Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kalli inda ya k'urawa ido a jikina.....Cikakken kirjina dake cike dana shanu naga yana satar kallon inda rigata ta yage, nasa hannuna da sauri na sake rufe gurin ina jin wani mugun haushinsa ni ban san meye a jikina ba da maza suke lalacewa gurin kallona, ni dai nasan bani da wani cikakken kyau ga shegen baqi sai kace me? ban sani ba ko nonowa na da suka rinjayi kirjina ne ke d'aukar hankalinsu ko kuma mazaunai na wanda suka cika bayana tamkar suyi magana ni kaina na san a fiska ban cika kyau ba amma na amince da cewar a jiki na cika cikakkiyar macan da kowane namiji yake bukata.

Da sauri na dago kaina ina kallonsa jin kamar yana magana cikin 'bacin rai! Aikuwa fad'a sosai yakewa Gimbiya Lawisa gami da nuna mata muhimancin mutun komai lalacewar dan adam tunda Allah ya karramashi to kaima sai ka mutuntashi." Gimbiya Lawisa cikin takaici take kallonsa sam bata dauka zai goyi da bayan yarinyar ba, ranta a 'bace ta bar gurin yaranta suka bi bayanta da sauri.......A nutse yace."Kowa ya koma bakin akinsa." Minti uku gurin ya watse kowa ya nufi inda yake....Hannuwansa na goye a baya ya tsirawa kasa ido yana kallo, cikin zuciyata nace"Anya kuwa wannan guy yana da lafiya gaskiya da matsala a tare dashi duba da yanda yake nacin kallon 'kasa sai kace wani makaho.
Rigata na dafe na yunk'ura da kyar na mike tsaye. nayi nufin shiga kofar dawakai naji maganarsa.
"Koma ki tsuguna inaso nayi magana dake." Da sauri na tsuguna tare da sunkuyar da kaina kasa.......sai da yaja dogon lokaci sannan yace.''Me yasa bakya mutunta Lawisa ko mahaifinki nada rawani a masarauta shiyasa kike gani tamkar daidai kike da kowa."

Maganar tayi min ciwo sosai amma sai na daure wa zuciyata dan saboda nasan bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane....."Ranka ya dad'e wallahi ina mutunta ta ina gaisheta a duk sanda zamu hadu itace dai ta tsane ni ban san me yasa ba kuma ko yanzu kafin al'amarin nan ya faru sai da na gaisheta tukkuna, maganar rawani kuwa mahaifina ba kowa bane a cikin masarautar nan fyace bawa mai d'aukar d'awainiyar dawakan dake cikin masarauta, sunana Sumayya sunan mahafina Lawi."

Shuru yayi yana kallonta yana tuno ranar daya dawo ranar da take cewa ba zata tsaya a rana ba ." Babu annuri yace."Okey kece ranar dana dawo kika nuna gazawarki akan tsayuwa a cikin rana ko."?
sunkuyar da kaina nayi gabana na faduwa.....Ya 'bata fuska sosai yace."Ke da bakin ki kin fad'i cewar babanki bawa ne wanda nasan a cikin bauta aka haifi iyayensa, sannan aka haifeshi shi kuma ya haife ki to me zai sanya ke! kike nunawa masarauta gadara gami da rashin girmama dik wanda yake sama dake."

Shuru nayi mishi dan banga rashin kyautawar da nayi ba, iyakacin bakin kokarina ina girmama duk wanda ya dace na girmama a masarautar to ban san kuma wane girma zan bata ba.

Tsaki yaja yace."Tashi kije amma kada ki sake kwatanta abinda kikayi a wannan masarautar wanda keda muqami ko kuma ya gaji sarauta shine zai nuna iko akan komai amma banda ke da kike a matsayin baiwa 'kasa da sama to wane gadara da izzah zaki nunawa mutane? kinyi sau biyu kada kiyi na uku idan kika sake da kaina zan hukunta ki."

Cike da mamaki nake kallonsa nace"Ranka ya dad'e a gafarce ni watakila maganar da zan fad'a ba za tayi maka dadi ba, sai nake ganin ita izzar da kake magana akanta ai ba abu ne mai kyau ba izzah! da buwaya gami da iko duk na Allah da Annabi ne, wani Sarki ko mai wani mulki dashi da muqarabbansa duk aro Allah ya basu kuma idan suka kauce hanya akan mulkin da Allah ya basu dole a lahira Ubangiji ya hukuntasu saboda haka ni banga ma'anar wannan maganar da kayi ba dan izzah! na d'aya daga cikin munanan ayyuka."


Kawai naga ya tsira min ido yana kallona fuskarsa tamkar hadarin dake dab da zubar da ruwa! sunkuyar da kaina kasa nayi na dafe a kasan gurin da hannuna nace"A gafarce ni idan maganar da nayi ta 'bata maka rai."
Mikewa nayi na shige kofar dawakan wanda ko ban juya ba nasan bina yake da kallo.

Ya jima tsaye a gurin yana kallon kasa! mugun mamakin yarinyar yake da kalaman da tayi wato tana nuna masa ba zata bi umarninsa ba, tana nuna masa shi din jahili ne be san abinda yake ba tunda gashinan a cikin maganarta har tana kawo masa hadisai! tunda yake ba'a ta'ba katse masa hanzari ba idan yana magana sai yarinyar yana da kyau ya nuna mata muhimancinsa a cikin masarautar.

Koda na gama abinda nake a ciki na fito samunsa nayi a tsaye a inda yake sai kace wani dogari yana tsaye hannu a goye a baya sai kallon kasan gurin yake yi, na girgixa kaina tare da kokarin ratse shi na wuce.

Gyaran murya yay kafin yace."Tsaya nan gurin." Da sauri na tsaya nayi kasa da kaina, karasowa yay ya tsaya daf dani har ina jiyo wucin numfashinsa, gabana ya shiga faduwa fuskata na dago na kallesa, naga sai kallona yake da tamkakkiyar fuskarsa, tsoro ne ya shiga jikina nace"Dan Allah kayi hakuri ranka ya dade wallahi ban fada maka magana ba dan na bata maka rai nayi nufin tunasar da kai ne akan abinda ka manta.

Cikin fushi yace."Kina nufin ni jahili ne kome."? Na girgixa kaina da sauri nace"A'a ba haka nake nufi ba." numfashi ya fesar mai zafin gaske yace."Kada na sake fad'in wata magana ki kawo min hadisai gami da fad'ar Allah yace annabi yace na fiki sanin munin abinda kike magana akai ni inayi miki magana ne akan girmama na sama dake a matsayin ki na baiwar dake karkashin masarauta yasa nace miki lallai ki girmama wanda yake saman ki amma tunda taurin kai zakiyi akan umarnina duk ranar da Lawisa ta sake daukar hukunci akanki zan bari tunda haka kike so.

A sanyaye nace"Yanzu na fahimci maganarka insha Allah zan kiyaye zan kuma cigaba da girmama wanda ke sama dani.

Ba tare da yace komai ba ya janye daga kusa dani ya koma gefe guda ya cigaba da kallona. ajiyar zuciya na sauke gabana na fad'uwa na kallesa, naga sai kallona yake ikon Allah mutumin wai kallon k'urrular me yake min ni ba kwalliya nayi ba ba komai ba amma ya dame ni da kallo......yagaggen wuyan rigana na riqe da sauri na bar gurin tafiyata na hard'ewa nasan idanunsa ne ya janyo min hakan.

Har sai data 'bace daga gurin sannan ya dauke idanunsa daga hanyar da tabi, yarinyar bata da wani cikakken kyau a fuska amma kuma Allah yayi mata kyawun sura tamkar ita tayi kanta, dugowa mai garin jiki gami da cikakken kirji da fad'in qugu wuyanta a cike dam!dam da wani irin guru-guru ba'kar fatarta lafiyayya lukwi lukwi sai she'ki takeyi abin sha'awa, shi kam tunda yake ganin ba'ka'ken fata bai ta'ba cin karo da fatar data burgeshi ba irin nata.....mirmushi yay gami da shafa siririn sajensa, hakika yarinyar da a waje take to babu abinda zai hanashi romancing da ita dan yayi masifar sha'awarta matsalar kawai yarinyar bata kai matsayin da zai had'a jiki da ita ba, makaskanciyar baiwa ce wacce take ci da sha a k'ar'kashinsa, daba dan haka ba da duk yanda zaiyi sai ya yaudareta ya mori albarkatun jikinta......Fitowa yayi daga gurin cikin sanyin jiki gami da rashin kuzari yake tafiya, kai tsaye sashen mahaifiyarsa ya nufa yana tafiya jama'ar dake shige da fice a gurin na gaishe shi Haruna ne yake take masa baya har ya isa kofar sashen mahaifiyarsa Haruna ya bude masa kofar falon, yayi saurin matsawa gefe shi kuma a nutse ya shiga falon da sallama a bakinsa.....
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_



*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
19&20
"Haruna wa'innan fa."? ya fad'a yana nuna mu da bakinsa.Haruna ya sunkuyar da kansa kasa cikin taushin murya yace." Ranka ya dad'e Mama Fulani itace tace nazo dasu domin su gabatar maka da kansu a a matsayinsu na wa'inda zasu taimaka min da d'awainiyarka."

Kansa ya sunkuyar 'kasa yana nazari kafin ya dago yana yi min wani irin kallo babu walwala a tare dashi yace."Mutum biyu nace kuma banda mace a ciki nafi bukatar maza sabida haka ke kina iya tafiya.'' Yana kallona ya 'kare maganar.

Dad'i naji ya rufeni jin abinda yace yasa da sauri na k'askantar da kaina da fadin"Godiya nake ranka ya dade.'' na yun'kura na mike tsaye risinawa nayi da fadin"A tashi lafiya." Da sauri nayi nufin barin gurin naji yace."Dakata." Nayi saurin juyowa ina kallonsa addua nakeyi a zuciyata kada yace ya fasa.

Gani nayi ya sunkuyar da kansa raina ya 'baci! nida su Haruna kasa'ke mukayi muna jiran muji abinda zece.........B'angaransa kuwa tunani yay kan cewar zamanta a sashen nasa zai iya taimaka masa ta wani bangaran shine dalilin daya sa ya dakatar da ita daga tafiya.

Kallona yayi a ya mutse yace."Meye sunanki ma."? Babu walwala a tare dani nace"Sunana Sumayya Lawi." Ya shiga girgiza kansa minti biyu ya kalli Haruna da fad'in " ka shiga dasu ciki ka nuna musu abinda ya dace akwai d'akuna a falo kuyi amfani da d'aya kai da 'yan uwanka ita kuma sai ta dauki daya inaso ku dawo sashena da zama har abadah kune hadimai na koda nayi aure."

Gabana ya dinga bugawa ina kallonsa kwalla na taruwa a idona nace"Ranka ya dad'e inada magana." Ya kalleni yana ya mutsa fuska. Saurin sunkuyar da kaina kasa nayi bakina na rawa nace"Ranka ya dade naji kana maganar mu dawo sashenka har abada ni ina da mara lafiya mahaifina bashi da lafiya kuma ni nake jinyarsa."

Kaina a kasa nake maganar ina kokarin mayar da hawayen dake kokarin zubowa.....shuru gurin yayi na kusan minti biyar kafin ya dago kansa ya kalli su Haruna da fad'in"Ku tashi kuje." Da sauri suka mike suna mika godiyarsu a gurinsa

Bayan barin su Haruna daga gurin na kai minti goma a tsaye be kula ni ba, sai duba wayarsa yake yi fuskarsa a murtuke. gabadaya naji gwiwowina sun sage na kalleshi inaso nayi magana ido muka hada dashi gwarjinsa ya hana ni cewa komai.

"Kina nufin kina tsaye 'kerere a kaina zanyi magana dake."? Ciki ciki ya fadi maganar, zubewa nayi gwiwa a kasa nace" Ranka ya dade a gafarce ni wallahi hankalina ne gabad'aya yana kan mahaifina."

Ajiyar zuciya yayi ya mike zaune had'e dayin wani irin zama na saurata hannunsa ya d'ora kan gwiwarsa, na kalli hannun yatsunsa guda uku na sanye da zubonan azirfa masu kyau sake sunkuyar da kaina nayi ina jiran jin ta bakinsa. kallona yayi a ya mutse yace."Mai yake damun mahaifin naki."? Da sauri nace" Daya daga cikin masu duba lafiya ya tabbatar mana da cewar hawan jini ke damunsa tsayin wata daya yana fama amma dai yanzu da sauki tunda an d'orashi akan magani.

Shuru gurin yay bayan na gama maganata, ya dinga kallon 'kasan kafet din da yake zaune kamar ba zaice komai ba daga bisani ya d'ago kansa tare da fad'in "Inaso kiyi min jagora 'bangaran naku domin na duba mahaifin naki."

Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa, girarsa dake cike da gashi ya d'aga min domin so ya tabbarar min da maganarsa.

Nace"Babu damuwa ranka ya dad'e idan ka shirya zuwa yanzu sai nayi maka jagora." Ina d'urkushe a gabansa ya mi'ke a nutse yasa takalminsa yace."Tashi muje." Da sauri na mike ina karkad'e jikina.

Tsayawa nayi ina jira yayi gaba nabi bayansa ya nuna min hanya da hannunsa ba tare da yace komai ba na fahimci abinda yake nufi da sauri nayi gaba ya rufa min baya.


Yanayin tafiya ta da tashi ba daya bane koda na waiwaya sai naga nayi masa nisa sosai d'an tsayawa nayi ina jiran zuwanshi.....Bangaran shi kuwa tafiya kawai yake amma hankalinsa tuntuni ya tashi sakamakon yanayin tafiyar da takeyi sassan jikinta na motsawa mazaunanta ba 'karamin tayar masa da hankali yayi ba hakan ya sake sanya masa rashin kuzari da karfin jiki ya dinga tafiya tamkar wanda 'kwai ya fashewa a ciki gabad'aya sha'awarshi ta tashi yana so ya samu yarinyar da zata d'ebe masa kewa.

Sai da ya kusa zuwa dab dani sannan na juya na cigaba da tafiya.....Yarima Ali ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa faffad'an qugunta ido wanda yake juyawa cikin zanin kamfalar dake jikinta........ajiyar zuciya ya dinga saukewa yana kokarin danne abinda ke taso masa.

Koda muka shiga gurin namu Tambaya dake bakin rijiya tana wanke kwanuka mikewa tayi da sauri ganina tare dashi yasa hankalinta ya tashi tana tsoro ko wani abu ne ya faru, ganin ta razana yasa nace"Ki kwantar da hankalinki babu abinda ya faru Yarima zai duba jikin babana ne."

Zubewa tayi gabansa tana gaisheshi gami dayi masa godiya. Cikin sanyin murya ya amsa tare da bata umarnin mi'kewa.
Na kalleshi a nutse nace"Ranka ya dade bisimillah ka shigo." Takalmansa ya cire a nutse ya rankwafa domin shiga dakin dake gajeriyar kofa ce shi kuma ya kasance mutum mai tsayi shine dalilin da yasa ya risina domun shiga dakin.

Guri na shiga karkad'ewa wai ko zai zauna, sai naga yaja ya tsaya yana kallon babana dake kwance yana bacci.....Cikin rawar baki nace"Ka ganshi ko wallahi yana jin ji......! hannu ya daga min alamanun baya bukatar maganata, nayi shuru ina kallonsa sai kallon babana yake kafin ya kalleni yace"Ina maganin da kuke bashi."?
Da sauri na dauko na mika masa, ya jima yana duba magungunan kafin ya miko min da fadin"Kada ku sake bashi maganin ku ajeshi zamuje yanzu nasa Haruna ya samo masa wasu insha Allah zasuyi masa."
Da sauri nace"To mungode shima na hausan da muke bashi mu daina."? Kallona yayi da sauri yace."Bayan wannan maganin akwai wanda kuke bashi."? nace."Eh akwai na hausa wanda na kar'bo gurin masu maganin gargajiya."

Tsaki! yaja da fad'in"Jeki dauko min maganin nagani." Na mike da sauri na fita tsakar gida na samu Tambaya ta gama wanke kwanuka tana tsaye jikin bango (garu)ta rungume hannuwanta a kirji.
"Tambaya ina maganin da ki'ka jiqawa babana." Da sauri ta shiga wani daki dake tsakar gidan ta dauko maganin cikin bokitin roba madaidaici karba nayi da sauri na shiga dakin, na mika masa .

"Ajiye ki bud'e nagani." Ajiyewa nayi a kasan guri nayi yanda yace. Ni dashi gabad'aya tsirawa maganin ido mukayi ganin yanda yake wata irin kumfa ga wari na tashi a cikinsa.
Dauke kansa yay rai a b'ace yace."Rufe." Jiki a sanyaye na rufe ina kallonsa, Yace."Wannan maganin kwanansa nawa a jiqe."? a sanyaye nace"Zai kai sati biyu." Cike da taikaci yace." Waye ya fad'a miki ana had'a maganin hausa dana bature a tare? shuru nayi kaina a kasa.....Ya cigaba da cewa"Magani kun jiqa shi tsayin sati biyu yana kumfa wari na tashi a cikinsa amma kuna d'irka masa so kuke ku kasheshi."? Nayi saurin kallonsa ina girgiza kaina. Yace."To ko dan gaba ba'a hada maganin hausa dana bature a tare sannan kuma idan kun jiqa maganin hausa to kuyi amfani dashi a lokacin idan ya kwana daya biyu ku zubar dashi domin ya tashi a aiki amma magani tsayin sati biyu a jiqe kuna bashi dole ku kasa gane kansa.

Nace"Kayi hakuri zamu gyara insha Allah.'' Shiru yayi ya sunkuyar kansa 'kasa, na dinga satar kallonsa ina mamakin wannan d'abia tashi bini bini kallon 'kasa sai kace makaho........"Anjima bayan isha'i ki shigo ki kar'bar masa wasu maganin insha Allahu zai samu lafiya." Murya na rawa nace"To mungode ranka ya dade."
Ba tare da yace wani abuba ya rankwafa da niyyar fita daga dakin........Bayansa nabi naga suna sallama da tambaya, har soro na rakashi ina godiya uffan bece min ba har ya fita daga zauran namu.....na koma cikin gidan da sauri na shiga yiwa Tambaya bayani da yayi akan maganin gargajiyar da muka jiqa.
*BINTA UMAR ABBALE*

Kuyi sharing👏🏻
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_





*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
21&22
Sai bayan dana idar da sallar isha'i tukkuna na shedawa Tambaya maganar komawa ta 'bangaransa da aiki. shuru tayi tana nazarin al'amarin tace"Sumayya dole ne mubi umarnin masarauta bamu da za'bi sai abinda suka ce damu saboda haka na umarce ki kije ki kula da Yarima bisa amana ki kyautata masa kamar yanda zaki kyautatawa iyayenki." Nace"Tambaya babu wanda nake ji sai babana ki duba kiga halin da yake ciki gashi kema bakya zama sosai kullum kuna gurin girkin abinci bana so a barshi shi kadai a gidan shiyasa wallahi tunda naji maganar hankalina ya tashi."

"Sumayya duk abinda Allah yayi nufun zartarwa akan mahaifinki to ko muna nan ko bama nan bamu isa mu hana Allah ikonsa ba, saboda haka ki nutsu ki kwantar da hankalin ki cuta ba mutuwa bace insha Allah Allah zai tashi kafad'unsa."

Shuru nayi ina sa'ke-sa'ke a cikin raina.
Tace"Tunda kinyi sallah sai kici abinci ki tafi kada ki 'bata lokaci a samu matsala.
A sanyaye naje na 'Dauko kula ta abincin na had'o da plate na zauna inda na tashi abincin na zuba a plate nayi bisimillah a nutse na fara ci, Tambaya miqewa tayi ta nufi inda mijinta yake kwance, a hankali ta shiga kiran sunansa, bude idonsa yayi ya kalleta a hankali ya mayar da idon ya rufe, tace"Malam kaji maganar da muke tattaunawa ko.'' ? idanunsa ya bude ya kalli gefan da nake zaune ina cin abinci.
A sar'ke yace"Sumayya kibi umarnin masarauta ko bayan babu raina bance ki bijirewa masarauta ba domin baki da wani tushe sai ita iyayenmu da kakannimu duk a k'arkashin masarauta suka rayu a haka duk aka haife mu saboda haka nake umartar ki da cewar kiyi biyayya kamar yanda kika ga munayi a matsayin mu na iyayenki."

Muryata na rawa nace"Baba dan Allah ka daina maganar mutuwa insha Allahu zaka tashi ka cigaba da sabgogin ka cuta ba mutuwa bace." Murmushi yay yace."Sumayya kenan to ina rokon ubangiji Allah ya tashi kafad'una na cigaba da rayuwa a tare daku.'"
murya na rawa nace"ameen baba Allah ya baka lafiya." amsawa sukayi da "ameen" na mike na fita domin wanke hannuna.

Lokacin dana shiga dakin Tambaya na kokarin mikar dashi zaune domin ta d'aura masa alwala taimaka mata nayi mukayi masa alwalar ta gyara shi sosai yanda zaiji dadin sallah ya tayar da iqama a nutse! kallona tayi tace"Kiyi maza ka tafi mana." Sai Naji zuciyata ta karye tunda na taso ban ta'ba zuwa ko'ina na kwana ba kullum ina tare da iyayena
A sanyaye na juya ina goge hawaye da hannuna nace"Na tafi." Itama tambayan cikin alhini tace"Sai da safe." Jin kuka naso ya kufce min yasa nayi gaggawar fita daga dakin, takalmana dake bakin kofar dakin na zura na fita daga gidan.


Haruna da su Isa na samu a falon suna aikace aikace, gaisawa mukayi na nemi kan kujera na zauna ina rarraba idona a katafaran falon nashi daya gaji da had'uwa, ko wace kusurwa hotonshi ne a manne wani da manyan kaya na sarauta wani kuma da 'kananun kaya cikin hotonan nasa babu wanda yayi dariya a ciki fuska a murtuke tamkar wanda akayiwa dole gurin daukar hoton, muryar Haruna ce ta katse min tunanin da nake, na kalleshi inaso ya sake maimaita min abinda yake fad'a, Yace."Sumayya ba zama zakiyi ba zaki hau sama ne ki bubbuga idan ya bude sai ki sheda masa isowarki idan da akwai abinda yake bukata kiyi masa sai kiyi mu dai mun gama aikin mu zamuje mu huta sai ya b'ukace mu.'' Na kalleshi da fadin"Ina ne d'akin nasa."
Wata matattakalar bene ya nuna min da fadin''Kina kaiwa karshen benan za kiga wata kofa mai biyu nan ne d'akinsa sai ki danna wani abu a jikin kofar zai yi magana.

Nayi shuru ina sa'ke-sa'ke mi'kewa nayi na kama hanyar benan, da k'yar nake hawa benan sabida santsin ties d'in ina hawa ina ri'ke sandar benan gabana na fad'uwa! ajiyar zuciya na ajiye bayan na gani a kofar dakin
Sai da na daidaita nutsuwa ta tukkuna na danna abinda zai isar masa da isowata. shuru ba'ayi magana ba, nasa hannu akan abun na latsa da kar'fi! Naji muryarsa yana fad'in "Wanene." "Nice Sumayya.'' Murya a hard'e na fadi maganar. shuru har tsayin mintina goma bai bude ba jikina yayi sanyi kamar nayi tafiya ta sai dai na daure na cigaba da tsayuwa, motsin bude kofar naji nayi saurin ja gefe tare dayin kasa da kaina, koda ya bude kofar ban kalleshi ba nace" Barka da dare ranka ya dade."

"Barka dai shigo ciki." Yafada tare da juyawa cikin dakin. Dago kaina nayi da sauri na mayar dashi qasa sakamakon ganinsa da nayi d'aure da towel gabana ya dinga bugawa kasa shiga dakin nai nayi tsaye a bakin kofar ina tararrabi."

Zama yay gefan bed dinshi yana kallon bakin kofar, "Ke! ki shigo nace dake."! A tsawace ya fad'i maganar, shahada nayi na shiga yace." Kulle kofar." hannu nasa na tura kofar dakin ta rufe, tsayuwa nayi jikin kofar kaina a qasa nace"Ranka ya dade gani nazo." Shareni yayi ya cigaba da murza vasilin a jikinsa, duk da kaina a qasa yake sai da naga cinyoyinsa d'an towel din ya dinga turewa daga jikinsa yana shafa vasilin din, ganin kamar yana so yayi tsirara yasa na juya masa baya.

"Ke! dodo ne ni da zaki juya min ba okey zan saki yanzu ki shafa min vasillin din tunda abin hakane." Ji nayi yawun bakina ya bushe, nace"Dan Allah kasa kayanka baligin mutum kamar ka bai kamata ana ganin tsaraicinsa ba.

"Wa'azi za kiyi min kome."? Shuru nayi masa, yace." Malama Zo nan ki shafa min vasilin din a bayana." Kasa juyawa nayi ballantana naje nabi umarninsa. "Ko bakya ji ne." Hanci na shaqa kunyar duniya ta isheni nace"Dan Allah kayi hakuri ba zan iya ba." Tsaki naji yaja daga hakan be sake cewa komai ba ya cigaba da shafa mai a jikinsa.

"To na gama sai ki juyo.'' A hankali na juya kaina a 'kasa ban yarda na kalleshi ba, yace" Zo ki kar'bi maganin nasa Haruna yaje gurin seda magani ya siyo zo in nuna miki yanda zaku dinga bashi.
Zuwa nayi na durkusa gabansa a nutse ya fito da magungunan daga ciki leda ya shiga nuna min yanda qa'idarsu take, muryata na rawa nace"Allah ya saka da alkairi mungode." Yace."Ki koma yanzu ki bashi maganin kamar yanda nace amma ki tabbatar kafin ki bashi yaci abinci ya koshi." Ina kokarin miqewa tsaye nace"Insha Allahu yanda kace haka za'ayi." da ledar maganin a hannuna na kama hanyar fita daga dakin.
Ka shingid'a yayi tare da bin bayanta da shu'umin kallo, sajensa ya shafa yana lumshe idonsa gabad'aya yarinyar ta rikitashi duk wani abu da yake daurewa yake yi amma yana bukatar wacce zata d'ebe masa kewa.

Sai da na tabbatar da yaci ya k'oshi tukkuna na bashi maganin kamar yanda ya umarce ni, mahaifiyata na kalla dake kokarin gyara masa shimfida nace"koda da safe ban shigo da wuri ba ai kinga yanda na bashi maganin ko."? Tace"Eh na gani insha Allahu zan kwatanta." Miqewa nayi na sakeyi mata sallama a karo na biyu, tace"To Allah ya tashemu lafiya." da ''ameen na amsa cikin sauri na fita daga dakin.


Yana kishingid'e kasan kafet din dake 'kasan bed dinshi na same shi da

Please Login or Register in order to submit comment