Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Hakanan ta sanya dan madaidaicin hijabinta saman doguwar rigarta,ta shiga kitchen ta diba ta fice.


Already har ya zauna saman qananun kujerun dake ajjiye a qofar gidan saman grass carfet,bai lura da tahowarta ba har sai data iso saboda ciyayin dake wajen,ta ajjiye try din yayi da shi kuma yaci gaba da kallonta,ta masa kyau sosai a idanu,tamkar ya saceta haka yakeji.


Kujera taja ta xauna,idan da sabo ta riga ta saba da irin wannan kallon,bama wajen dr adam kawai ba,har wajen sauran maza irinsa,tasha tsayawa gaban mirrow taga waishin me suke kallo?,ta tasa menene,sai daga baya anty zuhriyya ke gaya mata cewa
"Baiwar kyau bilkisu,ke ba zaki gani ba saidai a gane miki,kedin kamar yaya maimunatu sak kika dauko,sau nawa kike cewa ina da kyau?,to kowa ya shaida din itadin me kyauce fiye dani".


Ruwa da lemo duka ta tsiyaya masa tana miqa masa don ta katse kallon da yake matan,yasa hannu ya karba yana cewa
"Na gode sarauniyata,ashe cikin kowacce irin shiga kyau kike haka?" Murmushi kawai tayi tana kau da zancan ta hanyar gaidashi,saidai duk da haka bai haqura ba sai daya kodata son ranshi sannan suka shiga hira,wanda fiye da rabi yana sake yiwa kanshi campaign ne.


Shuru ne ya ratsa na dan wani lokaci,har ta tsammaci ko bashi da abun cewa,sai kuma yace
"Yarima AA yarima,ya dawo neman adress dinki ko phone number......,meye tsakaninku haka?" Bata rai tayi dajin abinda yace din,wato har ya soma bin qwaqwqwafinta kenan
"Ba abinda ke tsakanina dashi,hasalima ban sanshi ba" jim ya danyi,don zam zuciyarsa bata aminta da haka ba
"Amma daga yanda yake neman sanin wani abu daya danganceki cikin rudu da rudewa,sai nakega kamar akwai wani abu a qasa" sake hada rai tayi sosai
"Am telling you ban sanshi ha dr adam,pls mubar wannan maganar"
"Chapter closed" yace da ita yana aje cup din hannunshi.


Sun dan jima harma ta qagu su tafi,kafin daga bisani mommy ta fito,ta taka musu har bakin motarsu kana suka wuce,duk kunya ta cikata na yadda baturiyar babar adam din ke dada campaign na danta da kanta.


Sadda ta koma haka ta tadda kaya fal sun kawo mata wai duka da sunan dubiya,ta dauka iya wanda takeso ta rabe musu saura,anty zuhuriyya nata yaba sauqin kai da son jama'a irin na mamar adam.


***** **** ****** ****

Cikin kwanakin ya dinga jinsa tamkar ba'a duniya ba,baisan akwai kwanaki.mafiya tsauri sama da shekaru bakwai da yayi a rayuwarsa ba sai yanzu,babban tashin hankalinsa da dimuwarsa na bacewarta bat kamar walqiya,har yanzu ya gaza gano indo take.


Inda a nigeria ce ko wasu qasashen da kakan iya biya ko bin wasu hanyoyi domin sanin inda mutum yake to daya tabbatar cewa a tafin hannunsa take,saidai su qasa ce mai doka da order da kuma tsari.


Ganin qwaqwalwarsa na neman gazawa,ga wani dan banzan ciwon qirji da ya taba fuskanta a baya nason dawo masa yasa ya nemo abdulrashid.


Yana bahrain amma haka ya saki abinda yakeyi ya taho din,saboda tunda yaga kiran nashi ya tabbatar akwai abu na gaggawa daya taso,yasan kuma halin aminin nasa sarai,ba kowa yake iya gayawa damuwarsa ba,hakanan bashi da wani abokin shawara ko sirri saishi.


Kamar yadda ya zata din kuwa,ya tadda yariman a birkice gaba dayansa yana neman zaucewa wajen neman bilkisun
"Na ganta abdulrashid,na ganta harda yarinya da jikina yake bani tabbacin diyata ce,amma randa na ganta ranar ta bacemin,har yau kuma ban sake ganinta ba,duk kuwa da irin qoqarin da nake"
"Ka nutsu yarima,ka kwantar da hankalinka,i trust you,kana da fikira,hakanan kana da basirar da zaka iya nemota duk inda ta shiga,amma wannan rudanin rashin bacci da rashin nutsuwar shi zai sanya dukka basirar dake gareka ta subuce maka" haka ya dinga qoqarin kwantar masa da hankalin,wanda hakan yayi tasiri matuqa wajensa,don bayan ya sashi bacci a dakinsa yace idan ya tashi zasuyi maganar shima zaije ya huta kafin sannan,sai gashi ya tashi da cikakkiyar basirar hanyar farko da yake ganin zai cimmata.


A lokacin abdulrashid na falon zaune yana cin takeaway din daya musu yana kuma dakon fitowar azeez din,ga tsammaninsa bai tashi ba,abinda bai sani ba tuni ya tashi harya shiga yayi wanka ya kuma shirya ya fito gaba daya yana qamshin turare,duk da babu koda rabin kwalliya irin tasa saboda yanayin da yake cikin.


A tsaitsaye yake gayama abdulrashid din shawarar daya yanke din,ganin kamar a gaggauce yake yasa ya aje takeaway din yace suje ya masa bayani a hanya,ya mara mishi baya suka fice.


Abdulrashid dinne ke tuqi,yayin da abdulazeez keta kiram wayoyi,da alama wadanda zasu hadu dasu ne yanzu,sai daya gama yana kashe wayar ya soma magana da abdulrashid
"Zanyi amfani da damata da mutanen dana sani cikin qasar,ina da abokan harka da kasuwanci wadanda suke manyan security a qasar,zan samesu na zauna na musu bayani,inason su bani mutane daga cikin mutanensu da zan basu picture dinta,zasu lalubomin duk inda take in sha Allah,zasu xamemin tamkar informers,duk wani motsinta zan dinga sani,bazan qyaleta ba abdulrashid,tunda har tana raye bazan iya rayuwa tana wani bigiren ina wani ba,ina buqatar 'yata,inason inji duminta,inason dawowa da ita cikin rayuwata ko meye zaya faru a wannan karon a shirye nake da faruwar hakan" duk da maganarsa gasky ce amma saida abdulrashid yayi mamaki,don bai taba jin azeez din yayi kalamai kwatankwacin hakan kan wata diya mace ba tunda suke
"Hakan yayi....amma kasan cewa zaka kashe kudi" wani busashen murmushin gefan baki ya saki yana dan bubbuga wayar hannunshi cikin tafin hannunsa
"Kafi kowa sanin kudi ba matsalata bace,zan iya amincewa na rasa komai matuqar zan daidaita komai din" kai abdulrashid ya jinjina,kana yace
"Xaka iya yarima,fatan nasara"
"Na gode" ya amsa mishi yana dan zamewa ya jingina jikinsa da kujerar motar yana maida numfashi.


¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶ ¶¶¶¶¶¶


Maqale take da wayarta suna waya da hannatu bayan sun gama waya da mahaifinta malam bilyaminu,ta shaida mishi tafiyar da zatayi daga nan din zuwa dubai,don duk sanda zatayi tafiyar takan shaida mishi ya mata addu'a.


Tana ankare da amatu dake zaune gefan gadonta sanye da kayan bacci,fuskarta a hade ta hade qafafunta tana cillasu kadan kadan,dukka tana fushi ne kan bilkisun tace ba zata je dasu ba,yayin da abdulrahman ke zaune qasan dakin shi kuma yana game da game dinshi,duk da cewa shima fuskanshi a hade yake,ta rasa me yasa suke da qulafucin uwa haka?,har gwara ma abdulrahman da sauqi akan amatu maqale mata.


Sai data gama shirya kayan tsaf sannan ta isa gaban madubi ta shirya,don already tayi wankanta.


Cikin wata tsadaddar turn down collar long coat me belt ta shirya,wadda tayi masifar mata kyau,gami da fidda sigar kyanta,tana tsaka da rolling babban dankwalinta da zai rufe mata abinda yayi saura daya fito na wuya zuwa qirjinta wayarta ta dauki qara,sunan dr adam ta gani
"Ohhh" ta fada tana jinjina naci da matsi irin nashi,saita daga ta sanyata a handsfree
"Gani na fito,ko na tsaya mu wuce tare?" Kaman yana ganinta ta girgiza kai
"A'ah na gode....ka wuce kawai,nima gani nan" langabe mata yayi
"Dama nasan hakan zakice,shikenan na gode" bata sake cewa komai ba ta katse kiran,saita dauki wayar ta turawa assadiq saqo,saboda tun jiya ya kirata miscal kusan uku bata samu dagawa ba,kuma yau ta tashi da shiri bata bi kiran ba.


Saqon yana tafiya ta kashe wayar ta jefata cikin jakar hannunta,daidai lokacin da amatu ta kirayi sunanta,ta daga kai tana dubanta,sai kuma tayi shuru,tasan dai bazai wuce magiya da roqo ba.


A hankali ta dauke idanunta daga fuskar yarinyar tana lumshe idanu,sai taga kamar fuskarshi aka dora kan fuskarta,komai nashi kamanninsa tsaf gasu nan,inama ace basu dauki kamarshi ko daya ba?,inama ace da ita sukayi kama,da ba shakka sai tafi kowa murna,amma ba'a isa a hana Allah yinsa ba,ta sauke qatuwar ajiyar zuciya tana kiran abdulrahman,sai sannan yabar game din da yake ya taso ya iso gabanta,saita duqa gabanshi ta rungumeshi tana cewa
"Me zan taho maka dashi?" Dan shuru yayi kadan sannan yace
"Ball" dariya tadan saki
"Kai baka gajiya da qwallo abdul?,bayan ita fa?"
"Ko meye ma mami inaso" kanshi ta shafa shima tana duban fuskarshi kamar babansu ne a gabanta,kamar tayi yawa,harma tana mamakin yadda akayi bata taba kula ba duk da hotunanshi da take gani a baya,ko don abun baya ranta ne?,bata taba kawowa ba?,ko don bata taba tsaiwa ta masa kallon tsaf ba
"Barakallahu fika,kayiwa mami addu'a ta dawo lafiya kaji?" Kai ya jinjina sannan yayi kissing nata a goshi kamar yadda ta sabar musu.


Waiwayawa tayi ta kira amatu itama,ta taso ta taho tana tura baki,rungumeta itama tayi kamar yadda ta yiwa abdul din tana tambayarta me takeso
"Ko meye ma mami" kumatunta ta kama taja
"Nasan zabinki,amma sai kinyi dariya" murmushi ta saki wanda hakan yama bilkisu dadi sai tace
"Lets pray together....kowa ya hada hannunshi waje daya" take kuwa suka buda tafukan hannayensu tana karanto addu'a suna amin,harta gama suka shafa gaba daya,sannan ta karanta wasu addu'o'i ta shafa musu a kansu tana cewa
"Fi amanillah" ta miqe tana duba agogo kana ta janyo akwatinta suka sauko duka harda su amatun.


Cikin cave din data tara zuwa airphort ta fidda glass din daya kusa mamaye rabin fuskarta,wanda ya mata masifar kyau ta saka,sannan ta ciro qaramar wayarta ta kira fadwa abokiyar tafiyarta,ta shaida mata tana can airphort din,itama tace gata nan tana hanya su hade a can.


Daidai lokacin da yake cikin dakin motsa jikin wanda a yau ya tashi da sha'awar zuwa,saboda yadda gaba daya cikin kwanakin damuwar da yake ciki tasa ya manta da batunshi,a jiya da yakejin yayi abunda ya dace zuciyarshi tana ta gaya masa zaya ganta lokaci kusa,hakan yasa ya yanke shawarar zuwa ya motsa jikinsa ko kasalar da yake ciki zata ragu.


Wayarshi dake aje gefe ta dauki tsuwwa,sunan daya gani saman screen din ya sanyashi gaggawar barin abinda yake ya nufeta.


"Yanzu haka tana cikin passingers da zasu sauka qasar dubai" kalmar data rudashi,ta kuma sanyashi kashe wayar ba tare daya gama jin bayanan da yake mishi ba,hakan yana tabbatar masa da cewa sun ganta kenan,dubai....me kuma zataje yi a dubai again" cikin sassarfa da hanzari ya dauki qaramin towel da daya wayar tashi kamar zaya tashi sama ya fice daga dakin.


*_tofa ƙaƙa ƙara ƙaƙa_*
7/11/21, 4:34 PM - My Mtn Number: 57
*_wannan littafin na kudine,kuma bisa amana,fiddashi ko yadashi tamkar zalunci ne_*

*_Allah S W T yana cewa NI NA HARAMTA ZALUNCI ABISA KAINA,KUMA NA SANYASHI A TSAKANINKU ABUN HARAMTAWA,KADA KUYI ZALUNCI!_*

*_Addu'ar wanda aka zalunta bata da hijabi tsakaninta da ubangiji_*
_____________________________
*Ga wanda ke buqatar mallakar nashi,saiya tuntubi wadannan numbers din*

0903 234 5899
Ko
09033181070





Tun kafin ya qarasa gida ya kira dukka wayoyin da yakega ya dace ya kira din,ya riga ya gama yanke hukuncin cewa zaya bita,zai kasance da ita duk inda zata je a duniya,bazai sake yarda tayi masa nisa ba,ya samu information kan garin da zataje a dubai din,da kuma taron da zasuyi venue da time din,saidai kuma baisan masaukinta ba.


Hakan yayi masa dadi,ya kuma isheshi,tare da zame masa haske na alamun nasara tattare dashi.


Tuni ya yanki ticket cikin jirgi na biyu kuma na qarshe a ranar da xaije qasar,bai damu da tazarar yawan awannin da za'a shafe kafin tashin jirgin ba,yana shiga gida ya fada wanka ya soma shiri.

****** **** ******


Wannan shine xuwanta qasar na biyu,amma duk da haka sai takejin kamar zuwan farko,saboda yadda qasar ke qayatar da ita.


Su uku cab ya dauko daga airphort din xuwa masaukinsu,dukkaninsu abokan aikine,kuma akwai sabo dai dai gwargwado a tsakaninsu,don haka suna tafe suna taba hira har suka qaraso masaukin.


Kasancewar washegari itace ranar da zasu soma fita semina din,saiya kasance ranar kowacce kawai tayi wanka ta kintsa ne sun kuma zauna sun huta bayan sunci abinci,daga nan kowa ya kama sabgarsa.


Ga bilkisu kuwa mutanen gida ta kira,anty zuhriyya ta hadata da dukka yaran suka gaisa,kafin ta kashe sa'annan tahau watsapp.


Kamar wanda ke jiranta ashe assadiq na online,kusan shi ya riqeta lokaci mai tsaho suna hira,daqyar ya barta ta sauka,tana kashe data tana murmushi,assadiq mutum ne mai matuqar sauqin kai,hakanan ya iya hira wadda zaku kwashe awanni ba tare daka sani ba.


Saita sauke ajiyar zuciya tana saukowa daga saman kujerar da take nade,ta taka a hankali zuwa bakin window din dakin da suke ciki,ta daga labulayen wanda hakan ya bata damar ganin cikin hotel din sosai,dama sauran gine gine da titunan dake daura da wajen,kasancewar suna bene ne hawa na uku.


Shuru tayi na wani dan lokaci,tunaninta na daukarta zuwa rayuwarta ta baya yana tuna mata da wasu abubuwan da suka gabata na tsahon wni lokaci.


Ajiyar zuciya ta kuma saki tana shafa dogon gashinta mai tsaho da sulbi,rayuwa ta mata kyau yadda take buqata,saidai har yanzu batasan ina ne makomar rayuwarta.


Sakin window din data dafe tayi tana tunowa da hauwa'u,har yanzu bata samu nasarar samun yarinyar ba,yana daya daga cikin abubuwan da idan suka motsa mata takejin lallai tana da buqatar komawa nigeria a lokacin da anty zuhriyya tace,don taje ta matsa ta kuma nutsa da bincike ko Allah xaisa haqarsu zata cimma ruwa.


"Tunanin me kike haka dr bilqess?" Ta jiyo muryar fadwa na ratsa dodon kunnenta,waiwayawa tayi inda dr fadwa ke tsaye,ta saki murmushi,kafin tace wani abu dr fadwan ta sake magana
"Kodai kina tunanin babban dr ne?,ai suna qasanmu ina tunanin,ba matsala sai a masa magana" dariya ma maganar tata ta bata,tadan dara kadan
"Manta da wannan batun dr....meke faruwa?" List da guraren da sukeson xuwa bayan gama semina din ta gaya mata ko tana da interest,ita dinma maison yawon bude idanu ce,don haka tace zataje,amma da fatan ba zasu wuce kwanaki uku ba
"In sha Allah" tace da ita.


Tun bayan saukarshi qasar ya kasa zaune ya kasa tsaye a masaukinsa,yanata wassafa yadda haduwarsu zata kasance karo na biyu,ya sani cewa tilas ne ya fuskanci tirjiya da kafiya daga gareta,amma bai zaci zaikai har haka ba,bai zaci zata nuna bata taba saninshi kaf rayuwarta ba,bayajin yana da qarfin gwiwa dana qwanjin da zai iya jurewa wannan tarzoma tata,zuciyarsa bata da wannan jarumtar,indai har takai wani lokaci tana masa hakan tabbas komai zai iya faruwa.

¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶


Cikin nutsuwa suke fitowa daga dakin taron bayan sun qare zamansu na yau,kallo daya zaka yiwa fuskarta kasan cike take da fara'a da alama taron ya mata dadi,rungume take da wasu takardu yayin da daya hannun nata take riqe da qaramar jakar hannunta.


Idanuwansa qir saman fuskarta,yana jin wani irin abu mai qarfingana fusgarshi zuwa gareta,yanajin wasu yanayi yana dawo masa tar cikin kwanyarsa,zamanin da suka taba kasancewa tare da juna,lokacin da babu kowa cikin duniyarsu daga shi sai ita.


Sam batasan da wanzuwarsa ba,saboda hankalinta kacokam nakan fadwa,da alama wani abun suke tattaunawa,bata ankara ba,bata kuma zata ko tsammata ba taga mutum ya sha gabanta kana ya tsaya cak a gaban nata yana dubanta da idanunsan nan masu cike da wani irin sirri da kuma kwarjini.


Kallon second uku tayi masa idanunta suka dauki saqo suka aikawa qwaqwalwarta,take cikin sakannin dukka wata fara'a dake saman fuskarta ta dauke tsaf,kai kace bata taba dariya ba a duniyarta,saita kama hannun fadwa data fi kusa da ita wadda ta zuba ma azeez idanu tana dubansa cikin mamaki ta ja hannunta ta gewayeshi da zummat tafiya.


Saidai bai bata wannan damar ba,gabanta ya sake sha,kana cikin harshen hausa wanda ya fuskanci duka abokan tafiyar nata guda biyu ba yarensu kenan ba yace
"Ki taimakeni ki bani dama komai qanqantarta da zamuyi magana mu fuskanci juna nida ke,na roqeki da girman Allah" ya qarasa fada cikin wata iriyar murya kana cikin sanyi yana hada hannayensa guda biyu.


Cikin kalaman dake nuna zallar zafin da zuciyarta ke mata a sannan tace
"Ka sauraramin malam,ta yaya zanyi magana da mutumin da bansan wayeshi ba,na gaya maka bansanka ba,ban taba ganinka ko sanin waye kai ba,donme zaka damu rayuwata ka shugemin hanci da qudundune ne iyee?,mtsweew" ta qarasa maganar cikin jan tsaki kana cikin zafin nama ta kewayeshi ta wuce wannan karon ba tare data kama koda hannun fadwa din ba.


Bai damu ba ya rufa mata baya,bai damu da yadda su fadwa ke binsa da kallo ba,bai damu da yadda masu fitowa jifa jifa daga dakin taron ke binsu da kallo ba yaci gaba da binta
"Wannan maganganun da kike fada kina fadarsu ne kawai saboda bacin rai,ke kanki kin tabbatar ba haka bane,kinfi kowa sanin waye azeez a duniya" tafiyar tasu batayi tsaho ba,bai kuma ankara ba yaga ta shige cab,kafin yayi wani yunqurin tsaidasu har sunja sun wuce.


"Ya salam!" Ya fada cikin zafin rai da takaicin yadda idanunshi suka rufe bai kula da shammatar da tayi masa ba,saiya rintse idanunsa kana ya bude yana bin wajen da kallo tamkar zai sake ganinta,sai a sannan ya lura da yadda wasu ke kallon nasa,take qwaqwalwarsa ta tuna masa wayeshi?,wala'alla sun saba ganin hotonsa a mujallun qasarsu kenan
"Tur da rayuwar da zaka shahara kayi suna" ya fada cikin haushi takaici gami da jin zafi yana fadawa motarshi ya rufe bayan ya dage gilasan sama.


Daga ranar da sunanka ya shiga cikin jama'a,labarinka ya fantsama a bakunansu,wata harka ta sanya sunanka yake shige da fice cikin bakunansu,to daga ranar idan bakayi babban nazari,dogon tsinkaye da sanya lura da takatsantsan a lamuranka ba,saiya zamana baka da wani sirri na rayuwarka,saikayi da gaske zaka zama me kulawa kamewa da kuma rufe sirrinka,kome kayi abun tattaunawa ne da bada labari a bakunan al'umma.


Ya bude idanunsa bayan ya gama wannan gajeran tunanin,ya tashi motarsa kana ya fusgeta yana barin wajen.


Tun cikin motar ta kifa fuskarta saman cinyarta ta soma kuka,kukane dake tuna mata rayuwar da tayi a baya,yadda ta rabu da danginta 'yan uwanta,yadda aka tsareta a wani gida tamkar siyanta akayi,yadda ta rasa abu mafi qima tattare da ita wanda har yau bai dawo ba bazai kuma dawo ba,yadda ta samu rabon yaranta ta kuma rainesu cikin wahala har zuwa haihuwarsu.


Kafin su isa tayi kuka sosai mai yawan gaske,don haka tana shiga dakinsu ta shiga bandaki ta watsa ruwa gaba daya,batason su fadwa su shigo su sameta cikin wannan yanayin bare su tambayeta,don sirrin rayuwarta ne,private life dinta ne da bai kamata wani yaji koya sani ba.


Rigar material ta saka mara nauyi sannan ta hada gashinta waje daya ta tufke,wanda harda shi ta jiqa tana fatan ruwan ya ratsa har saman qwalqwalwarta ko zata ji sanyi.


Don ta hana kanta kowanne tunani saita janyo takardun data shigo dasu tahau dubawa,saidai ba gane komai dake ciki take ba,haka yaci gaba da kokawa da tunani da kuma yunqurin duba abubuwan dake jikin takardun.


Bata jima da yawa ba su fadwa suka shigo,ta amsa sallamarsu tana qoqarin dora murmushi saman fuskarta,saidai ga duk wanda ya kalleta yasan akwai wani abu mai girma dake cin zuciyarta.


Daga nasu bangaren duk da sun cika da mamakin hadin bilkisu da wannan babban dan kasuwar har kuma ta masa abinda ta masan wanda ya basu mamaki qwarai,su da sukasan cewa magana ma kadai dashi wani babban dama ne kuma abun alfahari ga mutum,saidai babu wanda ya tambayeta komai,suma sai kowacce ta kame bakinta,suka shiga sabgarsu data hada da wanka da cin abinci,abincin da bilkisu bata ma tuna dashi ba bare tabi ta kansa,hakanan tana zaune har suka kammala shirinsu sannan salwa daya abokiyar tafiyar tasu ta kalli bilkisun
"Mufa mun gama shiryawa" daga idanunta dakeson mata nauyi tayi ta dubesu,sam ta mance da agender zasu dan fita yau idan sun dawo daga taron,sai tasa hannunta ta dafe goshinta
"Banjin yau zan iya fita,kumin afuwa don Allah"
"Bb komai....saimun dawo to" salwan ta fada kana suka fice gaba daya abinsu.


Fitar tasu sai taji kamar sun bata wani space ne,don haka ta watsar da takardun gefe,wadanda dama kamar dole aka mata karantasu,ta zame ta kwanta sosai zuciyarta da qwaqwalwarta na lulawa duniyar tunanin da taketa faman hana kanta,ta lura da alama tunanin kawai sukafi buqatar yi a wannan lokacin,ta yaya ya biyota dubai?"ya akayi yasan nan zata zo?,shine abunda yafi daure mata kai.


Baiga laifi ko baiken kansa na sake barinta ta subuce masa ba sai daya koma masaukinsa,bacci ya qauracewa idanunsa,hankalinsa ya sake tashi da zuciyarsa ke raya masa idan chance dinsa na qarshe kenan fa daya bari ta subuce masa?,idan bazai sake ganinta ba kenan?,da qarfin tuwo ya samu da qyar ya cilla wannan tunanin gefe,yana fatan damarsa ba zata subuce masa ba.


Ya kira abdulrashid ya shaida masa komai,ya danyi shuru yana nazari sai kuma yace
"Ina ganin ta dauki zafin da ba zata taba tsayawa ta saurareka ta hanyar lallashi da lallami ba...." Haka zuciyata ke gayamin abdul,inajin kamar saina dan saka tsauri da qarfi sannan zata yarda da cewar ta sanni ma totally,wannan shine mataki na farko"
"Haka nima nake tunani.....but kada ka saka tsaurin nan naka yayi yawa,saboda kada ya haifar mata da tsanarka fiye data baya" idanunsa ya lumshe yaba gyada kai,kalmar tsanar na neman masa barazana
"Na fahimta" ya fada in a low tune.


Cikin daren ya gama tsarawa kanshi komai,ya gama tsarawa kansa komai ta fanjama fanjam,amma gobe dole ta tsaya ta saurareshi,dole ta yadda ta sanshi,dole yaji wani abu game da diyarshi jininshi.


Tunda suka fita duk tsahon awannin tana nan kwance inda suka barta,kiran wayar da suka mata kan ta sauko qasa ta riqe musu leda daya dan Allah basason su shiga daki su sake fitowa ya sanyata tashi ta zauna dole,sai da tadan nutsu sannan tayi rolling mayafinta ta zura plate shoes dinta ta fito zuwa farfajiyar hotel din ta soma dube dube.


Dai dai lokacin da KAMAL ke jingine jikin motar da suka shigo hotel din da ita,wayarshi riqe a hannunsa yana danne danne,yana tsaiwar jiran budurwarshi daya kawo hotel din,wadda ya daukota ne daga mazaunin dalibai dake cikin makarantarsu yarinyar ba tare da sanin iyayenta ba,suka kwashe sati suna sheqe ayarsu,yau kuma kwanakinsu

Please Login or Register in order to submit comment