Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dibanshi, parlorn ya fito ya kalli Matar yace "me kikace?".
Shafa'atu tace "ke yanzu yanzu fa daga gidan Er Rabi nake? Ina kikaji wannan karyar? Kun iya baza rumors wallahi".
Hajia Laraba ta goge zufan da keto mata tace "Wallahi ba rumors bane, naje anso sakona a Gidan Er Rabi, naga mutane cike, na tambaya akace diyar Gidan tayi accident ta rasu a hanyar Kankia, yanzu haka babanta yaje daukota zaa rufeta, ko Er Rabi na da wata diyar ne bayan Yasmin?".


Ihu Shafa'atu tayi ta daura hannu a kai, babu abunda takeyi sai Ihu, Hudu ya rada abunyi sai ji yayi zawo yazo mai, da gudu ya shige toilet ya bar Shafa'atu na chanyara Ihu tana neman Layin Er Rabi..


Zaid Fa? Zaid? Zaid na nan zube zaune a k'asa, hannunshi rike da kanshi wanda ke barazanar ballewa, Daga bisani kwakwalwarshi ta soma kai mishi cewa Yasmin ta mutu, nan kuma duk wata na'urar jikinshi suka soma tsayawa, fuskarshi tayi Ja, Yasmin ta mutu? Ya zaayi Yasmin ta mutu? Anya kuwa Yasmin ce ta mutu? Ya kamata ya tabbatar fa, amma in karya ne sai ya shake matar nan.


Zuciyarshi tace "To wanene ba zai mutu ba a duniyar nan? Kullu nafsin za ikatul maut, shima dai ba abun mamaki bane ya ji shi a kabari ya mutu, inalillahi wa ina ilaihir rajiun, Ya Illahi. Ya Salamu. Ya Rabb.
Tashi yayi yana tafia kamar mai koyon tatata, wani Okada ya sauke wata mata, tsaidawa yayi kawai ya haye, a kan machine din yace "Goruba Road". Tafiya sukeyi duk iskan Machine dinnan bai zuwa mishi.


Ana Kwanowa Unguwar su Yasmin zuciyarshi ta dinga mishi zugin zafi, daidai zuciyarshi ya dafe, so yake yayi kuka, ya kasa, bai san ta ina zai fara ba, mutanen da ya gani ya tabbata dai Yasmin ta mutu.
Bai da kudin ba mai Machine, don daga shi sai shi ya fito, ganin bai cikin hayyacinshi mai Machine yayi tafiyarshi.


Ko Minti daya Zaid baiyi ba da zuwa gurin Motar Baban Yasmin ya tsaya.
A nan waje, ba a shiga ciki da ita ba, aka nadeta a cikin Likafani don ta riga ta dunkule ta kone ba batun wanka, a nan waje aka mata Sallah, aka tafi makabarta don kaita Makwancinta.


A yayin da ake haka k'abarinta, Mallam ya fara tunatarwa.
Mallam yace "Ya ku Al'ummar Musulmi muji tsoron Allah, Mutum ba komai bane, farat daya zaka wayi gari kajika a k'abari, ba ciwo, in ajali yayi kira ba makawa sai mun tafi, mu kasance masu tsoron Allah a duk inda muke, mu kuma roka Allah yasa mu samu kyakyawan k'arshe".
Zaid yace "wallahi wallahi mutum ba komai bane ba".
Mallam ya cigaba da tunasar wa da jan hankali, har aka rufe Yasmin, Zaid na daga gefe yana kallon komai kamar Film.


Gida suka koma don karban gaisuwa kamar yanda akeyi, Yasmin tayi mutane kam ta ko ina zuwa ake gaisuwa.
Mallam yace "DonAllah wani abu nagani yanzu a wayan wani bawan Allah, naga abun shi ake yayi yanzu, kamar jira ake mutum ya mutu, a yi ta yada hotunan mamaci, wasu ma har daukar gawa suke hoto su daura a kafafan sada zumunci ta yanar gizo, wallahi mu daina, hakan baida wani amfani, mu guji sanya hoton mamaci, ku bar mamaci ya huta, addua kadai mamaci ke bukata, sunfi bukatar ta fiye da komai yada hotunansu karin nauyi ne, donAllah mu gyara mu daina, na lura abunda ke faruwa kenan, in akwai wadanda suka saka hoton wannan mamaciar a daure a cire, a mata addua, kuna iya posting wance ta rasu a sata addua donAllah banda hoto".
Kamar jira ake, da yawa suka ciri wayarsu suka cire hotunanta da suka saka a Status.


Zaid dai na takure wuri daya, yana bin kowa da ido.
Duk masu shiga yana kallonsu, masu fita ma haka.


Katsina aka dawo da Er Rabi duk da bata san wake kanta ba, Asibiti Baban Yasmin ya umurta akaita don baison ta farfado da tashin hankali ta tada ma yan zaman makoki hankali.


Aiko ta na farfadowa ta fasa Ihu, ta sake suman, su Hajia Shafa da mutanensu duk sun garzayo Asibiti wurin Bokanyarsu nan suke zaman makokinsu, duk da tana kwance kamar matatta, haka suke zuwa ganinta, ba wani dangi nata sai abokan shedanarta, tana cikin semi coma, Shafaatu ke karbar mata gaisuwar.


Har bayan Isha'i Zaid na Gidansu K'amshi, da k'yar Dr Ali ya lallabashi ya maidashi Gida. Ya kaishi har dakinshi ya zaunar dashi ya bashi baki tare da shawartarshi da duk lokacin da ya tuna Kamshi ya mata addua.


A B U J A.


Wani Whatsapp group mai suna NationWide a ka turo BC.
Idan Dalo ya kai ga
*Dr Yasmin Hamza died @27*
She was a Beautiful Doctor from General Hospital Kankia Katsina State....
Bata iya karasa karatun ba ta furta "Inalillahi wa ina ilaihir rajiun".
Mancy tace "Dalo mai ya faru?"
Hawaye takeyi jikinta ko ina ba inda baya bari, tace "Mancy Aunty Yasmin ta rasu".
Sanin wacece Yasmin tace "Meye? Inallilahi wa ina ilaihir rajiun, ciwo tayi?". Dalo ka amsawa tayi.
Da sauri ta rungumo tana lallashinta tare da shafa bayanta tace "ki ta Inallilahi wa ina ilaihir rajiun, ki mata addua Sadiya".
Dalo cikin kuka tace "Mancy.. Yaya. Yaya Zaid".


K A T S I N A


Ita fa ta tadashi dazun da safe wurin 9, tace "daga jin muryarka bakayi sallah ba, Allah ya shirya ka Zaid, nikam na tafi OR, zamuyi ma wani Yaro aiki zamu cire mai appendix, zamuyi CS ma ka min addua, in bangaji ba zan taho yau, in kuma nagaji sai gobe in Allah ya kaimu, ka kula da kanka, Be Happy".
Ko tak bata bari yace ba fa ta kashe wayar, bai sake kira ba, bata sake kira ba.


Tun daga ranar da ya fara ganinta a UK zuwa yau da yaji muryarta ya soma tunowa, yanda take Sonshi bai bace mai ba, yanda take daria bai bace mai a fuska ba, yanda take kiranshi bai manta ba, ya rasata wallahi rashi na har abada.
Yanzu Yasmin ta rasu? Ta tafi? Ta barshi? Yasmin ta tafi kwatakwata, Ya Allah, mai son shi ta tafi? Wallahi da sonshi ta Rasu, bai taba furta mata so ba, bata taba fushi ba, ba ta taba gajia ba, bata taba kosawa ba, burinta daya, burinta ya ji dadi, burinta ya kasance cikin jin dadi, ta zabi farincikinshi a kan nata, shikenan ya rasa Masoyiya ta hakika, zai iya rantsewa ba zai taba samun mai mishi irin son Yasmin ba.


Wayarshi ta yi vibrating, ya dauka jiki a mace.
Dalo ce.
Jiki a mace ya dauka " Dalo".
Cikin Kuka tace "Yaya, Aunty Yasmin ta rasu dagaske?".
Zaid ya hadiye bakin miyau mai daci da kyar yace "a gabana aka rufeta".
Dalo ta fashe da kuka tace "Kayi Kuka?".
Murmushi mai ciwo yayi yace "banyi ba Sadiya, na kasa".
Cikin kuka tace "Kayi Kuka Yaya, cry it all out".
Ta kashe wayar sakamakon wani kuka da ya ci karfinta.


Shima Zaid din kamar jira yake a bashi umurninya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya.
"Yasmin, Yasmin, Allah ka yafe miki, halinki na gari ya biki, Allah ka yafe mata Allah ka yafe min nima". Abunda yake ta cewa kenan yana kuka, ji yayi kamar shima zai mutu sakamakon zafin da zuciyarsa ke mishi, bai san awanni nawa ya dauka yana kuka ba, bai son kukan da yake harda Majina ba, ba sauti, hawaye ne kawai, mai zaiyi? World zai sha? Allah shi kyauta ya sha World ranar da Yasmin ta rasu, Yasmin bata son yana sa ma cikinshi wuta kamar yanda take cewa, wallahi ya bari ma gabaki daya, ba zai kara ba, bai iya bari tana da rai ba, amma yanzu ya bari.


*Mamaci baya son Kuka, kukan da kukeyi kuna k'ara ma mamaci nauyi ne*
Maganar Mallam ta dazu da dawo mishi.
Zumbur ya tashi ya fada toilet.
Abunda bai taba yi ba yayi in yana cikin damuwa. Alwala. Alwala yayi ya na mai jin kunya ya fuskanci Alkibla don yin Sallah.
Saboda bai iya tuna ranar da yayi raka'a biyu kacal ba farilla ba.
Salloli yayi da baisan yawan su ba, shi dai ya san duk sujjada yana ma Yasmin Addua.


E D O


"Ga Labee Ga Labee" abunda manyansu da yaransu suke fada kenan. Gida mai dadi, wani farinciki da jin dadi ya mamaye zuciyanta, oyoyo ake ta mata, ta duba fuskokinsu don ganin damuwa, babu sai tsantsar farinciki dake fuskokinsu.


Rungume Maminta tayi tana tambaya ko lafiyarta lau, Mami ta harareta tace na miki kama da mara lafia ne? Kai ta girgiza tace "Allah baki hakuri Mami" ta sake rungume Mahaifiyarta.
To ko Abbanta ne? Da sauri ta nufi dakinshi, ganinshi zaune yana jiran isowarta ya sata nufarshi da gudunta, suna hada ido ta durkusa a gabanshi tana zuba mishi gaisuwa tare da adduoi, ya shafa kanta yace "Labiba wannan zuwan bazata haka? Ina Muhammadun?".
Tayi daria tace "Lafia lau, gashi nan shigowa, suna waje da Su Yaya Ali".


"Abbanmu kana lafia?" "Abbanku na lafia Labee, ya Mamarsu Amira da su Amira? Lafiya lau Abbanmu".
Abba yace "ai banyi zaton yanzu Yayanku zai maido ki ba, na fi zaton sai kunyi hutu, ashe shima jira yake a bayar dake ya cireki".
Labiba ta kalleshi da sauri tace "ya cireni a ina?".
Abba yace "a makaranta mana, bikinku ai wata mai kamawa ne".


Sallamar Baban Amira ya sa ta kallon Kofar ta inda zai shigo, sai yanzu abun ya zo mata, sai yanzu ta gane, kowa lafia, babu abunda ya faru a Edo, wayau Baban Amira ya mata, dawo da ita Gida Yayi, ya rabata daga Katsina".


Be kalleta ba ya durk'usa a gaban Abbansu "Abbanmu barka da dare".
Gaisawa sukayi sosai kafin yace "ashe kuna tafe".
Labiba kallonshi kawai takeyi har sai da Baban yace "yaya dai Labee?".
Baban Amira yace "tagaji ta sha hanya, tun asuba fa muka fito".
Abbansu Yace "ai sai ki tashi kije kici abinci kiyi bacci ki huta".


Idonta ya kawo ruwa ta tashi, ta fita, tana fita kuma ta watsake ganin danginta nata haba haba da ita.
Samira ta janyota suka shiga dakinsu don a buga cikinta.
Ga yayyin Samira da Mamarsu ana ta mata gyatsine, amma ita ko a jikinta, tsakaninta da Allah take son su.


"Wai ke ina kika samo wannan?"
Labiba tace "wa?"
Tace "wanda suka zo rannan, wanda Abba ya ba su ke".
Labiba ta dan zaro ido, har ta manta dashi".
"Gayamana ina kuka hadu, naga masu kudi ne"
Labiba ta harareta tace "ke kika sani".
Tace "ko dai hadaku akayi?".
Labee tace "ba wanda ya hadamu, shi ya ganni".
Ta mike tsaye zata fita taji mamarsu Samira na cewa "ba a gaya mana inda aka samo shi, ko ba a so mu sani?".


Chak Labiba ta tsaya tace "yo ai ba wani abu bane, Mama, Yaya kawata da muke karatu tare ne".
"Wani aiki babanshi yakeyi?".
Labiba tace "ban taba tambayarshi ba, ga numbernshi ko zaku nemeshi? Barin in je dakin Mami".
Ta tashi ta fita.
Ba su manta ba, ba su manta rashin kunyar Labiba ba, Samira da mamarta suka hada ido, suna mamakin rashin chanzawar Labiba.


Haushi duk ya kama Labiba, ganin Yayanta ya yaudareta, aikam ita ba zata iya tsiya ba, komawa dakin Abbansu tayi ba kowata durkusa gabanshi.
Yace "yadai baki kwanta ba?".
Tace "Abba naji Labarin su Jawad da Babanshi sunzo, har ka sa bikin rana daya dana Samira".
Abba ya murmusa yace "Eh Labee, raba bikin duk wahala ce".
Tace "nifa Abba ba na son Jawad, hasali ma ban san sunzo ba".


Daidai da shigowar Maminta Parlon.
Abba ya muskuta yana kallonta.
Labibarshi ce wacce bata barin abu a ranta, ko meye damuwarta zata fito dashi fili, bata nuk'u nuk'u".
Maminta tace "tashi ki fita".
Abba yace "taje ina? Magana muke, ina jinki Labee".
Ko shakka babu tace "Abba, Zuwan Jawad biyu Katsina Yaya ya turo shi nan, nifa gaisawa mukeyi".
Abba ya kalleta sosai yace "kira min Kowa".


Fita tayi kanta tsaye, bata damu ba, gwara ta warware komai once and for all.
Haka Abbansu yake, in yana da magana, baya ware 'yan daki ya musu magana,Iyalenshi ne, insani abu ya faru, zaunar da kowa yakeyi ya zartar da hukunci.
Haka Labee ta dinga Kiransu har sai da aka cika Parlon.
Baban Amira na shigowa gabanshi ya fadi, yasan wannan zaman Labiba ne.


Kowa ya zauna Abba yace “Labiba, yi magana”.
Numfashi ta ja tace “Abbanmu, Jawad Danuwan Aisha ne, mun hadu sanadiyar Aisha, yana kirana muna gaisawa har wata rana yace yana son zuwa Gida, na barshi yazo, a zuwa na biyu ne suka hadu da Yaya, shine fa ya turo su nan”.


Abba ya saurareta da kyau yace “to naji haduwarku Labee, to sai me?”. Tace “Abbanmu Aure fa, ni gaskia son da nake mishi bana aure bane”.
Yace “Me kike nufi Labee?”.
Tace “Abba, a bar maganar Aurena da Jawad”.


Abba yace “Labee har Babanshi ya zo Cikin Parlo na, har ince na bashi ke? Har in karba Sadakinki yanzu kuma kice a bar maganar aurenku, ki sani karamar magana? ai ba zai yiwu ba Labee, ki maza ki fara mishi irin Son Auren, ba zanyi karamar Magana ba?”.


Labee tace “kayi hakuri Abbanmu, Auren dole kenan”.
Mamarta tace “Labibaaaa”.
Labiba tace “Abba aure ana so in anyi shi to zaayi zama na har abada, an fi so a aurar da Mace ga Zabinta”.
Abba yace “kina da wanda kike so ne?
Da sauri Baban Amira yace “Abba banso kowa yaji maganar nan ba, wani dan shayeshaye yake hure mata kunnuwa, wai shi take so”.
Tuni ‘yan Parlo sun fara tofa albarkacin bakinsu.


Abba yace “Labee, me nake ji? Dan shaye shaye kikeso?”.
Tace “Abba tsaya kaji, ba yin kanshi bane wallahi, k’addara ce ta maida shi haka, amma ya bari Baban Amira kai ka san waye Zaid a da, kai ka san ba halinshi bane, akwai dalilin da ya sa yake haka, ku tsaya kuji Labarinshi”.
Da alamu ta manta wa take ma magana.


Maminta ta jefeta da chazbin hannunta.
Shiru Labiba tayi.
Yaya Ali yace “Sigari kadai Abdulfatah ke sha, kika ce baki taba sonshi ko wani mai shan sigari, amma yanzu kice ga wanda kike so dan Shaye Shaye ne, baki isa ba to, bikin ki tare da Samira gwara ki shirya”.
Mamar Samira tace “Ku bar yarinya mana ta zabi wanda take so”.
Ita gwara Labiba kar ta auri mai kudi a barta da watsatse shiyasa ta fadin haka.


Ta k’i yarda ta hada ido da kowa ta ke cewa “Abba kai fa ka mana Alkawarin aura mana wanda muke so, kayi alkawarin ba za ka mana auren dole ba, haka ka ma yayyinmu da suka gabata”.


Abba ya gyaran murya yace “tabbas nayi ma diyana Alkawarin ba zan musu auren dole ba, wanda kika kawo shi zaa aura miki madamar baya da matsala, amma Labiba ke matsalar ta ki daban ne, da ba dan Shaye shaye bane, da na je har Gidansu Jawad na bawa Mahaifin shi hakuri na maida musu sadakinsu, na jaddada musu hakuri, amma auren dan Shaye shaye akwai illa sosai”.


Tace “Amma Abba..”
Ya katseta ta hanyar cewa “Ya Isa Labee, da dai wani ne ba wannan ba, in ba ki son Jawad din sai na samu mahaifinshi kafin ayi auren ki hanaku zaman lafia, na san halinki in har baki so abu ba, da kuma in kika sa kanki abu, to kar kisa mutuncina ya zube a idon jamaa, maganin kar a fara, kar ayi, amma ko kin ki auren Jawad dinnan, ba zaki taba samun wannan da kike so ba, don ni da hankalina ba zan aura ma Diyana dan shayeshaye ba, nagama magana, duk ku tashi ku ban wuri”.


Tuni hawaye sun wanke mata fuska, da gudu ta tashi ta fita daga parlon ta shige chan cikin dakin mamarta ta fada kan gado, kuka take sosai, zuciarta na mata zafi, haka daren ranan ta kwana kuka, Maminta na jinta tayi banza da ita don ta bata haushi sosai gaban mutane, ita ba a isa a gaya mata abu ta ji ba, sai abunda ta sa kanta tayi niyya.


Washegari haka ta kasance sukuku jikinta duk yayi laasar, ba ta jin dadin Maminta da Yaya Muhammadu, kyararta suke da tsangwamarta, duk ta fice musu a rai, to ba dole ba, tunda ba isa a saka ko a hanata ba.
Dakinsu Samira ta shiga nan ne take samun kwarin guiwan Samun Zaid don Mamar su Samira zugata takeyi kan ta nace ta dage sai Zaid, in ba ta auri wanda take so ba, zata dade tana nadama, ai ba zan yarda ba.


Haka ta yini a dakinsu Samira suna mata famfo, ta san da biyu suke bata shawaran nan, don dai kar ta auri mai kudi.
Zaid Fa?.


K A T S I N A


Jiya zaune ya kwana, bai kwanar Lafiya ba, baya da Lafia, jikinshi zafi sosai, massassara ce ta rufeshi, amma bai yarda ya kwanta ba, komai bai saka a cikinshi ba ya tafi Gidansu Yasmin , ji yake kamar zai ganta ta fito daga wani wuri, yanaso ace duk mafarki ne, wuri ya samu ya zauna, da yaji ance “ashe Yasmin lokaci yayi” sai ya fashe da kuka. Har wani abokin Baban yasmin ya nunashi yana tambayar shi waye wanchan? Ko danuwansu ne? Baban Yasmin ya kalli Zaid, ya yafito shi da hannu. Jiki a mace Zaid ya mike ya karaso su ya durkusa, daga inda ya durkusa suna iya jin hucin zafin jikinshi.
Baban Yas yace “kai wannan ma baka da lafia”.
Zaid ya murmusa yace “Ya k’arin Hakurin mu?”.
Baban yace “hakuri sai maaiki, kai zan tambaya haka, ina kula da kai jiya kowa ya tafi ya barka, yau kam tunda kazo kake kuka, Mamarta bata dangi nasan baka cikinsu, ba kuma ka cikin dangina, yaya kuke da Yasmin?”.
Gaban Zaid ya fadi, mai zai ce? Ya suke da ita? Zaice tana sonshi shikuma bai sonta? Wannan shine tsaka mai wuya”. Kasa amsashi yayi, abokin yace “kai ko Alhaji, ka san dai Mace ba a rabata da samari”.-
Alhajin yace “hakane, ko kaine Zaidu?”
Mai Zaid zaiyi? Ya fashe da kuka kawai, har babanta ya sanshi? Wani irinso take mishi?.
Allah sarki Zaid ashe dole kake kuka,haka kurum Yasmin na min maganarka, Allah ka gafarta ma Yasmin” abokin ya amsa daAmin.


Jiri Ke diban Zaid, da kyar yace “zan zauna”.
Alhajin yace “aa ka tafi Asibiti, baka da Lafia”.
Zaid yace “lafia na kalau”.
Alhajin yace “ka zauna”
Zaid ya koma chan wurin zamanshi a daddafe.
Yana zaune sai ga Doctors na General hospital katsina sunzo mazansu da matansu.
Gaban Baban suka gurfana.
Suka ma juna gaisuwa.


Dr Ali ya hango Zaid, ya karaso gunshi yana dafashi, da sauri ya janye hannunshi yace “Zaid you are sick”. Kallo daya Zaid ya mishi ya dauke ido.
Zama yayi kusa dashi, yace “Zaid wallahi baka jin dadi”.
Zaid cikin fada yace “Yasmin ce ta mutu, ta yaya zan ji dadi?”.
“Ba haka nake nufi ba, baka da lafia”
A takaice yace “Lafiata lau”.
Shiru yayi be sake ce mishi komai ba.
Drs sukayi mata Addua a bayyane suka tashi zasu tafi Baban Yas yace “DonAllah Drs ga dana chan ku duba min shi”
Wasu sukace “me ya sameshi?”.
Dr Ali yace “abokina ne, zan ganshi”.
Zaid tashi muje Asibiti, bai mai gardama ba ya mike, ya kalli Baban Yasmin yace “zan dawo anjima”.
Baban Yas yace “Yasmin ta yafe, ka dawo gobe”.
Zaid bai yi magana ba ya tafi luu kamar zai fadi, sai da Dr Ali ya tallafo shi.
Suka shiga Mota.
“Gida zaka saukeni”.
Ya fada cike da umurni.
Dr Ali yace “Zaid”
Yace “aa donAllah, banda karfin gardama kawai saukeni Gida”.
Dr Ali bai ce komai ba ya nufa Gidansu Zaid.


Tunda Zaid ya kwanta kan Gadonshi yake ji kamar ana sakko mishi da wani irin azaba, a hakarkarinshi da cikin cikimshi, wani irin tari yakeyi mai jini, ya na dafe kirjinshi, ga yunwar da ke cinshi, rabonshi da abinci, tun kafin yaji mutuwar Yas.
Bai ma da karfin fita, haka dare ya riskeshi, yayi Sallah, Sallahr Isha’i ciwon ya lafa ya samu bacci..


Ita kam yau ta kasa bacci, karfe daya saura ta gani, cikin kayanta ta ciro wayarta, rabon da ta kunnashi tun Jiya, ta kunna.
Ta shiga whatsapp.
Besty dinta online tana tambayarta me ya sa yau bata je School ba? Tace mata ta zo Edo amma weekends zasu dawo, besty tace ta gaida Gida
Labee ta tambayeta yaya jikin Baba? Ta amsa da ya ji sauki.
Status ta shiga, ta ga Post din Soulmate wanda yayi 18seconds ago, da sauri ta bude.
*Ya Allah ka gaffarta ma Yasmin, ka sa ta Huta, Allah ka yafe mata kurakuranta, I miss you Yas, alot*.


Gaban Labiba ya yanke ya fadi, wace Yasmin ta rasu? Wacce? Jikinta na rawa yana bari, ta dialling number Zaid kamar jira yake ringing daya ya dauka.


Ya na dauka tace “Wace Yasmin ta rasu, donAllah ba Aunty Yasmin ba”.
Zaid yace “Ta rasu Beebs, Yasmin ta rasu” ya fashe da wani irin kuka da ya sa Labiba Kuka.
Tace “na shiga Uku, inallilahi wa ina ilaihirrajiun, Ya Allah, ta rasu? Ya Rabb, me ya sameta?Shekaran jiya fa mintinmu Arbain muna waya”.
Yace “Accident fa, Motar ta ci da wuta, Wuta ya kasheta Beebs,”.
Tace “Alhamdulilah, tayi shahada, da wanda Gini ya fado mishi, da wanda aka kashe, da wanda wuta ta kashehi, da wanda” bai bari ta kai aya ba yace “nasani Beebs, na sani, Allah ka karbi shahadarta”.
Wani sabon Kuka ya sake, ta san yanda yake son Yasmin, ta san yana cikin tashin hankali, jibtake kamar tayi tsuntsuwa ta duro katsina, ta lalasheshi tace “How are you now?”.
Kusan da sauri kamar jira yake a tambayeshi yace “Beebbs i am not fine, i am Sick Wallahi, beebs ina ji cikin jikina i am dying”.


Hankalinta ya tashi, tace “in maka addua?”
Kamar yaro k’arami yace “ki min Addua”.
Hawaye take sharewa tace “ka dafe inda ke maka ciwo”
Da sauri ya dafe saitin zuciyarshi yace “na dafe”.
Tace “bismillahi Bismillahi Allahumma La Sahla illa ma ja’altahu sahla, wa anta taj alal hazana iza shi’ita sahala”. So bakwai ta maimaita mai.
Tace “kayi hakuri, zakaji sauki kaji?”.
Yace “ki kwanta”
Tace “To, in ka kasa bacci ka tashi kayi sallah ka rokar mata Yafiya gurin Allah, shi ta fi bukata kaji? Banda kuka, ka min Alkawarin ba zaka sake kuka ba”.
Yace “Beebs, ba na mata kuka mai sauti, ba zanyi magana ba kuma, amma Yasmin ce, yau kwananta biyu a k’abari”.
Labiba ta rufe baki sakamakon wani kuka da ya ci karfinta,tace “bye” ta kashe wayar.


Tana aje wayar ta fashe da wani irin Kuka mai tsuna zucia, Yasmin ta rasu, Allahu Akbar, Allah mai yanda yaso, Allah mai rayyukan mutane, duk lokacin da ya bukaceka sai kaje, shekaran jiya ta kirata fa, sun dade a waya har ta kosa Yasmin din ta kashe wayar don ta gaji da waya da ita maganganun da suka ba Labiba haushi a lokacin da take gaya mata su suka soma dawo mata *ki So Zaid da duk wani abun da kike dashi, da zuciyarki da jikinki, da ruhinki, ki soshi, ki kuma kula dashi*
Ta fada haka yafi so goma, ashe maganarsu ta karshe kenan? Ashe wasiyya ma ce kenan? Ya Allah, bata san Yasmin da dadewa ba, amma ta san tana da kirki sosai.
Tashi tayi ta dauro Alwala ta hau Sallah har karfe ukun dare, sosai ta ma Yasmin Addua.


Kasa bacci sukayi su duka,
Labiba tace bari muga ko yayi bacci, kiranshi tayi a waya, ya dauka, a lokacin wani tari yake mai karfi, ya dauka beebs, muryarshi taji tace “ka fara bacci ne?”.
A wahalce yace “aa beebs”
“Ya naji muryarka haka?.”
Yace “bani jin dadi, i naji kamar zan mutu, tarin Jinina ya karu”.
Da dan karfi tace “tarin jini? Wani irin tarin jini?”
A ranshi yace ashe bata sani ba, kafin yace wani abu wayarshi ta mutu Low battery.
Labiba ta kira ta kira kamar tayi ihu wayarshi kashe, nadamar duk wani abun da ya sa ta biyo Mallam Muhammadu Edo, da bata biyo shi ba da yanzu tana gefen Zaid, hankalinta kacokam yayi gun Zaid, jikinta duk ya mutu, me zatayi? Ta rasa abunyi.


Shi kuma ciwo yafi karfinshi ya sheme a daki yana jin ciwo ko ina a jikinsa.
Baccin da baizo idon Labiba ba kenan, zuciyrta ta gama yanke mata hukunci, katsina Zataje, katsina zata, ko biyar bata da shi.
Abunda bata taba yi ba tunda uwata ta haifeta yau tayi, Sata.
To sata ne mana tunda ba bata akayi ba, ma’ajiyar Maminta ta bude ta dauka naira dubu biyar.
Asubar Fari ta faki ido, ta fita, daga ita sai side bag, ko tsoro bata ji ba, ta tsaida Okada tace a kaita Tasha.


#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode


Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO😉


BABI NA TALATIN 3⃣0⃣
(FASA K'WAI 🥚)
(YAFIYA🤗)
(FARINCIKI😃)




Zaid ya runtse ido hawayenshi na fita, yace "Beebbs ina sonki da duk wani

Please Login or Register in order to submit comment