Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

" hahaha i love Nene already".
Ya sungumeta in bridal style ya na tafiya da ita.
Yace "Wanchan Abincin ya zamuyi da shi?"
Tace "mu kai gidan Baba".
Yace "nikadai zanje".
Tace "harda ni"
Yace "Nope".
Tace "pleasee".
Yace "Naqi wayon".
Tace "Haba Mijin".
Yayi daria cike da kauna.
Washegari ta karbi ziyarcin yan Bencin Eskaley.
***
B A Y A N S H E K A R A D A Y A


Duk Amaren bara sun haihu.
Ko wacce da diyarta Mace
Diyar Dalo Ummansu Jawad aka ma takwara.
Diyar Abdulmajeed kuwa taci Maryam.
Samira ta samu Fatima
Sai Labiba, Labiba ta haifi YASMIN.
**
Bai manta lokacin da Labiba za ta haihu ba, tana kallon Dadin kowa a arewa 24, ta kalla na minti 30 nakuda ta taso mata gadan gadan, baya Gida yana Chan Tudun Matawalle gun Baba, ta kirashi tace “ka dawo”.
Sai ko gashi ya dawo ya dauketa suka tafi Asibiti, motsi dubu sannu yake mata, tun karfe 9 suke abu daya sai karfe 12 ta haihu, da Zaid aka karbi Haihuwan don kin fita yayi, fitowar kan jariri kadai ya kauda kai saboda ya kasa jure ganin Labiba cikin azaba irinta haihuwa.
Kukan Jariri yaji.
Da sauri ya amsheta tare da rungumeta
Mace ce
“Mace ce?”
A kunne ya rada Mata “Barakallahu Fiki YASMIN, Allah ya miki Albarka”.
Sannu da godia ya jera ma Labiba ya kai 1000.
Zaid ya zauna ya tsantsara text ya tura ma Contacts dinshi.


*Alhamadulilah Allah has blessed me with a beautiful girl. The Father, Mother and daughter are in good condition.*


Asubar Fari Aunty Mariya, da Aunty Aseeyah suka zo Asibitin dauke da ruwan Zafi da kayan tea.
“Ja’iri jiya da na ke cewa ka daina barin diyar mutane ita kadai me kace?”
Yayi daria yace “Aunty kinsan muna gama maganar nan da ke ko minti 3 banyi ba ta kirani, ina shagon Eskaley kawai na wuce”.


To tunda garin Allah ya waye Zaid ke amsa kiran yan barka
Asibiti kuwa tururuwar zuwa ake, bayan an ga lafiayarsu aka sallamesu suka koma Gida.


Jawad ya kira yi ma Zaid barka.
“Haba Bro, ya zaku kira mu yanzu? Ka san dai babyta batayi kwari ba? Jiya sukayi 40days, yanzu ka sa dole Princess tace sai tazo wani Katsina Suna”.
Zaid yace “ka ma isa ka hana, Matata da tsohon cikinta kuka sa tazo Abuja Suna, ai wallahi sai kun rama mana bamu yarda ba”.
Jawad yayi daria yace “harda wani cewa The father the mother and daughter are all in good condition, kamar kai ka mata haihuwar”.
Zaid yayi daria yace “Ai ina jin na fita wahala, ni nayi nakudar na ji jiki sosai”.
Daria sukayi yace “to Allah ya raaya”
Ya amsa mai da Ameen.
Ran suna yarinya taci sunanta *Yasmin Zaid Ali Zaki*
Wannan kenan.


Shafa’atu? Babu wanda ya san inda take babu wanda ya san ko tana mace ko a raye, babu wanda ya san duriyarta abunda yafi ko wanne mahimmanci, babu wanda ya damu ya san duriyarta.
Tuni sun mance da rayuwarta kaf.
^^^^


Labiba ta gama Diploma dinta zatayi joining Umaru Musa Yaradua zasu bata level2.
Dalo kuma tana Nile University inda take karantar Biology, gida take kai Lubna in zata lectures.
*


Jiya Yasmin ta shiga Shekara 1 da haihuwa, a gida suka mata celebrating 1year birthday.
Zaid ya fito sanye da kayan shi na civil Defense ya fito fes abunshi.
Kallonshi kawai Labiba takeyi, sai kamshi yake zubawa, tace “Wallahi Ni dai ban taba ganin wanda Uniform suka mishi kyau ba kamarka, kamar don kai a ke yin khaaki dinnan”.
Daria yayi tare da manna mata kiss a baki ya, ya amshi Yasmin a hannunta tare da manna mata kiss a goshi.
Bacci take amma sai da yayi mata magana Yace “Daddy zaije aiki, ina son Yasmin da Mummynta“
Labiba na kallonsu cike do Soyayya.


Tace “Zanje Gida, Aunty Mariya tace Baba bai ji dadi ba”.
Zaid yace “Ciwon kai ne fa, kuma stress ne, aunty maria can exaggerate ehn”.
Labiba tace “kai ko Mijin, dole ta damu, Miji ai ba wasa ba”.
Ya kalleta tare da ida kashe mata kannanne idonshi yace “haka akeji in banda lafia?”
Tace “abunda ya fi haka ma”.
Daria yayi sosai ta rakashi har Mota tace “Motar nan tayi dattii fa, ka dauki tawa”.
Yace “ko jiya an wankeshi, k’ura ne”.
Tace “kar ace ma dirty dirty”
Yace “in dai ba ke zaki ce min ba ni ina ruwana da mutane?”.
Tayi daria tana kallonshi zaune a mita yanda yayi kyau, Khakin nan ya kara mishi girma da kwarjini a idonta”.
Wani tunani tayi tace “kasan bamu taba Zancen Mota ba? In short kafin aure me ma mukayi wanda couples keyi? Nothing, dama a dawo min da yanmataccina”.
Dariya yayi yace “i am late, sai na dawo, i love you kinji baby?”.
Tace “i love you too”.
Yayi daria yayi horn Maigadi ya bude mai Gate.


Wurin karfe 4 ta ja Motarta zuwa Tudun Matawalle da Abinci Basket biyu, daya na Gidan Aunty Mariya daya na Aunty Aseey.
Sai da ta fara shiga gaida Baba Aunty Mariya tace “yo ai tun safe ya fita wai yaji bacci”.
Ashe Zaid na gidan ya fito daga dakin Baba don shi yake mishi shara yace “ba na ce miki ya warke ba? Aunty kawai ta zata mijinta zai gangara ne”.
Aunty Mariya ta harareshi tace “zan bata ranka”.
Dariya yayi sosai Labiba tace “kyaleshi Aunty zan tayaki miki maganinshi”.
Daria sukayi yace “nidai na tafi, a gaida Baba”.
Zaid ya masu byebye ya tafi ya barsu nan, ta dan jima kafin ta shiga gidan Baban Amira
Kafin Maghrib ta koma Gida daga Gidan Aunty Aseey, tace su Amira su zo mata weekends ita da Sabit.


Bayan Isha’i ta tsanyara wankanta ta shirya cikin wani Material fitted gown, kamar bata haifi yasmin ba, yasmin barcinta takeyi.
Ta daura dankwalinta tana jiran dawowan Mijin.
Taji dirowar Motarshi.
Ta feshe jikinta da turare, mai makon ta ji shigowarshi, sai ta ga wayarshi.
Dauka tayi tana mamakin kiran “Hello”.
Yace “Beebs, gani nazo, ina waje?”.
Shiru tayi me yake nufi?
Taji yace “Ko jan aji zai hanaki fitowa? Zaki shanya Saurayin?”.
Tace “Oh My God, sorry boyfriend gani nan fitowa”.
Da sauri ta bude wardrobe ta dauko wani karamin gyale wanda take sawa da Jallabiya ta yafa a kafadarta, ta sake feshe kanta da turare, ta sa ma Yasmin Pillow ta kareta a tsakiyar gado ta fita waje tana rangaji kamar Bishiya.


Daga Mota yake kallonta, Sonta kamar ya fasa zuciyarshi, yana kallon yanda ko wani gaba na jikinta ke motsawa.
Fitowa yayi ya bude mata Motar ta shiga ya rufe ya zagaya ya zauna”.
Kara musu Ac yayi.
“Ina Yasmin?”
Tace “sleeping”.
Hannunta ya rik’o yace “Girlfriend”
Tace “boyfriend”
Yace “to nazo Zance, a min Tadi”.
Daria tayi ta ga Ledar Havillah Ice cream tace “Lahh Ice cream”.
Yace “dallah ba haka sukeyi ba, jan aji zaki dinga yi, ni zan miko miki ki karba”.
Tace “oh okay to bani”.
Yayi daria yace “Baby ga Ice Cream na siyo miki”.
Kamar dagaske ta kawar da kai ita kunya.
Daria suka fashe a tare.
Ice cream din ya fasa yana bata a baki yace “haka saurayi da budurwan zamani sukeyi ko?”.
Tace “ni ina zan sani, nima yau na fara”.
Yace “a sannu zamuyi k’ara’i”
Tayi daria
Ice cream din lebenta ya lashe, sun nisa da abunda sukeyi suka ji Yasmin ta chanyara Ihu.
Ai sakin Ice cream din sukayi suka fita a guje gudun ko wani abu ya faru da ita.
Zaida ya riga shiga dakin Ashe Farkawa tayi taga ba kowa.
Da sauri ya dauketa ya rungumeta a kirji yana rurrugata.
Labiba ta harari Yasmin da tuni tayi lamo ta koma bacci a kafadar Babanta tace “Yas you ruined our date, ina Zance da dan Saurayina kin katse mana Jin dadi”.
Zaid yayi daria yace “i love you both”.
Labiba ta rungumesu duka tace “ina sonku ku duka”.
*Tabbas Wannan Zaidun Labiba ne*


THE END? Yes Mankasss ya k’are.


*Alhamdulilah, Allah nagode maka da ka bani ikon gama wannan Labari na DANMAKAHO, Allah ka yafe min inda nayi kuskure, abunda na rubuta daidai Allah ka sa alumma su amfana dashi*”.


*DAN MAKAHO na ku ne Ma su yin Soyayya domin Allah*
*ALLAH KA KARA MANA SON MASU SON MU*
*Allah ka bamu ikon yin Soyayya ingatacciya, halalliya kuma muyita domin ka*


*Ina rokon Yafiya da gafarar duk wanda ya samu bacin rai Dalilin Dan Makaho*


*FIKRA WRITERS ASSOCIATION* _*Nagode*_


_Bibilicious freaking fans_ _Nagode_ Son So Fisabillilahi ❤❤


Allah ya hadamu da Alherinsa, ya sa mu cika da Imani.


#1love
#DanMakaho
#anatare
#FWASonSo
#nagode


*Biebee Isa* Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment