Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kawo miki wai ke kadai zaki ci kada ki bani." akushin dake gabansa na kalla! ya mi'ko min, nasa hannu na kar'ba a nutse na bud'a kaza ce guda anyi mata dahuwar magani sai kamshi take! da sauri na rufe ina kallonsa, hankalinsa nakan abincin gabansa, da sauri na kar'ba ina kokarin zuba masa yace."Mamma ta huttashe dani da kazar amarci."

Kallonsa nayi da mamaki a tare dani! yace."Ai na bud'a na gani ta dafo miki kaza tayi lugub! wai harda cewa ko roma kada na d'and'ana." yanda ya fad'i maganar a sakarce ya bani dariya nace"Ban hanaka ci ba idan kana bukata sai na baka."

"Kawai ki bud'e ina bukata." nace"To shikkenan ka gama cin abincin." Shuru yayi yasa spoon din dake hannunsa a nutse ya fara cin abincin...........Kad'an ya rage nace"Ka daure ka karasa ladan ka." girgiza min kai yayi yace."Na koshi haka ko kina so na kasa moruwa."? girgiza kaina nayi na mika masa tissue ya goge bakinsa, nace"To ya na zuba maka roman kazar ne."? ya mutse fuska yayi yace."Kici kayanki bana jin zan iya cin wani abu yanzu." Nace"To shikkenan nima ba yanzu zanci ba sai da safe zansa a d'umamin."

"Okey." yace ya dan kishingida yana kallon guri guda, a zuciyata nace"Abin yazo kenan! mikewa nayi na harhad'a kwanakun abincin na dauka na fita dashi, firji na kicin na bude nasa kwanon kazar na rufe da safe nake so naci a tsanake.........Dakin na koma na sameshi a inda yake har yanzu kuma guri guda yake kallo, sai dana zauna sannan ya dago kai yana kallona....




*Na kudi ne*
Koda zaki ganshi a gruop na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
96
Fulani na kashe wayarta ta kira Jakadiya tace maza taje fada ta shedawa Maimartaba cewa tana son magana dashi. Jakadiya da sauri ta tafi domin cika umarnin uwar gijiyarta, Maimartaba tunda yaji wannan kiran na gaggawa yasan ba lafiya ba.

Koda Maimartaba yazo ta sheda masa abinda yake faruwa ransa ya baci yace"Yanzu ashe har yanzu ba daina wannan al'adar ba."? Tace."Wallahi basu daina ba sunayi shiyasa na kira ka na sheda maka abinda ke faruwa saboda bana so su watsa mummunar magana akan wannan yarinyar babana ya tabbatar min da cewa babu wata mu'amular aure data shiga tsakaninsa da ita saboda tana cikin hali na rashin tsarki! yanda yayi min bayani haka yayi wa uwargida bayani amma ta nuna bata yarda ba tana ganin kamar yana kokarin kare matarsa ne shi kuma ya tabbatar min da gaskiyar magana."

Maimartaba yace."Na rasa ranar da Huwaila za tayi hankali yanzu ace da girmanta da komai taje kar'bar zanin gado ai wannan zubar da kima da mutunci ne da kin fada min tun na kan Lawisa dana dauki mataki amma yanzu ma bata 'baci ba da kaina zan shiga sashenta na gargad'eta akan abinda suke shirin aikatawa."


Maimartaba na shiga sashen Uwargida ya samesu su biyu ita da Hajiya Karima sai 'kus-'kus suke, ganinsa yasa duk suka nuna alamun rashin gaskiya, a nutse ya zauna yana kallonsu sai rige rigen gaisheshi suke.

Ya dinga amsawa yana nazarinsu duk alamun rashin gaskiya ya bayyana a tare dasu.


Ya kalli Uwargida rai a 'bace! yace."Yanzu abubuwan da kukeyi a masarauta shine daidai."?

Sunkuyar da kanta tayi a sanyaye tace"Allah ya taimakeka me yake faruwa ne."?

Yace."Ashe tambayata kike abinda ke faruwa bayan kin san komai."

Tace."Ranka ya dad'e a gafarce ni nasan akan abinda kake magana kasan wannan abu al'adar masarauta ce babu laifi dan duniya ta tabbatar da nagartar matan da Magajin sarki ya aura Ita dai Lawisa kowa ya tabbatar cewa cikakkiyar macace ita wannan d'iyar bayin ce bamu tabbatar ba tunda babu yanda banyi dasu ba akan su nuna min abin kwanciyarsu suka qi kaga wannan na nuna mana cewa akwai lauje cikin nadi watakila yarinyar nan ba cikakkiyar mace bace."


Cikin takaici yace."Huwaila wannan abun da kuke jahilci ne tsantsa, a shakarun baya da masarauta ta mayar da abun al'ada akwai jahlici da duhun kai a tare da ita, yanzu kai ya waye muna da ilimin addini daidai gwargwado to me zai sanya mu dinga fallasa sirrin aure! to daga rana irin ta yau na soke wannan al'ada kuma kada naji kada na gani wata a cikin ku ta tayar da wata magana akan matar Ali ba lallai sai jini ya fita a jikin mace za'a san budurwa ce ni wannan yarinya Sumayya bana shakka akanta saboda haka magana ta mutu anan ba na ganku kuna magana kasa-kasa ba to mutukar naji maganar nan ta watsu dukkanin ku sai na dauki mataki akan ku.""

Hakuri suka shiga bashi suna sunkuyar da kansu, mikewa yayi ya barsu gurin ba tare da ya tanka musu ba.


Yana fita Uwargida taja tsaki tana girgiza kafarta tabbas Fulani ce ta turoshi yazo yaci mata mutunci.....Hajiya Karima tace"To wai da yazo yana wannan fad'an waye ya fada masa halin da ake ciki ne."? cikin takaici tace"Waye zai fada masa idan ba Fulani ba itace ta turoshi yazo yayi mana tujara." Hajiya Karima taja tsaki da fadin"Kin san Allah Huwaila na tsani na bude ido na ganta da ina da yanda zanyi a kanta to da tuni nayi shegiyar mata ce da asiri baya cin jikinta.

Uwargida ajiyar zuciya ta sauke tace"Babu abinda banyi ba amma na kasa tasiri a kanta Fulani ta riga tayi nisa tasha gabana tunda itace mai d'a namiji ai sai abinda na gani duk abinda Maimartaba yake da umarninta baya san 'bacin ranta ita da d'anta yanda yake nuna mana rashin kulawa nida 'ya'yana yana damuna mutuka wallahi na rasa yanda zanyi na tarwatsa rayuwar su ita da d'anta.

Hajiya Karima cikin 'bacin rai tace"Huwaila sai dai kiyi hakuri kina gani dai Muddibo garin yunkurin 'kwatar hakkinsa aka kasheshi muna ji muna gani muka hakura muka rasa shi! kema hakuri zakiyi ki zubawa sarautar Allah ido idan kuma kina da wata hanya sai kibi ki 'kwaci hakkin ki."

Cikin damuwa tace"Bani da wata hanya da zanbi dik hanyoyin da nake bi sun toshe amma dole zamu zauna da 'ya yana mu yanke shawara a tsakaninmu."

Hajiya Karima tace"Hakan yayi ni zan tafi gurina sai mun sake haduwa." Uwargida ta mike domun yi mata rakiya, suna tafiya suna tattauna yanda za'ayi su cutar Fulani da d'anta

Hajiya Karima na isa sashenta kiran Lawisa tayi a waya tace"Lawisa kiyi rawa kiyi juyi kishiyarki fanko ce dan ba'a samu shedar budurci a tare da ita ba saboda haka ke din kin zama abin alfahari a kan kishiyarki.

Lawisa farin ciki ya rufe ta ta dinga dariyar murna tana fad'in"Gaskiya Hajiya naji dadin wannan labarin na kuma yi alfahari dan haka yau na tabbatar da cewa nice matar da Yarima zaiyi tunkaho da ita."


Hajiya Karima na dariya nishadi tace"Ai shiyasa na kasa hakuri nace lallai sai na kira ki a waya na sheda miki saboda haka ki nutsu ki kwantar da hankalin ki kicigaba da zaman aurenki lafiya amma kada ki manta da dubarun dana koya miki kinji ko." Tace"Nagode sosai hajiya insha Allahu ba zan manta ba." sallama sukayi kicin nishadi da walwala taje tai wanka ta d'and'ansa ado ta hakimce akan kujera tana jiran shigowarsa.


Koda ya shigo kasa dauke idonsa yayi daga kanta, ya zauna kusa da ita suna gaisawa! tana fari da ido tace"Ranka ya dad'e ina ta yaka jajen abinda ya faru.

Hankalinsa ya mayar kanta yace."Wane abune ya faru kike min jaje''?

Kai tsaye tace"Shedu sun sheda cewa matarka ba budurwa bace."!! wani banzan kallo yayi mata yace."Ke waye ya fada miki hakan "? cikin rashin wayo tace" Yanzu hajiyata ta kira ni a waya take sheda min."


Kai tsaye yace." 'Karya take." cikin mamaki tace." Hajiyan ce ke 'karya."? kansa ya daga rai a 'bace yace." na fada 'karya tayi miki ni nasan wacece Sumayya na hana zanin gado ne saboda bana son tonan asiri shine suke zargin rufa mata asiri nayi wanda kuma ba haka bane sumayya cikakkiyar budurwa ce kamar ke."


Murya na rawa tace"Gaskiya banji dadin maganganun ka ba aiko hajiya bata haifeka ba yana da kyau ka girmamata bai kamata ka kirata da makaryaciya ba."

Mi'kewa yayi ya hau sama ba tare da yace mata komai ba.

Hawaye suka wanke mata fuskarta, tunanin take akan dalilin da yasa bai bada zanin gadon Sumayya ba, wato itace baya so shiyasa ya fallasa sirrinta! koda yake ai itace tace lallai sai an fita dashi an nunawa duniya, hannu tasa ta goge hawayen fuskarta ta bishi saman.


A kwance ta sameshi bacci na kokarin daukarsa, zama tayi kusa dashi a sanyaye tace"Ina so muyi magana." Hannu ya daga mata ransa a bace yace." Kin ta'ba min rai saboda haka ba zan saurareki ba sai na huce."!


Cike da mamaki! tace"Saboda kawai nace Sumayya bata da budurci shin........Mari ya kwad'a mata yana tsuma yace"kada na sake ji kin fadi wannan kalmar akan Sumayya Wallahi duk sanda na sake ji sai ranki ya 'baci! ki tashi ki fitar min daga daki."!!!!!! Lawisa ido ta zura masa tana mamakin marin da ya kwada mata

Zabura! yayi a kanta, da sauri ta sauka daga gadon ta fita daga dakin tana kuka.

Bacci ne ya daukeshi mai cike da mafarkai marasa dadi da ma'ana.


Ni kam tunda naje na samu iyayena cikin koshin lafiya na watsar da damuwar dake damuna muka yini cikin walwala da farin ciki, sai biyar na yamma na koma gurina, na samu ko'ina tsaf kamshin turaran wuta sai tashi yake a ko'ina, wanka nayi na kimtsa jikina ina fitowa falo na samesu a jere gaisheni sukayi na amsa cikin sakin fuska nace"Kuna iya tafiya tunda kun gama aikin ku." sallama sukayi min suka fita, kafin na zauna sai da na duba agogo naga bakwai shaura, zama nayi kan kujera na dinga tsammanin shigowarsa a lokacin, bai shigo ba sai wajejen tara da rabi, koda ya shigo kasa gane kansa nayi dan magana ma sama - sama yayi min ya shige daki, minti biyar nabi bayansa na sameshi a kwance, a sanyaye nace"Baka da lafiya ne."? kallona yayi da fadin"Me kika gani."? nace"Naga jikinka babu kwari ne." tsaki yaja yace."Wannan abun naki ne ya 'bata min rai bayan haka kuma Lawisa ta kara min wani."

A sanyaye nace"Sai hakuri." kallona yay yace."Kwana nawa yake kafin ya dauke."? ban 'boye masa ba nace"Hudu ko biyar." ajiyar zuciya ya sauke yace."Yanzu dai yau kwana nawa."? nace"Kwana daya." 'bata rai yayi yana kallona, dariya nayi nima na tsira masa idona, yace"Dariya kike min saboda mugunta ko."? girgiza kaina nayi alamun A'a.

Mikewa yayi tare da rike hannuna "Muje toilet kiyi min wanka." ban masa gardama ba na rike hannunsa muka nufi toilet din,

Abin mamaki zir yayi bai bar komai a jikinsa ba, na rintse idona da fadin"Dan Allah kasa wandonka." jawo ni yayi muka fada cikin kwamin wankan ya hau tu'be min tufafin jikina! na dinga hanashi ina kokarin fitowa yana mayar dani! gajiya nai na kyaleshi ya tu'bemin kayan jikina tas, murya na rawa nace"Dan Allah ka bari na fita a ruwan nan kaga da najasa a jikina kada na 'bata maka."

Girgiza kansa yayi yana cigaba da shashshafa jikina! "Ba zan iya bari ki fita ba kawai ki dauki soso da sabulu ki cud'ani! hannunsa na cire daga breast dina nace" Ka bari to nayi maka wankan."

Kwanciya yayi cikin kwamin wanka na dauko soso da sabulu na fara cud'ashi! kasa hakura yayi ya janyota tsam ya matse a jikinsa tare da sa bakinta a nasa.......haka muka lalace a toilet tsayin lokaci mai tsayi, kafin muyi wanka mu fito................A daran ranar na bashi kulawa sosai sai da na tabbatar da cewa ya samu biyan bukata sannan hankalina ya kwanta muka kwana cikin farin ciki da kaunar juna.......




*Na kudi ne*
Kada ki karanta mun littafi idan baki biya ba! keda kika futa da littafin keda Allah idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal gruop#300 account... 0542382124.....Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
97
Kiran wayar Lawisa ne ya tayar damu daga bacci! wayar ta karaci ringing d'inta ta mutu bai daga ba, zaune na mike ina kokarin kare jikina da bargo wani kiran ya sake shigowa, a maimakon ya daga wayar sai naga ya mike daga shi sai karamin wando ya nufi toilet, wayar na dauka ina dubawa da mamakin wanda yake buga wannan kiran da sassafe! My Lawisa, sunan dana gani kenan yana yawo kan fuskar wayar, da sauri na ajiye inda take ina mamakin al'amarin, koda wayar ta katse bata sake kira ba, na tsirawa kofar toilet din ido ina fargabar shiga saboda nasan halin fitinarsa........'daure da towel ya fito da wani a hannunsa yana goge jikinsa, kai tsaye wardrobe ya nufa domin kintsa jikinsa, ina kokarin mikewa kira ya sake shigowa wayarsa, sai naga ko kallon wayar beyi ba yana ta kokarin fito da kayan sa, a sanyaye nace"Ranka ya dade ana kiran wayarka tun dazu."

Juyowa yayi ya kalleni babu walwala a tare dashi yace."Ina da kunne ai."! kallonsa nai ina mamakin yanda ya amsa min magana kamar wanda nayi wa laifi! jiya lafiya lau muka kwanta muna soyayya amma ya tashi da d'acin rai! girgiza kaina nayi na wuce toilet ina mamakin baud'ewar halinsa.


Tsaf na fito na sameshi ya shirya dakin sai kamshin turarukansa yake yana zaune a gefan gado yana daura igiyar takalminsa, na 'karasa gurin a sanyaye nace"Fita za kayi ne."? Shuru yayi min ya cigaba da abinda yake.........Zama nayi kusa dashi duk jikina ya mutu da abinda yake nace"Dan Allah ka fada min idan laifi nayi maka naga lafiya lau muka kwanta bacci amma ka wayi gari cikin 'kunci da 'bacin rai! gashi laifina yana nema ya shafi Wata.

Babu fara'a a fuskarsa yace." Sumayya baki min komai ba raina yana 'baci akan wannan jinin da kike dan wulakanci bai tashi zuwa ba sai a lokacina gashi daga yau ranar ki ta amarci ta 'kare."

A sanyaye nace"Ranar amarcina bata 'kare ba tunda baka kar'bi budurcina ba har yanzu ina da sauran ranaku masu muhimmanci ka kwantar da hankalinka insha Allahu zaka samu abinda kake so a tare dani."


Girgiza kansa yayi yace."Sumayya zanso kema jama'a su sheda cewa ke cikakkiya ce sai dai kash! lokaci ya shige miki yanzu koda na kar'bi budurcinki kin fitar da jini jama'a da yawa ba zasu yarda ba zasu ce 'karye ne idan na tuna hakan raina yana 'baci sosai wannan jinin naki yayi mana illah."

'Kwalla ce ta cika idona nace"Nima zanso masu kokwanto a kaina su tabbatar da cikar mutuncina to amma ina so ka sani hakan ba addini bane al'ada ce idan kai ka tabbatar ka amince da cewa ni d'in budurwa ce shikkenan dama haka ake bukata ka kwantar da hankalinka.

Girgiza kansa yayi yace."Ki kyale Lawisa ina so na koya mata hankali ne mahaifiyarta ce ke sheda mata cewa ke din fanko ce shine saboda bata da mutumci ta tunkareni da maganar."


Raina ne ya 'baci dajin maganarsa kawai dai na daure bance komai ba ina jinsa sai surutai yake akan Lawisan "Sumayya koda ke d'in fanko ce wallahi kin fiye min mata dubu ciki kuwa harda ita Lawisan wannan dalilin yasa na'ki daukar wayarta.

Murmushi nayi cikin zuciyata nace" Namiji kenan a gabana sai nuna min so yake, duk yanda yake aibata Lawisa a gabana gobe ina iya ganinsa yana rawar jiki akanta na riga nasan halinsa sam bashi da al'kibula amma dai na soma zargin yana sona tuna gashi yana jin haushinta akan ta kira ni fanko.

Mi'kewa yayi yana kallon agogo, a marairace nace"Yanzu ina ka nufa."?

"Zan shiga mu gaisa da Mamma na wuce asibiti." Nace"Dan Allah ka shiga ku gaisa da matarka ka duba lafiyarta meye dan ta kira ni fanko kake jin haushinta."

Tsaki! yaja yay gaba ya barni da baki a bud'e! bayansa nayi yunkurin bi sai na tuna da cewar babu suttura a jikina kuma watakila su Mariya na falon, saboda haka sai na juya da jiki a mace na nufi wardrobe domin kimtsa jikina.


Magajin sarki yana fita kai tsaye sashen mahaifiyarsa ya nufa nan ya samu Maimartaba suka gaisa Maimartaba cikin kulawa yace." Naga kayi shirin fita aiki baka dauki hutu bane."? Yace."Ranka ya dad'e hutun bashi da wani amfani gwara na cigaba aikina." Maimartaba yace."To babu laifin hakan Allah yayi maka jagora a cikin dukkanin al'amuranka.'' Ya amsa cikin nutsuwa, Fulani tace"Da alama dai bakayi break fast ba ko.'' yace."Mamma kamar kin sani kuwa ina bukatar tea a gurinki."

Tace."Ai nasan ka da 'kiwar cin abinci shiyasa nayi magana bari na kawo maka." Yace."To godiya nake Mammana." Maimartaba mikewa yayi da niyyar shiga fadarsa yace."Aliyu zaman fada a gurinka dai ya gagara aiki ya hanaka kazo ka koyi yanda ake mulki."

Murmushi yayi yace."Ranka ya dade mulki ai sai ku jajurtattu wallahi ni kwata-kwata bana sha'awar mulki ranka ya dad'e."

Maimartaba ya shiga jijjiga kansa yana murmushi yace."Ali kenan! kada ka bani kunya mana! nasan kasan da cewar duk inda mai suna Ali yake jajurtacce ne a fagen ya'ki da iya mulki mai yasa kai ka karaya kake ganin kamar mulki bai dace da kai ba.

Girgiza kansa yayi shima da murmushi a fuskarsa yace."Ranka ya dad'e ba wai na karaya bane! ina ganin yanda kake d'auki ba dad'i akan 'yan uwanka dukkaninsu sunsa ido suna ganin kamar mun kar'be mulki daga hannun kowa muna yanda muke so shiyasa nake ganin nan gaba ya kamata a sakar musu su kar'ba suyi ko sa kwantar da hankalinsu.

Maimartaba yayi murmushi yana kallonsa yace."Aliyu kenan! ai muma bamu ne muka tilasta lallai sai munyi mulki ba cancanta da nagarta gwamnati ta duba jama'ar gari sukayi mubaya har Allah ya tabbatar mana da mulki a hannun mu! bama hassada da 'bakin ciki idan Allah ya kar'ba daga hannun mu ya bawa wani dama shi mulki ga wani abin hallita baya dawwama Allah shine yake da mulki madawwami."

"Kwarai haka yake Allah shi kadai keda mulki babu wani Sarki ko governor ko shugaban kasar da zai dawwama akan kujerar mulki aro aka bashi komai tsayin shekaru sai ya sauka daga kujerarsa bayan nan kuma ya fuskanci kalubalan dake gabansa domin kuwa dole a ranar lahira Ubangiji ya tuhume shi, ranka ya dad'e ina rokon ubangiji Allah yasa sasaauta maka a ranar al'kiyama."

Cike da jin dadin adduar da yayi masa ya d'ora hannunsa a saman kansa yace."Allahumma ameeen Aliyu yaron arziki kwarai nagode da wannan adduar taka." Magajin sarki murmushi yayi yana me sunkuyar da kansa......cikin wannan halin ta fito daga kicin hannuna rike da tire na kayan tea. da sauri ya mike ya kar'bi tire din yana yi mata sannu! zama tayi gurin zamanta hankalinta akan mijinta Maimartaba yace." Kinyi tsammanin na fita ko."? tace."Hakane ranka ya dad'e." Yace."Na tsaya muna tattaunawa da Ali yau munyi hira mai tsayi irin wacce muka jima ba muyi irinta ba."


Murmushi tayi tace."Kai amma naji dadi sosai ina fatan kayi masa maganar zaman fada." Yace."Nayi masa magana yace shi baya sha'awar mulki." Fulani murmushi tayi tace"Idan kuma Allah ya bashi ya zaiyi." ? Maimartaba na 'yar dariya yace."Nima abinda na gama fahimtar dashi kenan." Kallonsa tayi yana d'an motsa tea tace"Babana idan Allah ya baka mulki ka kar'ba hannu biyu ka gode masa mu kuma zamu yi maka kyakkyawar addua." Yace."To shikkenan Mamma ina godiya da wannan karamcin." Maimartaba ya sauke ajiyar zuciya tare da fad'in "To ni zan shiga fada.'' Fulani mi'kewa tayi domin yi masa rakiya bakin kofa, Magajin sarki fatan alkairi yayi masa, ya cigaba da kur'bar tea din yana nazarin maganganunsu da mahaifinsa ya fahimci Mahaifinsa na so ya gaje shi a mulki shi kuma ko kadan al'amarin baya bashi sha'awa, amma dai zai cigaba da addua akan Allah ya za'bawa rayuwarsa abinda yafi alkairi.



To Sai kusa takwas da rabi na dare ya shigo gidan a jigace tarin yunwa da gajiya sun had'u sun dabaibayeshi, kai tsaye gurin Lawisa ya nufa saboda yasan ita dashi, Hadiman dake karakaina a gurin suka dinga zubewa suna gaishe shi, da kyar yake amsawa da ya gaji shuru yayi musu ya wuce su.



Cikin ado kamar koda yaushe ya sameta, tana ganin shigowarsa ta mike tsaye da sauri tana masa barka da zuwa, ko kallonta beyi ba ya haye sama! ajiyar zuciya ta sauke tana data sanin abinda ta aikata, a sanyaye tabi shi saman, ta sameshi yana kokarin shiga wanka, sannu da zuwa ta sake masa ya amsa ciki-ciki toilet din ya shige ya barta a tsaye, a sanyaye ta dauko masa jallabiya da gajeran wando ta zauna tana jiran fitowarsa, yana fitowa taje ta tareshi towel din hannunsa ta kar'ba tana goge masa jiki, kyaleta yayi yaje ya zauna a bakin gado, da sauri ta dauko mai ta fara shafa masa, ajiyar zuciya ya shiga saukewa ko yaya mace zata ra'bi jikinsa sai sha'awarsa ta tashi, kallonta yayi yana tunanin ni'imarta, yunwa da da gajiya basa hanashi fitinarsa lumshe idonsa kawai yake yana lasar lips dinsa, Lawisa ta dinga shashshafa jikinsa da gayya ta dinga tsokano shi aikuwa wawura ya kai mata ta fad'a jikinsa suka shiga ya mutsa juna

Sai da suka biya bukatar junansu sannan suka saurara, yaje ya sake wanka ya fito itama ta shiga tayi, ta sameshi na kokarin fita daga dakin, sunansa ta kira ya tsaya yana kallonta fuskarsa da alamun sassauci! tace"Kayi hakuri da magana ta akan Sumayya dan na lura saboda haka kake fushi dani."

Kafad'a ya d'aga a dakile yace."Nayi hakuri amma ki dinga kiyaye harshenki akan kici fuskar wannan yarinyar zan iya rabuwa dake."


Da wani irin mamaki! take kallonsa yace."Da gaske nake miki naga kina kallona inda kina so ki gazgata magana to ki kuma zuwar min da wata maganar banza a kanta."


Yana gama maganarsa yasa kai ya fice daga dakin.

Lawisa kasan kafet ta zube tana hawaye! yaushe tayi saken da yarinyar nan tayi mata illah! haka! Zai iya rabuwa da ita akan Sumayya shin wane irin so yake mata haka."? kuka ta dinga shar'ba tana girgiza kanta da mamakin al'amarin.


Ina shirin kwanciya bacci ya kira ni, a nutse na daga wayar muka gaisa na tambayeshi aiki yace."Lafiya lau ina fata kin wuni lafiya."? nace"Lafiya lau na wuni sai dai nai ta tsammanin shigowarka baka shigo ba."

"Kina bukatar ganina ne."? yafada cikin wata irin murya, dariya nayi nace" Sosai kuwa ina bukatarka na saka a cikin idona."

Ta'be bakinsa yayi yace."Sai dai kiyi hakuri sai da safe dan yanzu haka a kwance nake." Jikina ne yayi sanyi raina ya 'baci da dizgin da yayi min! dana san zai watsa min 'kasa a ido da

Please Login or Register in order to submit comment