Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wuta yana burin isa asibitin cikin qananun mintoci.


*na yau da gobe ne sisters*ðŸ™ðŸ½ðŸ™ðŸ½ðŸ™ðŸ½
7/11/21, 4:34 PM - My Mtn Number: 55

*_IDAN kaji ƙi gudu sai in sa gudu bai shigo wajen ba. Ƴan uwa abokan tafiya, gafa magani A GONAR YARO. domin tabbas idan kaji gangami akwai labari_*.

*_Ina masu wahala kullum cikin neman maganin sanyi (imfection) amma babu biyan buÆ™ata. Kinyi na asibiti har kin gaji babu canji, na gargajiyarma taÉ“awa kike babu wani Æ™yaÆ™yÆ™yawan sakamakon. Tofa kakarku ta yanke saÆ™a. Domin kuwa ga dama a tafin hannunku. Munada maganin NI'IMA, maganin GYARAN HIPS (mai gida bye bye😉). Muna da maganin BOOBS (mai gida welcome🙈). Maganin BASIR mai hana sakewar zama. Duk ku garzayo domin samunsu akan farashi mai sauÆ™i da rahusa, ga kuma inganci domin an samosu ne daga tsaftatacciyar hanya mai nagarta._*👇ðŸ»

*AISHA S BAYERO TRADITIONAL MEDICINE AND HERBAL RESEARCH CENTER...*

_KUNJI SUNAN KO? CENTER CE TA MAGUNGUNAN GARGAJIA, WANDA DUK WANI DAMUWA DAKE DAMUNKA IDAN HAR KAZO WAJEN S BAYERO TA KARE DA YARDAR ALLAH.. KADAN DAGA MAGUNGUNANTA SUN KUNSHI:_

_MAGANIN SANYI_
_MAGANIN NI'IMA SET_
_MAGANIN NANKARWA_
_MAGANIN KIBA BABBA DA KARAMI_
_MAGANIN HIPS_
_MAGANIN GYARAN NONO_
_MAGANIN RAGE KIBA_
_MAGANIN SAKA FEELING_
_MAGANIN CIDA KWAI_
_ZUMA YAR ASALI_
_MAGANIN BASIR KOWANNE IRI_
_HODAR NI’IMA_
_MAGANIN MALLAKA_
_GUMBAR NONON RAK’UMI_
_GUMBAR MADARA_
_TURAREN FARIN JINI_
_KAZA MARA KWAI_
_TURAREN MALLAKA 3 STEP_
_HAD’IN MATAR MINISTER 1_
_KAZA ME KWAI_

_STEP 2:_

_TURAREN MALLAKA ME KWALBA_
_ME KUNAMA DAN MATSI_
_TURAREN GOSHI_
_TURAREN QIRJI_
_TAUWADAR MATA_
_MEMORY_
_KAHON MALLAKA_
_YAJIN MAZA_
_TEA DIN MAZA_
_DAMBUN MATSI_
_MAN AYU_
_MAN DAMO PURE_
_KWALLIN IDONKA IDONA_
_GARIN SHA DAKA ME KYAU_
_KUBEWAR MATA_

_DUKA WADANNAN INGATTUN MAGUNGUNA NA GARGAJIYA HAJ AISHA NA DASU GANGARIYA.. HERBAL MAGUNGUNA NE MASU KYAU DA INGANCI.. TAFIYAYYU NA KASAR CHAD. CHADIAN HERBAL MEDICINE AND RESEARCH CENTER.. KYAU, INGANCI.. RAHUSA... SAI MAGUNGUNAN *AISHA S BAYERO TRADITIONAL MED AND HERBAL RESEARCH CENTER....*_

_NUMBER WAYAR WHATSAPP: 08121491609 KO KIRA TA NUMBER 08145873617._

_ADIRESHI: KUNTAU KARSHEN KWALTA KAN A KARASA YAN TIFA, DAIyDAI GADON KAYA CEMENT.._
Sai kunzo😘😘ðŸ¤ðŸ»
_________________________
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070



Hakanan fulani taji jikinta yayi sanyi bayan ta katse kiran data yiwa azeez kan zai qaraso suci abinci?,tayi shuru tana wani nazari,tare da karantar sake samun sauyi cikin muryarsa,jikinta ya bata tabbas akwai wani abu daya faru dashi,saidai batasan ko meye ba.


Afnan wadda fitowarta kenan ta dubi fulanin tana bata fuska
"Nikam ammi gaskiya sai nakega kamar kinfi qaunar ya yarima akaina,shi kullum kamar wani qaramin yaro,bayan ya girma har iyali gareshi?" Qaramin murmushi ta saka,ta waiwayo tana duban afnan
"Ba wanda nafi qauna cikinku akan wani,saidai kawai kina kishi dashi ne,sannan bugu da qari yayanku akwai damuwa tattare dashi,dole sai ana ci gaba da bashi kulawa da kuma saita mishi hanya"
"Damuwar mefa ummi,ni kaina na karanci sake sauyawarsa sosai a shekara bakwai din nan" tayi maganar tana kallon fulanin sosai tare da son jin abinda ke damun nashi.


Kai ta jinjina kawai tana gyara zamanta
"Kedai kiyi masa addu'a,Allah ya yaye masa"
"To ameen" tafada tana duban qasan tiles din falon,shuru ya ratsa wajen na wasu mintuna,kowa da abinda yake saqawa cikin ranshi,kafin daga bisani afnan tace
"Ina yaje ne yayan?,inata sauri na taddashi"
"Ya koma asibiti,karbo certificate of death na suhaima" ta bata amsa tana daddanna wayarta
"Allah sarki dota..." Afnan din ta fada cikin jimami,don sosai jininsu yazo daya da yarinyar,sai kuma ta sake cewa
"Kuma fa asibitin naso zuwa nima" bata amsata fulanin,da alama wani abune ya janye mata hankali cikin wayar,ganin haka yasa afnan din ta miqe,tana shawarin ko ta sami cave kawai taje ta duba asibitin,don tun randa taga wata kamar bilkisun hankalinta bai kwanta ba,jikinta yana bata itace,amma idan har ita din ce sai tafi kowa murna.


Dakin da mama sodangi take ta tura ta shiga,da yake yawanci idan tana da buqatar hira da ita kadai take xama tayi hirarta hankali kwance,tasu tafi zuwa daya sosai,akwai sabo mai girma tsakaninsu da shaquwa mai qarfi.


Samunta tayi xaune saman abun sallah tana jan carbi,saidai da alama tana azkar dinne kuma tunani yana fusgar hankalinta.


Gefanta ta zauna tana dubanta
"Mama baki idar bane?" Murmushi tadan saki tana aje carbin,a duk sanda wani cikinsu ya kirata da mama saiya tuna mata da bilkisun,zamansu tare ya sanya koda suka dawo rakiya bata daina kiranta da maman ba kamar yadda suke kiranta dashi ita da bilkisun a zamansu na mexico
"Na gama ranki ya dade gimbiya,kina buqatar wani abunne?" Kai ta girgixa tana murmushi kana tadan kashingida saman gadon nata tana cewa
"Dawai asibitin nan zanje,ina buqatar dan rakiya" gaban mama sodangi yadan fadi,itama ta tuna mata da wadda ta gani din kamar bilkisu
"Me zakije yi acan gimbiya?" Ajiyar zuciya ta saki
"Wallahi mama wata na gani kamar tsohuwar qawata bilkisu,na jima inason Allah ya nuna mini ita,to amma ina shakka da kokwanton daqayar idan ita dince,saboda ita waccan iyayenta ba masu qarfi bane,sannan tun kafin mu gama secondry aka aurar da ita,auren dole ga wanda bata so,kinga ko idan hakane banga ta yadda za'ayi na ganta anan ba" shuru mama sodangi tayi gabanta yana faduwa,wani abu yana darsuwa a ranta,a yadda afnan ke wassafa bilkisu sai takega tana magana ne kan tata bilkisun sak,babu wani maraba ko kuwa banbamci,to amma indai hakane me zai faru?,tana da buqatar tabbatarwa,tana da buqatar sanin bilkisu ce ko ba ita bace?,wadda take tunani akai ita afnan ke magana akai itama?
"Shikenan,aisai ki shirya na rakaki ko?" Cikin jin dadi afnan din ta miqe tana cewa
"Yauwa mama,aiko na gode" ta fita da hanzari don shiryawa.


Cikin qaramin lokaci dukansu suka gama shirinsu,suka cewa fulani zasu anguwa ne,ta musu Allah ya kiyaye suka fice suka tari taxi.


Sanda suke shiga a lokacin motar azeez ke fita daga asibitin,saidai babu wanda ya kula da wani cikinsu,wani irin tuqi yake yana jin kamar bazai iya kai kanshi gida ba,dukkan wani kuzarinsa ya tsiyaye tas.....ya buga ya raya qaura wambai su bashi adress din dr bilqees amma sunce sam ba tsarin asibitin bane,yayi haquri,idan wani issue ne yakeso su tattauna ya sameta gobe a ofishibta dake cikin asibitin,idan da buqatar ta bashi adress din zata bashi da kanta ko tayi musu umarni a bashi,saboda suna da kiyaye duk wani abu daya shafi mara lafiyansu ma bare likitansu dake aiki a qarqashinsu.


Ganin yadda ya kafe,hakanan suna ganin girmanshi da qimarshi a matsayinsa na wani babban mutum kuma sananne,sai suka danganashi da office din mamallakin asibitin gaba daya wato dr adam.


Yaje ya sameshi cikin tunanin meye hadin bilkisun tashi,da kuma sananne kuma fitaccen dan kasuwar duniya Aa yarima?.


Sanda ya iskeshi a office din ya tsammaci zai samu dukkan abinda yakeso,dr adam ya tsaya ya saurareshi,ya saki nannuyar ajiyar zuciya sanda yaji adress ma yake nema,baisan inda take ba kenan?,wannan shike nuna cewa ba wani abu bane mai girma tsakaninsu yadda yake tunani,koda yana cikin sahun 'yan takarar neman bilkisun to hakan na nufin tabbas bata bashi wani matsayi mai girma ba bare hakan ya daga masa hankali kenan?,sai yaji sanyi cikin zuciyarsa,nauyin dake qirjinsa ya ragu,shima kuma ya gayawa azeez din kwatankwacin abinda sauran ma'aikatan suka gaya mishi.


Yayi qoqarin nuna mishi muhimmancin adress din a gunshi,amma da gangan dr adam ya nuna bai fahimci komai ba,ganin xai bata mishi lokaci,kuma shi sam baida lokacin xama yayita roqonshi yasa ya tashi yabar mishi office din a fusace,ko a jikinsa don bazai taba yarda ya bayar din ba,babu abinda yafi tsana a duniya irin yaga wani na rabar bilkisu,burinsa a duniya a yanzu bai wuce ya aureta ta zama tashi shi kadai ba.


Sanda su afnan suka isa asibitin basu samu wani information a kanta ba,hakan yasanya itama ta buqaci adress dinta,suma basu samu ba,saboda dr adam kafin ya fita daga asibitin ya jaddada cewa kada wanda yazo daga baya walau mace ko namiji a bashi adress din dr din,da qyar suka samu suka tsira da lambar waya,wanda iya hakanma ya yiwa afnan dadi,tayi serving number a wayarta da xummar idan ta koma gida zata kirata.


Tana zaune daga gefan gadon,yayin da anty zuhriyya ke tsaye saman kanta tana sauraren abinda take gaya mata,tsayin mintuna da gama bata labarin anty zuhriyyan tana nazari,bilkisun ta buda baki a hankali muryarta tana rawa,alamun ko yaushe daga yanzu tana iya sakin kuka tace
"Ta yaya ma zai wani ce ni matarsa ce?,ta ina na zama matar tasa bayan ina da shaida ta takaddar saki da suka bani?" Ta qarashe fada,da alama abinda yafi damunta kenan cikin dukka batun.


Nannauyar ajiyar zuciya anty zuhriyyan ta saki tana sauke hannayenta dake rungume a qirjinta,sannan ta koma dab da bilkisun ta zauna,ta kama hannayenta ta saka cikin nata,cikin tattausar murya tace
"Daughter....wannan dukka ba abun damuwa bane,dukkan abinda kike tsoro daya daga cikinsu bazan taba bari ya faru dake ba,wannan karon ko dame sukazo dai dai nake dasu,a wannan lokacin a shirye nake duniya tasan dukkan abinda ya faru,matuqar suka mana kan kara wannan karon sai mun musu na rodi,babu wanda ya isa ya rabaki da yaranki koda kuwa sarkin kaisa ne da kanshi bare danshi ko matarsa,banason kisa wata damuwa a ranki da zata hanaki walwala,kici gaba da rayuwarki kamar yadda kika saba,baki da wata matsala kisa hakan a ranki kinji?" Ta qarashe fada tana mata murmushin qara qarfin gwiwa,wanda sosai kalaman anty zuhriyyan suka bata qarfin gwiwa itama,suka kuma rage tsoron dake zuciyarta.


A wani mugun hargitse ya koma gida,wanda kana kallon fuskarsa kasan akwai babban al'amari tattare dashi,mamaki kan meya sameshi daga futarshi zuwa dawowarshi safwa keyi,don daga dawowarsa yahau fidda kayansa gaba daya ya wuce direct zuwa toilet ya sakarwa kanshi sassanyan ruwa tsahon wasu mintuna kana ya fito.


Duk da ruwan sanyin daya sakarwa jikinsa amma hakan bai sanya launin qwayar idanunsa komawa dai dai ba,daren gaba daya bai saurari abinci ba,bai kuma bari kowa ya dameshi da surutu ba,hasalima kebe kanshi yayi shi daya a farfajiyar gidan,yayi zurfin tunani wajen neman hanyar dazai dai daita komai.


Wani irin dare ya gani mai tsaho baqi duhu da kuma fadi,wanda sam bai samu bacci ko daya a cikinsa ba.


Washegari ticket nasu ya basu kawai su wuce su duka,yace musu wani aiki ya tsaidashi qasar,sam ba haka safwa taso ba,taso su tafi tare ko yaci gaba da debe mata kewa,amma hakanan tana ji tana gani tabi su fulani suka wuce.


Suna zaune cikin airphort din afnan ta sake gwada lambar bilkisun karo na babu adadi,don tun jiya take faman kira amma sam bata shiga,harma ta soma fidda rai,ta kuma fara zargin lambar bogi suka bata saboda sunga ta matsa da son samun lambar.


Ba zato ba tsammani taji ta shiga,fuskarta wadace da fara'a ta dubi mama sodangi
"Lah mama....kinga ta shiga" ta gaya mata ne saboda yadda taga itama ta damu ta son layin ya shiga,maganar tata ta janyo hankalin mama sodangi gaba daya kan wayar
"Ma sha Allah" ta fada amma idanunta akan wayar,itama tana dakon jin an daga kamar yadda afnan ke dako.


Can qasa muryarta tayi sallama,saidai duk da hakan,haka bai hana mama sodangi gane muryarta ba,tabbas bilkisu ce,bilkisun ta,amma ga afnan data amsa sallamar donta tabbatar sai tace
"Don Allah ina magana ne da bikisu bilyamin?" Kai ta gyada daga bangarenta,tana aje mug dake cike da ruwan tea a gefanta
"Eh itace" murmushin jin dadi afnan ta saki tana gyara zamanta
"Ma sha Allah,kai amma gaskiya naji dadi sosai....nasan baki gane me magana ba ko?"
"Eh gaskiya....muryar ta dan kwanta min"
"No wonder.....sunana afnan abdallah mu'az kaisa,kin tunani?" Ta fada cike da confidence tana jiran amsar bilkisun.


Mummunar faduwar gaba taji ta ziyarceta,ba shakka afnan ce,afnan ce qanwar yarima,ina suka samu phone number dinta?,ta nan zaya bullo mata kenan ko kuwa me yake nufi?,koma meye yanzun ita din a shirye take,ta shirya musu,tana jin wata dakiya na ratsa zuciyarta,don haka ta sake dake zuciyarta itama tadan saki muryarta kadan
"Ya aiko ki kenan ko?,meye saqon nashi?" Cikin mamaki da rashin fahimtar zancan tace
"Waye ya aikoni?,baki ganeni bane?,afnan ce fa,afnan classmate dinki"
"Ina magana ne kan abdul'azeez" murmushi ta saki,tana raya wani abu a ranta,toko ya yarima ya santa dama?,akwai wani abune tsakaninsu take jiran aike daga gareshi?,to amma idan har ta sanshi ya akayi bata taba tambayarsa ita ba?,ya akayi bata taba nemanta ba?,duk da cewa shidin tasan halinsa sarai ba lallai ya gaya mata ko ya bata labarin yasan wata class mate dinta ba
"Awwnnn.....kinsan yaa prince kenan?".


Gaba daya bilkisu ji tayi kamar tana shirin raina mata wayau ne kawai,don haka saita datse kiran tana jan dogon tsaki,ta kashe wayarma gaba dayanta ta aje gefanta.


Duk da cewa afnan bata kai ga jiyo tsakin ba,amma mamaki ya cikata na yadda akayi bilkisun ta katse mata kira,hakanan bata nuna wani alamun jin dadin haduwarsu ba,bugu da qari kuma ta ambaci sunan yayanta kamar akwai wata sanayya sosai tsakaninsu.


Da wannan daurewar tunanin ta waiwaya tana duban mama sodangi
"kinga mama,kodai bata gane ni bane?,na zaci zanji tayi murna"
"Ba zata taba murna ba tunda har tasan wacece ke,wace ke a wajenta" mama sodangi ta fada cikin ranta
"Bari na sake kira na qara mata bayani,nasan bilkisu ba haka take ba,hala ma ba itace ta daga wayar b....." Dafe hannunta mama sodangi tayi wanda take qoqarin taga ta sake kiran bilkisun,zuwa yanzu maman tanajin ba zata iya ci gaba da boyewa afnan alaqar dake tsakaninsu da bilkisu ba,ya kamata ace ta sani
"Karki kirata gimbiya,saboda koda kin kirata ba zata daga ba" da mamaki saman fuskarta ta kalli maman
"Saboda me mama?"
"Kinsan DANGANTAKAR dake tsakaninku?" Saita girgiza kai da sauri.


Bata boyewa afnan komai ba ta bata labari,tayi ne da yaqini da kuma zuciya daya,tayine bisa gaskiyarta koda fulani zata hukuntata,saboda ta tabbatar cewa kosu yaranta basu san tirka tirkar da aka tafka ba.


Girgiza kai kawai afnan keyi cikin mamaki da girgiza matuqa,yaushe duka hakan ya faru?,yaushe amminsu ta aikata wannan danyan aikin babu shawara ko masaniyar daya daga cikinsu?,me yasa ammin tasu tayi sha'awar hada wannan danyan aikin?,ko tasan itace qawata da nake yawan yi mata maganarta shi yasa tun a wancan lokacin da nace za'a mata auren dole,masarauta ta taimaka ta shiga tace a'ah nabar maganar?,saita miqe tana duban mama sodangi
"Bilkisu rayuwarta abar tausayi ce a lokacin,nasan da haka a qurarren lokacin da babu abinda zan iya yi mata,wannan abu da akayi mata tamkar xalunci ne aka yiwa rayuwarta,bai kamata nabar ammi ba,ya kamata na tunkareta da maganar...".


Saurin riqo hannunta mama sodangi tayi tana girgiza mata kai
"A'ah,kinfi kowa sanin wacece fulani,bata haka ake bullo mata ba,ki sassauta zuciyarki ki kwantar da hankalinki,mu samu isashshen lokaci da zamuyi tunani akai" ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi bayan ta samu ta taushi kanta da qyar kana ta koma ta zauna,tayi shuru cikin zuzzurfan tunani tana sake tariyar labarin da mama sodangi ta bata,tsahon wani lokaci a hankali tace
"Ya akayi ya prince ya yarda da wannan aikin shi kansa?" Ta fada cikin salo na tuhuma,kai mama sodangi ta kada
"Bashi da laifi,saboda a lokacin yana kan qadamin neman mafita,hakanan uwa ce,umarni ya karba daga gareta"kanta itama ta girgiza
" a wajena shima mai laifi ne mama sodangi,kamar anyi amfani dashi ne an bata rayuwar wata baiwar Allah" ajiyar zuciya mama sodangi ta saki ba tare data sake iya cewa komai ba,daga haka shuru yaci gaba da wanzuwa tsakanin har zuwa sanda suka shige cikin jirgin,kana ya lula dasu duniyar sama don ya sadasu da qasata nigeria.


Ta bangaren bilkisu kuwa tea dinta ta dauka taci gaba da sha hankalinta kwance,donta riga ta yiwa kanta da anty zuhriyya alqawarin lokacin tashin hankali ya dade da wucewa gurbin rayuwarta,tana shan tea din tana tuna wasu abubuwa,tun daga shigowarsa office dinta har zuwa kiranta yanzu da afnan tayi,sai data kammala sannan ta samu ruwa mai sanyi tasha,tabi lafiyar gadonta tana son rama bashin baccin da bata samu jiya tayi ba.


Ta dade sosai tana baccinta kafin ta farka,ta shiga tayi wanka ta sauya kaya sannan ta dauki wayarta ta sauko qasa.


Ta samu dukka yaran suna falo suna kallo,tabi kowannensu suka gaisa tadan tsokani na tsokana a cikinsu sannan ta samu daya daga cikin kujerun ta zauna tana tambayar anty zuhriyya,najwa dake yunqurin shiga kitchen don duba abincin data dora musu tace
"Yanzun nan ta shiga daki,itama ta kwanta"
"Ok to" bilkisu ta amsa tana qoqarin kunna wayarta,donta tabbatar ba zata rasa saqonni ba ta watsapp da kuma sms.


Tun kafin wayar ta gama saituwa kiran dr adam ya shigo,ta lumshe idanunta kana ta bude tanajin kamar karda ta daga,don batason qarin wata damuwar,amma ganin yadda yake kiran kawai ya shaida mata bazai daina kira ba harsai ta daga,don haka ta daga din.


Ƙatuwar ajiyar zuciya ga sake sannan ta jishi yana cewa
"Mommy ta daga" idanu ta fiddo dukka waje,wato kusa da mommyn yake yake gaya mata ta daga,shi ko kunya baiji
"Ina ruwan bature da kunya" wata zuciyar ta gaya mata
"Kin bani wahala yau bilkis,kinsan ba zaki samu zuwa aiki ba sa'annan kuma ki kashemin waya?" Murmushi ne ya kubce mata na mamakinsa,jin yadda ya marairaice mata kamar zai saki kuka
"Au....kai na kashewa wayar ma?"
"Yes,eh mana,nasan nine babban dalilin kashe wayar,wato kada dan anacenki ya dameki ko?"
"A'ah,kawai dai banjin dadine yau din gaba daya,kuma idan nabar wayar a bude kira xaita shigowa,kuma ba lallai na samu damar dagawa ba"
"Mommy...kinji ashe bata da lafiya" ta jiyoshi adan rude yana gayawa mommyn,ta gwalalo idanu tana sake mamakin dr adam,wai me yasa ya fiya tabara ne haka?,kafin tayi wani tunani har taji muryar momyn,da alama zuwa tayi ta amshi wayar daga hannunta.


A ladabce ta gaidata ita kuma tayi mata sannu da jiki,tana jiyo muryar dr adam sama sama saidai batajin me yake cewa,katsam ta tsincin mommyn na neman adress din gidan wai zata zo dubata,ba zata iya hanata ba,don uwa ta wuce wasa komai kashinta,saidai ta tabbatar da cewa plan ne na dr adam din,shi ya shirya hakan,kuma da tasan hakan zata faru da ba zata ce bata da lafiya ba,hakanan badon taso ba ta karanta mata adress din
"ai bamu da nisa ma sosai,nasan street din" ta gayawa bilkisun.


Koda wayar ta koma hannunsa cikin shan kunu tayi masa magana,duk da baya ganinta amma zaka gane hakan kan muryarta
"Na gode daka hadani da mommy"
"Nifa babu ruwana,bama lallai nazo ba,ita keson zuwa ta miki sannu da jiki kuma ta ganki" tasan ya fada ne kawai,amma babu ta yadda za'ayi ace za'azo din bai biyota ba,shi me neman kuka an jefeshi da kashin awaki dama?.


"Gashi kince baki da lafiya,kuma tafiyarku dubai larabar nan,ya za'ayi?" Mutum ce ita mai qwazo da neman sani koda yaushe kan abunda ya shafi aikinta,batason rasa tafiyar don tasan ba qaramin qaruwa zasuyi ba,don haka tace dashi
"Babu damuwa,ina saka ran kafin sannan na sake warwarewa,don yanzunma da sauqi sosai"
"To Allah ya qara sauqi ya nuna mana,sai munxo" ya fada cikin salon shauqi,da alama yana cike da farincikin samun adress dinta yau da yayi,da haka sukayi sallama.


Tana shirin ajjiyewa wani kira data lura tun suna waya da dr adam ke shigo mata ya sake shigowa,lambar nigeria ce,kuma tana da yaqinin assadiq ne,hakanan badon taso ba shima ta daga ta saurareshi,saidai ta shaida mishi batajin dadi,hakan ya sanya hirar batayi tsaho ba yayi mata sallama,saita sake kashe wayar gaba daya donta samu ta huta sosai.
7/11/21, 4:34 PM - My Mtn Number: 56

*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070


Washegari da yammaci suna zaune dukkansu a falon gidan,tana sanye da doguwar riga mai hade da hula tana yiwa yaran bitar karatun addini,kamar yadda ta maidashi wajibi kan wuyanta,dukka yaran gidan suna daukar karatun addini ne a wajenta,wanda bata sanya ta tsaya sosai kan hakan,tana soke duk wani uzuri da zai taso yaci karo da karatun yaran ya kawo musu cikas,shi yasa ko tafiye tafiye bata fiya son yi ba sabida hakan,don najwa ma tuni ta sauke a hannunta,yanzu haka hadda takeyi a wajen nata dai,yayin da yaran kowanne yayi nisa a biye,ateeq ma dan yake daya sauke,baifi sura biyu zuwa uku suka rage masa ba.


Hatta su amatu dake da shekaru shida sun doshi izifi na goma sha shida a biye,wannan abun ba qaramin dadi yakewa anty zuhriyya da abbaa ba.


Ƙaraurawar qofar gidance tayi qara,bilkisu ta dubi ateeq
"Ko baqin abbaa ne?" Kai ya girgiza
"Anya ko?,yace su sun fasa sai dare,ko naje na tambayoshi" kai ta girgiza
"Aah qyaleshi,jeka ka bude kaga waye" ya amsa mata da hanzarinsa yana miqewa,ita kuma taci gaba da sauraron haddar da najwa ke bata.


Baquwar fuska ce ta shigo falon da sallama,wadda bata fita tar a bakinta,kana mata kallon farko zaka gane baturiya ce,hakanan ga kama nan sosai ta fuskar dr adam akan fuskarta,da alama kenan ita ya dauko,kalar fatar ne ya dauko mahaifinsa,shi yasa haskensa baiyi bauuuu ba kamar nasu,yadan russuna haka kadan.


Idanunta kan bilkisu da alama ta ganeta kenan,tunda tana ganin hotunanta wayar dr adam wanda yakan dauketa ba tare ma da tasan yanayin hakan ba.


Cikin girmamawa da fara'a ta tarbeta,ta shiga kitchen da kanta ta hado mata snacks da drink,ita kuma tana ta bin bilkisun da kallo bakinta yaqi rufuwa,da alama bilkisun ta kwanta mata sosai.


Zama tayi a qasa tana gaidata,saidai sam matar tace saidai ta dawo kusa da ita su gaisa sosai,duk da yadda takejin kunya amma haka ta daure,ta dawo gefanta kadan ta gaidata tana sunkuyar dakai,dai dai lokacin da anty zuhriyya suka fito ita da abbaa,da alama tayo masa rakiya ne zai fita.


Tsaiwa yayi suka gaisa cikin harshen mutan qasan brasil,sannan yafice,anty zuhriyya kuma ta dawo wajen baquwar tasu,itama suka soma gaisawa da harshen qasar.


A wajenma tsayawa yayi suka gaisa da dr adam,duk da baisan waye ba amma yaga yabata bashi girma na musamman,hakan ya sanya ya saka ayar tambaya akansu,haka dai suka gama gaisawa ya shige motarshi ya wuce.


Tana zaune tana sauraren hirar mommy da anty zuhriyyan ta soma ganin kiran dr adam a wayarta,saidai sarai tana sane taqi dagawa,tasan ba zaua wuce yace mata yana waje ba,ta fito ya ganta,qarshe daya gane ba dagawar zatayi ba saiga gajeran saqo
"Bazanyi zuciya ba,bazan kuma tafi ba har sai naga kyakkyawar fuskar nan taki" kamar kuwa anty anty zuhriyyan tasan meke faruwa tace ta dauki ruwa da lemo takai masa,bayan ta tambayi mommyn tace mata tare suke.




Please Login or Register in order to submit comment