Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuka nace"Shine ya kashe shi wallahi shine dama yace sai yaga karshen soyayyarmu bukatarsa ta biya ya kashe shi ya huta."



*Na kudi ne...!*
Kada ki karanta min littafi idan baki biya ba ke kuma da kika futa da book din keda Allah! idan kina bukatar biyan kudin ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124..Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA*
*SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
79
Wani irin kallon mamaki Tambaya keyi min, ina gunjin kuka nace"Da gaske ne shine ya kashe shi dama yace yana da hanyoyi da yawa da zai iya raba tsakanina dashi domin ya samu nasarar aurena."!
Tambaya kafad'una ta ri'ke tana jijjigani tace."Sumayya ki shiga nutsuwarki dan Allah ki daina sambatu sai surutai kikeyi marasa kan gado da ma'ana shin waye wannan da kike magana akansa."?.

Hanci na sha'ka na kalleta har yanzu na kasa tsayar da ruwan hawayen dake zuba nace"Tambaya Yarima yayi al'kawarin sai ya aureni ko ta halin 'ka'ka bayan mahaifinsa ya gargadeshi akan ya janye maganar aurena sai ya 'kudiri mummunar aniya a kanmu nida Haruna ya tabbatar min da cewa duk rintsi sai ya san yanda yayi ya aureni domin biyan bukatarsa."

Kallona ta dinga yi tana girgiza kanta gabadaya yanayin ta ya nuna alamun tsoro da tashin hankali......Ganin kawai ta kura min ido tana kallo yasa nayi yun'kurin mikewa, tayi saurin rike hannuna na zauna jiki a sanyaye tace"Sumayya da gaske kike Yarima ne silar mutuwar Haruna." Murya a dashe nace."Tabbas ko shakka ba nayi shine ya kashe s......! saurin rufe min baki tayi kafin na karasa maganar dukkaninmu muka kalli bakin kofa saboda sawun tafiyar mutane da mukaji......Murya na rawa tace"Sumayya ki bar wannan maganar a cikin ki duk rintsi kada ki fito da i ta, idan kin fad'a Yarima yayi silar mutuwar Haruna babu shakka zamu shiga tashin hankali a masarautar n........Katse maganarta tayi dalilin shigowar babana da wasu 'yan sanda guda biyu mace da namiji. cikin tashin hankali muka
Mi'ke tsaye. "Malam wannan ce Sumayyan ko."? A sanyaye Lawi ya daga kansa. ya kalli 'yar uwarsa da fad'in ''Merry je kiyi aikin ki." Gani nayi ta nufo inda nake da ankwa a hannunta, bakina ya dinga motsi jikina ya dinga karkarwa a lokacin gabadaya kwakwalwata toshewa tayi na dinga tunanin adduar da zanyi, Tambaya kuwa kuka ta fashe ta durkushe a gurin tana rirrik'e kafar ma'aikaciyyar a lokacin da take kokarin daure min hannu.

Kallonta tayi cikin yanayin hausarta tace."Kiyi hakuri ba zamuyi mata komai ba mutukar bata wahalar damu ba." Tambaya ta kalli namijin tana kuka tace"Dan darajar Allah da annabi kada ku tafi da ita wallahi bata da laifi akan faruwar wannan al'amari." Yace."baba dole ne ayi binkice akan 'yarki domin itace ta girka abincin dake dauke da guba a ciki idan ba tayi mana gardama ba to zata samu sassauci idan kuwa ta tsaya gardama za tasha wuya a gurinmu." Tambaya kallona tayi tana marairaicewa! naji wani irin tausayinsu ya rufe ni, babana tsabar tashin hankali duk kammaninsa sun sauya ya kasa magana kawai ya jingina jikin bango (garu) sai kallonmu yake.

Cikin kokarin danne tashin hankalina nace"Tambaya ki daina kuka dan Allah kiyi min addua insha Allahu mai gaskiya baya ta'bewa Allah zai kub'tar dani daga dukkanin wata musiba."

Mi'kewa tsaye tayi tana kokarin magana suka tasa 'keya ta, Lawi da saurin gaske ya shiga daki yana share hawaye ita kuwa Tambaya bayanmu ta biyo tana kuka had'e da ri'ke min hannun riga sai hakuri take bawa jami'an tsaron.........Dandazon mutanan dake gurin yasa nayi saurin sunkuyar da kaina kasa na dinga tafiya kaina a sunkuye ina kiran sunan Allah a zuciyata, motarsu suka saka ni, na dukufar da kaina k'asa band'ago kaina ba har sai dana muka fita daga gidan.


Suna zaune suna tattanawa dangane da faruwar al'amarin sa'kon mai girma governor ya iso, mai girma governor yayi umarni da cewa lallai a rufe asibitin *ZINARIYA HOSPITAL* sai gwamnati ta gama binkice akan mutuwar da mutane keyi a cikin asibitin." Maimartaba beji ciwo akan umarnin governor ba koda bai bada umarin rufe asibitin ba dama ya yanke shawarar rufe shi..........Galadima da Ciroma cike da tsantsar farin ciki suka bar fada, suka had'u a gurin guda suna ta 'bab'baka dariya bukatarsu ta fara biya gwamnati ta shigo cikin al'amarin zasu san yanda zasuyi su had'a kai da gwamnatin domin su ruguza asibitin.


Ta jima kanta a kasa tana kaiwa Allah kukanta kafin ta d'ago kanta tana zubar da hawaye ta daga hannuwanta sama ta dinga addua tana 'kas'kantar da kanta a gurin mahallicinta, Mamma Fulani ta dade hannunta a sama tana neman sasaauci gurin Ubangiji kafin ta shafa a fuskarta a nutse ta juyo tana kallon mijin nata dake zaune akan kujera, tace"Ranka ya dad'e Har yanzu bai dawo ba kenan."? Maimartaba ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya yace."Bai shigo ba har yanzu gabad'ayan mu mun gaji da zaman fada kowa ya shige gurinsa.'' Kanta ta d'aga ta kalli agogon dake kafe a falon tara na dare, a sanyaye tace."Inasha Allahu, Allah zai dawo mana dashi lafiya." Maimartaba ya amsa da ameeen tare da mikewa tsaye! sallama yayi mata ya nufi gurin Uwargida Huwaila.......Tana zaune a bakin gado kunnanta makale da waya sai 'ba'bbaka dariya takeyi da alama tana cikin nishad'i, Tace."Ai al'amura gabad'aya sun dagule wannan karon mun samu nasara akansa dan har yanzu yana hannun 'yan sanda kuma gwamnati ta shigo cikin al'amarin asibitin da yake tutiya dashi gwamnati ta rufe shi, wannan dalilin yasa duk na kira wayarku na sheda muku cewa yau kuyi bacci harda munshari dan bukatarmu daf take da ta biya." Daga daya b'angaran aunty Safiyya ta dinga k'yakyata dariyar farin ciki tace"A gaskiya naji dadin wannan abu Wai!! ya muka ga idon mutsiyaci a cell a gwara yasha duka dan ya bamu wuya." Uwar gida tace"Ai be zama lallai su doke shi ba yanzu abinda nake so daku shine gobe da sassafe ku shigo cikin nuna alhini da damuwarku bana so ko kad'an a gane akwai sa hannunmu a cikin al'amarin." Aunt Safiyya tace."Kada ki damu Mama zamu shigo da wuri kuma ba zamu nuna farin cikin mu ba zamu nuna tsantsar damuwar mu dangane da faruwar al'amarin." Uwar gida tace"To shikkenan sai kun......shigowar Maimartaba dakin yasa ta kasa karasa maganar kashe wayar tayi ta ajiye kusa da ita tana masa barka da shigowa.

Guri ya samu ya zauna a nutse yace."Dawa kike waya da daddare haka."? Tace."Wallahi Safiyya ce ta kira ni yanzu take sheda min cewa na nema mata alfarma a gurinka wai tana so ta 'kara jari akan wanda take juyawa gashi tana jin kunyar Tambayarka kudi."

Murmushi yayi yace."Da alama basu san abinda yake faruwa ba a masarauta ba." Da sauri tace."Me yake faruwa ranka ya dad'e."? yanda ta nuna damuwarta sai ka rantse da Allah bata san komai ba.

Maimartaba cikin nutsuwa ya sheda mata dukkanin abinda yake faruwa, fashewa tayi da kuka ta ri'ke kanta tana fad'in "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'una! wannan yaro yana ganin tashin hankali wai shin me Aliyu yayi wa mutane ne suke nema suga bayansa."

Maimartaba tace."Wallahi ni kaina na rasa abinda yasa mutane suke nuna masa 'kiyayya al'amarin yana bani mamaki mutuka! ada ina zargin daga waje al'amarin ya fito sai da na zauna nayi tunani sosai na gane cewa a kwai saka hannun wasu daga cikin masaurata.".


Tana kuka da fyatar majina tace"Allah ya taimake ka shin kai wa kake zargi da aikata wannan aikin dukkaninku cibiyarku d'aya ashe akwai wanda zai iya neman ran d'an uwansa."

Maimartaba yayi murmushi mai ciwo yace."Hulaiwa baki san mulki ba har yanzu mutane na iya aikata komai akan mulki na lura da tun sanda na fara kiransa da Magajin sarki fuskokin wasu daga cikin makusanta na ya nuna b'acin rai ni ban kira Aliyu da Magajina ba wai dan ya gaji kujerata Ali sunan surikina ne wato mahaifin Fulani ke kin sani itama ta sani wannan dalilin yasa nake kiransa da wannan suna na Magajin sarki."!

Uwar gida girgiza kanta ta shagayi kafin ta sauke ajiyar zuciya tace"Babu shakka mutum daya ne zai iya aikata wannan rashin imanin ba kowa bane sai Waziri shine makusancin ka wanda kafi aminta dashi shine kuma zai cutar da kai da zuriar ka Waziri bai ta'ba haihuwa ba tsayin shekarunsa wannan dalilin zai sa ya aikata mugun abu akan 'ya'yan 'yan uwansa sabida yana ba'kin cikin shi Allah be bashi haihuwa ba......

Cikin wani irin yanayi Maimartaba yake kallonta yana mamakin maganarta akan d'an uwansa mafi kusanci dashi wato Waziri." Ganin ya nuna alamun alhini yasa tace"Nasan dole za kayi mamakin maganata ranka ya dade kada kayi mamaki halin dan adam wallahi ko shakka ba nayi Waziri zai iya kashe Yarima saboda wannan dalilin dana fad'a maka.".

Maimartaba girgiza kansa yayi cikin yanayi na damuwa yace."Huwaila kada ki sake wannan maganar zargi bashi da kyau Waziri yana da kyawun zuciya na yarda ba zai cutar dani da zuria ta ba idan da wa'inda ya kamata a d'ora zargi a kansu to Ciroma da Galadima ne domin sune suka fito da hassadar su a kaina kada fa ki manta gwagwarmayar da nasha dasu a lokacin da Allah ya bani mulki nasha wahalarsu kafin su rabu dani nayi mulki cikin nutsuwa, Waziri kuwa tunda muke dashi bai ta'ba nuna min hassadar sa ba yana kaunata yana kuma kaunar zuria ta wannan al'amarin da ya faru yafi kowa damuwa bana zargin akwai saka hannun Waziri dangane da faruwar al'marin."

Huwaila shuru tayi bata sake tofawa ba, ta dauka mijin nata zai dauki maganarta babban burinta ta raba zumuncin dake tsakaninsa da dan uwansa Waziri saboda ta fahimci cewa Wazirin kamar shi yake hana Maimartaba ya kula da 'ya'yansa tunda ta lura da irin kaunar da yake wa Magajin sarki gabadaya taji ta tsane shi dan ita duk wanda zai kaunaci Fulani da d'anta to bata kaunarsa.


Magajin Sarki tare da Acp Mahmud a station, cikin nutsuwa suka gaisa da juna Acp yace.''Ranka ya dade ya kuma ji da faruwar wannan al'amari."? Ajiyar zuciya ya sauke yace.'' Sai godiyar Allah.'' Acp yace."Ranka ya dad'e wannan al'amari daya faru yayi mutukar girgiza mu mun shiga alhini da damuwa dangane da faruwar al'amarin dalili kuwa shine wannan asibitin naka asibiti ne mai mutukar muhimmanci a gurin al'ummar dake cikin wannan jaha mai albarka duka-duka asibitin bai kai rabin shekara da kafuwa ba amma ya kawo mana cigaban da bamu ta'ba tsammani ba, sai dai mace-macen da ake samu a asibitin yasa dukkaninmu jikin mu yayi sanyi dayawa daga cikin mutanan dake kwad'ayin zuwa asibitin domin a duba lafiyarsu tabbas nasan zasu tsorata su janye jikinsu domin tsira da ransu, ranka ya dad'e muna so kayi mana cikakken bayani akan dalilin daya sa ake samun wannan matsala a cikin asibitin ka." Acp ya 'kare maganarsa yana kallonsa.

Dago kanshi yayi da niyyar magana, dan jaridar dake tsaye ya matsa kusa dashi yana gyara masa abin magana, shi kuma Acp ya gyara biron hannunsa....Yana fara maganar ya fara rubutawa a jikin takardar dake gabanshi............A nuste yace."Acp Mahmud wannan al'amarin da yake ta faruwa sai nace maka family issue ina nufin abinda ya shafi cikin gidanmu . wannan al'amarin tunda na diro duniya yake faruwa dani bazan 'boye maka ba kuma bazan 'boyewa media ba al'amarin nan daga cikin gidanmu na sarauta yake fitowa, Acp a rayuwa ta banta'ba nufin wani da sharri ba amma ni kullum cikin 'kokarin so a ga bayana ake abin na damuna mutuka gaya."

Acp ya girgiza kanshi a nutse yace."Ranka ya dad'e Allah ya kare ka daga sharrin abinqi.'' Ya amsa da ameen yana goge gumin dake goshinsa.....Acp yay rubutu jikin takardar ya d'ago a nutse yace."Ranka ya dad'e afuwa shin ya akayi kasan abincin ka na dauke da guba mai karfi ka bawa hadimanka suka ci muna so muji yanda akayi haka ta faru."

Murmushi yayi ya girgiza kansa yace."Acp kasan Allah ban san abincin nan na dauke da mugun abu ba, yanda al'amarin ya faru shine........Na sauko cikin shiri domin zuwa gurin aiki na samu Amintacciyar hadimata tana aikace-aikace muka gaisa da juna nan take sheda min cewa ta kammala breakfast lokacin na duba time naga idan na tsaya break zan 'bata lokaci dalili kuwa shine akwai marasa lafiyan da zan duba sai nace ta bari kawai bana bukata, ta biyo ni da magana akan na daure naci abinci saboda yanayin aikina....still na sake duba agogon hannuna na kalleta naga ta nuna yanayi na damuwa, nace ba zan tsaya ba amma ta had'a abincin ta bayar a kawo min ofis. da wannan na fita na barta a sashen nawa. ina zuwa ofis na samu coffee nasha na cigaba da gudanar da aikina misalin sha biyu shaura na rana sai ga Hadimi na Haruna marigayi ya shigo ofis d'ina da kayan abinci a hannunsa, muka gaisa yake sheda min abunda yake tafe dashi, time na duba naga idan naci abinci a lokacin zan samu matsala kai tsaye nace ya koma dashi bana bukata idan kuma yana so to ya samu wani ya taya shi ci." daga wannan magana sai na sallameshi na cigaba da aikina. to daf da zan tashi d'aya daga cikin masu kula da hospital din yaga gawarwarkin wad'annan bayin Allah a can gurin shukoki a guje yazo yana sheda mana abinda ke faruwa, Acp wannan shine cikakken bayanin da zan iya yi maka dangane da faruwar wannan al'amari.

Acp Mahmud girigza kanshi yay yayi rubuce rubuce a jikin takardar kafin ya d'ago kansa yana kallonsa Yace.'' Ranka ya d'ade tilas mu aika yanzu yanzu azo da wannan yarinyar domin alamu na nuna mana cewa akwai sa hannunta a cikin faruwar wannan al'amari."
Kallonsa yayi yana girgiza kansa yace."Acp ba wai zanyi maka katsalandan a cikin aikin ba amma kasan Allah yarinyar nan ta gari ce, ni zan bada shaida a kanta ba zata ta'ba yarda a had'a baki da ita a kashe ni ba, ni nasan ta ciki da waje nasan wacece ita Sumayya ba zata iya kashe kishayi ba ballanatana mutum mai rai."

Acp yayi murmushi yana kallonsa a nutse yace."Ranka ya dade kai da kanka kace itace ta girka abincin nan to amma me yasa kake 'kokarin kare ta."? Girgiza kansa yayi yay shuru yana kallon kasan gurun....Acp yace."Kayi hakuri ba zamu yi mata komai ba kawai zamu tsoratar da ita ta fad'a mana gaskiyar lamari."

Ajiyar zuciya ya sauke yace."Okey to babu damuwa." Acp ya dauki waya ya kira daya daga cikin ma'aikata, ya shigo sanye da kayan aiki qamewa yayi yana miqa gaisuwarsa, Acp yace."Kuje da Merry gidan Sarki zaku dauko wannan yarinyar Sumayya zamuyi binkice akanta." qamewa yayi da fadin"Okey sir.'' da sauri ya juya ya fita...........





*Na kudi ne!*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
82
"Dan Allah kar kaqara." nafada ina sake janye jikina. Lumshe idonsa yayi ya bude a take na sunkuyar da kaina gabana na wani irin faduwa ganin yanda lokaci guda idanunsa suka jirkice."
"Idan bakya so na ta'ba ki to tashi muje mu kwanta." Hannuwana nasa na rufe kirjina hawaye na zubo min nace"Nifa ba zan yarda na kwanta daki d'aya da kai ba tunda dai kai ba muharrami na bane." Tsira min ido yayi babu yabo babu fallasa yace."Nace dake babu abinda zan miki kin tsaya taurin kai ko tom zaki janyo na kwanta a kanki yanzu."

Kallonsa nayi ina girgiza kaina hawaye na sake zubo min, ni dai ban san da wane nataccan mutum Allah ya had'ani ba."


''Ki daina zubar min hawaye bakya gajiya da kuka Sumayya kina dani bai kamata ki dinga zubar da hawaye ba."

Cikin zuciyata nace "Zubar da hawaye dole ne tunda Allah yasa ka sauka kasar nan nake kuka har yanzu na kasa samun sassauci."


A zahiri kuwa shuru nayi ina kallonsa tare da kare kirjina da hannuwana, murmushi yay ya kawo hannu zai ta'ba ni zabura nayi da sauri na matsa ina girgixa masa kaina.

Dariya yasa yana kallona, na dinga watsa masa harara hawaye na zubo min, matsowa ya sakeyi sai kawai na mike da sauri zan bar gurin.

'kuguna ya ri'ko kawai ya janyo ni na zauna a cinyarsa, kansa ya d'ora a kafadata, naji ya sauke zazzafar ajiyar zuciya, hucin numfashinsa ne yake nema ya kassara ni! kafad'ata na gotar ya sake mayar da kansa yana shanshana wuya na, kafin nayi wani yun'kuri naji yana sumbatar wuyana sai goga fuskarsa yake a gurin, cikin tashin hankali nace"Dan Allah ka bari na yarda zan bika dakin."

Shuru yayi yana cigaba da abinda yake, gabad'aya jikina ya mutu kasala duk ta baibayeni tuntuni hawaye ya daina fita tsoro da fargaba duk sun dabaibaye ni.


Hannuwansa yake kokarin 'dorawa a kirjina na rike katamau! muryana na rawa nace"Ka bari."!!! Girgiza kansa yayi a kasalance yace."Ki bari na ragewa kaina damuwa." cikin takaici nace"Ranka ya dade wani lokacin kaine kake janyowa ina maka abinda be dace ba yanzu dan Allah meye amfanin wannan iskancin da kake min."! a kufule nake maganar.

girgiza kansa yayi saitin kunnena yace."Ni ba d'an iska bane.'' fuzgewa nayi na mike ina kallonsa dik ya koma wata kala nace"To idan ba d'an iska bane menene kawai ka matseni a jikinka kana wani abu."

Hannu ya miko min da fadin "Zo my love ina cikin mayen sonki." Naji kamar na kwad'a masa mari! girgiza kaina nayi nace"Ba sona kake ba dan inda kana sona ba zakayi kokarin yin wani abu dani ba har sai na zama mallakinka." Hannu ya miko zai rike nawa na kauce! ina watsa masa harara, mikewa yayi tsaye, abinda nagani yasa ni saurin kautar da kaina, gabansa ya mi'ke sosai har ya nuna ta gaban rigarsa, gabana na faduwa nayi yun'kurin barin gurin, hannuna ya rike ya juyo da fuskata yana kallona, na dinga kauda kaina dan bana so naga abinda yake firgitani!


"Sumayya." sunana ya kira can cikin ma'koshi!! kasa amsawa nayi gabana sai faduwa yake yace."Kinga abinda kika janyo min ko."? k'in kallonsa nayi kawai naji ya dauki hannuna ya d'ora a gurin, ihu! mai karfi na kurma! na tunkud'eshi ya fadi saman kujera! fita nayi daga tsakanin kujerun na dinga nuna shi da hannu ina girgiza kaina, ganin ya yun'kura zai mike yasa a guje na bude kofar kicin na shiga na kulle ina haki! da kiran sunan Allah!

Yarima a jigace! ya haura sama ya zube kan bed yana jan numfashi, hannu ya dora saman joystick d'inshi tana nan a mike tana harbawa, a raunane yace."Kaico! kaicon ki da kai kanki inda bai dace ba! kaicon ki da sha'awar abinda ke karkashin ki!!! jijjigata yayi yaji kamar ya murd'eta ya huta da takaici! mikewa yayi zaune yasa hannu ya dafe goshinsa zufa ce kawai take keto masa, idanu yasa kan agogon dake kan bedside Uku shaura na dare, mikewa yayi yana rangaji ya shiga toilet ruwan sanyi ya dinga kuzawa kansa yana kiran sunan Allah a zuciyarsa.


Jingina nayi jikin kofar na dinga wani irin kuka abubuwa biyu sun dame ni Mutuwar Haruna ta tsaya min a rai! sai kuma masifar wannan taqadirin da Allah ya jarrabeni dashi hakika da ina da inda zanje bayan masarautar nan to dana gudu na huta da masifar wannan bawan Allah.


Zamewa nayi na zauna kasan ties had'a kaina nayi da gwiwa ina takure jikina sosai nake addua a zuciyata akan Allah ya kawo min mafita.


Tsakanin Magajin sarki da Sumayya babu wanda ya rintsa yanda suka ga rana haka suka dare!


Asubah nayi na bude kicin din na fito, lokacin yana kokarin saukowa ko kallonsa banyi ba na karasa bakin kofa, hannu nasa naji ta a rufe gefe na matsa sakamakon karasowarsa gurin
Daf dani ya tsaya yana sanye da jallabiya ash color sai kamshin turare yake, na dauka zai min magana sai naga shima ya dauke kansa, kofar ya bude ya fita, da sauri nabi bayansa.........Hadimansa na ganin fitowarsa suka karaso gurin ganina yasa sukayi sak!! yace."Sumayya ta kwana a sashena dalili jiya ni da ita bamu shigo da wuri ba sai bayan sha biyu na dare wannan dalilin yasa na hanata tafiya sashensu." yafadi hakane domin kada su zargi wani abu.

Sunkuyar da kansu sukayi suna masa barka da fitowa, gaba yayi ba tare daya amsa musu ba da sauri suka rufa masa baya domin shiga massalaci.


Ina kokarin shiga gurin mu babana ya fito daure da alwala, ganina yasa ya zube a gurin yana godewa Allah! mikewa yayi ya rike hannuna cikin murna yace."Sumayya ina fata ba suyi miki komai ba."? Nace"Ba suyi min komai ba baba amma dai basu gama binkicensu ba." A sanyaye yace."Ni da mahaifiyar ki bamu rintsa ba saboda fargaba kwana mukayi muna addua akan Allah ubangiji ya kubutar dake." Hawaye na share ina jin tausayinsu na ratsa ni nace."Baba insha Allahu Gaskiya tana tare da mai gaskiya in Allah ya yarda Allah zai wanke ni." ya amsa da ameeen da fadin" Ki shiga ciki mahaifiyarki ta ganki ko hankalinta ya kwanta." Da sauri nace"To baba." Lawi sai da yaga shigewarta cikin gidan sannan ya nufi massalaci domin gabatar da sallar asubahi.


Tambaya rungume ni tayi ta dinga kuka da kyar na rarrasheta tayi shuru ta dinga duba jikina wai ko sun dake ni. nace"Tambaya ki kwantar da hankalin ki babu abunda akeyi min sai tambayoyi."

A jiyar zuciya ta sauke tace."Sumayya jiya na shiga tashin hankali da damuwa sakamakon zuwan 'yan sanda da tafiyarki na dinga addua ina rokon Allah akan kada ya basu dama su cutar dake ina jin tsoron kada wani mara imanin ya keta miki alfarmarki."


Girgiza kaina nayi nace"Tambaya Allah ya kare ni kuma zai cigaba da bani kariya albarkacin adduarku insha Allahu wani mummunan abu ba zai faru dani ba."
Zazzafar ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da kallona kai kana ganinta zaka san tana cikin tashin hankali mai tsanani, sai da na tabbatar hankalinta ya kwanta tukkuna naje na dauro alwala, na dawo kuryar dakin na shiga nasa hijabi kana na tsaya kan dadduma a nutse na tayar da sallah.

Ganinsa a massalacin yasa jikin Ciroma da mu'karrabansa yayi sanyi ikon Allah yaushe ya dawo gidan? kai amma ba suji dadin ganinsa ba. Maimartaba da Waziri kuwa babu wanda ya kaisu farin cikin ganinsa ko bayan da'aka idar

Please Login or Register in order to submit comment