Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sama domin in sheda masa lokacin dana sakko na samesu su biyu a falon." na karasa maganar ina sake sunkuyar da kaina......Fulani na shirin magana ya katseta da fad'in "Me kike nufi da wannan maganar kina nufin Maddibo ko Shatima wani na iya samin guba a abinci."? Shuru nayi gabana na fad'uwa sabida yanayin yanda yay maganar ya nuna min 'bacin ransa."

"Sumayya." naji ta kira sunana, amsawa nayi ina kallonta, tace"Tun ganina dake na farko naji kin kwanta min a raina sosai na yaba da nutsuwarki da hankalinki ina mutukar son mutum mai gaskiya da rikon Amana, inaso ki ri'ke amanar dana dam'ka miki hannu biyu kisa idonki sosai akan masu shige da fice a sashen babana, tunda ka kan 'yan uwanshi maza da mata da kuma sauran bayin dake cikin gidan nan inaso kisa idonki sosai akan shige da ficen su a sashen sannan ki dinga lura da abincinsa gami da abin shansa ruwa ko lemo ko makamancin haka Ina neman wannan alfarmar a gurin."

Cikin sanyin jiki nace"Insha Allahu zan kula da amanar da kika bani nayi al'kawarin bin umarninki." Murmushi tayi a nutse tace"Tashi kije Allah yayi miki albarka." na amsa da ameen ina jin sanyi a cikin raina. yun'kurawa nayi a nutse nace"A tashi lafiya ranki ya dade." Hannu ta daga min alamun naje da sauri na bar gurin zuciyata tas tabbas addua bata faduwa 'kasa banza.

A nutse ta kalleshi gami da fadin"Babana me ka fahimta a maganar yarinyar nan? ni ina ganin wannan al'amarin daya faru da akwai saka hannun 'yan uwanka ina nufin Shatima da Moddibo."

Kallonta yayi mamaki tattare a fuskarsa, tace"Ko shakka bana yi akwai saka hannunsa a ciki amma inaso kasa ido sosai a kansu sannan ka kula da kanka ba komai xaka ci a gabansu ba akwai mummunar manufa a zuciyarsu."

"Mamma bana tsammanin Shatima ko Moddibo wani zai iya cutar dani a cikinsu ni nafi tunanin wani abu yarinyar nan tayi amfani dashi gurin girkin wanda ya janyo hakan bana zargin kowa akan faruwar wannan al'amari.

Murmushi me ciwo tayi tace" Nima bana zargin kowa amma dai tunda nace maka kayi takatsantsan dasu to kayi domin hausawa na cewa makashinka na gindin ka nasan baka manta irin zaman marinar da akeyi a cikin gidan nan ba, kowa ka ganshi ka kalle shi kawai mafi akasarinsu babu kyakkyawar manufa acikin zuciyarsu."
Shuru yayi yana nazarin maganar mahaifiyar tasa.

***
Lahira tace"Wai ya naga kin fito jikinki duk a sanyaye." Ajiyar zuciya na sauke nace"Lahira ina cikin tsaka mai wuya amma na roki Allah ya fitar dani cikin ruwan sanyi." Tace"me ya faru." A nutse na warware mata dukkanin abinda ke faruwa.
Lahira a jiyar zuciya ta sauke tace"Gaskiya dole ki shiga tashin hankali amma mungode Allah da ya sanya Maimartaba da amaryarsa masu fahimta ne, daba dan hakaba nasan da tuni kina fuskantar hukunci."
Nace"Hakane Lahira amma shi Yariman bai yarda da cewa 'yan uwansa zasu cutar dashi ba ban san abinda ke cikin zuciyarsa ba." Lahira shuru tayi tana tunani kafin tace"Dama ai bai za ma lallai ya yarda ba saboda ganin sun taso tare abu makamancin wannan bai ta'ba faruwa ba a tsakaninsu dole ya shiga ko kwanton cewa zasu iya cutar dashi." Nace"nima nayi kokwanto da farko daga bisani da nayi tunani sai na gane hakan zata iya faruwa tunda yanzu gabad'ayansu idanunsu ya rufe babu abinda suke so sai mulki na fahimci cewa suna masa hassada dan ganin kamar shi zai gaji mahaifinsa." Lahira tace"Dama abinda yake faruwa kenan yanzu duk wani abu da 'yan uwansa zasuyi masa a kan mulki ne saboda haka shawarar da zan baki itace ki zage damtse ki kula da amanar da kika d'auka kiyi iyakacin bakin kokarin ki gurin ganin kin kareshi daga sharrin masu sharri."
A sanyaye nace"Insha Allahu zan lura zanyi iyakacin bakin kokarina."
Da wannan maganar muka rabu da juna.

Sosai nayi farin cikin ganin babana a zaune yana cin abinci da kuzari a tattare dashi, cikin farin ciki na ajiye jakata na zauna kusa dashi ina murmushi nace"Baba nayi farin cikin ganinka a zaune kana cin abinci da hannunka hakika hankalina na tashi a duk sanda zanga Tambaya na baka abinci a baki yau naji dadi sosai dana ganka ka samu lafiya kana ciyar da kanka abinci da hannunka." Murmushi yayi a nutse ya kalleni yace."Ai tun bayan fitarku ke da mahaifiyarki naji kwari a jikina da kaina nayi wanka nayi dukk sallolin da ke kaina Sumayya hakika bamu da abinda zamuyi wa Yarima sai dai addua gami da fatan gamawa da duniya lafiya naji dad'in taimakon da yayi min Allah yayi nufin zan samu lafiya ta dalilinsa hakan yasa na yanke shawara kancewa bayan sallar isha'i zaki rakani nayi masa godiya kan alkairin da yayi min."

Ina murmushi nace"Gaskiya ne baba Yarima ya cancanci godiya daga gurinmu insha Allahu zanyi maka jagora zuwa gurinsa kamar yanda ka bukata." Yace."To masha Allah kema ki dauki abinci kici dan naga kamar da akwai yunwa a tare dake." Cike da walwala nace"Baba lokacin dana shigo ina dauke da yunwa mai tsanani amma ganinka a zaune kana cin abinci da kanka yasa naji cikina ya cika yanzu bana jin yunwa ko kadan." Yana dariya yace."Sumayya ban yarda ba dole kici abinci domin bana son ki zauna da yunwa. kwanukan dake gabansa na janyo
Cike da tsokana nace"To bari na fara cinye wanda ka rage saboda na samu albarka idan ban koshi ba sai na karo wani." Hannunsa na dama ya d'ora a saman kaina fuskarsa dauke da yalwataccen murmushi yace."Allah yayi miki albarka Sumayya." Ina kokarin kai abinci bakina Na amsa da ameeen baba."

Tsaf na gama cikin abincin na gyara gurin na gyara masa shimfid'arsa kana na shiga tattaro kayan wankin mu kwata kwata bana san zama da daud'a shiyasa kullum gurin mu zaka sameshi a tsaftace babu kazanta ko kad'an.
Wanki na fito dashi tsakar gida na ajiye a guri guda kana na koma cikin dakin, na sameshi yana duba littafin addini nace"Baba bari naje na duba dawakai bana so hankalina ya dauke gurin wanki na manta ban basu abinci ba."

Ya kalleni yana girgiza kansa nasan abinda yake ji a zuciyarsa game dani,sunkuyar da kaina kasa nayi yace."Ina alfahari da Allah ya bani ke a matsayin 'ya kin fiye min haihuwar maza goma Sumayya ina alfaharin samunki kuma ina mai tabbatar miki da cewa yanda kikayi mana biyayya kema da yardar Allah naki 'ya'yan zasuyi miki."
Murmushi nayi cikin jin dadin adduar da yayi min nace"Insha Allah baba kada ka damu zan cigaba da kula da aikin ka har sai sanda ka samu kwarin jikin ka." Murmushi yayi ya zuba mata ido har ta fita daga dakin, ajiyar zuciya ya sauke yana addua akan Allah ya bashi tsawan rai a duniya yaga auranta da abinda zata haifa...........
*BINTA UMAR ABBALE*

*Kuyi sharing👏🏻*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_




*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
29&30
Tana zaune a kan kujera ya shigo ya sameta, zama yay a gabanta ya dafe kansa kana ganin fuskarsa kasan yana cikin damuwa....Kallon fuskarta nayi itama nan take na gane akwai abinda ke damunta, Uwargida Huwaila mai babban daki ina nufin uwargidan Maimartaba itace tare da Moddibo a zaune abin duniya ya ishe su, Kallonsa tayi cikin tsantsar bacin rai da takaici tace " Wai shin Moddibo ka tabbata duka maganin ka juye masa a abincin."? Ajiyar zuciya ya sauke a cizgune yace"Wallahi gabadaya na juye domin ki tabbatar da magana ta ma kinga muzubin maganin." Hannu ya zira a aljihu ya dauko wata madaidaiciyar kwalba.......Tace"Amma gaskiya abin ya bani mamaki wallahi, wannan maganin karfi ne dashi banyi tsammamin Yarima Ali zai shura a gurin ba." Yace."Ni kaina al'amarin ya bani mamaki wallahi a yanda nasan maganin nan da saurin kisa banta'ba tsammanin zaiyi rai ba." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Shegen yaro karfin jini gareshi to tunda ya tsallake wannan zamu barshi ya huta idan an kwana biyu mu cigaba da bibiyarsa dan ba rabuwa Zamuyi dashi ba har sai munga baya motsi sannan zamu hakura." Muddibo tsaki mai karfi yaja yace."gaskiya naso ya ya she'ka barzahu amma babu komai kamar yanda kika fada cewa ba zamu rabu dashi ba har sai mun cimma munufarmu a kansa."
Tace"Ka manta kawai idan an kwana biyu zan sake kiranka mutattauna yanda za'ayi." Yace."Shikkenan sai naji daga gareki." Sallama sukayi da juna kowanne zuciyarsa cike da mugun nufi akan Bawan Allah.


Sai kusan biyar da Rabi na yamma na gama wanki lokacin Tambaya ta dad'e da dawowa ina jin tashin maganarsu a daki suna hira ita da babana na dinga jin wani irin farin ciki da nishadi a cikin zuciyata hakika ina matukar so na ga iyayena na walwala da farin ciki.

A gurguje nayi wanka na fito na kimtsa jikina da sauri na kallesu nace"Ni zanje sashen Yarima domin na dafa masa abinda zaici da daddare." Cike da nuna kulawa sukayi min fatan alkairi

Da sauri nake tafiya ina kallon rana wacce take 'kokarin fad'uwa hakan ya nuna min cewa yamma tayi sosai daf ake da kiran sallar magariba tunda safe ban kara komawa sashen ba sai yanzu, addua nake a cikin zuciyata akan kada Allah yasa ya tuhume ni da wata magana.

Su Haruna na samu a harabar gurin muka gaisa a gurguje na wuce su daya daga cikin masu tsaron kofar ne ya bude min na shiga falon........Can na hangoshi kwance kan doguwar kujera yayi filo da hannuwansa babu wata sutturar arziki a jikinsa vest ce mai duhu sai short nickar a jikinsa, kaina a kasa na 'karasa inda yake, tsugunawa nayi kamar koda yaushe nace"Ranka ya dade barka da yamma." Shuru yayi bai tanka min ba. satar kallonsa nayi ta kasan idona naga ya k'urawa rufin dakin ido, ganin yanda kwayoyin idanunsa suka kad'a yasa naji wani iri a jikina. gaishe shi na sakeyi yayi min banza.

Jikina ne yayi sanyi da halin ko'in kular da yake nuna min, a rayuwata na tsani nayi magana a shareni, muryata na rawa nace"Ranka ya dad'e zan shiga kicin yanzu inaso ka fada min abinda kake bukatar ci da daddare."

"Me ya hana ki shigowa da wuri."? a dakile yayi maganar, nace" Wallahi na tsaya nayi wanki ne shiyasa ban samu damar shigowa da wuri ba." Shuru yayi yana sake gyara kwanciyarsa, ta kasan idona nake kallonsa naga yana bin ilahirin jikina da kallo. sunkuyar da kaina kasa nayi ina adduar rinjaye.

"Kin iya tuwo."? Yafad'i maganar a kasalance. da sauri nace''Ranka ya dade kowane abinci kake bukata na zamani dana gargajiya na iya insha Allah baka da matsala."

Ji nayi ya sauke wata ajiyar zuciya kamar wanda yaci kuka ya koshi! saurin d'ago kaina nayi ina kallonsa har yanzu ni yake kallo koda muka hada ido bai dauke kansa ba, yace."Kiyi min tuwo amma bana san wannan abar mai wari a cikin miya. " na gane daddawa yake nufi nace"To insha Allah ba zan san daddawa ba." Mikewa nayi da sauri na nufi kicin din....Wani irin kallo ya bita dashi yana lumshe idonsa, a duk sanda zai kalli wani sashe na jikin yarinyar sai yaji kamar ana 'kara rura masa wutar sha'awarta a cikin jikinsa.
Kullum so yake ya yakice abin daga jikinsa abin yaci tura da yarinyar yake kwana da ita yake tashi, a zahiri da bad'ini yasan yarinyar ba kalarsa bace domin hausawa suna cewa *'Kwarya tabi 'kwarya* yana ganin ko iskanci zaiyi bai dace yayi da 'yar bayi ba wacce take ma'kaskanciya a 'kasan sa, dalilin daya sa kullum yake kokarin cire sha'awarta a cikin ransa abin nacin tura, sam rashin kyawunta da 'bakar fatar ta basa damunsa abubuwan dake da wahalar samu daya hango a jikinta yake kulafuci yana ganin zai huta sosai a jikin yarinyar, yaso ace tana daidai dashi ne to da babu abinda zai hanashi auranta kodan ya kawar da 'kulafuncinsa a kanta.

Mi'kewa zaune yayi ya rufe fuskarsa da tafukan hannayensa ya kai mintina goma a haka kafin ya mike yabi bayanta kicin din


Motsin tsayuwarsa naji a bakin kofa nayi saurin juyawa ina kallonsa, tsorata nayi sosai ganin yanda yake kallonsa da idanunsa da sukayi ja gashi sai lumshesu yake......Baki na rawa nace"Ranka ya dade kana bukatar wani abu ne."? Girgiza kansa yay alamun baya bukatar komai.
Jikina a sanyaye na juya domin cigaba da aikina amma inaa! tsabar yanda idonsa ke tasiri a kaina yasa na kasa ta'buka komai.
'Kasa - 'kasa naji yace.'' Idan kin gama kizo ki gyara min toilet d'ina." Na kalleshi inaso nayi magana sai naga ya juya ya tafi.
Tsayuwa nayi ina mamakin maganarsa na dauka ai gyaran gida dasu toilet duk nasu Haruna ne ni bani da hurumin hakan, to kodai yana da wata munufa ne? wani sashe na zuciya ta yake fada min haka.. shuru nayi ina nazari, to ko ma dai wace irin manufa yake da ita a kaina bana fatan ya samu galaba a kaina toilet zan shiga in gyara masa da tsarkakkiyar zuciya. saboda haka ina gama ayyukana na nufin dakin nasa domin aikata aikin daya umarceni.

Zaune na sameshi a kan sofa idanunsa tsaye a kofar shigowa hada ido mukayi nayi gaggawar sauke kaina kasa, cikin tsarguwa na k'arasa kofar toilet din zanin jikina sai hard'eni yake tsabar yanda ya 'kureni da idanunsa, toilet din na bude na shiga ba tare da nace masa komai ba gaskiya na fara gajiya da wannnan masifaffan kallon da yake min.........Girman toilet din da yanda aka 'kawata shi ya dinga bani mamaki bandaki gurin zubar da najasa an narka masa dukiya kamar baza'a mutu ba, girgiza kaina nayi na tattare zanina cikin sauri na soma aikina so nake nayi saurin gamawa kada magariba tayi.....Undis dinsa na tattara nasa cikin abin wanki ina kokarin kunna washing machine din ya shigo toilet din, ban yarda na kalleshi ba nace"Ranka ya dad'e za kayi wani uzirin ne."? Inda nake tsaye ya durfafo gabana ya tsananta fad'uwa adduar rinjaye na shigayi a cikin zuciyata.

Daf dani ya tsaya yana fesa min hucin numfashinsa, kasa kallonsa nayi sabida yanda naga ya koma wani iri gabadaya yanayin fuskarsa ya sauya kalar tausayi. babu zato naji ya riko hannuna ya d'ora saman short nickar din dake cikinsa, a zabure! na cire hannuna ina kallon gurin.....gabansa naga ya mike cikin wandon yana sake kokarin kamo hannuna yasa a gurun....bangajeshi nayi da karfin gaske! yayi taga-taga zai fad'i! cikin zafin nama na bude kofar toilet din na fita gabana na dukan uku uku anya kuwa zan iya cigaba da zama da wannan guy kuwa? gabadaya yanda na fahimce shi baya nufina da alkairi.

Bayan fitar ta daga toilet din goshinsa yasa a jikin bango (garu) yana furzar da wani irin huci mai zafi daga bakinsa, ya rasa wace irin masifa ce wannan gabad'aya ya rasa gane kansa da abinda ke damunsa burinsa bukatarsa ta biya da yarinyar ita kuma taki ta bashi had'in kai yarinyar gabadaya ba tsaransa bace har ya ajiye girma da muqamin sa yana biyayyarta tana wula'kantashi yana ganin dole ya nuna mata kuskuranta akan irin abinda take masa, da kyar yay wanka ya daura alwala ya fito fuskar nan babu fara'a ya kintsa jikinsa, k'asa ya sauka, lokacin na kammala komai na shirya gurin cin abincin ina zaune abin duniya ya isheni......tunda naga yanayin fuskarsa nasha jinin jikina, koda ya karaso inda nake sake risinar da kaina nayi da fadin"Barka da fitowa." Wuce ni yayi ya nufi hanyar fita ba tare da yace komai ba. bayansa nabi da kallo ina ayyana abubuwa da yawa a kansa.
Bayan fitarsa da minti goma nima na bar gurun.


Sai bayan daya gabatar da sallar isha'i ya shigo kai tsaye gurin cin abinci ya nufa ya zauna daya daga cikin kujerun gurin, wayarsa ya d'auko ya shiga ma'adanar hotuna tarin pictures ne na matan turawa da bakake fata wanda ba zasu irgu ba, yawanci kuma duk tsirara suke pictures din yake kallo wai ko zai samu sasaaucin abinda ke damunsa. Cikin wannan halin na fito na sameshi, kai tsaye inda yake na nufa.
Dan risinawa nayi murya k'asa nace''Ranka Ina iya zuba maka abincin." A watse ya kalleni yace."haka kawai zan zauna anan gurin babu dalili."? Da sauri nace"Afuwa ranka ya dade." Mikewa nayi cikin nutsuwa na bud'e fulas din dana sa tuwon a ciki na dauk'o leda biyu nasa akan plate na mayar da fulas din na rufe miyar na bud'e itama nasa ma a plate na bude daya fulas din dake dauke da jar miya waccan nasa mata naman rago itama nasa masa a plate kana na mayar na rufe ruwa da lemo na ajiye masa gabansa naja gefe na tsaya kaina a kasa nace"Ranka ya dad'e na had'a komai."
Dago kansa yayi yana bin abincin da wani irin kallo yana ya mutse fuska yace."Ke! wannan wane irin tuwo ne ba'ki sai kace ke."!! Naji ciwo cimin fuska da yayi, cikin dauriya nace"Ranka ya dade tuwon dawa ne.'' Tsaki yaja mai karfi ya mike a fusace ya d'aga k'yallen da abincin ke kai ya watso min a jikina.! cikin rashin mutunci yace."Waye zaici wannan ba'kin abun ko an fad'a miki kowa ma jaki ne kamar ki! dallah malama matsa ki bawa mutane guri."! Cikin hayaniya yake maganar har yana dukan daning d'in da hannunsa....
*BINTA UMAR ABBALE*


*Kuyi sharing please👏🏻*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_




*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
31&32
Cikin wani irin yanayi na 'kunar zucci nake kallonsa kafin na kalli jikina gabad'aya gaban rigata ya 'baci da miya har wajejen wuyana da gefan fuskarta ya samu rabonsa, idona naji yana kawo ruwa wannan irin wulakanci ne dacin mutumci mutumin nan yake min, danne damuwa ta nayi na kalleshi yana zaune sai huci! yake kamar wanda akayiwa gagarimun laifi nace"Ranka ya dad'e kai ne ka bukaci da ayi maka tuwo ni kuma sai nayi tunanin tuqa maka na dawa saboda nasan abun marmari ne zai fi maka dadi akan sauran dan me zaka wulakanta ni ka wulakanta abinci babu kyau abinda ka'aikata domin akwai mutane da yawa da suke neman abinda zasu kai bakinsu kai ka samu kana watsar wa."
Cike da jarumta nake maganar.

Wani irin kallo naga yanayi min na k'askanci kafin ya tattaro yawun bakinsa ya tofa min a fuska cikin izigalanci yace."Ki 'bace min daga gurin nan na daine ganin wannan ba'kar fuskarta ki a idona."

Takaici kamar ya kasheni nasa hannu na goge yawun daya tofa min, baki na bude zanyi magana ya daga min hannu alamun baya bukatar yaji abinda zance, banyi shuru ba domin na riga na dauki aniya akansa, Nace''Kana yawan kushe hallitar Allah shin wai me bak'in mutum yayi wa mutane ne da suke 'kyamatarsa kada ka manta yadin da akayiwa d'akin Allah ado ba'ki ne,, da farin mutum da b'akin mutum duka Allah ne ya hallicesu kuma bai fifita wani akan wani ba duk daya suke a gurinsa wanda yafi kyautata masa shine mafi kusanci dashi, amma kun d'auki karan tsana kun d'orawa 'bakar hallita wannan yana nuni da cewar kuna nunawa Ubangiji cewar bai hallita ba."

Mi'kewa tsaye yayi ya nuna min kofar fita da hannunsa. Girgiza kaina nayi na bar gurin zuciyata na wani irin tafarfasa gabad'aya halayyar sa bata da kyau girman kai gami da izzah muna nan ayyuka ne wanda Allah baya so yana da ilimin addini daidai gwargwado yasan abubuwan da yake aikatawa basu da kyau amma saboda shed'an ya riga ya gama yi masa fitsari akansa kullum daukar kansa yake wata tsiya alhalin kuma a gurin Allah ba komai bane.

Koda na shiga gurin mu kai tsaye ruwa na zuba a bokiti na shiga band'aki domin wanke jikina nasan idan na shiga daki iyayena suka ga jikina a 'bace zasu tambayi dalili shiyasa nayi wannan dubarar, bayan nayi wanka zanin kamfalar na d'auro a kirjina na yafa dankwalin na fito, ina tsaka da d'aura alwala Tambaya ta fito daga daki, tace"haba ni tun dazu nake jin motsi ina daki nace bari dai na duba na gani ashe kece."tana kallon fuskata tafadi maganar, kokarin kawar da abinda ke damuna nayi nace"Ai ina shigowa bandaki na nufa nayi wanka ko jikina ya warware." Tace"Ai kam wannan uban wanki da kikayi ai dole jikin ki yayi miki tsami amma me yasa baki d'umama ruwan zafi ba? ina ganin da da ruwan zafi kikayi wankan sai kinfi jin dadi."

Nace"Nima sai da na fara wankan sannan nayi tunanin hakan." Tambaya kicin ta wuce domin ajiye kwanonin abinci dake hannunta ni kuma bayan na daura alwala dakin na shiga na samu babana zaune a kan dadduma yana lazimi sannu nayi masa na shige cikin kuryar dakin domin na kimtsa jikina.

Irin dai kayan nasa a jikina na fito da hijabin da nake sallah a wuyana, dadduma na hau na tayar da sallah..........Tambaya ta shigo dakin hannunta rike da silba mai murfi a kusa dani ta ajiye silbar tace"Idan kin idar ga abincin ki nan." kuryar dakin ta shiga domin gabatar da tata sallar, bayan na idar da sallar na jima hannuna a sama ina rokon Allah yasa naci jarabawar daya d'ora min na kuma tsananta addua ta akan ya kareni daga sharrin masu sharri. shafawa nayi a fuskarta na juya ina kokarin cire hijab din wuya na, sai naga babana na shafa fuskarsa da dukkanin hannuwansa hakan ya nuna min cewar adduata yake shafawa a fuskarsa.

Ina murmushi nace"Baba barkan ka da dare." Shima da murmushin a fuskarsa yace."Barka dai yarinyar arziki." silbar abincina na janyo a nutse nace"Naso na dawo da wuri muci abinci a tare domin samun tabarraki." da yalwatacciyar fara'a a fuskarsa yace."Na riga naci abinci Sumayya amma kawo na sa miki albarka."

Da sauri na miqa masa silbar abincin ina murmushi, bisimillah yay yasa hannunsa ya d'ibi dafadukan shinkafar dake cikin silbar a bakinsa yasa yana taunawa yace."To gashinan nasa albarka."

Silbar na janye na gyara zamana ina murmushi nace"Godiya nake baba Allah ya kara maka lafiya." ya amsa da amin yana kallona da murmushi a fuskarsa.

D'akin ne yay shuru na minti biyu kafin na kalleshi a nutse nace"Yanzu idan na kammala cin abincin zamuje can sashen Yariman ko."? Yace"Af kinga na manta wallahi gwara da kika tuna min maza gama cin abincin muje."
"To nace" na mayar da hankalina gurin cin abincin...Tsaf na kammala na fita da kwanon ina shiga dakin na tarar dashi a tsaye kuryar dakin na leqa Tambaya na kan dadduma da carbi a hannunta nace"Zamuje sashen Yarima da Baba." Hannu ta daga min alamun sai mun dawo." Koda na juyo sai na tarar har ya rigani fita murmushi nayi nabi bayansa da sauri.


Lokacin da muka isa sashen shuru dan su Haruna ma a harabar gurin muka samesu nan yake sheda min ai Yalla'bai din ne yace su fita su bashi guri zuwa anjima sa dawo." hakan ya nuna mun cewa har yanzu yana cikin 'bacin ran abinda ya faru tsakani na dashi.....Babana na kalla a tsanake nace"Baba zauna bari na hau sama na sheda masa zuwanka.

Ya samu kujera ya zauna a nutse ni kuma na nufin saman domin sheda masa zuwansa.....Na jima ina nocking kafin naji yace."Waye."? A sanyaye nace."Nice." shuru na minti biyar naji alamun bud'e k'ofar matsawa gefe nayi kaina a kasa......Wani irin kallon banza ya

Please Login or Register in order to submit comment