Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gabanta mummunar faduwa,ta soma zazzare idanu,babu abinda yazo ranta illa
"SHINE!" zuciyarta ta gaya mata da qarfi
"Wala'alla ma dakinki zashi" zuciyarta ta sake gaya mata,sakin kwanon hannun nata tayi da hanzari ba tare data shirya ba,a miliyan tayi dakinta kamar zata tashi sama batare datako waiwayo ba bare taga waye,wanda hakan ya baiwa sassan jikinta damar motsawa dakyau,bataci biriki ba sai data tabbatar ta isa dakin,kana ta sanya muqulli tarufe qofartata gam.


Mamaki ne yasanyashi tsaiwa yana kallonta gamida mamakin wacece wannan?,ganin baida amsa saiya tabe baki gamida dage kafadunsa yawuce zuwa kitchen donyin abinda yafito dashi.


Koda yakoma dimma hirar kadan suka qara ya bata haquri,ya qarasa shanye coffe dinsa kana yayi shirin kwanciya yakwanta,kafin bacci yadaukeshi yatuna abinda yafaru mintunan da suka wuce,saiya tabe baki gamida jan qaramin tsaki,idan bamai matsalar qwaqwalwa ba wazaiyi haka?,kawai daga jin taku saika yar da kwanon hannunka kahau gudu,sake gyara kwanciyarsa yayi yana jan tsaki gamida rufe idanunsa,ya aje komai gefe yanason bacci ya daukeshi.


****** ****** ****** ****


Kimanin qarfe sha daya ne na safiyar ranar,su ukune zaune a falon nata saman dining suna karyawa,fulani aisha da yaranta uswa da sumaira.


Diyar uswa ce akan cinyarta tana bata farfesun nama a hankali yayin da suke taba hira wadda ta shafesu,daidai lokacin jakadiya ta qaraso,ta zube tana shaida mata saqon son ganinta da saudat(qanwar maimartaba mahaifiyar kamal) keson yi.


Kai ta gyada kana ta bada izinin ganinta,ta dauke idanunta ta maida kan yaran nata,sai ta yiwa sumaira inkiya data dauki sahla dake saman cinyarta,ita kuma ta miqe tana goge hannunta da tissue.


Cikin nutsuwa qasaita take saukowa daga wajen dining din zuwa ainihin falon,tana sane da zuwan saudat din gidan kimanin kwanaki hudu,amma bata nemeta ba kamar yadda ta nemi sauran abokan zamanta.


Tuntuni tasoma shaqar wani abu dangane kan saudatun,hakanan takejin sam takunta bai mata ba,tun kafin yau dama ba wani alaqa mai kyau bace can can tsakaninta da saudatun tunda aka aurota,hakanan jininsu bai hadu ba,hakan kuma baya rasa nasaba da aurotan da yayi a wata qasa,wanda a lokacin saudat din sam bataso hakan ba,akwai qawarta dataso hadashi da ita kamar kamar me,taji ba dadi sosai,don a sannan ita dayace ta rage mishi qanwa kuma abokiyar shawara,dama duka duka su ukune Allah ya baiwa sarki mu'az,Allah ya yiwa babbar yayarsun rasuwa,tabar yaro daya wanda yake hannun saudat din tana riqo.


Cikin qasaita shigo shan qamshi da kallon komai É—ai É—ai tashigo falon,don dukka cikin gidan babu sassan da yakai na fulani aisha kyau da tsaruwa da kayan ado na alfarma dake sake nusashe dakai cewa nan fa akeyin sarautar,don ita gada tayi daga fannin mahaifi dakuma miji,sarauta saidai ta nunawa wasu
"Bismillah" ammi tafada tana nuna mata daya daga cikin kujerun cikin nata salon qasaitar da isa,saida saudatun tazauna kana itama tayiwa kanta mazauni kan kujera maicin mutum biyu,kana ta dora qafarta daya saman daya idanunta kan saudat
"Matar dan uwana" ta fada kamar yadda ta saba kiranta dashi
"Maman kamal....yaushe a gari?" Ta fada a dake,saita dan yatsina fuska
"A qalla yau kwanana hudu cikin gidan nan,amma da mamaki idan kikace bakisan da zuwa na ba" hannayenta ta watsa kafin ta hadesu waje guda
"Ba abun mamaki bane,saboda kowanne mutum akwai irinsa,ba kasafai na fiya damuwa ko bibiyar al'amuran dake wakana cikin gida ba,indai lamarin bawai yajibanceni bane" wani duba ta mata tanason fahimtar meta fada din,magana ce cikin magana ko kuma magana tayi kanta tsaye ba tare da kowanne nufi ba?,saita gyada kai sa'an nan tace
"Haka ne" daidai lokacin da sumaira ke saukowa rungume da sahla,kana ta qaraso cikin girmamawa,fuskarta a sake kasancewarta maison jama'a fiye da kowa cikin 'ya'yanta,tazauna saman daya daga cikin kujerar tana gaida saudatu da suke kira da mom,gami da tambayarta 'yan uwanta yaran saudatun wato safna da safina
"Qalau" ta amsa a taqaice,daga bisani uswa ta sauko itama ta gaidata,saidai ita daga gaisuwar bata qara komai akai ba saima qoqarin miqewa da take don barin wajen,kasancewarta gwanar miskilanci ce itama kamar dan uwan nata abdul'azeez,dukka fulani aisha na ankare da yadda take amsa gaisuwar tasu,wanda tasha bamban da yadda take treating su walida qwarai
"Ke zonan,don uwarki me yasa ne baki da hali,kodon kinga mun aurar dake ne yasa kike ganin kanmu daya" ta fada cikin zafi zafi,kamar da biyu take maganar.


Uswa dake tafiya ta waiwayo kana tace
"Wa wai?,ni?" Wanda ita harga Allah bada wani abu tayi maganar ba,kusan nature dinta kenan
"Ban sani ba" ta amsa mata a gadarance.


Batace komai ba ta dawo din tasamu waje taxauna,saita soma fada mara dalili,ta inda take hawa bata nan take sauka ba,waita yaye kowa bata neman kowa.


Dukkan wani takunta da abinda fulani aisha ke nema ya gama bayyana kanshi,don haka saita shareta yadaga waya tasoma amsa kira,bata tsagaita ba har sai data gama taga yaran suna tashi suna wucewa ciki kana ta ajjiye.


"ƴan mexico ana can dai,ƙiri kiri an hana abdul'azeez dai rayuwa cikin ahalinsa,bayan bashi da wadanda suka fisu" saudatun ta fada kamar meyin fada,murmushi fulani aisha tasaki cikin nutsuwa tana aje wayar hannunta,kana ta daga idanun nata ta zubawa saudatu su.


"Komai na rayuwa ai lokacine,sau da dama wasu abubuwan sukan xama alkhairine a rayuwar dan adam,musamman nisantar wasu gurare da muhallai,karki damu innar abdul'azeez,akwai lokaci" sarai ta fahimci magana take gaya mata cikin magana,saita miqe tana tabe baki tana duban aishan da wani irin kallo
"Ni zan wuce,dama leqowa nayi mu gaisa,tunda ku baku neman kowa" murmushi tayi kamar babu wani cikin maganarta daya bata mata rai,kana ta miqe tana dubanta
"A haba,mukan nemi mutane mana,musamman wadanda mukasan muhimmancinsu me yawa ne cikin rayuwarmu,sa'an nan tarayyarmu dasu tana da wata fa'ida da alfanu,kamar dai ke" tasan gatse tayi mata sarai,takuma fahimci babu wani abun dazai kashe bakin aishan,don haka tayi gaba,zuciyarta cike fal da quluwarta,tare da ninka alwashin qudurinta cikin ranta.


Murmushi tasake sosai sanda saudatun tafita
"Kainuwa kenan......dashen Allah" tayiwa kanta da kanta kirari,kana takoma tazauna inda tatashi,tana ci gaba da wassafawa da qiyasta yadda abubuwa zasu ci gaba da wakana.


Rai a bace ta isa sashen adama,wanda har takai dukka barorin daketa faman miqa mata gaisuwa cikin girmamawa babu wanda ta amsawa ko mutum daya.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 27
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*
*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070
_________________________
*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*

*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*

*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸ™ŽðŸ½â€â™€ï¸

*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaÉ—a ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯ðŸ½â€â™€ï¸ðŸ‘¯ðŸ½â€â™€ï¸

*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*
*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*

*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*

*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞ðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾




Kamar yadda tace din babu kowa cikin falon sai mama sodangi itama dake jiran fitowarta,ta gaida maman kamar yadda tasaba duk yammaci sannan tazauna suka fara karatun.


Sai data soma dajin kataratunsu na jiya sannan tadora musu da wani sabo bayan ta tabbatar sun fahimta wancan kuma yazauna yadda ya kamata.


Awa guda kacal sukaci a karatun aka bude qofar dakin da bilkisu tasan babu kowa a ciki,hakan yaja hankalinta don dama a tsorace take,ta daga kanta da hanzari tana duban qofar dakin,safwa ce ke fitowa,sanye da wasu riga da wando masu azabar kyau da suka amsheta,saidai sun bayyana duk wata sura ta jikinta,tashin qamshi take sosai,kanta yasha gyara,hakanan a fake yake da ribbom kalar kayanta,hakan yasake qawata kwalliyar tata.


Ido suka hada da bilkisu,suka kalli juna na wasu sakanni kafin bilkisun ta janye nata idanun,itama safwan ta janye tana qarasowa falon,gami da mamakin wacece wannan maikyau haka?,choculet beauty.


Saman kansu ta tsaya,alamun sangarta qarara suna bayyana tattare da ita,ta dubi mama sodangi
"Sodangi da Allah inason peppersoup din kifi,Allah yasa kuna da?"
"Eh akwai ranki yadade.....akwai"
"Ohkey" ta fada tana zagayawa saman kujerun don ta zauna,da alama ta gama bada nata umarnin kenan,da niyyarta ta fada takoma cikin dakin,amma hakanan batasan meye yaja hankalinta ba taji ra'ayin xaman falon,saita zauna daga bayansu tadora qafarta daya saman dsya tana dan latsa wayarta,yayin da wani sashe na hankalinta yake kansu.


Tunda mama sodangi tabar falon zuwa kitchen don yin aikin safwan sai bilkisu take jinta incompatible,zaman sam bai mata ba,ta dinga tsarguwa tana jin kamar safwa na kallonta ne,uwa uba batasan wacece safwan ba,don haka ba tare da wani dogon sharhi ba ayau ko tambaya suka rufe da addu'a ta tattara tawuce daki.


Fuska safwa ta yamutse,don me ita ba zata kulata ba kamar kowa?,donme ba zata girmamata ba kamar saura?,wacece ita?,don taga tana da kyau
"Wacece waccan" safwa ta jehowa rakiya tambayar data rudata lokaci guda har tahau inda inda,wanda da safwan ta gogu da rayuwa yaci ta karanci wani abu
"Na.....'am....iyee?" Take gumi ya yanko mata,ta sanyata a tsaka mai wuya,batasan ainihin amsar da zata bata ba,sa'an nan tana ankare da gargadi dakuma jan kunnen mai qarfi da mama sodangi tayi mata koda safwan zata tambayeta wace bilkisu,kuskuren da tayi guda daya shine bata tambayi mama sodangin amsar Da zata baiwa safwa ba a duk lokacin data jefa mata tambayar ba kamar yanxu
"Yar uwata ce,tare mukazo" tasamu kanta da shirya wannan qaryar,baki safwa ta tabe tana kada kai
"Shine take acting kaman wata tsiya,baku shaida mata wacece ni ba?" Kai ta kada da sauri
"Bata sani ba Allah ya taimakeki,kiyi haquri,rashin sanine,tayi kuskure amma zan mata bayani,saidai duk da haka tana da matsala,bata magana mai tsaho,likita ya hanata" ita kanta yadda ta shirgo qaryar tabaiwa kanta da kanta mamaki,amma babu yadda ta iya,don shine kawai mafitar da zata kare kanta da bilkisun ma gaba daya.


Sai taji zuciyarta kuma tayi sanyi
"Barta kawai tunda lalura gareta,na tsammaci izza ce"
"Ko kadan ranki yadade" tasake fada da sauri,daga haka safwan bata sake cewa komai ba,saita maida kanta ga wayarta,rakiya kuma ta miqe tanufi kitchen tana sharce gumi.


Zaune yake kawai cikin motar bayan ya fakata daura da wani wajen wasan yara dake kusa da unguwarsu,ya jima zaune a ciki a yadda yake,bawai don yana wani abu ba ko kuma yana da abunda zaiyin ba,hakanan kawai baya son komawa gidan,ya tabbatar da cewa indai baiyi da gaske na safwa zata zo ne ta tafi bayan ta tayar masa da qaton tabon da yaketa qoqarin warkarwa amma abu ya gagara,tunda a halittarsa ne,jininsa ne haka babu yadda ya iya.


Sam bashi da sha'awar komawa yaci gaba da tu'ammali da magungunan,dalili kenan daya sanya yake gudun duk wani abu da zai sanya ya nemesu.


Wayarsa dake hannunsa tun dazun tadauki sauti,wanda hakan ke nuna kiranshi ake,da hanzari yaduba,sai yaga ammi ce,don haka yadan kwantar da kujerar da yake zaune akai ya jingina bayansa sannan yadaga
"Barka da warhaka ammi" gyaran murya tayi kadan sannan tace
"Yauwa....barka kadai,ya makaranta?"
"Alhmdlh ammi,ya maimartaba"
"Komai lafiya....azeez nace ba?"
"Na'an ammi"
"Meye dalilin da zaka sauke safwa a gidan da yarinyar nan take?,ina hankalinka yatafi?,ko so kake ka jawo mana matsala ehen?" Cikin kwantar da murya da girmamawa yace
"Babu komai ammi,babu abinda zai faru" shuru tadanyi na wasu sakanni sannan tace
"Ka tabbatar da abinda ka fada,idan ba haka ba..."
"Please ammi karki damu,ba abinda zai faru....in sha Allahu"
"Ina saka ran haka". Daga nan suka aje wannan maganar suka shiga wata kuma daban.


Shiga nan fita can,bashi ya isa gida ba saida dare yashiga yasoma danyin nisa,duk da daya batayi ba,yabude motar bayan ya fakata yakashe,yakulle sannan yanufi cikin gidan.


Bai tsammaci zai taddata a falon ba,saiya sameta zaune tana kallon tv,hannunta riqe da cup na lemo.lokaci lokaci tana kurba,duk tayi hakanne don kada bacci ya dauketa ba tare daya dawo ba bata sani ba.


Kai ta daga suka hada idanu,sosai ta bata rai,don bataji dadi ba,wuni taso suyi tare ta morewa zuwanta,amma ta lura kaman yana avoiding dinta ne,baison zamansu inuwa daya,bayan duka don shi tazo din.


Ya lura taji babu dadi sosai,don haka ya sakar mata murmushi wanda ya wanke dukkan wani bacin ranta tashun farko,saita saki ajiyar zuciya kawai tana lumshe idonta,lokaci guda kuma ta budesu akanshi,take tahau shagwabar tata data saba,yasamu daya daga cikin kujerun yadan dosana kamar yadda yasaba zama a falon,bai wani fiya zama harya sake koya dauki dogon lokaci ba.


Dole wannan karon yadan zauna da ita,yabiye mata,yadan jima duk asonshi na yaja ra'ayinta karta bishi samanshi,saidai ina sam bata yarda ba,cewa tayi saita rakashi tazauna tayi gadinsa har yayi bacci sannan tasauko,a yadda yasan sangartar safwa,yasan bataqi ya matsa mata ma gefan gadonsa ta kwanta ba,zatace tunda su sunsan babu wani abu tsakaninsu to ina ruwansu da wani,yadan dafe goshinsa da hannunsa yana ayyana yadda zaiyi da ita,saidai kafin ma yagama tunanin ita harta aje cup din hannunta tadauki key din daya shigo dashi da wayarsa tasoma haurawa saman,saiya bita da kallo kawai,babu yadda zaiyi da ita,iyaka idan sunje ya lallaba tasauko,don haka yamiqe yabi bayanta.


Dai dai lokacin da mama sodangi ke fitowa daga dakinsu,tunda taha safwa batayi bacci ba hakanan itama saita kasa,yanzun kuwa data ga tayi saman azeez din duka sai taji ranta a jagule,bata shakkar azeez amma tana sane da abinda yake damunshi,kuma babu wanda yafi qarfin shaidan sai wanda Allah ya kare,ita sam wannan ziyarar ta safwa batayi mata ma'ana ba,tayi mamakin duk tsantsenin fulani da kularta akan azeez data bari safwa tazo,kodon tana ganinta a tsakaninsu?,gaba daya saita kasa nutsuwa takoma tazauna tana kasa kunne taji saukowar safwan.


Ko a jikinta haka ta baje saman gadonshi tana masa hira,kamar yadda suka saba ba komai yake iya bude baki ya bata amsa ba,a hakanma yana qoqartawa duk don kada taga ya wulaqantata,haka yashiga wanka da kayan jikinsa yashirya a ciki sannan yafito.


Idanu tasa tana qare masa kallo,yadda kayan suka bala'in masa kyau,quruciyarsa qarara tasake bayyana,hakanan wannan sihirtaccen kyan nasa mai kashe gangar jiki da zuciya,shima kallonta yake hannayensa harde a qirji,yadda suka zubawa juna idanu yasa yasoma jin wasu abubuwa na yawo cikin jikinsa,yayi nisa wajen qoqarin yaqar abunda yake ji din,bai ankara ba yajita cikin jikinsa ta rungumeshi tana sakin qaqqarfar ajiyar zuciya,take qamshinta yasoma shiga hancinsa,gashinta dake fake yasoma gugar fuskarsa,tsigar jikinsa ta zuba,ya janyeta da sauri daga jikinsa,idanunsa na nuna zallar bacin rai
" meye haka safwa?"ya fada a kausashe,saita sake zuba masa idanu kafin daga bisani qwalla tacika idanunta,tajuya masa baya da sauri ganin suna niyyar gangarowa
"Saboda na rungumeka yarima shine kakemin tsawa haka?" Ta fada muryarta tana rawa,sai yayi qoqarin cooling kanshi,yasani wala'alla shine mutum na farko daya soma.mata tsawa a rayuwa,tunda yasan sarai irin gata da shagwabar da take gaban iyayenta
"Babu komai nagode,nina kawo kaina,ko kuma nace soyayyar da nake maka ta janyomin" saita soma takawa zata fita daga dakin,don harga Allah taji haushi sosai,a wajenta runguma ba komai bace,don hatta da mahaifinta takan iya rungumeshi,a wajenta da waccar da wannan duka daya ne,sannan idan kanason mutum ba komai bane hakan,tunda ba wani abu ka aikata da zai nuna a jikinka ba.


Karon farko daya kama tsintsiyar hannunta,wanda sai dayaji sosai ajikinsa,dukkan gabbansa suka amsa,ita kuma abinda ya sanyayar da ita kenan,saboda makamancin hakan bata taba faruwa ba a tsakaninsu.


Saman kujerar dake dakin ya ajeta,kana yazauna sosai a gabanta yana duban fuskarta
"Duba da girmanki kike wani kuka?,kin manta shekara biyu kawai.na baki zaki zauna gabana kina kuka?,oya share hawayen" murmushi ya kubce mata,saita sanya bayan hannunta tana goge qwallar data soma zubo mata,sai data gama tsaf sannan yace
"Akwai abubuwan da mu a idanunmu zamu dinga kallonsu ba komai bane,saida a addininmu haramunne kuma dole kowanne baligi da baliga su gujeshi,kamar yanzun,kebancewar da mukayi kadai ni dake musulunci ya hanata,kinsan dalili?"saita girgaza kai
"Saboda indai mace da namiji suka hadu a wani kebantaccen waje wanda daga shi sai ita,to ba shakka shaidanne na ukunsu matuqar ba ma'aurata bane su,i did'nt mean anything,nasan xakita tunanin abubuwa kala kala,to duka ba wannan bane....yanxu kinga dare yayi,bai kamata ace muna nan zaune a tare nida ke kadai ba,kije dakinki ki kwanta,i promise gobe xamu wuni tare" kalamansa sun wanke duk wani fushi da bacin ranta gaba daya,ba lafuzzan bakinsa ba,hatta da sound din azeez din mai taushine da wanke zuciya,ta jima bai zauna haka ya jera mata kalamai masu nuna kulawa da lallabawa haka ba,saboda tsabar miskilanci da jinin sarauta dake yawo a jininsa,shi yasa yau take jinta a duniyar sama tana yawo.


Salin alin ya rakata har qofar dakinta tashige,sai da yaga ta shiga sannan ya saki ajiyar zuciya,dai dai lokacin da mama sodangi itama ta maida qofarta tarufe tana sakin ajiyar zuciyar itama,ba shakka akwai matsala kuma za'a samu damuwa ita tasani,jikinta yana bata mawuyacine idan ba lokacin karbar qaddarar bilkisu bane nabiyu ya durfafota,kafin ta kwanta ta yankewa kanta shawara,shawarar da take fatan xata canza komai,ciki harda tunanin bilkisu dakuma rayuwar azeez gaba daya.

******* ******* *******

Washegari hakanan babu yadda ya iya ya kashewa safwa lokacinsa gaba daya,wuni gida sur,daga nan zuwa can,wuni yayi mata dadi qwarai fiye da dukkan wasu wuninnika na rayuwarta,tayi yadda takeso takasance da azeez din son ranta,wanda tsahon tarihin soyayyarsu basu taba kashe awanni haka masu yawa tare ba.


Saidai duk da hudubar da yayi mata daren jiya hakan bai sanya ta fasa tabashi ba,musamman idan taga wani abu daya burgeta ko yayi mata,hakan yasake takurashi da matsa mishi,ya fuskanci kusam dabi'arta ce haka,ta saba har batasan sanda takeyi ba,haka yadinga qoqarin kakkauce mata har zuwa sanda suka dawo gida.


A ranar kam yayi kwanan wahala qwarai,yasan kuma dalilin tashin ciwon nasa bai rasa nasaba da safwa din,shi yasa washegari da take shirin komawarta hakan ya masa dadi,duk da cewa bai nuna ba.


Tun safe take ziryar samanshi amma saita tadda qofar a rufe,tayi kiran wayoyinshi dukka a kashe,yana dakin kuma duk knocking din da takeyi yana jinta,yana sane yayi hakan,don baiso tashigo ta qarawa wuta fetur.


Data gaji take tambayar mama sodangi
"Ina tsammanin yafita ne,qila akwai wani uzuri daya fiddashi" wannan amsar da bilkisu taji ta bata ya sanyata jan tsaki,tana ziro qafafunta qasa da niyyar fitowa daga qunshen data yiwa kanta,cikin zuciyarta tana cewa
"Ashe bainan,inataso nafita amma nake zaune".


Riga ne a jikinta shirt mai gajeran hannu sosai,wanda hakan ya bayyana santala santalan hannayenta,iyakar rigar qugunta,sai wando high waisted wide leg daya dace sosai da rigar,baqar doguwar riga ta dora akai mai sulbi saqar wasar oman,tayi rolling da mayafin rigar,sai tayi wani kyau,kai kace baqar balarabiya ce.


Dai dai lokacin tasan dukka suna kitchen,don kusan dama da ita ake girkin,tasan lokacin kowanne abu,don haka can ta nufa kai tsaye.


Gab da zasu shiga sukayi kacibus da safwa tana fitowa,hannunta riqe da cup data cikoshi da fresh milk,bayan ta gama zirga zirgar neman azeez din.


Kallon juna sukayi,bilkisu ta rabata tawuce,yayin da safwa din ta bita da kallo harta shige,kana ta qarasa ficewa daga kitchen din,zuciyarta na raya mata bilkisun sam batayi kama da hadimai ba,batasan me yasa yarinyar ke tsaye mata ba,take kuma cika mata idanu.


"La la la,mama kika ce tare zamuyi,badon na shigo ba saidai acemin an gama?" Tafada tana duban qullin alkubus da mama sodangi ke bugawa zata turara
"Aina dauka yau hutun uwar dakin nawa ne yamotsa,tuba nake" murmushi tayi kawai tana hayewa saman wata kujera mai dogon mariqi tana duban rakiya dake qoqarin hada miyar alkubus din,mamakin inda suka samu kayayyakinmu na nigeria takeyi,saidai bata tambaya ba,don ba mutum ce ita mai bin qwaqwqwafi ba
"Ba amana" ta fada a taqaice tana jifan rakiya da hararar wasa,dariya tadan saki kana tace
"To ya zamuyi?,tunda so kike ki sake zama ta É—aka ta É—aka"
"Kul" mama sodangi tayi saurin kwabar rakiyar,sai ta sadda kai
"Afwa mama". Murmushi kawai bilkisun tayi,wani lokaci maman tana bata dariya,ita har yau wani girma take bata,bayan itadin bamai girma ko qima bace,saita sauko ta cire after dress din nata tana amsat bugun daga hannun maman
"So nake nakoya sosai,shi kadaine yafi wahalar dani a girki".


Suna tsaka da aikin safwa tasake shigowa zata aje cup din hannunta,hakanan idanunta suka dinga yawo kan bilkisu,saboda yadda dirinta da shape dinta suka bala'in fitowa ba,ba namiji ba ko.mace ta kalleta ba shakka zatasan cewa ba qaramin ajiya Allah yayi a wajen ba,sai a sannan tasake yarda,bawai tsaho kawai sirantaka ko farar fata ce zallar kyau ba,tunda ga choculet colour skin mai matsaikacin tsaho dauke da qirar data bata mamaki,bata mantawa kwanaki saida ta dinga amfani da supplement don ta fidda qirarta sosai kawai donta burge azeez dinta,tabi sassalkan gashinta da kallo,wanda bugun fulawar da take yahadu da santsin gashin yasanya daurin dankwalinta warewa,gashin duka ya bayyana.


Cikin sakan qasa da talatin sassanyan qamshinsa ya baibaye ilahirin kitchen din,kafin daga bisani lallausar muryarsa mai cike da kwarjini dakuma izza tabiyo baya da kyawawan lafuzza na sallama.


Dukkansu suka juya,banda bilkisu wadda cikin sakanni da basu wuce uku gudun zuciyarta ya ninku,kowacce gaba ta jikinta tadauki rawa,zuciyarta kuma take yanke ta gaya mata waye,sai taji kamar an kafeta,ko wuyanta ba zata iya motsawa ba bare ga juya,dana sani da nadamar abinda yafito da ita daga daki suka baibayeta,tanajin yadda mama sodangi da rakiya suke gaidashi cike da tsa tsar girmamawa yana amsawa cikin ginshira da isa ta sarakai.


Sam bai kula da mutum ba bayan wadanda sukayi magana dashi,har sai da safwa dake tsaye a bayanta tayi magana cikin shagwaba
"Hey dear....karkacemin kana cikim gidan nan?" A hankali yadauke idanunshi daga kanta,duk dabaisan wacece ba amma zuciyarsa ta gaya masa yarinyar rannan ce,abu guda daya tak dabai manta ba tsaho da sulbin gashinta da idanu sukan iya gani koda bilkisun na nesa dakai,wani abu yakeji yana tsirga masa,dalili kenan daya sanya ko cikakken kallo bai yiwa mace sai idan ta kama dolen dole
"Hey...." Ya amsa mata kwai a taqaice,yana sake qoqarin lanqwasa kansa da yiwa idanunshi shamaki wajen maida dubanshi ga halittar dake tsaye,ganin kamar yana gab da gaza hana idanunshi saiya juya zai fice,safwa ta rufa mishi baya,yayin da mama sodangi ke tambayarshi idan yana da buqatar wani abun yafadi akawo masa
"Ba abinda nake buqata" ya amsa mata ataqaice yana ficewa.


"Yarima yarima kenan
"Wai nikam mama,dama can haka yake,bayacin abincine waishi" dan dariya mama sodangi tayi
"Kin taba ganin mutumin da baya cin abinci?kawai dai mutum ne shi mai qa'ida tun yana yaro,hakanan yana da tsantsami,abu qalilan zai gani ya fasa cin abinci ,yana da tsari dakuma kalar

Please Login or Register in order to submit comment