Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bari, in ka janyo shi a jiki a hankali zai shiryu, kai ka sa Dan Makaho ya kangare, tsinuwan da kake mishi ya bar damunshi, ya giga, wallahi duk mai zaka mishi yanzu ba zai dameshi ba, daga ranar da ka fara La’antarshi, daga ranar rayuwarshi ta chanza, ka samu gurbi Babba wurin durkushewar Rayuwarshi, kana da kwamasho Babba, Wallahi Baba Allah sai ya tambayeka”.


Juyawa tayi ta barshi tsaye a nan. Wannan Aljannace? Daga ina ta fito? Matar Muhammadu kadai ya iya ganewa, be son wacece ba. Maganganunta, sosai sukayi tasiri a ranshi.
Kanshi yayi nauyi yana barazanar rabewa biyu, wani irin yanayi yake tsintar kanshi a ciki, sosai maganganunta suka shigeta, tambaya daya kawai zuciyarshi ke wurgo mishi, MEYASA? Meyasa mene? Shine bai sani ba.
Na dan lokaci guda ya dawo daidai sai da ya ji muryar Shafa na cewa “taho Alhajina rabu dashi”.


Kamar robot da ake controlling da remote ya juya yace “ai da kin bari na lallasa shi, tsinanne”.


Zaid na ciki bai san wainar da ake toyawa ba.
Anty Asy tace “me kikace mishi Labeeba?” “Waazi na mishi Aunty, bai kamaya yana tsine ma dan cikinshi ba”
“Labiba ba yin kanshi bane”
“Yana iya yak’ar Asiri”
“Nidai Labiba da bakije ba, yanzu in yayanki ya ji fa?”
Labina ta yi gaba tace “shi yasa ba zaki gaya mishi ba”.
Aunty Aseey ta bita da ido.


Ran Labiba k’al ta shiga daki, wayarta ta shiga lalubar numbern Abu Sideeq, kamar dazu wayar kashe, zama tayi ta shiga rubuta message na ban hakuri a kan abunda ya faru ta tura mishi.
Shiko Mankas Wanka yayi ya zumbula Jallabiyarshi ya fita daga Gidan.


Alhaji Ali Zaki duk yayi wani sukuku, kamar mara Lafiya, wani iri yake jin kanshi, Hajia Shafa na lura dashi, ba ta san meke samunshi ba, amma zata sa mai ido ta ga iya gudun ruwanshi.


Bayan Maghrib Zaid ya shiga duba Dalo, ya ga Alhaji Ali zaune shi kadai a Parlo, har zai wuceshi yaji muryanshi na kiran ZAID. Chak ya tsaya saboda rabon da ya ji Babanshi ya kira shi da Zaid har mantuwa ta mance, ya dau seconds kafin ya juyo ga inda Baban ke zaune, daga inda yake ya hango wani abu mai wuyan fassaruwa a idon mahaifinshi.


K’afarshi ta mai nauyi, ya k’arasa jiki a mace.
“Zaid”
Ya k’ara fada wannan karon muryanshi cike da fargaba.
Hawaye ya cika idon Zaid, Hamdala ya farayi a zuciyarshi Mahaifinshi ya dawo daidai, duk da ya san Tashi ta k’are, atleast kafin ya bar duniya zai samu soyayyar Mahaifi.


Muryar Hajia Shafa ta chanza Mood din Baba nan da nan ya rikide kamar wanda aka jona ma Charge “Uban me kake so ka tasani gaba kana kallo?”
Runtse Idon da zaid yayi yayi daidai ta fitar hawaye daga idanunshi, for a moment, yayi zaton babanshi ya dawo hayyacinshi, har ya fara celebrating da zuciyarshi, ashe bai chanza ba, ba zai taba chanzawa ba in har matar nan na kusa dashi.


Kafin ta k’araso yayi saurin share hawayenshi, da yardan Allah Anamimmiyar matar chan ta bar ganin hawayenshi.
Dakewa yayi yace “Dama Maganar Dalo ne, ta gama makaranta, zaman gida kawai takeyi, so kafin ta samu admission, ya kamata ta fara wani abu, ko ta dinga zuwa koyon Dinki, ko cakes, ko wani abu dai haka, zaman Gida is depressing her”.


Baba yayi shuru yana kallon Hajia Shafaa, ya na jiram Go ahead dinta, aiko ta girgiza kai, yace “banda kudin enrolling dinta a ko ina”
Zaid yace “ni ina da kudin, kawai permission dinka nake so saboda fita zata dinga yi, kuma ka hanata fita”.
Hajia Shafa na son magana amma sosai take tsoron tashan Zaid sai ta rada ma Baba abu a kunne.
Baba yace “ Uban wa ya baka kudi? To eh din na hanata fita din, salon ta zubar min da mutunci ta ja min abun kunya, ka gama maidata karuwa ta je ta janyo min magana a waje”.


Zaid ya cije bakinshi tare da kallon Shafa’atu yayi k’wafa yace “In ba zaka bari ta fara training ba, ka bari taje hutu wurin Mancy”.


Shafaatu tace “a kan mene? Ba inda zata”
Zaid ya juya gareta yace “zan zubar miki da hak’ora Wallahi”
Baba yace “zo ka fara zubar min da nawa, DanMakaho wallahi ka fita idona”.
Tashi yayi ya bar musu wurin ranshi na soyuwa, ya san Dalo ta gama jin komai, be son ganin kukanta kawai ya fasa shiga wurinta ya fita daga Gidan Baki daya.


A B U J A


Mimi ke kwance Ruf da ciki tana buga game a wayar Mancy, a shekarunta ta iya bude wayar Mancy ta kunna game.
Wayar Mancyn ne ya fara ringing, ba tare da ta san waye ba tayi swiping ta amsa cikin muryarta da “Hello”
Kamar jira take ta fashe da kuka, “Mimi ina Mancy? Ki bata wayar” muryan addanta Dalo taji, Mimi ta fara kuka tace “Adda Dalo are you crying? Stop crying, barin kaima Mancy wayar” da kuka ta fita daga dakin tayi hanyar dakin Abbansu.


A babban Parlo Jawad ya ci karo da Mimi, kuka takeyi sosai wayar Mancy a hannunta, da sauri ya rage tsahonshi ya rungumota jikinshi ya na tamabayarta Lafia? Cikin kuka da muryarta na yara tace “Adda Dalo Is Crying” yace “Who is crying?” Maimakon ta amsashi sai ta mik’a mishi wayar, ganin DALO yayi a rubuce, kara wayar yayi a kunnenshi yace “Hello?” Dalo batayi magana ba sai sheshek’ar da takeyi, bata san waye ba, kawai sai ta kashe wayar.
Haka kurum ya samu kanshi da swiping wayar ya bude ya sake bin number da kira.


Ta dauka da Sallama, yace “Meyasa kike kuka?” Maimakon ta amsa sai cewa tayi “Ina wuni?” Daidai fitowar Mancy da Abba daga Daki, kamar mara gaskia Jawad ya tashi, kafin Mancy ta ankara wayarta ke hannun Jawad Mimi ta fara zubo zance.


“Mancy, Adda Dalo is crying out loud” Abba yace “a ina?” Jawad yayi saurin Mik’a ma Mancy wayar ta amsa, ta ga wayar is still on call, da sauri ta kashe tana murmushin yak’e tace “Dalo na da reason din kuka ne? Ai komai sai ta mai kuka” jawad dai ya yi gaba yana sak’a wani abu a ranshi.


Abba yace “Mancynsu, ko zaa ma Alhaji Ali magana ne? Ko hutu Dalo ta zo mana?” Mancy tayi jim tace “bari dai mu gani Abbansu,sai mutane biyu sun Amince” yace Dawa dawa? “Da Alhaji Alin, da kuma Hajia(Ummansu Jawad)” Alh yace “saboda gidanta ne?” Mancy ta girgiza kai tace “saboda tana da hakki” yace “shikenan zamuyi maganar” tace “to shikenan ina zuwa barin sa Mimi bacci” ta saba mimi a kafadarta tana babanta byebye, shi kuma ya zauna don kallon Channels.


Mancy na shiga daki tayi dialing numbern Dalo jikinta na rawa, Dalo na dauka ta fashe da kuka, Mancy hankalinta ya tashi, da kyar ta lallashi Dalo ta samu ta gaya mata abunda ke faruwa, ran Mancy ya baci, tace “kiyi hakuri Dalo, sharri kayan kwalba, Alhaji ya buk’aci zuwanki Hutu Abuja, all we need to do is convince your Father, inshaAllah zaki zo wurina, kuskurena daya da na k’i tafiya da ko kece, amma inshaAllah, komai zai wuce, zan samu Alhaji ya kira Babanku ya nemi alfarma gunshi, inshaAllah ba zai hana ba”.
Tayi ta lallashin Dalo, har sai da ta sa ta Daria.
“Mancy dazun waye ya karbi wayar daga Hannun Mimi?”
Mancy tace “Oh Autan Hajia ne, Jawad”
Dalo tace “Oh Okay”.
A haka suka cigaba da firan Uwa da diya har sai da Dalo ta sake, Mancy tace “Barinje gurin Alhaji” sukayi Bankwana.


K A T S I N A


10:45 pm duk sun kwanta, Aunty Asee ma dakin yau zata kwana saboda Baban Amira baya nan, Labiba ce ke chatting, tana ganin wayarshi ta yi ringing ta katse ta kara shigowa bata tabawa.


A karo na kusan Goma ya kira Wayarta a kashe, duk kiran da ya mata bata dauka ba sai ya zuk’i sigari, da ya ga abun na neman zautar dashi, ya fito waje kan Dakalin da suke waya.
Yafi karfin Awa daya zaune wurin, sauro duk sun cijeshi, amma ko a jikinshi.
Haka Ya cigaba da kiran Wayarta, Message ya tura mata.


“Ban taba Shan Giya ba, ban taba siyan Giya da hannuna ba amma yau na siya, Beebs, Ki na da Zabi uku, ko ki zo dakina yanzu, ko ni nazo dakinki yanzu, ko kuma na sha Giyar nan, kuma in na shata Alhaki a kanki, kina da ikon hanawa, in baki hanani ba, ko me ya faru, its on you, have your self to be blamed”.


Tirkashi, ta karanta message din ya fi so nawa, gabanta na faduwa, kar fa yazo dakin nan don yau harda Aunty Aseeyah, ya zata yi in ya zo?”
Message ya sake shigowa yana mai tambayarta “In zo ne? Ko zaki zo ne? Ko in sha giyar? Which is Which?”.


A ranta tace “to ya sha giyan mana ina ruwana? To kuma kar Allah ya kamata tunda tana da ikon hanashi ta ki hanashi kar ace tana da kwamasho, ko be sha giyan ba be da hankali yana iya zuwa dakin nan, kuma kar Aunty Asee ta farka ta samu wrong impression. Bata da wani zabin da ya wuce ta je ta iskeshi, cikin sando ta mik’e a hankali ta bude k’ofar ta fita a hankali.


Nanauyar ajiyar zuciya ya sake a lokacin da ya sanyata a idonshi, da taimakon hasken Farin wata ya ga fuskarta daure yake tamau wai ita fushi take, wani murmushi ya subuce mai daga baki.


Gyara tsayuwarshi yayi, a hankali take takowa gareshi, har ta iso gareshi ta tsaya a gabanshi.


Chan k’asar mak’oshi yace “Bibbbssss, KE TAWA CE”.


#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode


Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉


Babi na Sha Bakwai 1⃣7⃣
(K'AMSHI☺)


Cikin wata iriyar murya yace "K'AMSHI" Dariya tayi tace "Zaid dina ni kadai" hakan da ta fada ya sa shi tunawa da Labiba, da sauri ya waiga ya ga bata wurin da ya barta dazun, ya sake juyowa ga Yesmin yace "yaushe kika dawo?".
A tak'aice tace "jiya"
"Ba ki gaya min zaki zo ba?"y
"Ba zai zama zuwan bazata ba in na gaya maka"
Dan guntun murmushi yayi yace "K'amshi".
Itama murmushin tayi tace "Zaidun k'amshi".


Daga gefe ya ga travelling bag dinta yace "oh baki ma shiga cikin gidan ba?" tace "eh zuwana fa kenan" yace "okay kije, zan zo cikin Gidan, barin yi Sallah"
Gaba tayi tace "alright sai ka shigo" tafiya tayi ta bar wurin da k'amshinta kamar ko da yaushe, ciki ya shige shi kuma don yin sallah.


Daga Window Labiba ke lek'ensu, jikinta rawa yakeyi sosai, ranta ya sosu, kallon fuskokinsu ya tabbatar mata da cewa akwai tsantsar soyayya a tare dasu, "uhmm wannan itace Mai Aji? Gashi nan suna ta zabga k'walisa, dama ya na da kamar wannan mai zai yi da ita Mara Aji? Uhm su masu Aji".
Da k'yar ta bar wurin ta kabbara sallahr La'asar, zuciyarta na mata zogi.


Da sallama ta shiga Parlon duk suka hau shewa , Annah ta rugo ta rungumota "oyoyo Aunty Yesmin" itama ta rungumeta tayi "oyoyo Annahn Aunty Shafa" sukayi daria baki daya, "Dr Yasmin" Hudu ya fada cike da k'auna da Bege.
Murmushi tayi tace "Uncle Hudu muna lafia?" Ba ta jira amsar sa ba ta zauna kusa da Aunt Shafa tace "Aunty Ina wuni?" Shafa ta amsa ta na tambayarta mutanen Gidan.
Sunyi Minti 10 suna magana kafin Zaid ya shigo da Akwatin Yesmin.


Cewa yayi "K'amshi, ga Box dinki" da sauri ta tashi yan parlon suka bita da muguwar harara, tace "har kayi Sallahn?" yace "Yup" tace "sai ina?" yace "zan shiga na ga Dalo sai na dan fita".
Gaba tayi don zuwa dakin Dalo tana fadin "wai har yanzu Dalo baki bar zaman daki ba? Haba sai kace wata Mata mai Takaba?" Zaid ya rufa mata baya yana daria, a tare suka shiga dakin, aikam Dalo taji dadin ganin Aunty Yesmin dinta, Zaid yace "nidai ma fita, sai bayan Maghrib kuma" byebye k'amshi tace, dalo ta gyada mai Kai.


"Wai ke ba nace ki dinga fita parlo ki na zama ba? taso muje" da sauri Dalo tace "donAllah ki barni a wurin zamana, please" Yesmin tace "Waye yace daki shine wurin Zamanki? My friend taso muje Parlo inda mutane suke".


"Dalo tace banyi sallah ba" Yesmin tayi hanyar k'ofa tace "kiyi sallah ina jiranki kizo, in baki zo ba, ni zan zo". Dalo tace "Yes Ma".


Tunda ta fito daga dakin Dalo "Aunty Shafa take tarbanta da harara har sai da Yesmin ta zauna kusa da ita taja zabga murmushi.
Aunty Shafa'atu tace "Kinga Abunda ke hada ni dake kenan ko Yesmin? Na gaya miki ba ruwanki da yan iskan chan, wurina kike zuwa, ba wurinsu ba, ni kika sani ba su ba, haka wanchan zuwan da kikayi sai da mu kayi fada da Mamanki ta kanki, indai abunda zaki dinga ja min kenan ki bar zuwan man Gida gaskia".


Nan da nan Yesmin ta chanza fuska tace "Kinga Aunty Shafa ba sai kin min gorin Gida ba, yanzu zan bar miki Gida, kuma ki sani wallahi sai nace Mommy ta zame hannunta a cikin Lamarinki kaf".
Da sauri tace "haba Yesmin, ni ba gorin Gida na miki ba, baki fahimceni ba, kiyi hak'uri, kin san you are always welcome, kawai dai banson ganinki da Dalo daDan Makaho".


Harara ta zabga mata ta ja akwatinta ta yi dakin da take sauka in tazo. Hudu kam bin bayanta yayi cike da k'auna.
Shafa ko ranta a bace ta zaro waya don Kiran "Er Rabi".


YASMIN wacce aka fi sani da k'amshi a Jami'ar Oxford University dake England.
K'amshi kamar yanda 'yan Nigeria masu karatu a England suke ce mata, k'amshi kyakyawa ce doguwa sosai mai dan diri, kamar sunanta K'amshi 'yar k'amshi ce, in ta zauna a wuri ta tashi shikenan gurin zai dauka da k'amshinta, ko handshake tayi da friends dinta to sai fa ta bar tambarin k'amshinta a hannun mutun K'amshi yar gayu ce sosai.
Akwai wani K'ungiya na 'yan Nigeria masu karatu a UK (UKKSA) United Kingdom Kastina Students Association, ne ta ke haduwa da Zaid Ali Zaki wanda shine Vice president of the Association, k'amshi ce Treasurer.


Suna gaisawa don baida shariya ko kyaliya, sosai Guy din ke birgeta, daga gaisuwa ba abunda ke hadasu amma ta na so alak'arsu ta wuce gaisuwa.
A hankali a hankali haduwarsu ta fara yawa don akwai wani gaggarumin taron da zasuyi na
(UKKSA) wanda Taron zai hada da Shugaban k'asn Nigeria, Gwamnan Katsina, Director na Scholarshi board na Katsina, shiyasa suke haduwa sosai a kwanankin nan, aikin da suke yi ne ya sa suke yawan haduwa tare.


Kowa na son shishige ma K'amshi amma ita yar shan k'amshi ce, sai wanda ta za6a take magana, amma sai gashi tana son shige ma Zaid amma bai wani bata fuska ba bayan gaisuwa, a hankali taji ta na matuk'ar son shi, sosai take so ya furta mata kalmar so don ba za ta iya gaya mishi tana sonshi ba.


Ajinta take ja, don abun kunya ne ace kamarta K'amshi yanda tayi suna a universities din England musamman Cambridge da Oxford ace ta bada kanta wurin Namiji ai yawa ne, shiyasa take kama kanta, bata bari son Zaid ya fito fili ba balle a gane, Makarantansu ba daya ba balle ta dinga ganinshi har ta kasa hakura wata rana ta tareshi ta furta mai So, sauk'inta kenan ba su faye haduwa ba sai sunzo Meeting suke haduwa, bayan anyi Taron kuma bata sake ganinshi ba.
Wannan Kenan.






SHEKARA BIYU DA SUKA SHUDE


Hajiya Shafa'atu ta kalli Hajia Er Rabi ranta na k'una tace "wallahi ba zai yiwu ba, shekaru 15 nayi a banza?" Er Rabi ta katseta da cewa "Aa fa Shafa'a, bukatar da kika rok'a an biyaki fa, kince kina so ki dawo Dakinki kuma ki mallake mijinki, ba ki dawo ba? Baki mallakeshi ba? Sai dai in ba ki saka Alhaji Ali wani abu ba, ba tunanin zai maki ya biya maki buk'atarki, Ai wallahi in baki gode mai ba, ba kya butulce ba".


Da fada Shafa tace "Yo ina amfanin mallake mijin, Tunda dan sa na daga hannu ko abun duka ya dakeka? Ina amfani? Kalla fa jikina duk shatin Belt, wallahi yaron nan haka ya hadeni da Hudu ya shaude mu da Belt, nidai wallahi ai man maganinshi, ba fa zata yiwuwu ba".


"Yanzu dai shima zai dawo k'ark'ashinki, sai yanda kikayi dashi, burinki ma zai cika na ganin ya bar Gidan, don shima zaki mallakeshi kamar Ubanshi, tashin farko ki mai umurni da barin K'asar gaba ki daya ba tare da ya k'ara dawowa ba, ita wannan kanwar ta shi kuma karamar Alhaki ce, murjeta kawai zakiyi".


Shewa sukayi tare da chafe wa "Allah ko kawata? To yanzu meye abunyi?" Er Rabi tace "kar ki damu kawata, zan hada maganin zuwa gobe, zan turo miki Yass gobe"
Sake chafewa sukayi Shfa tace "Shegia kawata, wasa wasa kin fa zama wata bokanyar kanki".
Dariya tayi tace "ke ko yau da gobe ko? Da su dinga cinye mana kudi ai gwara mu mun ci ma Mata kudi, ai kinsan samu nayi Baban Annah ya hadani da Aljannah guda wallahi Miliyan Ashirin na sayeta".


Ran Shafa bace tace "wallahi kar na sake jin kin kara furta Baban Annah, salon taji? So kike ace baban diyata boka ne? Banson iskanci fa Er Rabi". Wayan cewa Er Rabi tayi tace "yi hakuri kawata, gobe zan aiko Yass barin tafi". Sum sum ta tashi ta bar Gidan Alh Zaki tana mai borin kunya.


WasheGari


Uwa Uwa ce ko da uwar banza ce, ita ta san ba tayi dacen Uwa ba, ita ta san Uwarta na daga cikin Matan da ke cikin Halaka in har Allah bai shiryar dasu ba.
Uwarta ta kasance Matsafiya kuma Bokanya mai yin Shirka, ita kuma tana da kwamasho wurin taimaka mata wurin isar da sakwannin ga masu yin shirka kawai don kyautata mata kamar yanda ta ke kyautata mata itama.


Uwarta ce gatanta tunda har ita ce take biya mata bukatunta, Ubanta bai da mararraba da Mattace tunda baida say a gidanshi, mamarta itace Gidan, itace ke musu Providing komai na buk'atunsu, ita ke dawainiya da ita da Uban nata,ita kadai ce diyarta to Son duniyarta ta daurama tilon gudan Jininta, shiyasa tayi muk'u muk'u ta turata karatun Likitanci a Oxford University, ta bata Mota, ta kaita kasar waje karatu, ta bata duk wani jin dadi na rayuwa meyasa ba zata mata abunda take so ba?.


Tana yin ma Uwarta Biyayya don ta kyautata mata kamar yanda take kyautata mata. Ta san tana cin haram tana rayuwa irin ta haram, amma son Mahaifiyarta ya rufe mata komai bata ji bata gani.


Murza Sitiyari tayi cikin k'warewa har ta isa Gidan Alhaji Ali Zaki, honk tayi a ka bude mata ta shiga da Motarta, sak'on ta dauko a wata paper bag ta shiga Gidan da Sallama.


Ta na shiga Cikin Parlon, shi kuma ya fito daga Kitchen dauke da Plate a hannu.
Idonshi na hagu ya murza a hankali yace “Yesmin K’amshi?”.
Bakinta wanda ya dade a bude tace “Zaid?? Kai ne? Me kakeyi anan?” Murmushi yayi yace “Me nakeyi a Gidan ubana?” Da mamaki tace “You mean this is your House?” Girgiza kai “This is My Father’s house”.


Nan da nan K’wak’walwarta ya kaita ga tunani, maganar mamarta taji a kwanyar kanta kamar a lokacin ake gaya mata.
“Ki ce ta saka mai wannan a k’ark’ashin Gado, wannan kuma ta barbada mishi a gaban daki da ya tsallaka shikenan zai shiga Duniya”.
Wannan kuma a yi hayak’i dashi, duniya zata manceshi, ba wanda zai tunashi balle ya damu da inda ya shiga, ita kuma Sadiya a bata wannan ta sha itama zata shiga duniya, ba zata ma hadu da yayanta ba a duniyar da zata shiga balle su shaida juna balle su tuna Gida”.


Wani zufa ya keto mata, bakinta na rawa tace “Aunty Shafa’atu mamarka ce?” Fuskarshi ya sauya , kamar ba zai amsata ba yace “Matar Babana ce”


Baya baya ta fara yi, kafin ta juya da gudu ta bar wurin, da sauri Zaid ya bi bayanta yana kiranta “K’amshi” amma bata juyo ba.
Kafin ya k’arasa gunta har ta shige mota, ta yi horn aka bude mata ta fita daga gidan a sittin.
Mamaki kamar ya kashe Zaid a tsaye, lafiyanta kuwa?”.


Tuk’i take cike da ganganci, Allah ya kaita Gidansu Lafia, tana shiga ta wuce dakinta straight.
Tunani barkatai.
Istighfari ta fara yi, kuskure daya, kuskure daya zatayi ta kai Zaidun ta ga Halaka, saura kiris ta batar da Zaid a shafin Duniya, Inalillahi, yaron da Mamarta da Aunty Shafa’atu suke son halakawa Zaidunta ne, Zaidunta fa, kai bata yiwuwa wallahi, sai inda karfinta ya k’are”.


Ta dade zaune kafin ta shiga toilet tayi Alwala tayi sallah, ita bata taba shirka ba, amma tana yadawa, Allah ka yafe mata.
Knock taji a kofarta, da k’yar ta bude.
Mamarta ce.
“Yasss yadai? Munyi magana da Hajia Shafa’atu tace “bakije ba, baki kai saqon ba? Ya akayi?”.
Dan guntun tsaki tayi tace “Oh Mommy wallahi ban dan jin dadi, har na fita kuma najini wani iri, shiysa na dawo” Er Rabi ta kamota “ayyah sorry Yass baby, sannu muje in baki paracetamol” Yesmin tace “Mommy karki damu nasha, ina so na kwanta ne”.
Er Rabi tace “Ayyh my baby shiga ki kwanta kinji, ki huta sorry”.
Er Rabi ta kira Hajia Shafa’atu ta shaida mata diyarta bata da lafia amma da ta warke InshaAllah zatazo aikota.


Bayan kwana biyu Yesmin ta fito tace “zata kai ma Hajia Shafa’atu sak’o”.
Er Rabi tace “Yass dauko kayan na k’ara miki bayani” k’amshi tace “ban manta ba, amma tuna min” haka Er Rabi ta sake mata bayani.


Yasmin ta fita daga Gidan a Motarta bata tsaya ko ina ba sai a wani Islamic Chemist, ta buk’aci a bata garin Zogale da garin habbatus sauda, da garin tazargade dana ‘da’d’doya, fasawa tayi ta hadesu guri gura tace wani sassak’e garesu? Sukace akwai na baure akwai na mangoro, tace duk a bata. Haka tayi hadadden magungunan ta biya ta shiga Mota ta wuce Gidan Alhaji Zaki.


Hudu na Parlo ya daura k’afa daya kan daya ya jiyo wani k’amshi na k’amshi, da sauri ya mik’e tsaye gami da hade miyau da ya ci karo da kyalyawar halitta na K’amshi, cike da shan k’amshi tace “Aunty Shafa na nan?” Baki na rawa Hudu yace “barin kirata ta na ciki”.
Samun wuri tayi ta daura k’afa daya k’an daya, tana kadawa a hankali.
Jim kadan sai ga Aunty Shafa ta fito da sauri hards rungumeta, itama ta rungumota.


“Yass ya kike ya jiki? Ashe bakiji dadi ba?” “Wallahi kam Aunty amma da sauki”
“Ya sSchool ko an gama?”
“Aa da saura, saura shekara daya”
“Inye Doctor Yesmin, yanzu ina sak’ona?”.
Cike da bariki k’amshi ta kalli Hudu, hudu yayi saurin cewa “kar ki damu Baby, ni k’anin Aunty, na san komai”.
Aunty Shafa tace “kar ki damu Yasmin”.


Ta ciro k’ullin da ta siyo yanzu a Islamic Chemist kamar yanda Mamarta ta mata bayanin wadan chan magungunan, haka ta mata bayanin a wannan “gasu Aunty, wannan a ba yarinyar aAbinci, wannan shi zaa saka a krkashin gado, wannan shi za a barbada a k’ofar dakinshi”.


Aunty Shafa tace “Hudu Dan Makaho na nan?” Yace “eh ya na nan” tace “to sai ya fita sai mu shiga dakin.
Hudu yace “to hakan zaayi”.
Mikewa tayi tace “barinje in adana” Hudubya zauna kusa da k’amshi, tayi saurin tashi ta rufa ma Shafa’atu baya.


K’amshi ta musu Sallama ta tafi, ta so ganin Zaid amma bakomai, ta san inda yake, zata cigaba da kareshi, wannan shine son da take mishi.


Mankas na barin Gidan Hajia Shafaatu da Hudu suka shiga dakinshi, suka daga Katifarshi suka wurga Sassaken iccen Mangoro da na baure.
Gaban dakin kuma suka barbada Garin Habbatus Sauda mai Zogale, ta dafa Abinci ta barbada garin Hibban a cikin Abincin Dalo ta mik’a mata ransu k’al yau zasu shig duniya.


Har bayan Isha’i bata ga Dalo ta fito ba, Zaid ya dawo, bin bayanshi sukayi suka ga ya shiga daki.
Su ka tsaya jiran tsammani amma shiru, a kan idonsu Dalo ta fito da plate din Abinci alamun ta cinye tas. Mamaki ya kamasu.


Har kwana biyu ba wani labari, cike da damuwa ta kira Er Rabi tace “ke ba wani bayani, yara na nan kamar mayu, ba wanda yayi yunkurin barin Gidan”.
Da mamaki Er Rabi tace “Be yiwuwa, maganin da Er Lale da kanta ta hada fa” cikin fushi Shafa’atu tace “koma Er dada ce magani beyi ba” Er Rabi tace “kwantar da hankalinki, yesmin zata kawo miki wani hadin, ki turo 800k”.

Please Login or Register in order to submit comment