Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

masa da fad'in "Allah ya tsareka a duk inda kake." ya amsa da ameen ya Allah." Ajiyar zuciya na sauke na zauna kan kujera ina jin wani irin farin ciki a cikin zuciyata, inama ba zamu sake samun matsala da juna ba.



"Aunty Lauratu bana so wani mummunan abu ya biyo baya akan abinda kuke kokarin aikatawa dan Allah kada kuyi mata lahani ku kyaleta ita da cikinta nima insha Allahu zan samu." Lawisa ce take wannan maganar.......Hajiya Karima tace"Wato Lawisa har kin saduda ko? yarinya tayi sanadiyar da aka rataye d'an uwanki ki dinga nuna tausayinki akanta meye amfanin wannan yarinyar idan bamu bi dare da rana mun kasheta ba."!!!

A tsorace! ta kalli Mahaifiyar tata za tayi magana Lauratu tace"Ke! dallah rufe mana baki mara wayo kawai! wato ke har kin amince da dadin bakin da yayi miki ko har kina magana akan mu tausayawa kishiyarki to bari kiji wannan yarinya Sumayya ba zata haife cikin jikinta lafiya ba sai munyi ajalinta."


"Aunty Lauratu dan Allah ku bar al'amarin kada ku janyowa kanku wata masifar kunga garin irin haka Muddibo ya rasa rayuwarsa wallahi ni yanzu duniyar gabadaya tsoro take bani kuyi hakuri da daukar fansar nan kada ku janyo mana tashin hankali."

Hajiya Karima tace"Kinga Lawisa tashi ki koma gurinki tunda ba zaki bamu hadin kai ba, kije kawai kafin ku dawo daga inda kuka nufa komai ya zama tarihi." Lawisa jiki a sanyaye ta mike ta bar musu gurun, koda ta koma sashenta kasa aikata komai tayi ta dinga tunanin yanda zata 'bullowa al'amarin tana jin tsoron mahaifiyarta da kanwarta su janyowa kansu wata masifar gashi Wali baya gari bare ta sheda masa idan ta kira wayarsa bata shiga abin duniya ya taru yayi mata yawa sam bata so suyi tafiyar nan wani mummunan abu ya faru.


Ranar talata ranar ce ta kama ranar tafiya ya shigo gurina cikin shiri sai dai babu walwala a tare dashi, ganin haka yasa na danne damuwata na shiga kwantar masa da hankali ya rungume ni tsam! a jikinsa yana bani hakuri nace"Dan Allah ka daina bani hakuri kana sanyawa gwiwata tana sanyi wallahi." fuskata ya sumbata yana kallona yace."Sumayya dole na baki hakuri tafiyar nan kamata yayi ace dake zanyi domun na kula dake da babyna amma Allah bai nufa ba insha Allahu Allah zai kula min dake."

Nace"Ka gama magana tunda kace Allah insha Allahu zai kare ni cikin kariyarsa, hannuna ya rike muka fita falo tare yace."Sati uku kamar yau ne insha Allah ki kwantar da hankali ki.'' nace"Allah ya kaiku lafiya ya kuma dawo daku lafiya cikin nasara." Ya amsa da ''Ameen ya Allah." Hannuna ya saki da sauri ya kama hanyar fita, naji zuciyata ta karye hawaye suka zubo min da sauri nayi gaggawar shigewa daki dan bana bukatar ya juyo yaga halin da nake ciki, kwanciya nayi kan gado na dinga share hawaye ina jin wani irin kewa da damuwa a cikin raina...



*Na kudi ne.*
Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biya ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne saki kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
104
Tunda suka tafi na kasa sakewa a gurina haka kawai sai na dinga jin fargaba da tsoro na dinga ganin tamkar wani mummun abu zai faru dani, kawai sai na tsiri zuwa gurin Mamma na wuni a can sai yamma nake komawa gurina, yawan zuwan da nake gurinta yasa ta gane cewa ina da ciki sosai ta nuna farin cikinta a fili tayi ta mamakin al'amarin nidai kunya ta hanani nace mata komai kasa hakuri tayi sai da ta tambayeni watannin cikin na fad'a mata watansa biyar, tace"Amma saboda baku da kirki dake da babana aka rasa wanda zai fada min ga ciki yayi kwari ban san dashi ba haka kuma Maimartaba bai sani ba meye abin 'boyewa a ciki." shuru nayi ba wai dan bani da abin fada ba sabida nasan idan na fad'a mata irin abubuwan da suka dinga faruwa kafin samuwar cikin sai ranta ya 'baci shiyasa nayi shuru domin fada mata bashi da amfani. wayarta ta dauka ta shiga kiran yaron nata, ina daga inda nake ina jin muryarsa suna gaisawa, tace"Babana ashe ka iya munafurci dama."? Da sauri yace."Mamma me ya kawo wannan maganar kuma."? tace"Sumayya nada ciki amma saboda rashin kirki kwanaki dana tambayeka kace babu saboda kana so kayi wasa da hankalina ko." murmushi yayi yace."Afuwa Mammana ni kaina wallahi yarinyar 'boye min tayi sai daga baya na ganshi." tace"To daka tabbatar dashi me yasa baka zo ka fada min ba." Yace."Mamma ki gafarce ni wallahi ina jin kunyar nazo na fada miki cewar Sumayya nada ciki shiyasa nayi shuru da bakina idan ya fito nasan dole ki gani." Tace"Ni ban yarda da maganarka babana watakila dai akwai abinda kake 'boye min." Gabansa ne ya fad'i! yace.'' Haba Mamma me zan 'boye miki kina matsayin uwata dan Allah ki yarda da maganata." Ajiyar zuciya ta sauke tace"To na amince da maganarka amma Sumayya zata dawo gurina ta zauna har sai sanda kuka dawo tukkuna."

Yace."To babu komai Mamma ai kamar yau zamu dawo tunda yanzu gashi har munyi sati guda." Tace."To masha Allah ina rokon Ubangiji Allah ya dawo daku lafiya.'' Ya amsa da ''ameen ya Allah." kashe wayar tayi ta juyo tana kallona da murmushi a fuskarta tace"Kinji yanda mukayi da mijinki ko." nace"Naji mamma nima zanfi so na dawo nan din." Tace"To shikkenan bayan sallar isha'i sai kuje tare da Jakadiya ki dauko abunda zaki bukata." nace"To godiya nake ranki ya dad'e."



Tana wani irin kuka take fad'in "Wallahi na daina yarda kana amfani dani da kwaroran roba(Condem) sai kace karuwa zaka dinga gudun haihuwa dani wato ita wacce kake so ka bari ta dauki ciki ni kuma ka yaudareni ka dibga min kwayoyi yanzu kuma ka dawo kana sa condem to na gane yanxu wallahi idan baka daina ba sai na tona maka asiri."! cikin kuka na fitar hayyaci take maganar."

A fusace! yace." Lawisa kada ki fasa tona min asiri a gida idan kin fad'awa iyayena abinda yake faruwa a tsakaninmu wallahi sai kinyi mamakin hukuncin da zanyi miki! kuma bazan cire condem ba duk abinda zakiyi sai dai kiyi."

Da sauri ta janye jikina tana kuka tace"Ni kuma wallahi na daina amincewa da kai kana cutar dani da mugun halinka sai Allah ya saka min."!! mari ya kwada mata yana huci! yace."ai baki fi karfina ba yanzu zan biya bukata ko kina so ko bakyaso." kafin tayi wani yunkuri ya turmushe ya shiga biyawa kansa bukata ba tare da ya cire condem din ba.........sai da yayi me isar sa sannan ya daga ta yaje yai wanka ya fito ya shirya jikinsa ya fita ya barta cikin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali.

Tare mukaje gurina da Jakadiya ta zauna a falo ni kuma na nufi dakina domin harhad'a 'yan kayan da zan bukata, ina sanya 'kafata a cikin d'akin santsi ya kayar dani! wata irin fad'uwa nayi cikina ya daki! 'kasa da karfin gaske! rintse idona nayi tare da kiran sunan Allah da karfi! dakin ne yayi duhu! cikin karfin hali nayi yunkurin mikewa! naji saukar duka akaina! fad'uwa nayi ina kiran sunan Allah da karfin gaske nace"Jakadiya."!!!!!! a guje! ta shigo dakin tana amsawa tare da laluben mukunnin fitila, ji tayi an bangajeta an fita a guje! salati tasa da sauri ta kunna fitilar! dakin yayi haske! ganin ta a kwance tana murkususu yasa hankalinta ya tashi! zubewa tayi a gabanta tana kiran sunanta jikinta sai rawa yake.......Cikin karfin hali nace"Jakadiya mutuwa zanyi."!! hawaye ta share tace"Ba zaki mutu ba sumayya Allah zai toni asirin duk wanda yake kokarin cutar dake......da sauri ta mike ta fita nan ta samu masu tsaron gurin a tsaitsaye suna magana tace''Ina fata dai kun gane wanda ya fito yanzu." gabadayansu suka ce "Babu samu nasarar kama ta ma dan kayan dake jikinta irin na bayi ne shiyasa ba muyi tunanin wani abuba." Jakadiya da sauri ta bar gurin dan ba taga amfanin tsayuwarta ba.


Su Mariya ne suka rufu akanta suna mata firfita gabadayansu hankalinsu ya tashi da abinda ya faru da uwar dakin nasu, suna cikin dakinsu suka jiyo ihun ta dalilin da yasa kenan suka fito a gigice!

Ganin jini ya 'bata mata zanin jikinta yasa hankalinsu ya kara tashi shikkenan suma suna cikin gariri dole a tambayesu yanda akayi suka bari ta shigo gurin har ta samu nasara.


Mamma da Jakadiya suka shigo dakin hankalinsu a tashe! lokacin Sumayya ta galabaita mutuka, mamma ganinta cikin mugun yanayi yasa ta fashe da kuka rungumeta tayi jikinta duk ya 'baci da jini tace"Sumayya Allah ya saka miki." jin miryarta yasa na 'kan'kame! hannunta ina nishi! nace"Mamma Lauratu ta samu nasara akaina shikkenan nasan sun kashe min baby." wasu zafafan hawaye suka shigo zubo min........Rungumeni tayi tana tofa min adduoi...cikin wannan hali Shatima ya shigo hankalinsa a tashe yace."Mamma ku kamata muje asibiti a dubata." Mamma ta mike jikinta duk ya mutu ta riga ta futar da rai da cikin da ta kwallafa rai dashi.......


Jin cewar matar mai asibitin ce yasa likitoci suka rufu a kanta sai da suka tabbatar da cewa komai yayi daidai sannan hankalinsu ya kwanta.........Mamma ajiyar zuciya ta sauke mai sanyi lokacin da ta gama sauraran jawabin da Dr Sadiya take mata, tace"Alhamdullh dr dama ni fargabata kada ace cikin ya zube tunda dai Allah ya takaita to sai mugodewa masa kuma sannuku da kokari Allah ya saka muku da alkairi." Dr Sadiya tace"babu komai ranki ya dade an jima kadan zaku iya shiga ku dubata yanzu tana bacci." Mamma tace"To babu damuwa." Dr Sadiya ta bude musu wani daki suka zauna a ciki suna jajanta al'amarin..........A daran Maimartaba da Waziri tare da Mahaifinta Lawi sai da suka zo asibitin suka duba ta basu tafi ba sai da ta tashi suka tabbatar da lafiyarta sannan suka tafi ita kuwa Mamma kasa tafiya tayi tasa Shatima ya shedawa D'an uwan nasa abinda yake faruwa, lokacin yayi ta kiran wayarsa bata shiga tace ya bari da safe sai ya kirashi ya fada masa...............

Hannuwana ta rike tace"Sumayya ba kuka za kiyi ba Allah zaki godewa daya kare ki daga sharrin masu sharri Kiyi shuru ki kwantar da hankalinki ki fada min dukkanin abinda yake faruwa."


Hawaye na share a hankali na soma yi mata bayanin abubuwan da suka dinga faruwa a tsakanina dasu.

Hawaye ta share tana girgiza kanta tace" Wannan rashin imani da rashin tsoron Allah na hajiya karima yana bani mamaki! wato ashe bata hakura ba shine take so ta dauki fansa akanki ai bake kika sa aka rataye danta ba da zata dinga bibiyarki da sharri! ki daina kuka sumayya insha Allah sunyi na farko sunyi na karshe sai an dauki mataki mai tsauri akansu sai sunyi da sun sanin abinda suka aikata miki, dama ita wannan Lauratu shaidaniya ce dan ta kashe mutum ba sabon abu bane a gurinta to wannan karon sai tayi nadamar abinda ta aikata.

Da asubah bayan ta idar da sallah, kira ya shigo wayarta koda ta duba sai taga yaron nata ne a nutse ta daga tare dayin sallama............Murya a sha'ke Lawisa ta amsa tare da fad'in "Mamma ina fata kun tashi lafiya." a sanyaye tace"Lafiya lau Lawisa ina fatan kuna nan lafiya?" kuka ta fashe dashi! Mamma hankalinta ya tashi tace"Lawisa lafiya kike kuka ina babana yake."? Lawisa kasa magana tayi ta cigaba da gurshe'ken kukanta.

Mamma jikinta dik yayi sanyi tace"Lawisa ki daina kuka ki fada min abinda ke faruwa ko fada kukayi dashi ne."? murya a sar'ke tace"Mamma ki gafarce ni nasan idan kikaji abinda yake tafe dani hankalin ki zai tashi." Tace"Lawisa ai yanzu hakama a cikin tashin hankali nake dan jiya da daddare Kanwar mamakin Lauratu ta shiga har gurin Sumayya tayi yunkurin cutar da ita dan yanzu hakama muna asibiti."


Lawisa taji gwiwarta tayi sanyi jikinta na rawa tace"Mamma dan Allah kuyi hakuri Aunty Lauratu ba zata aikata haka ba." cike da mamaki tace"Lawisa kin san halin kanwar mamanki nima na san halinta na kuma nasan abinda za tayi da wanda ba zata aikata ba Lauratu shigarta prison nawa saboda aikata munana ayyuka shine Mahaifiyarki ta hada baki da ita suke bibiyar rayuwar Sumayya saboda su dauki fansa akan abinda ya faru."


Lawisa kuka kawai take gabadaya kanta ya kulle ta rasa wane irin tunani za tayi dama tasan dole sai asirinsu ya tonu shiyasa tun kafin su aikata ta hanasu saboda gudun abinda zai faru dasu.

Mamma tace"Ki daina kuka ki fada min abinda ya hadaki da mijinki." Hawaye ta share ta dan juya ta kalli toilet yana ciki yana wanka bayan ya gama sasakarta wallahi tai rantsuwa da Allah sai ta tona masa asiri tunda ya kasance azzalimi.


Cikin kuka da nadama ta shiga fada mata abubuwan da suke faruwa. Mamma ta shiga tsantsar tashin hankali dajin abinda Lawisa ke fada mata, babanta shike gudun haihuwa har yana saka kwaroron roba sabida kada ya samu zuria! wannan al'amari yayi masifar tashin hankalinta, waiwaya tayi bayanta tana kallon Sumayya dake bacci! cikin zuciyarta tace"Wannan yarinya babu abinda zance dake a duniyar nan kinyi min hallaci tabbas samun irin masu halinki zaiyi wahalar gaske........Ajiyar zuciya ta sauke tace"Lawisa daina kuka ki saurareni." hawaye ta share tace"Ina jinki Mamma." Tace"Kiyi hakuri kinji ko insha Allah haka ba zata sake faruwa ba, sannan duk ranar daya kuma zuwa zai sadu dake da kwaroro a jikinsa kada ki amince dashi! idan kun dawo gida zan dauki mataki akansa inaso kuma ki rufa asirin maganar nan dan idan kin fito kin fada kin tonawa kanki asiri sannan kuma kin tona asirin mijinki amma hakikanin gaskiya babana bai kyauta miki ba amma kada ki damu zan dauki mataki akansa." Zuciyarta tayi sanyi tace"To shikkenan Mamma nagode sosai Allah ya kara girma." Sallama sukayi ta kashe wayar tana jin sanyi a cikin ranta, tana juyowa suka hada ido ya fito tun dazu kuma komai kunnensa. hannu ya mika mata da fadin" Bani waya ta." jiki a sanyaye ta mika masa ya kar'ba yana kallonta yace."Sai da kika fada mata ko."? hawaye ta goge tace"Ya za'ayi ba zan fada mata ba kana cutata.'' Yace'' To kin janyowa kanki saki." kallonsa tai gabanta na mugun faduwa! yace." Na fada miki cewa duk ranar da kika kuskura kika fitar da sirrina wani yaji to zan miki hukunci da bakiyi tsammani ba munyi haka da Sumayya kuma ta kiyaye ke da yake baki da mutunci kika kira mahaifiyata ko? to kisa a ranki cewa daga yau ke ba matata bace."!! Ihu! ta kurma! ta zube a gurin tana kuka da rokonsa akan kada ya saketa ya tausaya mata, fizge kafarsa yayi yasa kayansa ya fita daga dakin ransa a mugun bace.



*Na kudi ne*
Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip group #600 normal gruop#300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number.
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?
106
Koda nayi wankan sai naji dadin jikina na shirya tsaf na fito falon kawai sai na samu Tambaya ita da Mamma a zaune suna hira. wani irin farin ciki ne ya lullubeni dama tun ina asibiti nake tunaninta gwara Baba shi yaje tare dasu Maimartaba, fuska a sake na zauna ina gaisheta ta amsa cike da kulawa kallon da take min ne yasa na gane cewar taji dadin ganina kalau tace" ya jikin naki." ? nace"Jiki yayi sauki alhamdulillahi." Mamma tace." Da kikayi wankan Kinji karfin jikin naki ko."? nace"Sosai kuwa Mamma naji dadin dana gasa jikina." tace." To haka akeso sai kici abinci kisha magani nima zan shiga nayi wankan." nace"To mamma a fito lafiya." Tambaya tace"Ranki ya dade a fito lafiya watakila kafin ki fito ni na tafi." Mamma tace"A'a Tambaya kada ki tafi ki bari na fito tukkuna." Tace."To shikkenan ranki ya dade.'' Mamma mikewa tayi ta shiga dakinta..........Tambaya ta kalleni tare da sauke ajiyar zuciya tace" Sumayya naji dadin da wannan mata bata samu nasara akanki ba jiya dai saboda tsabar fargaba da tashin hankali kasa rintsawa nayi sai da na samu labarin dawowarku daga asibiti hankalina ya kwanta dalilin da yasa kenan na shigo domin na duba lafiyarki."

Nace."Tambaya duk mutumin daya dogara da Allah to babu shakka Allah na tare dashi, Lauratu tayi nufin cutar dani Allah ya kareni daga sharrinta wannan kad'ai ya isa ya nuna mana 'Kadaitakar Ubangiji sun nufe ni da sharri na mayar da al'amarin gurinsa shi kuma ya mayar musu da sharrinsu kansu Allah nagode maka."

Ajiyar zuciya ta sauke tace"Sumayya ni kaina na 'kara jin tsoron Allah a zuciyata wannan abu da ya faru da Hajiya Karima da k'anwarta ishara ce Allah ya nunawa masu irin halinsu." Nace"Hakane Tambaya yana da kyau duk wani musulmi ya tsarkake zuciyarsa ya kuma kadaita Allah shi kad'ai kada ya hadashi da abokin tarayya sannan kada ya zalinci wani idan an zalince sai ya barwa Allah da sannu zai saka masa abisa zalinci da akayi masa Allah kasa mufi karfin zociyoyinmu."

"Ameeen tace tana girgiza kanta.......Mamma ta fito daga dakinta cikin kamala gabadaya falon ya cika da kamshin turaranta, Jakadiyarta ce a bayanta hannunta rike da tarin kayan sawa. gurun zamanta ta zauna da mirmushi a fuskarta tace" Tambaya na barki kina jirana ko."?


Tambaya ta sunkuyar da kanta tana murmushi tace"Aa ranki ya dade babu damuwa ai ina fata kin fito lafiya."? tace"Lafiya lau Jakadiya bata wannan kayan na hannunki.'' da sauri Jakadiya ta mika mata kayan.....Tambaya tasa hannu biyu ta kar'ba fuskarta yalwace da fara'a.

Mamma tace"Kije kiyi amfani dasu daga yau ki daina amfani da kaya irin na bayi a masarautar nan kun zama masu 'yanci insha Allahu idan Maimartaba ya samu nutsuwa zamu zauna dashi za'a sanja muku gurin zama.


Cike da murna da farin ciki nace."Mamma godiya suke da wannan karamanci Allah ya saka da alkairi ya kara girma." Murmushi kawai tayi ba tace komai ba, Tambaya godiya kawai takeyi bakinta yaki rufuwa addua take gami da fatan alkairi. Mamma ta dakatar da ita da tare da fadin" Godiyar ta isa haka duk wani abu da taga anyi musu a masarauta sun cancanta ne saboda haka babu kalmar godiya a tsakaninsu. Cikin tsantsar farin ciki Tambaya tayi mana sallama Jakadiya tabi bayanta tare da kayan da Mamma tayi mata kyautarsu

Sai Bayan La'asar Maimartaba ya shigo, cikin nutsuwa na gaisheshi ya amsa cikin kulawa tare da tambayata yanayin jikina, nace"Naji sauki sosai." shuru gurin yayi na yan mintina kafin ya kira sunana na amsa a nutse tare da sunkuyar da kaina kasa, Yace."Kiyi hakuri abubuwan da suka faru dake inaso ki daukesu a matsayin kaddara insha Allahu abu makamancin wannan ba zai sake faruwa dake ba."

Nace"Ranka ya dade insha Allah magana ta wuce a gurina na barwa Allah komai suma wa'inda suka aikata mugun abu akaina na yafe musu har abada sannan kuma ina nema musu shiriya daga gurin Ubangiji." Yace."To alhamdulillhi dama haka akeso mutum ya kasance mai saukin kai da saurin afuwa." Ya kalli Mamma a nutse yace."Hajiya Karima ta samu nutsuwa kuma tayi mana bayanin yanda duk al'amura suka kasance yanzu haka tana can cikin damuwa da tashin hankali tayi kuka tamkar ruwan hawayenta zai 'kare gabadayanku tana neman afuwa a gurinku keda Sumayya tayi alkawari akan insha Allahu ba zata sake aikata abu makamancin wannan ba, na yafe mata saboda na yarda da tubanta kuma inaso ku yafe mata mussaman ke Sumayya." Mamma ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye tace"Ranka ya dade shiriya dai ta Allah ce amma wallahi gani nake kamar karya take so take a kuma sakin jiki da ita ta sake aikata wani mugun abun yana da kyau a dauki mataki a kanta."


Girgiza kansa yayi yace."Fulani ki kyautata zaton alkairi akanta a yanda take kuka take rokon gafara yasa na gazgata tubanta saboda haka kema inaso ki cire shakku akanta kiyi mata kyakkyawar addua.'' Tace."To shikkenan ranka ya dade Allah ya yafe mata ya yafe mana baki daya. Yace."Yanzu jikin Ciroma ne yayi tsanani nasa an daukeshi an kaishi asibiti hakika yana bukatar addua dan bai san inda kansa yake ba."
Gabadaya daga ni Har Mamman jikinmu ne yayi sanyi dan jin yanda Maimartaban ke mana bayanin yanayin jikin d'an uwan nasa.

Uwargida da tawagar 'ya'yanta ne suka shigo falon, kallo muka bisu dashi jiki a sanyaye suka samu guri suka zazzauna.......Maimartaba ya bisu da kallo cikin nutsuwa yace."Ina fatan dai lafiya." ? Hajiya Huwaila ta fashe da kuka tana girgiza kanta, kawai sai suma su aunty Safiyyan suka shiga kuka.


Falon ya rikice da koke-koke! Maimartaba yasha jinin jikinsa tabbas ruwa baya tsami banza.


Mamma ta matsa kusa da Ita kafad'arta ta dafa cikin nutsuwa ta shiga kwantar mata da hankali akan tayi shuru dukkanin abinda yayi tsanani maganinsa Allah.


Huwaila ta kama hannunta ta rike tana hawaye tace"Fulani ki gafarce ni hakika na dade ina cutar dake da d'anki bana kaunarku kullum cikin shirya muku mugun abu nake, babu irin jifan da banyi miki ba Allah na kareki Aliyu kuwa babu irin abinda ba muyi masa ba nida 'ya'yana Allah yana 'kareshi Wannan yarinyar Sumayya ita ta zama garkuwa a gareshi dan duk wani abu na cutarwa da zamu nufeshi dashi itake wargazashi sosai muka dinga tsoratar da ita akan hakan amma da yake yarinyar arziki ce ba taji tsoro ba ta cigaba da bashi kariya hakika samun jajirtattun mutane masu tsoron Allah irin wannan yarinya zaiyi wahalar gaske! a lokacin da hukuncin rataya ya sauka akan Muddibo dukkaninmu hankalinmu ya tashi domin mun dauka zai fad'o sunayenmu a cikin wa'inda suke bashi gudumawa domin cikar burinsa sai mukaji shuru har aka rataye shi sunayenmu basu fito ba wannan abinda ya faru da Sumayya yasa gabadaya jikinmu yayi sanyi muka ga dacewar muzu mu nemi afuwa a gurinku akan abubuwan da suka faru a baya hakika mun tsorata da irin mutuwar da Lauratu tayi ga Hajiya Karima cikin wani irin mugun yanayi mara kyau ga Ciroma a kwance rai a hannun Allah babu shakka hakkin wa'inda suke zalinta ne ya sauka a kansu Ranka ya dade muna neman gafara a gurinka kema Sumayya ki yafe mana abinda muka aikata a gareki." Cikin kuka ta 'kare maganar.


Gabadaya shuru mukayi muna jajanta al'amarin, ni banyi wani mamaki sosai ba sabida dama na riga na san abinda yake faruwa.....Maimartaba da Mamma ne naga hankalinsu ya tashi gabadaya ma sun kasa magana.

Aunty Bishira tazo ta kama kafafun Mahaifin nata tana hawaye tace"Ranka ya dade kayi hakuri da abinda muka aikata ka gafarce mu kada kace ka yafewa duniya mu."

Girgiza kansa yayi a nutse yace."Bishira ni bani kukayi wa Laifi ba gurin Allah zaku

Please Login or Register in order to submit comment