Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

aka yiwa dinkin babbar riga ta alfarma yake,yacika kujerar yanata baza rigarsa,jinsa yake kansa daya da shugaban qasa,gyaran murya yayi sa'an nan yasoma magana
"Amm....dafarko maigado babu abinda zance dake saidai nace Allah ubangiji yayi miki albarka,yadda kika min biyayya kema Allah yasa ki dace haka,Allah yajiqan maimunatu,yasa ta huta,wanda ba shakka naso ace tana raye taga wannan lokaci" ya fada yana share qwalla wadda ko digon danshi babu a idanun nashi bare kuka
"Abinda nakeso dake bilkisu kiyi biyayya,ban yafe miki ba idan kika saba kan dukkan abinda aka umarceki dashi,kibi duk umarnin da kowaye cikinsu zai baki,Allah yayi miki albarka,ya qaddaea saduwarmu". Wannan kusan itace sallama ta qarshe data dimga tunawa tsakaninta da mahaifinta sanda take zaune cikin jirgi tana qoqarin maida qwallarta,a maimakon tsoro da zullumi dakan cika dukkan wanda yasoma shiga jirgi karon farko yake tsintar kansa a ciki a'ah,maganganun mahaifinta ne kadai ke bitar kansu cikin kwanyarta.


Su uku rak ne taga sun shiga cikin jirgin wanda suke tafiyarsu daya,daga ita sai mama sodangi,sai wata matashiya wadda a qalla zasuyi sa'annin juna da ita wanda taji mama sodangi tana kira da rakiya.


Tafiyar awanni suka sauka a qasar mexico,mexico city,tuni motar da zata daukesu ta iso,da alama ma tun kafin isowar jirgin nasu take dakonsu.


Motace maikyau ta alfarma,aka zuba kayansu sa'annan suka fice daga babban filin sauka da tashin jiragen sama na garin.


Duk da yadda zuciyarta take a cunkushe amma hakan bai hana idanunta wulqawa bisa titina da kyawawan gine ginen da suka qawata garin ba,shuru ne ya biyo baya cikin motar,sai mama sodangi da drivern da yake baqar fata wanda da alamu ma dan qasa nijeria ne suke taba hira jifa jifa,da alamu ba yaune karon farko da suka san juna ba.


Shudewar wasu mintunan na daban suka isa unguwar,wadda tsarinta dakyanta ya fita daban,bata sake gasgata hakan ba saida suka sanya kai cikin gidan,tana biye da mama sodangi wadda take kamar 'yar jagora a wajensu,yadda take saka kai cikin gidan ya isa ya shaida maka ba baquwa bace cikin gidan,ta sanshi sosai.


Sai data soma sada bilkisu da wani daki daya sanya bilkisun tsaiwa cak cikin 'yar fargaba tana dubanshi,komai na dakin fari ne da gold,an tsara dakin ne dai dai da ra'ayin tsari da colours din da azeez yakeso,kusan wannan shine favourite colour na bilkisun,ba wani tarkace bane a dakin amma komai na cikinsa mai aji da kyau ne,yana da fadi sosai,akwai cupboard dressing mirrow sai wani lafiyayyen dunqulallen gado da aka lullubeshi da wani ni'imtaccen farin net,akwai bedside lockers hagu da dama na gadon,wanda akan kowacce akwai fitila akai,sai wata corner daga can hannun hagu na dakin da aka dan mata ado aka aje litattafai na karatu na turanci,da fitila wadda take shige data gefan gadon,saidai tafi ta gefan gadon girma da dan haske,gaba kadan da wajen sofa ce qwaya daya iyama fara qal da ratsin gold,daga gaban gadon lallausan carfet ne madaidaici da wani dan qaramin table mahadin gadon,qasan dakin ba tiles bane hakanan ba carfet bane,wani shimfidadden abune mai kyau da ita kanta batasan sunanshi ba,labulaye ne masu kyau tsari dakuma kauri zagaye da dakin,farare ne da akayi musu adon wata rumfa daga saman kowanne golding colour haka madauran labulen suma duka kalarsu kenan,dakin bai cika haske sosai ba,saidai bashi da duhu kuma,amma luf luf yake,wanda akwai yiwuwar idan yamma tayi lis babu hasken qwan lantarki to babu shakka zai iya yin duhun.


Qaqqarfar ajiyar zuciya tasauke tana ambaton sunan Allah,kana ya dosana mazaunanta a gefan gadon,tunanin gida yana bijiro mata,tana shanshano irin nisan tazara data yiwa gida,bama gida kawai ba qasarta ta haihuwa gaba daya,wanda tunda take wannan shine karo na farko data taba barin qasarta zuwa wata qasar.


Tana nan zaune bayan awa guda aka mata knocking,rakiya ce,ta nemi izinin shigowa ta bata,cikin girmamawa ta neme izinin gyara mata kayan sawarta da sake karkade mata dakin,duk da bawani qura yayi ba bare datti,bata hanata ba ta bata dama,tana nan zaune a inda take tana kallonta lokaci lokaci,harta gama kana tashiha bandakin na wasu mintuna tafito,da alama sake wankeshi tayi.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 23
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070___________________________
*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*

*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*

*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸ™ŽðŸ½â€â™€ï¸

*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaÉ—a ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯ðŸ½â€â™€ï¸ðŸ‘¯ðŸ½â€â™€ï¸

*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*
*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*

*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*

*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞ðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾





Mintina ashirin tsakani mama uwani tashigo dakin,fuskarta dauke da murmushi tadubi bilkisu
"Lokacin wanka yayi,sai kuma abinci idan kina da sha'awar ci" kai ta girgiza don ita babu wata yunwa da takeji,wanka kuwa harya soma zame mata jiki,wasu irin mayun sabulai man shafawa da turarukan wanka suke bata take amfani dasu,bata taba ganin set irimsu ba tunda take,sun sake fidda ainihin kalarta,sun kuma qarawa fatarta kyau sheqi dakuma santsi,kamar wadda akewa wankan inji,saita miqe ta durfafi bandakin.


******* ****** ********

Satinta guda cas a gidan ba tare da taga wani da za'a iya kira da sunan mai gidan ba,hakanan ita kanta mama sodangi bata taba yi mata wata magana data danganci aurenta ba,a satin gaba daya zaman daki tadinga yi safe da yamma har zuwa dare kwanciyar bacci,bata aikin komai a gidan,daga wanka sai bacci sai cin abinci,sai kuma idan ta gaji ta kwanta,don ko kallo batayi,daga bisani data gaji ne takan zauna tayi tilawar izifi hamsin data samu haddacewa,sannan tayi na sauran litattafan data haddace wanda suke kanta,idan tagaji tasake komawa ta kwanta,takuma fadawa tunanin duniya.


Tunda mama sodangi ta mata tayin ko falo tasamu tadinga fitowa tana kallo ko hira dasu,ta nuna bata sha'awa bata sake takurata ba koyi mata maganar ba,sau tari takan jiyo hirarrakinsu ita da rakiya,kodai na cikin gidan sarautar kona duniya,wani lokaci kuma taji kwarafniyarsu a kitchen idan suna hada abinci.


Dukkan wani abu na buqata a gidan babu abinda babu,hatta da tsinken sakace a ajjiye yake yana jiran ayi amfani dashi,hakanan duk abinda ta nuna tana da sha'awa ko tanaso saita sameshi,saidai ita sam bataga manufa ko amfanin zamanta cikin gidan ba,tasha yiwa kanta tambaya,waishin an daukota ke don a hanata yawo ko a hanata ganin jama'a?,an daukota ne don a killaceta ta rayu ita kadai?.


Yanayin rayuwar data taso ya sanya cikin kwanaki takwas kacal kwanciyar taso sanya mata zazzabi da ciwon jiki,saboda ta riga data saba kullum cikin struggling take,tattakin zuwa makaranta da dawowa da qafafunta,aikin gidan umma luba har zuwa dare,wankin qannenta da nata wani lokaci harda na mahaifinta da hidimar kula da qannen nata,sai gashi yanzu shuru bata aikin komai,hakanan babu kowa kusa da ita.


A kwana na goma ne takai maqurar takura,don haka bayan ta idar da sallar la'asar saita nemi medium mayafi tayi rolling dashi,ta zura slippers dinta tana niyyar fita,sai kuma taji ta kasa fitar,don haka takoma gefan sofa tazauna hannayenta dafe da saman sofa din tana dan tura qafarta gaba da baya tana tunanin yadda zata fita din.


'Yan maganganu taji daga falon,muryar mama sodangi ce,sai daga baya kuma tadaina jin motsinta,bayan kamar minti goma sai gata ta turo qofar dakin tashigo.


Kamar koyaushe da murmushi saman fuskarta,wanda shike sanya bilkisu jin nauyinta,bai kamata koda yaushe tana kallonta da fuskar murmushi ba,ita kuma ta dinga maida mata da daurarriyar fuska,dole takan sanya itama tasake mata murmushin a yawancin lokutta.


"Ranki ya dade yau za'a leqamu kenan?,aiya kamata,kinma yi qoqarin zaman,gwara ki fita kiga gidan,bakiga ma gidan ba bare akai ga fita kiga gari" murmushi tasake yi mata,yadda take maganar kamar tanayi da sa'arta ne,sam babu ruwan sodangi,tana da sakin jiki da haba haba da jama'a,yadda takejin hirarrkinsu da rakiya kawai ya isa ya gaya maka haka.


Juyawa tayi zata fita don haka tamiqe tabita a baya har suka iso falon,babu kowa sai rakiya dake xaune qasar carfet ta zubawa tv idanu,da alama tana dason kallo,ganin fitowar bilkisun ya sanyata miqewa zumbur tana cewa
"Barka da fitowa ranki ya dade" cikin girmamawa,abun saiya mata banbarakwai
"Yauwa rakiya" ta amsa mata fuska a sake duk don tasaki jikinta,don ita bata ga wani bambanci ba tsakaninta da rakiyan,zata iya cewa tama fita ita a wajenta.


Saman carfet din itama tazauna yadda tagansu zaune maimakon kan kujera
"Subhanallah,ya zaki zauna a qasa Allah ya taimakeki?" Kai ta gyada
"Nafison nan din" jin ta fadi hakan yasa ta qyaleta.


Kamar falon zai dauki shuru sai kuma mama sodangi ta soma sako hira,ba dadewa rakiya ta biye mata sukaci gaba da hirarsu yadda suka saba,basu saka bilkisun ba,hakanan itama bata sanya musu baki ba don bata da abun cewa,bata da ilimi kan hirar tasu,saidai tana saurarensu,rabi kuma idanunta nakan tv tana kallon wani film da ake haskawa a daya daga cikin tashoshin talabijin na qasar mexico.


Kusan awa daya da rabi wayar mama sodangi tadauki kida,da hanzari ta daga kana cikin girmamawa tasoma gaida me kiran
"Allah ya taimakeki kowa da komai lafiya qalau.....gata yauta fito muna tare da ita" shiru tayi nadan lokaci sannan tace
"Yau muna tare da yarima,yashigo gidan dazu awa daya data shude,ya bada uzurinsa Allah ya taimakeki ayi masa afuwa,yanzu haka yana dakinsa a sama yana hutawa".


Sai a sannan bilkisu ta fahimci dawa ake magana,takuma fahimci dalilin da yasa tun sanda tashigo falon tadinga jin wani baqon lallausan qamshin turare,ashe shine yashigo gidan?,tayiwa kanta tambayar,sai taji wata matsananciyar faduwar gaba,tamkar wadda aka tsikara tamiqe zumbur ta nufi hanyar dakinta don komawa,mama sodangi dake amsa waya tabita da kallo tana mamakin abinda ya tasheta.


Har zuwa dare bata sake ba bata kuma saki jikinta ba,gani take kamar zuwa kowanne lokaci zai iya neman yin magana da ita koya nemi ganinta,gefe guda kuma tana taraddin wayeshi?,mutumin qwarai ne ko na banza?,yarone ko tsoho?,managarcin mutum ne ko akasin haka?,kai tana tsammanin ma mawuyacine ya zama nagartaccen,saboda tana hasashen babu ta yadda za'ayi nagartaccen mutum ya yarda yayi irin wannan auren,daga qarshe ma taga baiken kanta na takurawa kanta da tayi da ire iren wadan nan tunanukan,tunda koma meye halinsa koma yaya yake bazata iya canza qaddararta ba,hakanan ba zata sauya abinda yariga daya faru ba.


Qarfe bakwai na dare yasauko daga saman nashi,ya tsuke cikin qananun kaya da suke sake fidda zallar quruciyarsa muraran,hakanan shigar tasake yi masa kyau ainun,ba abinda jikinsa yake sai fidda sassanyan qamshin turarensa wanda yake iske mutum tun kafin shi din ya qaraso wajen.


Da dan sassarfa yake saukowa yana duba agogon dake daure a hannunsa,da alama sauri yake zai fita,mama sodangi dake zaune bayan ta idar da sallar isha'i ta waiwaya jin takun saukowarsa
"Ranka ya dade kafito kenan?" Ayagance cikin nuna aji na masu ajin yace
"Eh....zan danje wani guri,zan dan jima amma acan,so koda ban shigo da wuri ba babu wani damuwa"
"Amma baka tsaya kaci abincinka ba,sannan....." Saikuma tadan sadda kai alamun girmamawa
"Baka nemi ganinta ba ita kanta,fulani takirani daxun,na baka dukkan kariyar data dace...." Labbansa ne suka dan motsa da alamu murmushi yake sonyi,mama sodangin kamar uwa ce a gareshi,banda haka babu mahalukin da zai tsaya yayi masa wannan maganar ko suyita dashi
"Karki damu da dukka wannan....tace na karba plan dinta na karba,nayi mai wuyar aiko?" Shuru mama sodangin tayi bata sake cewa komai ba,don bayaga mahaifiyarsa itace mutum ta biyu data san halinsa fiye da kowa,sai yayi gaba kawai,harya kusa kuma sai yace
"A hadamin salad kafin ku kwanta,idan nadawo zanci" ya qarashe maganar yana ficewa daga gidan.


Ajiyar zuciya mama sodangi tasaki,itadai taga yadda za'ayi wannan auren,amma ta wani fannin tana ganin qoqarin azeez da tsananin biyayyarsa ga mahaifiyarsa,tunda bai nuna rashin amincewarsa ba ko kadan,ya amshi dukkan wani tsari na fulanin yadda takeso.


Kusan raba dare tayi zaune tsuru cikin duhun dakin,ta kasa samun nutsuwar da zatayi bacci,duk wani motsi da ake cikin gidan kan kunennta,mama sodangi itace mutum ta qarshe data kwanta bayan tagama hada mishi salad din ta aje masa tare da sauran dukkan abinda zaya buqata,don tasan bazai tana yarda yaci girkin rakiya ba,hasalima bataga wannan fuskar da zata dafa mishi wani abu ba,zata iya cewa batama taba ganin yana magana da ita ba,duk da tana hidima ne a qarqashin sassan mahaifiyarsa.



Sai data daina jin motsin kowa da komai kafin daga bisani bacci yayi awon gaba da ita.


******* ***** ********


Duk da yadda ta matsu takuma gaji da zaman dakin amma hakanan a kwankin taci gaba da zaman,tun randa tafito falon bata sake fitowa ba,tunda taji yashigo gidan zuciyarta ta bata tabbacin yadawo kenan,kuma koda yaushe za'a iya samunshi cikin gidan,ba tare da tasan bai fiya zama a gidan ba,yawanci idan yafice tun safe sai dare,da darenma idan yadawo yagama abinda yake sake fita yake,bacci ne kawai ke dawo dashi gidan.


Wata guda ta kwashe a haka,saboda tsabar zaman waje daya fatarta tayi wani mugun murjewa ta qara haske kamar wadda ke shafa wani mai,saidai takura dakuma yawan tunanin gida data sanya a ranta ya sanya ko qanqani batayi wata qiba ba.


Wata guda da kwanaki uku a wani dare tana tsaye bakin window tajiyo satar amsar lokuttan da yake dawowa gidan cikin hirar mama sodangi da rakiya,saita saki ajiyar zuciya,takoma tazauna tana qiyasta da lissafa yadda zata dinga tsara fitarta falo da dawowarta dakinta,qaramin murmushi ya kubce mata,sai takejin kamar tasamu wani qaramin 'yanci,kamar fursunar da aka kwance daga kurkuku.


****** ***** *******

Washegari tsaf ta shirya abunta da wuri,sai daukin lokacin dataji yana fita takeyi yayi tafito daga dakin,kamar wadda zata wata qasa zuwa wata,tana zaune gefan gado,lokaci lokaci tana duba agogo har lokacin yacika,saita sake gyara zamanta ta qara mintina ashirin qwarara akai sannan tamiqe tana gyara rufin kanta,ta murda qofar dakin a hankali ta fito.


Babu kowa a falon,amma tana iya jiyo motsinsu da 'yar hirarsu sama sama cikin kitchen,batayi qasa a gwiwa ba tasauya akalar tafiyar tata zuwa kitchen din,lokaci lokaci tana bin duk inda tawuce da kallo,ko ba'a gaya maka ba kasan gini da tsarin gidan dukka turawane suka yishi.


Sallamarta tasa suka waiwayo da hanzari,nan suka marabceta dakyau,dukkansu suna mamakin ganinta yau har cikin kitchen din. Mama sodangi ce ta miqa mata kujera cikin nuna farinciki tace
"Zauna mana,ai bakya tsaya ba ranki ya dade" murmushi kawai bilkisun tayi,taja kujerar tana zama a lokaci guda kuma tana gaida mama sodangin,ta amsa cikin kulawa da jin dadi,hakanan Allah ya daura mata qaunar bilkisu da damuwa da halin da take ciki,sam batajin dadin yadda ta matsawa kanta ta tattare kanta a waje daya,don dai bata da yadda zatayi ne,hakanan batason wuce gona da iri da kuma shige hurumin aikinta,shi yasa kawai tayi shuru,tana addu'ar Allah ya daidaita lamarin,wanda ta lurama tanayi ne dominsa sam kamar bata gabanshi,hasalima naya wunin gidan ballantana tace.


"Kiyi haquri,kinji abun breakfast shuru ko?,na tsaya na soma hadawa yarima ne kafin namu,saboda zai fita,yau naji dadi sosai daya nemi abinci,don ba kasafai yafiya neman abinci ba cikin gida" ta tafas batace ba,don sai take ga kamar bada ita ya dace mama sodangi tayi wannan maganar ba,domin itan kamar baquwa ce.


Taji dadin xaman kitchen din sosai,bata dai cewa komai a maganarsu amma tana sauraren hirarrakinsu da kuma motsinsu sanda suke hada hadar hada abun karin safe,sanda aka gama mama sodangin ta ware mata nata,sai taji sha'awar tazauna taci a cikinsu,don ta manta rabon data ci abinci da wani,tun sanda tabaro gida cikin qannenta.


Da farko sunqi sun soma dari dari,daga baya da sukaga ta saki sai suma suka sake,sosai taci abincin har tayi mamakin kanta,don rabonta dacin abinci mai yawa kamar wannan harta manta,lallai ba shakka mutum rahama ne,yayin dasu mama sodangi ke mamakin yadda ta tsame hannunta haka da wuri,don su a ganinsu abincin da taci bai wani kai yakawo ba,murmushi kawai tayi,su a wajensu ne haka,amma ita a wajenta abinci taci mai yawa,ta riga data saba kusan dukkansu har qannenta cikinsu ya riga ya kanannade da yunwa,shi yasa komai yunwar da sukeji kuma komai yawan abinci basa masa ci mai yawa.


Dadin da xaman yayi mata yasa bata koma daki ba,kusan tare suka yini anan falo,tun bata biyewa hirarsu har tasoma murmushi kawai,ta lura ko tsakanin rakiya da mama sodangin akwai shaquwa sosai da sabo,wala'alla shi yasa aka hada tafiyar tasu tare.


Bata koma daki ba sai data kintaci cewa kowanne lokaci daga yanzu zai iya dawowa,saita musu sallama tawuce ciki.


Tun daga lokacin saiya zame mata jiki,daga zarar ta fuskanci yafita saita fito su wuni tare da mama sodangi da rakiya,tsahon zamanta bata taba jin muryarsa ko ganin gilmawarsa ba,hakan kuma baya rasa nasaba da yadda take takatsantsan da komai nata.


Lokaci yaci gaba da garawa a haka,sannu sannu tasoma sakin jiki dasu mama sodangi,sai gashi takan dan buda baki ta amsa hirarsu daya biyu,daga baya sai ya zamto dukkan abinda za'a girka tana sanya hannu ta tayasu da wasu abubuwan,kamar blending kayan miya,yankan salad,gyara kifi ko nama da sauransu,tunda dama mama sodangi itake girkin gidan.


Tafi tafi sai sabo yasoma shiga tsakaninsu,ta fara fahimtar halayyarsu kamar yadda suma suka soma fahimtar nata halin,tasoma jin mama sodangi kamar mahaifiya a gareta,saboda yadda kalaman bakinta ke fita kullum irin na uwa ne,hakanan kulawar da take bata itama irin ta uwa ce,tasoma jin rakiya kuma kamar ta samu sabuwar 'yar uwa,wadda zata rage mata kewa da radadin 'yan uwanta data baro,abinda bata taba sanin tana dasu ba a halayenta sai suka soma raguwa,kamar miskilanci,zaman shuru da sauransu,a gidansu da makaranta idan bada qannenta ba bata sakewa tayi hira da kowa,sai gashi a yanzun tana iya hira da mama sodangi da kuma rakiya kanta,don sun san yadda zasu ja hankalinta suyi hira da ita,duk da cewa ko sau daya bata taba gaya musu ko basu labarin abinda ya shafi kanta ko ahalinta ba,saidai tana yawan ambatar qannenta da basu labarinsu,da kuma fadin yadda tayi kewarsu,hakan da mama sodangi ta fahimta yasa taga bari tayi wani abu,me zai hana ba zata qara fadin sakewar datayi ba ta amintar da ita?,saita shaidawa fulani cewa ya kamata a siyawa bilkisun waya,saboda bata da ita,kuma tana da buqatar jin mahaifinta.


Ita ta sanya azeez ya siya wayar ya kaiwa mama sodangi,ita kuma ta kaiwa bilkisu da kanta,saidai tace mata jiya data fita yi musu cefane ne tabiya tasiya mata saboda qannenta,bata shaida mata daga hannun data fito ba,don yadda ta karanci bilkisun idan taji wala'alla ba zata taba yarda ta amsa ba.


Farinciki tare da qaunar mama sodangi ya cikata,sanda ta riqe wayar a hannunta anty zuhriyya ce kawai tasoma fado mata,sai taji idanunta sun tara qwalla,ta tuna sanda tayi mata alqawarin waya a randa ta kammala secondry school,tace itace gift dinta,ashe qaddara zata zo ta ra ganawarsu,ashe qaddara batayi mata tanadin gama makaranta ba,babban burin rayuwarta,ashe dukka ba zata gani ba.


Data kalli wayar dakyau sai taga ta mata girma,kamar ta girmi girma da matsayinta,kamar tayi zari idan ta riqe waya kamar wannan,saita maidawa mama sodangi ta mata bayani a sama mata wadda bata kai wannan ba,murmushi kawai mama sodangi tayi,can qasan ranta tana fadin da tasan su waye ahalin sarautar gidan kaisa da batace wannan wayar tamata girma ba,amma saita lallabata cikin dabara harta amintar da ita riqe wayar.


Kusan wayar saita tashi bata da amfani a wajenta,tunda bata da lambar kowa da zata kira ya sadata da mahaifinta shi kuma ya bata qannenta,taji muryarsu,hakan yasa ranta yadan sosu,saita aje wayar gefanta,taja filo ta dora kanta kana tayi rub da ciki.


A irin haka mama sodangi ta shigo ta sameta,tazo dubata ne ganin shuru bata fito ba
"Na tsammaci kina nan kina waya da gida?" Saita miqe ta zauna sosai tana dubanta,don ta sosa mata inda yake mata qaiqayi
"Mama ban riqe lambar kowa ba cikin gidan" Dan shuru tayi maman tana nazari,sai kuma tace cikin hanzari
"Lubabatu fa?" Maimaita sunan bilkisu tayi a ranta,ko itadinma bata da lambarta,koda tana da lambarta ma bata jin xata iya kiranta,maganar mama sodangi ta katse mata tunaninta
"Inada lambarta,bari na kira ta idan tana da lambar ta bayar,idan kuma babu taje ta amso miki ko?" Kai ta gyada tana jin sanyi cikin ranta,qaunar mama sodangi na sake yawa cikin ranta
"Na gode" ta furta sanda take shirin fita a dakin,da murmushi ta juyo
"Babu godiya a tsakaninmu,don kedin uwar dakina ce,dole nayi duk mai yiwuwa don in faranta miki" daga haka tafice.


Ba'a rufa awa guda ba mama sodangi tadawo da lambar mahaifin bilkisu,kasa zama tayi sanda taji tashiga tana ringing,sai tayi tsaye gaban mudubi tana kallon kanta da kanta,wayar kange akunnenta cikin zumudin son jin an daga.
7/11/21, 4:32 PM - My Mtn Number: 24
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*
*_Allah SWT yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*
*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*
0903 234 5899
Ko
09033181070
_________________________
*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*

*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*

*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆ðŸ¾â€â™€ï¸ðŸ™ŽðŸ½â€â™€ï¸

*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaÉ—a ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯ðŸ½â€â™€ï¸ðŸ‘¯ðŸ½â€â™€ï¸

*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*
*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*

*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*

*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞ðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾ðŸ¤žðŸ¾



Daf da zata tsinke kamar ba za'a daga ba taji sallamar mahaifinta na ratsa dodon kunnuwanta
"Wake magana?" Ya tambaya
"Baba....bilkisu ce" ta fada bakinta yana dan rawa
"Bilkisu?!....wace bilkisun?"
"Mai gado baba"
"Ke!....mai gado?,ince dai lafiya ko?" Ya tambayeta,saita sauke ajiyar zuciya
"Lafiya qalau baba". Daga haka tasoma gaidashi ya amsa mata sannan tace
"Baba...su hannatu nakeso ka bani zamuyi magana dasu"
"Kina tantama ne kan lafiyarsu ko.maigado?" Ya jefa mata tambayar,da sauri tasoma girgiza kai kamar yana kallonta
"Ba haka bane baba,kawai najima bangansu ba banji muryarsu ba,shine kawai dalili" ta qarashe fada tana fatar kada ya hutsance mata ya hanata magana dasu
"Keda ganinsu kam ai sai bayan shekara daya....yanzu dai ina

Please Login or Register in order to submit comment