sak!,kamar yayi kaki ya ajjiye.


"Kaiiiii" yaji ance,sai a sannan hankalinsa yakai kai,amaturrahman ce tsaye daura dasu tana kallonsu,cikin mamakin ganin me kama da ya abdul dinta.


Tattausan murmushi ya saka yanajin qwalla na shirin taho masa,ya miqa mata hannu itama,amma saita noqe,saboda tana sa wuyar sabo da rashin yarda,abdul dake zaune saman cinyarsa yace
"Kizo kiji amatu,yace waishine daddynmu"
"Daddy?" Ta maimaita cike da mamaki da zumudi,kalmar data dade tana son ji sakamakon yadda kullum 'yan ajinsu kowa baida zance saina mom dinsa da dad dinsa,wannan ya sanyata tahowa itama harda saurinta,ya hadasu gaba daya ya sake rungumewa yana yiwa Allah kirari gami da shafar kawunansu,yana jin wani irin madaukakin farinciki yana ratsashi,wani abu daya qulle masa daga qirjinsa zuwa zuciya shekaru bakwai baya yaji yana raguwa gamida narkewa.


Daga kitchen kuwa sanda ateeq ya shiga tana gyaran salad,ya isa ma'ajiyar farantai da kofuna ya soma hadosu hadin gambiza,saita kalleshi
"Me kuma zakayi dasu?"
"Baqi akayi ummi tace nakai musu ruwa" amshewa tayi tana maidasu inda suke tana sake zabo wasu
"Shine zaka dauki kofuna wari da wari haka?" Ita ta shirya masa komai saman farantin ta bashi,saidai kafin yakai ga fita santsin tiles ya kwasheshi ya watsar da wasu kayan,Allah yasa kofunan basu zubeba,ta qaraso da sauri ta amsa
"Allah ya shiryeka,banda abun ummi ta manta dama ba'a abun arziqi dakai?,bani nan suna can suna zaman jira" karbe tray din tayi tayi gaba zuwa falon da zummar takaiwa baqin ta dawo taci gaba da girkinta.


Sam bata taba kawowa a ranta baqi maza bane,tunda tasan antyn babu wani namiji da take mu'amala dashi dahar zata kawoshi gida,abbaa kuma baya nan bare tayi tunanin mazanne,hakanan tunaninta ko mafarkinta bai taba kawo mata cewa wai abdul'azees bane cikin falon nasu.
7/11/21, 4:34 PM - My Mtn Number: 62

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070



K'arar sakin data yiwa tray din hannunta ne ya janyo hankalinsa ya kuma ankarar dashi
"Subhanallah" ya fada yana sauke su amatullah daga jikinsa wadanda yaketa musu tambayoyi iri daban daban ta yadda zasu sake jiki sosai dashi.


Taga tahowarshin amma saita kasa daga qafarta,saboda tana tsammanin ba'a zahiri bane,har ya iso inda take tsayen ya durqusa ya tattare dukkan abinda ta zubar din ya dora saman farantin,saiya miqe yana dubanta.


Sunyi mugun dab da juna,wanda da zai qara taku guda tak zai iya yin masauki a jikinta
"Ki dinga bi a hankali,kada ki jima kanki ciwo kija mana asara maman twince" ya furta cikin wani irin salo da sautin murya,hucin bakinsa da numfashinsa duka na dukan wuyanta,wanda ya sabbabawa tsigar jikinta zubawa,ya kuma qara gudun zuciyarta
"Muga hannun,Allah yasa bakiji dai ciwo ba" taji yana fada,bata ankara ba har ya kama hannun nata ya sanya nashi tafin hannun cikin nata,ya soma murxawa a hankali
"Alhmdlh,babu abinda yayi" kamar wadda ta farka daga wani mafarki ta fusge hannunta da mugun sauri,ta juya da niyyar barin falon,amma ina ya fita zafin nama,caraf ya kamo faffadan qugunta daya qawata da mazaunai,wadanda suka bayyana sakamakon yadda rigar tabi jikinta.


Taku ya qara tana sake rage tazarar dake tsakaninsu,kamar mai rada yace
"Na gode da halaccin da kikamin,na gode da kikabar yarana suka rayu a mahaifarki sa'annan kika haifesu,kika shayar dasu kika tarbiyyansu duk da abinda suka faru,na gode na gode....." Iya qarfinta ta saka ta hankadashi,sa'annan cikin gudu kamar wata qaramar yarinya ta cilla zuwa dakin anty zuhriyya qirjinta na mugun bugu.


Da kallo yabi bayanta har ta bace masa sannan ya lumshe idanunsa lokaci guda kuma ya budesu
"Oh my god,ya rabbi" ya furta can qasa,ta yadda idan ba bakinsa ka kalla da kyau ba bazaka fahimta abinda yace ba,murmushi ya qwace masa saman fuskarshi.


Sam ya manta da yaran saida yaji muryar amatu na cewa
"Uncle...." Ya bude idanunsa a kansu,ashefa duk suna tsaye suna kallonsu,saiya sake musu murmushi suma,ya duqa gabansu yana kama kumatun amatun
"Not uncle,its daddy right?" Saita daga kanta tana murmushi.


Kusan morewarsa yayi shida yaransa cikin falon,don babu wanda ya sake fitowa,shi da kansa yake mamakin yadda yaran suka

Please Login or Register in order to submit comment