Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kasuwa,amma idan nakoma zan hadaki dasu,shikenan dai ko?" Kai ta gyada a sanyaye,badon taso ba,don tasone a yanxu yanzu suyi magana,amma babu yadda ta iya.


Haka tazauna zaman jira,duk bayan minti daya saita irga mintunan da suka rage yakoma yakirata yabasu,rakiya tadinga mata dariyar ta qosa da yawa,yayin da mama sodangi take kallon ta cike da tausayi,don tasan ita kadai tasan ciwon da taji na rabuwa da qannenta da tayi.


Murmushi tayi sanda rakiya ke ci gaba da yi mata dariya
"Rakiya kowa fa yabar gida gida ya barshi,dan uwa dadine dashi" sai taga ta kauda kai tana murmushi
"Mu duk bamusan wannan ba ko mama sodangi?" Da yake ta koyi cewa mama a wajen bilkisu,murmushin maman tayi kawai ba tare da tace komai ba.


Sai bayan wajen awanni takwas sannan baban nata yakira,a sannan har tayi laushi,ta sanya wayar a gaba kawai da tugumi,ta yanke tsammanin zaya kira,tana dagawa muryar hannatu tasoma ji,wayyo Allah,farinciki kamar su faso wayoyin suga junansu,tana iya jiyo muryoyinsu dukkanin yaran a rude,kowa so yake ya ganta kuma yayi.magana da ita,da qyar tayi controlling kukanta don kada ta karya musu gwiwa,tasa hannatu ta sanya wayar a handsfree,sannan tace da daya da daya kowa yayi.magana da ita.


Haka aka dinga bin layi,kowa tana biye masa tare da bashi lokacinta sosai,sam.ta manta a agaban mama sodangi take,saita dinga jinta kamar gata a gida a gaban qannan nata,duka saida suka gama gaisawa da kowa sannan tasoma tambayarsu kan abinda ya dameta
"Kuna cin abinci?,kuna zuwa makaranta?" Hannatu ta amsa mata
"Kullum yaaya sai munci har sai munce mun qoshi,dakinmu mu kadai babu mai takura mana,an kawo.mana kaya masu yawa dakyau,duka mun bada wadan can,kuma baba ya sanyamu a makaranta islamiyya harda ta bokon da kikace zaki sakamu,kinga ya hutashsheko" wata nannauyar ajiyar zuciya tasaki tana godewa Allah,wannan labarin data ji shi ya rage mata damuwarta kaso hamsin cikin dari,yakuma haifar mata da wata 'yar qaramar nutsuwa da a baya bata sameta ba,lallai addu'a bata faduwa qasa banza.


Tun daga ranar tasamu abunyi,kullum ta Allah saita kirasu da daddare taji ya suka wuni?,me sukeyi yanzu?,tun tana dari dari da tunanin baban zaiyi fada,koya hanasu wayar harta saki jiki,ganin bai sake cewa komai ba,ga mamakinta harda mama ladi wataran saita amshi wayar sun gaisa,wannan yasake haifar mata da nutsuwa da kwanciyar hankali.


Uwa uba kuma ganin babu wani abu daya biyo bayan auren nata,rayuwarta take cikin gidan daga mama sodangi sai rakiya kadai take gani,wanda take zaman dominsa bata taba ganin gilmawar koda mai kama dashi ba bare shi,koda sautin muryarsa bata taba ji ba,saidai taji mama sodangi lokaci bayan lokaci takan jefa zancansa tsakaninta da rakiya,yarima yace in masa kaza,ko dauke abu kaza saboda yarima yakusa shigowa,hakan yasa wasu lokuttan da yawa take manta meya kawota qasar?,take manta cewa ma tana da wani abu waishi aure,saita sake sakewa,batasan cewa BABBAN QALUBALE NA BIYE DA RAYUWARTA A GABA BA.


Zamansu da rakiya yasa ta fuskanci tana da rauni wajen karatun addini dana boko ma,hakan yasanya ta dorawa kanta nauyin karantar da ita daga ilimin da Allah ya bata bayan kowacce sallar la'asar,tashiga internet tayi browsing duka litattafan da zata fara koya matan,suka baiwa mama sodangi ta nemi inda ake printing akayi musu,saboda ita din kamar 'yar garice a qasar,tasan kan qasar sosai,kuma hakan baya rasa nasaba da yawan zuwa da fulani aisha keyi tare da abdul'azeez tun bai fara ma karatu anan ba.


Yanayin qwarewar bilkisu yasa mama sodangi itama taji sha'awar zama ayi karatun harda ita,sai daliban nata suka zama biyu,anan falo suke zama ta karantar dasu,a sake suke tambayar dukkan abinda basu sani ba,ita kuma ta basu amsa daidai gwargwadon saninta dakuma yadda hukuncin yake a alqur'ani ko hadisi,sosai karatun yake musu dadi har ita bilkisun,don ya sake taimaka mata wajen debe mata kewa,tare da tuno mata wasu karatuttukan data manta.


Wannan zaman yasake haifar da sabo sosai a tsakaninsu gamida fahimtar juna da qauna.


**** ***** **** *****


Ƙarfe hudu harda wani abune na yammaci,dai dai lokacin bilkisu na zaune a falon gidan,cikin doguwar riga data nada mayafinta a kanta,duk da cewa ba wani zama yayi sosai ba amma ya mata kyau sosai.


Gefanta rakiya ce itama,wani series suke kalla,su duka sun bada hankalinsu kai,duk da cewa rakiyan ba fahimta take ba,bilkisu ce ke gaya mata duk abinda yake faruwa ta hanyar subtitile,don ba yaren turanci suke ba,harshen qasar mexico ne.


Mama sodangi ce tafito cikin doguwar riga da wadataccen mayafi,hannunta riqe da wayarta dakuma atm card,idanunta a kansu ta qaraso falon
"Tashi rakiya muyi sauri mu dawo,yau siyayyar da yawa"
"Toh" ta fada tana miqewa da hanzari,sai bilkisu ta bisu da kallo
"Mama yau kuma ni kadai za'a bari kenan a gidan" dubanta tayi
"Ranki ya dade siyayyar tana da dan yawa ne,shi yasa na gayyaci rakiya muje tare,nasan koda na gayyaceki ba lallai ki amsa" ta qarashe tana murmushi,don tasha yiwa bilkisun tayin tazo suje din kodan ta miqe qafarta amma bata taba zuwa ba.


Ga mamakinta sai taga tamiqe tana cewa
"Xanje" tayi hakanne don kawai tana tsoron gidan,tana tsoron xama ita kadai,uwa uba data duba time ma dawowarsa sai taga mintuna kadan suka rage,tana tsoron yadawo ya taddata ita kadai ya zatayi?.


Fidda wayarta maman tayi tana cewa
"Ta kwana gidan sauqi ai,amma bari mu tambaya maigidan tukunna" jin ta ambaceshi sai bilkisun ta qara sauri tawuce daki,don kada ma tace mata ta tambaya da kanta.


Mintuna qalilan tasake shiri tafito,tayi tsaf da ita,hakanan ta aje wani kyau mai daukan hankali,duk wani sirrin kyau nata da wahala da talauci suka boyeshi yanzun ya bayyana sanadin hutun data samu,qiba ce har yau babu abinda ta qara,tana nan 'yar firit dinta.


Taji dadin fitar sosai,taga gari yadda ya kamata,tsari da yanayin garin yayi matuqar burgeta,tun daga ranar saiya zamana sukan fita tare lokaci bayan lokaci,cefane ko wankin kai ku kuma shan iska kawai.


A haka rayuwa taci gaba da garawa,bata sanshi sanshi ba,bai santa ba,bata taba ganinsa ba bai taba ganinta ba,bata taba nemansa ba,bai taba nemanta ba,tamkar kowa zaman kanshi yake ba tare da wata alaqa ta hada dayansu da dayan ba.



*_BAYAN WATA BIYAR_*



Duk ranar Allah da zata fito ta fadi saita lissafa adadin kwanakin da suka rage mata cikin gidan da garin gaba daya,kwanakin da suka rage mata takoma qasarta kuma cikin ahalinta.


Ayanzun watanni biyar data shafe gani take taci nisan zango mai yawa a tarin tafiyar dake gabanta,hankalinta akwance yake sosai fiye da baya,sai taga ashe dukkan yadda ta tsammaci abun ba haka bane,ashe da tasan haka tafiyar zata kasance da babu damuwa ko kukan da zatayi,idanma zata koka din.....zata koka ne kadai saboda rabuwa da zatayi da 'yan uwanta na tsahon lokaci....

_tofa masu karatu,yanzu wasan zai fara_


***** ***** ******


Kamar kowanne yammacin rana ta Allah buwayi da sukan zauna bilkisun ta dora musu karatu,yauma suna zaune a falon gidan bayan gama sallar la'asar da mintuna qalilan,ayau mama sodangi tana kitchen tanason kammala abincin darensu,kafin tazo sai bilkisu tasoma yiwa rakiya nata qarin karatun don kada a bata lokaci.


Tana sanye da wani skert ne dogo wanda yafi zubi da buje,mahadi da hijabin jikinta wanda dukka tsahonshi bai zarta qugu ba,yadine mai taushi ruwan madara da aka yiwa dige dige dakuma adon furanni da dark pink,fuskarta tafito sosai tayi kyau kaman wata baby,hakanan kayan sun haskata qwarai,ta baiwa qofa baya,yayin da rakiya ke kallon qofar.


Da fari sunji qarar tsaiwar mota a qofar gidan,basu kula ba,don sunyi tsammani maqotansu ne sukayi baqi,don sunsan su din babu mai zuwa wajensu a irin wannan lokacin,tunda dai lokacin dawowar azeez baiyi ba a yadda aka saba bare suce shine.


Mintina kadan bayan nan sukaji ana taba qofar parlour dinsu,kafin suyi wani yunquri an bude qofar,da alama wanda yabude din yana da muqullin falon.


Tare suka daga kai gaba dayansu,saidai yadda bilkisu taga rakiya ta miqe cikin girmamawa da tsananin nutsuwa yasa bilkisun kasa juyawa,wata matsananciyar faduwar gaba da bata taba jin irinta ba kaf rayuwarta ta ziyarceta lokacin da sassanyar muryarsa ke furta sallama afalon,muryar data karade dukkan kunnuwanta suka zarce zuwa ga qwaqwalwarta,tsintar muryar rakiya tayi tana fadin
"Barka da warka Allah ya baka yawan rai,barka da isowa" kanta a qasa,bisa dukkan alamu dokarsa ce baya son ana kallonsa,itadai bata sake jin muryarsa waida zummar amsa gaisuwar da rakiya ke kwarorowa ba,tamkar mutum mutumi haka bilkisu taci gaba da zamana wajen a daskare,zuciyarta tana wani irin gudu kamar zata fasa qirjinta,yayin da gumi yajiqe mata fuska zuwa wuyanta,bata motsa ba sai dataji ya kammala.takunsa gaba daya da alama ya gama hawa saman,sannan tayi wani irin yunqurawa ta kwasa da wani azababben sauri tawuce dakinta.


Da kallo rakiya ta bita harta qulle,saita maido dubanta ga littafin da suke karantawa tana danne dariyar dake taso mata,tabbas batasan waye azeez ba,inda tasan wayeshin da bata damu kanta kan boye kanta haka ba,ko yanzun ma kallo guda tak yayiwa muhallin da suke zaune bai qara na biyu ba ya qara gaba,bai damu daya duba baquwar daya gani xaune a wajen ba sam,sai wani murmushin yasake kubce mata sanda take hango fuskokinsu a tare
"Zasu fa dace da juna" ta fadawa kanta da kanta a fili,sai kuma ta damqe bakinta tana zare idanuwa tana duban falon,Allah yasa babu kowa,litattafan nasu tahau tattarewa kawai tabi mama sodangi kitchen.


"Wai kaddai ace harkun gama karatun,duk saurin da nake nagama na cimmaku" sai data aje litattafan saman freezer tana danne dariyarta sannan tace
"Inafa aka gama mama,yarima ne yashigo muna tsaka da karatun,tana ganin yashigo ta kwasa tawuce daki shikenan karatun ya qare" murmushin itama mama sodangi tayi tana kashe gas din,itakam wannan abun nasu batasan farko tsakiya ko qarshensa ba,fata dai Allah ya zabama rayuwarsu abinda yafi zama alkhairi tayi addu'ar cikin ranta.


A mugun gajiye yashigo gidan,don asubancin da yayi yau yafita a gidan yajima baiyi irinsa ba,wanka kawai yayi yadawo yaxube a katafaren falonshi,kwanciyar rub da ciki yayi bayan ya tasa ruwan cikinsa da filo yana lumshe idanuwa,sanyin ac dana sauran ruwan jikinsa yana ratsashi.


A hankali yasoma jin tsohon feeling dinshi da yaketa qoqarin adanawa yanason taso mishi,don haka saiya mirgina yakoma kwanciyar rigingine,kana ya jawo wayarshi yayi kiran abdulrashid,saboda kwana biyu basuyi waya ba.


"Mr ango,yanzun nake cigiyarka a raina,ina tunanin idan nakoma gida na kiraka,tunda kai angonci ya boyeka" idanunsa ya lumshe kana yabude yana dan dukan tsakiyar kanshi,don sam bai gane angoncin da abdulrashid din ke magana akai ba
"Angonci ne mefa?" Dariya abdulrashid yasaka
"Karka rainawa kanka hankali....bansani ba nima" sai a sannan yatuna cewa shidin fa andaura mishi aure watanni kusan hudu ko biyar da suka shude
"Allah ya shiryeka abdulrashid..."
"Kaidai zance Allah ya shiryeka azeez,wannan attitude din naka bansan sai yaushe zaka rabu dashi ba" murmushi yasaka mai dan sauti
"Wanne attitude gareni?,wai har na kaika?,kaga kira nayi mu gaisa ba fada ba" ya fadi yana dakatar dashi.


Hira sukayi mai dan tsaho sosai,wanda ta jawa abdul'azeez din lokaci,har lokacin magariba yakusa sannan ya aje wayar,yashiga bandaki ya sake watsawa jikinsa ruwa,don shi wani irin mutum ne mai mugun tsafta da qyanqyami,hakanan wanka baya isarshi.


A gurguje yake shiryawa din yanason fita kamar kullum wayarshi tasake daukan ruri,safwa ce,saiya yarfar da hannu
"Safwa!" Kana ya daga wayar
"Its time for prayer fa" ya gaya mata a taqaice,saboda qa'idarshi ce bayason kiran waya lokacin sallah.


Kamar yana gabanta ta murguda baki kana ga juya idanu
"U r in mexico and am in nigeria mr man,ko ka manta ne?" Qaramar dariya yayi
"Yes maaaa"
"Ohk,no more excuse da zaka bani,yanzun lokacinane gaba daya"
"Bance a'ah ba,but...yanzun lokacin sallah ne,and i have visitors,friends dina ne daga wata qasar....nayi alqawari i wil cal you" shagwabe mishi tayi yadda ta saba,wanda hakan ya sanya yaji tsigar jikinsa na wani xubawa yarrrr,ya lumshe idanunsa yana sauraren kukanta,a hankali yabude bakinsa
"Stop it please safwa,i said i promise" ajiyar zuciya tasauke
"Na yarda,amma vedio call?"
"Yes" ya amsa mata a taqaice,hakan ya mata daidai,saita saki murmushi tana masa sallama,yau rana ce ta musamman a wajenta,don ba kasafai yafiya yarda suyi vedio call ba,yakance mata tsarinsa kenan,don haka tana aje wayar ta dira daga kan gadonta cikin sauri,tahau hargitsa cupboard dinta,ta ciro wani riga da skert ta watsa saman gadon tawuce toilet cikin sauri kamar wadda ake jira,tanaso ayi mata gyaran gashi na garari,don tasan azeez din yana matuqar son suma,tun ranar data sani din kuwa duk randa zayazo sai taje an mata gyaran gashi an mishi ado mai kyau azubo dashi yadda zaike gani,saidai kosau daya bai taba tankawa ba,saidai ya kalla yadauke idanunshi,hakan bai dameta ba,saboda tasan halin miskilancinsa,ko iya kallon da zaiyi ita ya gamsar da ita.


Wanka tayi sharp sharp sannan tafito ta shirya,kana ta zari muqullin motarta tafito.


Saman daya daga cikin kujerun alfarma dake katafaren falonsu na farko tasamu mahaifiyarta zaune akai,yayin da wata mace ke durqushe gabanta riqe da qafarta,da alama pedicure take mata,itan kuma tana riqe da wayarta tana latsawa,kallo daya zaka mata kasan hamshaqiyar hajiya ce data jiqu da naira.


Dago kai tayi da sauri tana duban safwa data rungumota ta baya
"Fita zakiyi?" Ta jefa mata tambayar tana karantar zallar farincikin dake shinfide kan fuskarta,kai ta gyada
"Zanje retouching ne amma,yau azeez ya yarda zamuga juna" saita saketa cikin sauri tanufi qofa,baki wangale ta bita da kallo,xasuga juna kamar yaya?,qasar zaizo?,bata samu damar mata tambayar ba don tuni takusa kaiwa ga qofa,saita daga murya kawai tace
"Banda tuqin ganganci,ki dawo kuma dawuri tun babanki baizo yaga ke daya kika fita ba"
"Ohkey mom!" Ta fada yadda zata jiyota,saita girgiza kai kawai ta maida kan wayarta,ita kanta tana jinjina yadda diyar tata take bala'inson abdul'azeez din,tamkar babu wani namiji da yayi saura a duniya saishi,saidai tana godewa Allah daya sanya wanda takeso din ya cancanci a soshi,ba gama garin mutane bane.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 26
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*
*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070
_________________________
*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*

*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*

*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸ™ŽðŸ½â€â™€ï¸

*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaÉ—a ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯ðŸ½â€â™€ï¸ðŸ‘¯ðŸ½â€â™€ï¸

*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*
*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*

*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*

*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞ðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾
_____________________________
Bata tsaya an mata wani iso ba kamar sashen fulani aisha,kawai ta cusa kanta inda tasan xata samu fulani adaman,a sannan tana zaune ne ita diyarta Aafra,'yarta ta biyu wadda ayanzu haka kudin aurenta ke hannu,duk da ba'a sanya rana ba,tanason hadata ne da autarta ta aurar dasu lokaci daya.


Da sauri tazauna tana gyara zamanta ganin shigowar gaggawar da saudat din tayi mata tana duban yanayinta,gaidata afra keyi,maimakon ta amsa saita ce
"Bamu waje zamu gana da babarki" duban maman nata tayi kamar ba zata tashi ba,amma inkiyar da fulani adaman tayi mata ya sanyata miqewa tana tura baki,ta dauki wayarta tana gyara yafen mayafinta tafice.


Qaqqarfar ajiyar zuciya tasaki sanda take zama,cikin damuwa fulani adama tadubeta
"Wai lafiya kuwa saudat?"
"Inafa lafiya,har yanzu haqarmu ta gaza cimma ruwa,daga sassan aisha nake,komai nasu yana tafiya dai dai,da alama ma yadda suka tsara,babu alamun wani abu dake damuwarsu,akwai matsala fa adama,tabbas akwai matsala,wankin hula zaya kaimu dare".


Maganar itama ta sanya damuwa a ranta,saita sauke ajiyar zuciya cikin damuwar tace
"Yanzu babu wani abu kenan da xamu iya yi,ba shakka wannan babban abun kunya ne a wajenmu"
"Ina zuwa,akwai wani aiki dana sanya ayimin" saudat ta fada bayan ta zaro wayarta ta soma danne danne.


Dab da kiran zai katse muryar kamal ta bayyana
"Hey mom" ya fada da alamun muryarshi na nuna tafiya yakeyi a qasa
"Hey....kana ina ne?" Dan tsaki yaja yana yarfa hannu
"Ganinan a qasa,mom nayi nayi ki matsawa daddy ya siyamin mota amma kinqi,kullum saidai mu qare da aron ta wancan dan girman kan,haba da Allah bafa girmanmu bane,shi yasa kowacce beb ka taya sai kaga hankalinta na kanshi indai ta sanshi"
"Kaga dakata.....kaima kasan halin babanka sarai,bazai siya ba,shi yasa naketa fafutuka wannan lamarin ya tabbata komai yadawo hannunmu,bama mota ba har private jet zaka mallaka" dan tsalli yayi gamida sakin ihu,wanda qila da anan gida nigeria yake sai an tsaya kallonshi
"Wow mom....akwai kuwa latest news"
"Dama shi nakira ji....gayamin ya ake ciki"
"Yarima ya daina kwana a gida kwata kwata,kusanma sai ku kwana mu yini wani lokacinma sai yayi almost two to three days bamu ganshi ba,infact....dana lura dakyau ma sai na fuskanci da yawa daga cikin kayanshi basa gidan"
"Me hakan ke nufi kenan?" Tayiwa kamal tambayar,amma idanunta suna kan adama
"Well,ina tunanin kamar yasauya gida ne fa"
"Ina yakoma"
"Idn't know gaskiya mom,kinsanshi da tsare gida,bayason yawan tambaya ko sanya idanu"
"Dole kazama mai tambaya,kuma dole kazama dan sa idonsa koda bayaso,ya zama lallai ka binciko mana ainihin abinda yake faruwa,dakuma inda yakoma"
"Ohkey....i will do my best" daga haka ta katse wayar tana duban adama.


Babu wanda ya iya cewa dan uwanshi da komai,har tsahon wasu mintuna kafin adama ta magantu
"Tabbas aisha ta sauyawa abdul'azeez gida ne,kuma ina da yaqini da tabbacin akwai dalilin da yasanya tayi hakan,akwai abinda takeyi ko take shirin yi wanda take boyewa batason kowa yasani" kai saudat tajinjina cikin gamsuwa
"Hakane,nima na yarda da hasashenki....zan matsawa kamal har sai ya binciko mana komai cikin qaramin lokaci" tattaunawa sukaci gaba dayi a tsakaninsu ta yadda zasu bullowa komai harna tsahon wani lokaci.

******* ***** *********


Tunda yatashi a safiyar yau gaba daya yaji bashi da sha'awar fita ko ina,don hatta da qasan gidan bai sauko ba bare mutanen gidan susan yana cikin gidan.


A samanshi yayi wankansa yadda yasaba,yashirya cikin kaya marasa nauyi dukka farare kamar yadda yawanci yafi son fararen kaya a shigarsa,yana da coffe maker ya hada coffe dinsa da wani sauran cake yasha,yagama dukka sabgoginsa a waya,kamar kiran ammi da maimartaba da sauran mutanen da yake da hulda dasu,yakira safwa ma suka dan kashe wasu lokuta kana ya katse wayar,ya debi litattafan makarantarshi,ya isa can quryar falonsa ya murda wata qaramar qofa saiga wani qawataccen balcony dan madaidaici da aka bullo dashi ta backyard na gidan,wajene da aka masa kwalliyar furanni daketa bawa wajen qamshi kala kala,tun daga qasa har jikin bangon wajen,sai kujerun hutawa guda uku da table,daga balcony din kana iya ganin backyard din fes.


A nutse ya isa kan daya daga cikin kujerun yazube litattafansa,kana yasoma tattakawa harya isa gaban qarfen da aka tokare balcony din dashi,dafe qarfen yayi yana qarewa backyard din kallo,kafin yadauke idanunshi ya cillasu cikin gine ginen da yake iya hangowa cikin unguwar.


Shuru unguwar take kamar kowanne lokaci,sai mutane tsilli tsilli dake wucewa,wanda yawanci a qasa suke tafiya da alama ba nisa zasuyi ba,wasu mata wasu maza,wasu mace da namiji wani lokaci da 'yan yaransu.


Ajiyar zuciya yasauke sannan yasake dawowa yazauna kan kujerar bayan ya kwashe litattafan ya azasu saman cinyarsa,yasoma budawa a hankali yana nazarin karatuttukan ciki.


Sosai karatun yake masa dadi,saboda yanayin wajen dakuma yadda yake sake fahimtar abinda yake karantawa sosai kamar ana bude qwaqwalwarsa ana zuba masa shi.


A hankali yasoma jin surutu,wanda da fari yayi qoqarin tokare hayaniyar don kada tashiga karatunshi ta bata mishi yanayin da yake jin dadinsa.


A hankali a hankali sai surutun yasoma yawa,yakuma so ya dameshi,hakan yasa yasoma mutsu mutsu yana yana gyara position na zamanshi ko xai daina jin hirar,saidai abanza, duk yadda ya gyara zaman baijin canjin muryoyin da yakeji.


"Bilkisu!" Yaji an qwala kira,hakanan yaji kamar an fusgi hankalinsa,saiya dauke kansa daga kallon littafin zuwa bangaren da yaji muryar tana fitowa.


Su biyune zaune saman wasu 'yan kujeru masu kyau da aka tanada a wajen saboda hutawa,sun tasa botiki kowa dai dai a gabansa suna faman wankin inner wears,sunata hira gami da dariya da alamu lokacin na musu dadi,kuma babu abinda hake damunsu,da alama sune suka isheshi da surutu kenan tun dazun.


Su biyu ne,rakiya da wata wadda baisan ko wacece ba,sanye take da doguwar riga na wani yadi mai sulbi da qyalli wanda kana masa kallo daya zakasan ya jibanci gidan sarauta,an masa dinkin doguwar riga,wadda daga sama ta kamata datayo saman cikinta kuma zuwa qasa ta bude sosai,hannunta gajere ne sosai don ko gwiwar hannu tsahonsa baikai ba,gashin kanta da yasha gyara shekaran jiya yana fake a ribbom,duk motsin da tayi sai jelarsa ta tayata motsawa,fuskarta akwai alamun nutsuwa da walwala,amma wacece ita?,ya tambayi kansa yana zuba mata idanunshi gamida sake karantar yanayinta
"Idan kun gama bilkisu ga abinci can na kammala" cewa mama sodangi dake qarasowa wajen tana dubansu.


Wannan karon baiji me ta fada ba,saidai fuskarta shimfide da murmushi take wa mama sodangin magana,bata qara minti daya ba maman ta juya tabar wajen,yayin da kuma sukaci gaba da aikinsu da kuma karadinsu,shi kuma yaci gaba da nazartarta.


Baisan adadin lokacin daya kwashe ba yana bibiyar lamarinsu,daga bisani ya farga,tamkar wanda aka tashi daga barci yayi firgigit,ya janye idanunshi daga kansu yana jan wani mugun tsaki,haushin kanshi sosai ya kamashi,baiga dalilin da xai sanyashi xama yana wannan abun ba,yaduba agogon dake maqale a wani saqo dake wajen,yasake jan tsaki haushi yana sake cikashi ganin lokacin daya narkar a banza,saiya tattare takardunsa kawai kana yawuce ciki,yasanya maqulli ya rufe qofar.


Kan gadonshi ya fada da qarfinsa cikin rub da ciki yana sauke qaqqarfar ajiyar zuciya,hakanan wata kasala tana lullubeshi,sai ya lumshe idanunsa yana furzar da iska daga bakinsa,surarta yadinga gani cikin duhuwar idanunsa tana masa yawo,sai yayi hanzarin bude idanun nasa gamida maida kwanciyarsa rigingine,ya kuma goye hannayensa a qirjinsa idanunsa suna kallon rufin dakin.


Wasa wasa saiga abun nason shiga tunaninsa,saiya miqe yasake zama sosai yana jan tsaki,babu shiri yatashi zumbur ya isa cupboard dinsa yasoma zaro.kayan da zai iya sanyawa,sam babu plan din fita a yanzu a tsarinsa,amma dole yafita,don baison yazauna yayita fama da tunanin da zai dameshi,ya shirya a gaggauce kana ya rufe saman yasauko yafice daga gidan gaba daya,bayan yadauki motarsa dake aje gaban gidan.


******* ***** ********




Please Login or Register in order to submit comment