Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

'kwarai kuwa mutukar gurin daukar cikinsu da haihuwarsu na barazana da rayuwarki to gwara ki hakura.'' cikin takaici nace" Mace koda haihuwa ko babu haihuwa sai ta mutu! kuma inaso kasani duk macan data mutu gurin haihuwa tayi shahada saboda haka ka daina wannan maganar dik wata wahala mai shigewa ce iyayenmu da kakannin mu a haka duk suka tara 'ya'yansu dan haka dan Allah ka daina wannan maganar sam bata dace ba su 'ya'ya rahama ne sannan kuma a ranar lahira Annabi Muhammad (SAW) zaiyi alfahiri da jama'arsa.........




*Na kudi ne.*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya ni! Keda da kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300....account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
91
Har yanzu fuskarsa babu sassauci yace."Nasan da haka ba sai kinyi min wa'azi ba a tsarina ni bana son tarin 'ya'ya da yawa bayan haka kuma ita haihuwar wahala gareta mutanan da dana yanzu ba daya bane nada sunfi kwari da karko na yanzu kuwa haihuwa daya biyu sun lalace shiyasa bana son ki haihu da yawa." Murmushin takaici nayi nace"Ni kam wannan magana ta isheni wallahi duk yanda nake so na fahimtar dake yanda al'amarin yake ba zaka fahinta ba saboda haka mu bar maganar iya adadin 'ya'yan da zan haifa a duniya Allah ne kadai yasan yawan su."

Shuru yayi yana kallona, babu alamun nadama a fuskarsa na dinga mamakin halinsa bashi da rufi ko kadan duk abinda yake zuciyarsa fada yake yi kansa tsaye in banda abinsa waye yake gudun rahama ai 'ya'ya rahama ne amma shi tun kafin ma yayi auran ya yankewa kansa hukunci Allah dai yasa kada zama da turawa yasa ya dauki munanan dabi'unsa dan gashi alamu nan."

Kaina na sunkuyar ganin yana kure ni da kallo nace"Ka tafi gurinka dan Allah ko da akwai abinda kake bukata."

Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ina bukatar abubuwa guda uku amma nasan da wuya na samu duka.


Kallonsa nayi ya daga min kai da fadin"farko dai ina bukatar naji ki a jikina na biyu ina bukatar abinci na uku kuma nayi wanka."


'Bata fuska nayi nace"Tashi muje falo na baka abincin." girgiza kansa yayi yace."Kije ki kawo min nan ni babu wani falo da zanje." na jima ina kallonsa kafin nayi yun'kurin mikewa sai na tuna da kayan dake jikina da sauri na koma na zauna gabana na faduwa.

Bargon dake jikina yake kokarin janyewa na rike da kyau ina girgiza masa kaina nace"Dan Allah dauko min hijabina gashi can akan kujera.


Cike da mamaki yace."Lallai kin raina ni zaki aika."? girgiza kaina nayi yace."Dallah tashi ni ki kawo min abinci me zaki boye min bayan komai nawa ne."

Idona ne ya kawo ruwa nace"Ni dai dan Allah ka miko min hijabin wallahi kayan masu fitar da tsaraici ne." kallona ya shigayi yana girgiza kai yace."Tsaraici.''? kaina na sunkuyar ina sake rufe jikina da bargon, mikewa tsaye yayi kawai yasa hannu da karfi ya fizge bargon daga jikina, tsigar jikina ta mike da sauri na takure jikina guri guda ina watsa masa harara!

Wani irin kallo yake bina dashi tun ba kirjina ba nasa hannu ina karewa, ajiyar zuciya ya sauke a hard'e yace."Tashi." 'kin tashi nayi na takure jikina hawayen bakin ciki na nema ya kufce min......"Kin san Allah idan baki tashi ba zan aikata miki abinda bakya so yanzu." jin abinda yace yasa da sauri na kalleshi, gani nayi idanunsa ya sauya, gabana na faduwa na mike, ya bini da wani irin kallo da hannu ya nuna min k'ofar fita, ina takure jikina na kama hanyar fita a jikina naji kallona yake shiyasa da saurin gaske na bude kofa na fita.......a gurguje nake hada masa abincin kawai naji motsinsa a bayana, da sauri na juyo kirjina da nasa ya had'u hannuwansa duka ya d'ora akan mazaunaina! ya wani matseni a kirjinsa yana matsa min mazaunai! kirjinsa na doka da karfi! tsaki naja da sauri na janye jikina, bina yake da kallo kamar maye, nayi gaggawar daukar tire din dana shirya masa abincin na barshi a tsaye a gurin.

Ina ajiye tire din na dauki dogon hijabina nasa na zauna kan kujera gabadaya raina ya 'baci da irin abinda yake min.

Koda ya shigo dakin be kalli inda nake ba, yaje ya zauna gaban abincin a nutse ya zuba abinsa ya fara ci, sai da ya kammala tsaf ya tashi ya nufi toilet........jin shuru bai fito ba yasa na shiga tunanin abinda yake a ciki, motsinsa naji nayi saurin kallon kofar toilet din daga shi sai gajeran wando da vest jikinsa ya nuna alamun ruwa wanka yayi, kallonsa nake har ya isa kan gadona ya kwanta hankalinsa kwance ya rufe jikinsa da bargona.......Nace"Bangane ba." shuru yayi min.......nace"kasan bai dace ba ko dan Allah ka tashi ka tafi gurina hakan bai dace ba."

"Sumayya bazan tafi ba yau anan nayi niyyar kwanciya idan kuma kina da karfi kizo ki fitar dani." nace"Wacece ni ranka ya dade Allah ya baka hakuri." mikewa nayi na kama hanyar fita gwara na bar masa dakin akan mu kwana tare nasan halinsa zai iya haike min.

Kawai na ganshi a gabana ido jawur na kalleshi! bai tanka min ba ya murza key a jikin kofar ya zare keyi din ya barni a tsaye!

Hawayen takaici suka zubo min, a gaskiya lamarinsa akwai wuyar sha'ani! juyawa nayi naga ya koma ya kwanta tare da lullube jikinsa da bargo.


Jiki a sanyaye naje na kwanta kan sofa ina kudindine jikina da hijabina, miryarsa naji ciki ciki yace."Ki zo ki kwanta ba zanyi miki wani abuba."

Share shi nayi ina jin wani irin haushinsa a raina, magana yake min nayi masa banza daya gaji sai yayi shuru can kuma na dinga jin saukar numfashinsa a hankali nan na gane bacci ya daukeshi, a hankali na gyara kwanciyata ina addua a cikin zuciyata.


Da asubah kusan a tare muka tashi dan ina jin motsin shigarsa toilet na bude ido, zaune na mike ina salati can naji kira ya shigo wayarsa, a nutse na mike na iske inda wayar take, lokacin kiran ya katse wani ya shigo, ina kokarin daukar wayar ya fito daga toilet din jikinsa sanye da kayansa na jiya daya cire da alwala a tare dashi, a nutse na mika masa wayar na nufi toilet domin daura alwala, koda na fito samunsa nayi zaune a gefan gado ya rufe fuskarsa da tafukan hannayensa, gabana ya fadi! da sauri na karasa kusa dashi tare da fadin"Lafiya."?


Fuskarsa ya bude yana kallona da jajeyen idanunsa yace."Sumayya daya daga cikin matan da nayi wa operation ce ta mutu misalin uku da rabi na dare.

Kafafuna suka shiga kyarma zama nayi kusa dashi ina kiran innalilihi wa'ina ilahi raji'un."!!!! dakin yayi shuru na minti uku kafin ya sauke zazzafar ajiyar zuciya ya kalleni, hawaye na share nace"Ubangiji Allah ya jikanta Allah yasa aljanna makomarta."


Ya amsa da "ameeen ya rabbi Jiya fa lafiya lau aka fito da jaririn kafin na fito daga hospital din sai da na tabbatar da komai yayi normal sannan! ashe bayan tafiya da minti arba'in jini ya tsinke mata kafin ayi wani yunkiri ta mutu ta bar jaririnta." murya na rawa ya karasa maganar......Nace"ikon Allah kenan! kaga ita waccar matar yaron ne ya mutu ita tana raye! wannan kuma gashi ta mutu ta bar yaron Allah babu yanda baya tsara lamarinsa, dama haka rayuwar duniya take Allah Ubangiji yasa mu cika da imani." Babu kuzari a tare dashi ya amsa da ameeen ya rabbi! mikewa yayi da fadin"Bari naje masjid." A sanyaye na bishi da kallo har ya fita daga dakin.

Ina kokarin nad'e daddumar da nayi sallah ya shigo dakin, kallo na bishi dashi ina mamakin abinda ya shigo dashi, na dauka ai ba zai dawo ba, yanayin fuskarsa ya nuna cewar lallai akwai magana a tare dashi.

Zama yayi kan gado da fadin"Zo Sumayya." a nutse naje na zauna gefansa, ya jima yana kallona kafin yace." Bana so ni dake muyi aure a bebai yana da kyau tun kafin zaman aure ya had'amu ki san abinda nake so da wanda bana so a tsarina mace d'aya ta isheni sai dai nasan hakan ba zai yuwu ba sannan bani da ra'ayin tara 'ya'ya koda matan aurena zasu kasance hud'u to na riga na tsara rayuwata bance kowace mace dole sai ta haihu dani ba! yara biyu zuwa uku sun isheni rayuwar duniya Sumayya ina da tausayi mutuka wanda shine dalilin daya sa kwata-kwata naji haihuwa bata burgeni saboda irin wahalar da mata kesha kafin suyi bana so duk haihuwa ya kasance sai kinsha wuya kin galabaita saboda haka na zaunar dake na fada miki tsarina itama Lawisa zan zauna da ita a yau na fad'a mata ra'ayina ina fata zakiyi wa maganata kyakkyawar fahimta.


Cikin wani irin yanayi na alhini da damuwa nake kallonsa, tsabar mamakin maganarsa ma ya hanani cewa komai baya son haihuwa ya riga ya tsarawa kansa rayuwa wannan wane irin bayahudan mutum Allah ya had'ani dashi, dauke kaina nayi kawai ina girgiza kaina!

Ya juyo da fuskata muna fuskantar juna yace."Banji kice wani abuba." Murmushin takaici nayi nace"Ai ni maganar taka ce tayi min nauyi shiyasa kawai nayi shiru ina auna maganar."


Yace."Wane irin kina auna maganar okey to ina sauraranki naji a wane ma'auni kika ajiyeta." yakarasa maganar tare da tsare ni da ido.

Kallonsa nayi babu wasa a tare dani nace"Ni dai nasan musulma ce gaba da baya kuma nasan addini daidai gwargwado to a matsayina na musulma wacce ta kadaita Allah shi kad'ai ban isa na tsarawa kaina rayuwar da nake so ba koda zan haifi 'ya'ya dubu a duniya to ba zan ta'ba butulcewa Allah ba.'''


"Bangane inda maganar ki ta dosa ba." fuska a murtuke yayi maganar, Nace"Ina nufin ban yarda da wannan tsarin naka ba ban sani ba ko ita Lawisan.......Mik'ewa tsaye yayi a zafafe! ya nuna ni da hannu yace."Ke ki shiga nutsuwarki fa ko dan kinga ina bibbiyar lamarinki kada ki manta da manufar da zan aureki kawai hallacin ki a kaina yasa na janye mummunan kudirina akanki! yanzu nazo ina fad'a miki ra'ayi kina wata magana kin san dai ke baki isa ki ruguza min tsari ba ko."?

Kallonsa nayi naga sai wani huci! yake nace"Allah ya huci! zuciyarka ni bana munafurci shiyasa tun kafin tafiya tayi nisa na fad'a maka nawa tsarin saboda haka kaine zaka zauna ka nemawa kanka mafita."


Ya jima yana kallona kafin yaja tsaki mai karfi ya kama hanyar fita daga dakin, kallo na bishi dashi ya bude kofar dakin a fusace! ya fita.

Ajiyar zuciya na sauke na tallafe ha'bata gabana na faduwa da wannan gagarimar matsalar da take kokarin kunno mana Magajin sarki baya son haihuwa saboda wasu banzayen hojjojinsa marasa tushe da maka wanda ni kuma nake ganin duk abinda za'ayi sai dai ayi amma ba zan bi hanyar da yake kokarin d'ora ni a kai ba wallahi bazan 'kayyadewa kaina haihuwa ba sai na haifi iya adadin 'ya'yan da Allah ya hukunta."

A nutse na fito falo cikin kwalliya kamar koda yaushe kuma ko alama ban bar wani 'bacin rai a fuskata ba wanda zai sa ta fahimci wani abu, muka gaisa cikin mutunci da kulawa kafin ma fara karyawa kamar yanda muka saba............Falon ya shigo tsaf dashi cikin shirin fita, kamshin turaransa duk ya cika mana hanci, amma fuskarsa kawai ta isa ta nuna maka cewa yana cikin 'bacin rai! dauke kaina nayi har ya karaso inda muke ya zauna gaban mahaifiyarsa yana gaisheta.


Ta amsa cikin kulawa da fadin"Babana jiya ai gajiya mukayi da jiranka muka kwanta ina fata dai anyi aiki cikin nasara." ?

Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma sai hakuri wallahi jiya ban shigo ba sai can dare koda na shigo kai tsaye sashena na nufa saboda nasan kunyi bacci." kallonsa nayi ina mamakin 'karyar dayayi, ya cigaba da cewa."Alhamdulillahi lafiya lau muka gudanar da aikin mu sai dai bayan dawowata gida d'aya ta amsa kiran ubangiji ta mutu ta bar yaron ita kuma dayar yaron ne ya rasu amma yanzu haka tana cikin koshin lafiya."


Girgiza kanta ta shiga yi cikin alhini da damuwa tace"Ya Allah kaji k'an musulmi Ai tayi shahada babana duk matar data mutu gurin haihuwa Allah yace."Aljanna ce makomarta sai dai muyi fatan samun baiwa irin tata." Kallonta yayi yana girgiza kansa yace."Hakane Mamma Allah kasa mu cika da imani." Ta amsa da ''ameeen ya rabbi."' Kallonsa nayi a nutse nace"Barka da asubah."

"Barka dai." ya amsa a takaice! Kokarin mi'kewa yake tace"A'a ba zaka tsaya kayo break fast ba."? girgiza kansa yayi yana duba agogon hannunsa yace."Mamma gabad'aya bani da kuzari wallahi cikina ya cushe bana sha'awar komai a yanzu mybe idan naje ofis na samu Coffee nasha ya isa." Tace"Babana bana so kana zama da yunwa kada fa ka manta kune kuke hanamu zama da yunwa to me yasa kuma kake karya doka."?

'Yar dariya yayi yace."Mamma kada ki damu insha Allah idan naje ofis zan samu wani abu naci yanzu babu lokaci dana zauna nayi break din.".

Tace."A ina zaka samu abu kaci kawai dai ka fad'a ne! bari kawai Sumayya ta had'a maka snaks ka tafi dashi." yace."To Mamma." Tace."Sumayya ki duba dakina akwai snakas cikin firji sai kisa masa a leda yanda zai isheshi." nace."To ranki ya dade." A nutse na mike na nufi dakin nata...........Suna hira na fito na same su, na mika masa ledar kar'ba yayi ba tare daya kalleni ba, na koma inda nake ina kallonsa da mamakin abinda yake min.....sallama naji sunayi da sauri nace"Ranka ya dade Allah ya tsare ya kiyaye gabanka da bayanka." a dakile ya amsa min." hakan besa ta gane akwai matsala a tsakanina dashi ba tunda sau tari haka yake amsa min magana a ciki shiyasa bata fahimci komai ba, nima nayi saurin korar 'bacin raina na fuskanceta sosai muka cigaba da hira cikin mutunci da mutunta juna.




Haka muka kasance da juna tsakanina dashi babu yabo babu fallasa dan duk wannan shige min da yake ya daina watarana ma idan ya dawo daga asibiti baya nema na nice nake fitowa nayi masa barka da zuwa! ko kadan ban damu da wulakancin da yake min ba saboda na riga nasan ni nake da gaskiya a duk inda zamuje shiyasa fushinsa sam be daga min hankali ba...............Yau saura kwana biyu daurin aure gabadaya masarautar ta hargitse sai abubuwa akeyi irin na al'ada Mamma ta mayar da hankalinta sosai gurin gyarani da ingantattun magungunan matan da take sawa a kawo mata, kullum sai bani wani turere na tsuguna akai haya'kin na ratsa a jikina, ni da kaina na tabbatar ingancin turaran dan ba headquarter na kawai ke kamshi ba gabadaya jikina ne ke kamshi duk inda na gifta kamshi na mussaman ne ke tashi............Jakadiya ce ta zauna tayi min 'kananun kitso irin na bare bari da yake ina da tsayin gashi yasa tufkar kitson ta kwanta gefe da gefen fuskata, ana ya gobe daurin aure da sassafe ta shigo dakina da kayan lalle(kunshi) haka na zauna tasa min salatif a kafafuna da hannayena kana tasa lalle akai tasa leda ta d'aure! ta gyara gurin, zama tayi kusa dani tana d'ebe min kewa, sai da mukayi zaman awa hudu da rabi tukkuna ta cire min lallan, na dinga bin kafafuna da kallo ina murmushin farin ciki tunda nake banta'ba adon lallai irin wannan ba Lallai jakadiya tana da zane sosai yanda ta fitar da zanan kunshi ragadau ya dinga burge ni gashi yayi wani irin jajawur, hannuwana na kalla nace"Jakadiya kinga kamar na hannun ya fi fitowa." tace"Eh ai da yake shi aka fara cirewa shiyasa yasha iska ne." murmushi nayi ina kallonta ta shiga turare min kafafuna da wani turere data zuba a cikin wani dan madaidaicin kaskon wuta.



'Bangaran Lawisa ma shiri suke sosai ita da mahaifiyarta Hajiya Karima ta tashi a tsaye tasa Lawisa sai bankar magunguna take lallai sai tafi Sumayya ni'ima a gurin miji! duk wani gyara da ake bukatar amare suyi a lokacin auransu kowacce tayi nata daidai gwargwado yayinda shi kuma angon nasu yayi musu bajintar kayan lefe kowacce akwati goma sha biyu cike da kayan amfani sannan kuma yasa an gyarawa kowacce sashen da zata zauna a gidan, dan bashi da ra'ayi had'asu a guri guda, duk abinda kowacce zata bukata tana dashi a sashenta.

*RANAR DAURIN AURE*
Masarautar ta cika da jama'a manyan mutane attajirai masu mulki malamai da sauran jama'ar gari kowa ya samu halatar daurin auran *Yarima Ali Abdul-aziz* inda wakilai suka sheda daurin auran kowacce akan sadaki dubu dari - dari bayan kammaluwar daurin auren sai masarautar ta hargitse da bushe-bushe gami da wassanin al'ada Ango yayi shirin hawa kilasa domin nuna murnarsa da Allah ya nuna masa zuwan wannan rana mai albarka.......Har dare ana abu d'aya a masarautar wassani iri-iri aka dinga gudanarwa, Sai da Ango ya shiga gida tukkuna kowa ya watse wa'inda suke masarautar suka nufi gurinsa wa'inda kuma suka shigo domin taya murya suka dinga fita jama'a kamar ranar idi! babu shakka jama'ar gari sunyiwa masarauta kara sun nunawa Sarki Abdul-Aziz Abdullahi kauna shima yaji dadi sosai dan kafin taro ya watse sai da ya mika godiyarsa zuwa gare su..



*Na kudi ne...*
Kada ki karanta min littafi idan baki biya ba! keda kika fita da littafin keda Allah! idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300....account... 0542382124....Binta umar gtbank.....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannam number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
92
Tare suka shiga sashensa da Shatima, suka kimtsa jikinsu cikin kayan sarauta komai iri daya sukayi sosai sukayi kyau kana ganinsu kaga angwaye, da yake tare da Shatima aka daura auran shima amaryarsa 'Yar sarkin kazaure ce sun jima suna soyayya sai kawai iyaye suka zauna suka tattauna al'amarin lokaci guda akayi komai aka gama sai bayan da'aka daurawa Yarima aure da mata biyu tukkuna shi aka daura masa aure da tashi amaryar mai suna Mansura......koda suka fito kai tsaye sashen Waziri suka nufa sukaje suka gaisa dashi da iyalinsa sukayi musu bangajiya Waziri ya jima yana musu addua da fatan alkairi kafin su fito su nufi sashen Galadima shima iyalinsa duk suna nan sai hidima sukeyi, suka gaisa a tsanake Galadima yaji dadin ganinsu ya dinga farin ciki yana yi musu fatan alkairi, koda suka fito sai suka nufi sashen Ciroma yana zaune a kan kujera Hajiya Karima na kusa dashi sannan 'ya'yansa gabadaya sun kewaye shi suna magana, shigowarsu tasa dukkaninsu suka kalli bakin kofa......Ganinsu su biyu cikin kayan sarauta yasa wani bakin ciki ya lullu'besu da tuni harda Muddibo acikinsu Sunyi sanadiyar mutuwarsa sun kwantar da hankalinsu suna rayuwar jin dadi. Hajiya Karima ce ke wannan maganar cikin ranta, Ciroma kuwa b'acin ransa ya danne ya dinga murmushi yana amsa gaiswarsu tare dayi musu fatan alkairi Hajiya Karima kuwa lokacin da suke gaisheta kawar da kanta tayi sai da Wali yayi mata magana tukkuna ta amsa a ciki. gabadayansu basu ji dadin abinda mahaifiyarsu tayi ba har yanzu ta kasa 'boye 'bacin ranta gaban kowa nunawa take, suna fita Lawisa ta mike tabi bayansu, da sauri tace."Dan Allah ku tsaya." Magajin sarki da Shatima suka tsaya suna kallonta kamar wata mutuniyar arziki ta nufe su, Ya dinga kallonta yana mamakin kyawun da tayi tai ado sosai tayi kyau tamkar wata balarabiya lumshe idonsa yayi yana tunanin irin ni'imar da zai samu a tare da ita, ta tsaya kusa dashi kamshin turaranta ya bugi hancinsa bude idonsa yayi sosai yana kallonta, tace"Dan Allah kuyi hakuri da abinda hajiya tayi muku wallahi dukkaninmu bamu ji dadi ba."

Shatima yace." Haba babu komai wallahi kada ku damu Hajiya uwa ce komai tana iya yi mana mu hakura." Murmushi tayi tace"Nagode sosai.'' Shatima ya kalleshi sai yaga ya k'urawa k'asan gurin ido, yace.''Bari nayi gaba na bar amarya da ango su tattauna." da sauri ya dago kansa yana harararsa, Dariya yayi ya bar gurin, kokarin tafiya yake ta rike hannunsa, ya juyo yana kallonta cikin wani irin yanayi yace." Kina bukatar wani abune."? murmushi tayi tace.'"Babu abinda nake bukata sai angona hakika yau ina cikin murna da farin ciki da Allah ya tabbatar mana da alkawarin mu.'' shuru yayi yana kallonta a sanyaye tace" naga kana kallona ko dai kwalliyata ba tayi kyau ba."? tafada tana duba jikinta


Girgixa kansa yayi yace."Kinyi kyau sosai dalilin daya sa ma kenan na kasa dauke idona a kanki ." wani farin ciki ya ziyarce ta hannunsa ta damqe da fadin"Lallai tunda kana son ado zan diga yi maka mai kayatarwa." shima murmushin yayi yace.''Nagode amaryata anjima zan kira ki kizo ki taya ni hira." dadi ya sake rufeta lallai malamin da yake musu aiki gwani ne yau ita da Yarima ne suke hirar soyayya babu fada, fari tayi da ido tace"To shikkenan angona." hannunsa ya cire daga cikin nata ya bar gurin, kallon so da kauna tabi shi dashi har sai daya 'bace daga gurin sannan ta koma ciki cike da murna da farin ciki, kasa boye farin cikinta tayi ta shedawa mahaifiyarta sauyin da'aka samu Hajiya Karima ta dinga murna tana kara kuranta aikin malaminta.

Samun Shatima yayi a tsaye a wani guri yana jiransa saboda haka yana karasowa suka nufi sashen Uwar gida Huwaila da jakadiyarta suna magana shigowarsu yasa ta washe baki kamar mutuniyar kirki ta dinga tsokanarsu su kuwa sai sunkuyar da kai suke suna murmushi jakadiya ta gaishesu da sauri ta fita daga falon, suka zauna a nutse suna gaisheta, ta amsa cikin sakin fuska tace"Tun dazu 'Yan uwanku suke zaman jiran shigowarku ku gaisa suyi muku Allah ya sanya alkairi ganin dare yayi sosai yasa nace ko wacce ta tafi dakinta daga baya sai su dawo ku gaisa sosai! ta fadi hakane domin ta karesu gabad'ayansu ana gama daurin aure kowacce ta shiga motarta ta tafi a cewarsu ba zasu tsaya zuciyarsu ta buga a banza da wofi ba sun tsani suga mahaifinsu na nuna kulawa akan dan uwansu ba kuma sa kaunar wani alkairi ya same shi hassada suke masa sosai suna ganin kamar mahaifin nasu yafi kaunarsa saboda yana namiji.

Magajin sarki yace."Allah sarki aunt's d'ina banji dadi ba wallahi amma babu komai in Allah ya yarda duk zamu bi gidajensu daya bayan daya muyi musu bangajiya." Tana dariyar yake tace"Haka yayi kyau Tabbas zasuji dadi idan kuka ziyarcesu yana da

Please Login or Register in order to submit comment