Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mara jin magana Aliza kuwa a hankali ta k'arasa wajen sa.



Jawota ya yi ya d'orata saman cinyar sa ya ce "Oya kiss your daddy," kiss ta bashi a check d'in sa tana dariya shima dariyar ya yi ya bata kiss a forehead d'in ta ya ce "Gobe ma zamu wuce Dubai a can Zan saki school kamar yadda nayi karatu primary da secondary d'ina a can haka ma my Aliz zata yi sannan maman ki ma school zata koma," Sabeeha dake tura bakin jin haushin k'in dukan Alizah ta buga tsalle ta ce "Wayyo da gaske My?" D'aga mata gira ya yi nan kuwa su Sabeeha har da rawar murna ya ce "Ku je ku shirya muje yiwa su Mama Sallama," ba b'ata lokaci suka yi wanka suka shirya suka fice.




Da gidan Mama suka fara sannan gidan Ummi a can suke jin Rinaz ta haifi namiji sunyi murna sosai sannan a can suke jin auren Rashida da Faisal driver d'in Doctor next week sun dad'e a gidan sannan suka nufi gidan Umar Sameeha ta tare su cikin farin ciki suna ta fira abin su Alizah kuwa sai da ta yi musu fitina domin kaca kaca ta yi da kayan dressing mirrow d'in Sameeha.




Bayan sunbar Nan sai gidan Sabreen can suka yi dinner suna ta kwasar fira inda Alizah ta mak'ale sai ta d'auki Aiman yaron da ko da kud'i aka had'ata bazata iya d'auka ba kan Sabeeha ta hana a bata ta dinga kuka har da cewa sai ta gayawa Uncle da Daddy dakyar suka rarrashe ta ta yi shiru da kukan ta da kana ji kasan na shagwab'a ne.



Suna barin gidan Nasreen shopping suka wuce bayan sunyi siyayya suna fitowa suka yi ana Kiran sunan Sabeeha suna waigawa suka ga Yallab'ai khamis tare da fareeda har ma da yara uku gaisawa suka yi cikin fara'a sannan su Yallab'ai suka yi Mata Allah ya Sanya alkhairi kowa ya shiga motar su suka tafi Alizah na damun su da tambaya "Momma na papa wancan Uncle d'an lukutin waye?"



"Malama ki yi mana shiru ke bakya gajiya da surutu ne tunda muka fito baki yi shiru ba," Maleek dake yiwa dramar tasu dariya ya ce "A'a baby kyale ta ta yi tambaya ai abinda Bata sani bane," shiru Sabeeha ta yi bata Kuma magana ba domin tasan yanzu sai su had'e mata Kai.



Nan Alizah tai ta jera tambayoyi domin ko a school haka take shiyasa teachers d'in su ke ji da ita gata da k'ok'ari da uban surutu shiyasa Maleek yasa ta school da wuri a haka suka koma gida.




Washe gari suka d'aga zuwa Dubai inda aka samarwa Alizah wata private school aka sata haka ma Sabeeha ta koma makaranta ya yinda Maleek ke zuwa office abinsa haka rayuwar su ta cigaba da gudana cikin farin ciki da k'aunar juna.





ALHAMDULILLAH

Anan na kawo k'arshen littafina Mai suna 'YAN UKU kuskuren da nayi a ciki Allah ya yafemun Allah ya bamu ikon amfana da abinda littafin ya kunsa Allah ya yafe mana kurakuren mu Allah yasa mu cika da imani ameen.





Ina jaddada godiya ta ga masoyana Allah ubangiji yabar zumunci ya barmu tare Allah ya sake had'a kanmu Nagode Nagode daga taku a ko da yaushe HAFSAT MAGAJI DABO SHANONO (RUHAZ).
Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment