Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mu barka ka shiga."


Muddibo ya dinga wani irin huci! yana zaginsu, gami da fad'in "Idan mai gurin ya dawo zai nuna musu muhimancinsa a gurinsa." a hankali nace"Ranka ya dade barka da yamma." ko kallona beyi ba ya bar gurin, Da sauri daya daga cikinsu ya bude min kofa da fadin"Maza shiga kiyi aikin ki ki rabu dashi." Da sauri na shige ina mamakin al'amarin, to me ya kawo Muddibo sashen Yarima bayan yasan baya nan? idan an bude masa ya shiga me zaiyi a ciki, ina ayyukana ina tunanin al'amarin, sai bayan magariba na gama aikina na fito lokacin sun fito daga gurin sallah bude min kofa sukayi na fita tare dayi musu bankwana,

Ganin gari yayi duhu yasa na kara sauri domin isa gurinmu kawai naji an tare ni!! gabana ya fadi ina dago kai muka hada ido dashi! ido jawur yake kallona cikin dauriya nace"Ranka ya dade kana bukatar wani abu ne."? Wawan mari! ya kwada min na fadi a gurin! tsaye na mike ina kallonsa hannuna dafe da kumatuna! wuya na ya shaqe na dinga kakari!! sai da ya galabaitar dani tukkuna ya sake ni! na sake faduwa a gurin! Ya tsuguna gabana yana kallona ina kallonsa makogwarona ya bushe kamas! Yace."Zan saki aiki a sashen Yarima wallahi tallahi idan kika kuskura kika ki aikatawa sai nabi dare da rana na kashe ki."!!!! Gabana ya dinga faduwa! ya cigaba da cewa'' Kin saba lalata mana aiki to wannan ce damarki ta karshe mutukar banga biyan bukatata ba to ki tabbata zakiyi kwanan barzahu! sai na kasheki.''!!! nace"Ranka ya dade babu mai kashewa sai Allah haka kuma babu me rayawa sai Allah! mutukar kaga na mutu to kwana nane ya k'are."

Hancina ya kaiwa duka! a take ya fashe! jini ya shiga shatata! ido jawur nake kallonsa, sai huci! yake! nace"Ranka ya dade wane irin aiki zanyi maka."? Murmushin mugunta yayi yace."Wato kinga uwar bari ko."? shuru nayi ina kallonsa hancina na cigaba da zubar da jini! Hannu yasa a aljihu ya d'auko wani abu a d'aure a takarda! " Wannan maganin nake so kisa masa a lemo." Kar'ba nayi ina kallonsa, yace."Kin gane ko."? kaina na daga masa! ya yunkura zai mike tsaye na kwance maganin na watsa masa a fuskarsa! da sauri na mike tsaye! zan gudu, ya tad'o kafata na fad'i a gurin! cikin fitar hayyaci na 'kwallara 'kara! wanda yayi daidai jin saukar wani irin bugu a kaina! idanu na na rintse na zube a gurin ina kiran sunan Allah! Muddibo na jin sawun mutane da sautin maga
na yasa da saurin gaske ya bar gurin..............





*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
85
Hayaniyar mutane na dinga ji sama-sama a kaina na mika hannu cikin mawuyacin hali nace"Ku taimake ni ku kira min iyayena mutuwa zanyi." Rumfa sukayi a kaina suna so su tantance abinda ke faruwa, cikin bushewar makogwaro na sake cewa"Uwani ku taimaka min ku kira min iyayena mutuwa zanyi." Uwani tasa salati tana fadin"Ai wannan Sumayya 'yar gidan Lawi ce." Da yake da karfi tayi maganar babu wanda beji ba, Tambaya turmutsawa tayi cikin mutane ta iske inda d'iyarta ke kwance cikin jini! dan dutsen da Muddibo ya buga mata yayi nasarar fasa mata kai.
Jiki na kyarma ta zube a gabanta hawaye na shatata a fuskatarta hannu tasa ta tattaro ta jikinta ta rungumeta tana kuka had'a kiran innalilihi wa'ina ilaihi raji'un.! Mika'il ne ya karaso gurin da toch a hannunsa yana haskawa dawowarsu kenan yaje ya dauko Yarima daga asibiti ya samu labarin abinda ke faruwa shine yazo ya ganewa idonsa, aikuwa ganin Sumayya cikin mawuyacin hali yasa a guje yaje ya shedawa Yallabai din halin da ake ciki.

Tare suka zo gurin da jama'i guda d'aya lokacin Sumayya ta suma dan bata san wanda yake kanta ba, Tambaya kuka kawai take tana jijjigata gami da kiran sunan Allah tana langwa'bewa! Jama'ar dake kewaye dasu suna ganinsa suka bashi hanya, ganinta cikin jini ya daga masa hankali, tsugunawa yayi yana kallon fuskarta, Tambaya ta fashe da kuka da fadin"Ranka ya dade ka taimaka mana kada mu rasa ta." Maganarta ce ta dawo dashi nutsuwarsa ya kalli Lawi dake gefe a tsugune ya had'a uban tagumi! yace."Me ya faru da ita."? Lawi yace."Wallahi ranka ya dade dukkaninmu bamu san abinda ya faru ba kawai dai munji ihunta ne koda muka zo gurin sai muka ganta kwance cikin jini."

Juyawa yayi ya kalli jama'ar da sukayi dafifi a gurin, yace."Kowa ya tafi.' da sauri suka watse! ya kalli Tambaya jiki a mace yace."Zamuje da ita asibiti domin taimaka mata." Tana kuka tace"Allah ya saka maka da alkairi." Hannu yasa yana kokarin daukarta, Lawi yace."ranka ya dade da kanka." Kansa kawai ya girgiza masa shi yanzu meye ba zaiyi wa yarinyar nan ba watakila ma gurin bashi kariya ta had'u da tsautsayi koma dai menene idan ta farfad'o tilas tayi masa bayani.
Mikewa yayi da ita a hannunsa, Mika'il da security dinsa sukayi gaba da sauri, Tambaya da Lawi suka rufa musu baya.

Bayan mota ya kwantar da ita, ya dan gyara ta domin ya samu gurin zama ya kallesu sun bashi tausayi mutuka ciki kokarin kwantar musu da hankali yace."Insha Allah da kafafunta zata dawo ku daina damuwa kuyi mata addua." Lawi ya sauke ajiyar zuciya da fadin"Ubangiji Allah ya tashi kafad'arta." ameen yace tare da bawa Mika'il umarnin tafiya, sai da motar ta 'bace wa ganinsu sannan suka nufi sashen su cikin halin damuwa gami da rokon Allah sassauci!

Tun mota yake bata taimakon gaggawa dan bakinsa da nata ya had'a ya dinga hura mata iskar bakinsa gabadaya jikinsa ya baci da jinin dake fita ta goshinta, hannusa guda yasa ya danne inda jinin ke zuba ya cigaba da bata taimako irin nasu, cikin ikon Allah kuwa suna daf da shiga asibitin ta farfad'o Allah ya godewa ya rike hannunta tsam a cikin nasa.

Cikin kwarewa da sanin makamar aiki ya tsayar da jinin dake zuba daga goshinta, duk wani taimako da yasan tana bukata sai da yayi mata ya samu nutsuwar zuciyarsa, zama yayi gefanta tare da rike hannunta guda, fuskarta ya tsirawa ido tana ta bacci dan sai da yayi mata allura kafin ya fara aikinsa.

Ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa ties ido babban burinsa yarinyar ta samu nutsuwa ta sheda masa abinda ya faru da ita, tabbas yana zargin wasu daga cikin ma'kiyansa ne suka soma farautar ta, shi kam ya rasa yanda zaiyi da rayuwarsa da makiya.


Agogon hannunsa ya duba karfe daya da rabi na dare, ashe ya jima a zaune yana tunani, hannunsa dake cikin nata yayi nufin cirewa ta rik'e! sai yayi saurin kallo ta yana kiran sunanta


Jin muryarsa ta doki kunnena yasa nayi gaggawar bude idona! idanuwanmu ne suka had'u, kawai hawaye ya kwace min na rintse hannunsa dake cikin nawa ina kallonsa hawaye na ambaliya a fuskata,


Jikina ya matso sosai jikinsa har rawa yake yace."Sumayya sannu kinji ko ki fada min inda ke miki ciwo."

Hannuna na dora saman goshina naji shi a nannad'e! cikin sanyi jiki ya dauke hannuna dake gurin yace."Zai daina ciwo insha Allah! kiyi hakuri kinji ko." Kaina na daga ina kallonsa tausayinsa na ratsa zuciyata.

Yace."Ko zaki tashi zaune."? kaina na girgiza alamu A'a. Dakin yayi shuru na minti biyar kafin yace." Zaki iya yi min bayanin abinda ya same ki."?

Kai na d'aga alamun "E" ya sake matsowa kusa dani murya a kasa yace." Ina sauraranki.


Muryata na rawa nace"Muddibo ne." da sauri ya kalleni nasan mamaki yake jin na ambaci sunan Muddibo.


Yace."Muddibo ne sumayya me yayi miki." ? nasa hannu nagoge hawayen dake zuba, nace"Aiki ya sani nace ba zanyi ba shine ya kwada min mari hakan be isheshi ba ya dauki dutsen wuta ya buga min akaina kashe ni yayi niyyar yayi kamar yanda ya fada zuwan mutane gurin yasa ya gudu.


Gani nayi ya sunkuyar da kansa fuskarsa kamar ta nuna alamun rashin yarda

Nace"Dama nasan ba zaka yarda ba." ya kalleni babu walwala a fuskarsa yace."Sumayya dole nayi kokwanto akan hakan shin wane irin aiki ne ya sakiyi masa kikai masa gardama."'?


"Magani ya bani yace." Lallai na zuba maka a lemo." Kallona yayi yana mamakin maganata! nace"Ni kuma na kwance maganin na watsa masa a fuskarsa."

Cike da mamaki yake kallona kafin yace." Sumayya me yasa kike da tsaurin ido ne? saboda kawai Muddibo ya baki magani kisa min a lemo sai ki watsa masa a fuska sa'anki ne ko kuwa ? Muddibo zai iya daukar mummunan mataki akanki."

Raina a bace nace"Akan na kashe wani gwara ni a kasheni dama aini baiwa ce kowa yana iya amfani dani ta kowace hanya amma nayi rantsuwa ba zan taba bari amanar Allah ta cini ba."!


Girgiza kai yake yana kallona yace."Kwarai ina yaba miki! bisa namijin kokarin da kike gurin ganin kin kare raina da lafiyata, amma me yasa baki bi umarnin muddibo ba, me yasa baki kar'bi maganin ba idan yaso ke kuma sai ki san yanda kikayi kika zubar dashi a wani gurin, na tabbata tsaurin idon da kikayi masa ne yasa yayi miki wannan mumman dukan, Sumayya inaso ki san da cewa ni kad'ai ne zaki iya yiwa zafin kai! na rabu dake amma baki isa kiyiwa wanda yake sama dake tsaurin ido ya kyaleki ba."

Shuru nayi ina nazarin maganarsa, eh kamar yanda yace dana sani na yaudareshi na karbi maganin daga bisani sai na zubar kawai. wani lokacin ne idan zuciyata ta dauki zafi ni kaina bana iya tank'warata."


"Kin tabbata cewa Muddibo ne ya aikata miki wannan mummunan abun."? Kaina na daga ina goge hawaye, Yace." Lallai za'a ramawa kura aniyarta dan ba zan k'yale Muddibo ba sai naci mutuncinsa wallahi tallahi sai yayi daya sanin ta'ba lafiyarki, ni akan wannan zan dauki mataki a kansa daga baya kuma sai ya shedawa Police Maganin me ya baki kisa min a lemo."

Dad'i naji a cikin zuciyata jin cewa zai dauki mataki akansa, nace"Daka dauki mataki akan yunkurin kashe ka da yake ina ganin shi yafi amfani tunda ni ba'a bakin komai nake ba a cikin masarauta kamar yanda ka gama fada yanzu."


Girgiza kansa yayi ya rintse hannuna da nashi yace."Sumayya a cikin masarauta ba'a bakin komai kike ba kamar yanda na fada miki yanzu amma sanadiyar faruwar wannan al'amari masarauta zata san kina da muhimanci a tare da ita."
Lumshe idona nayi kawai na tsinci kaina da d'amke hannunsa dake cikin nawa, gabad'aya muka had'e yatsun hannunmu guri guda tamkar masu d'aukarwar junanmu al'kawari.

' Dakin ne yayi shuru na tsayin lokaci kafin naji ya kira sunana, idona na bude ina kallonsa, yace."Kiyi bacci kada kisa damuwar komai a cikin ranki kinji ko." Lumshe ido nayi a hankali nace"Dan Allah kayi hakuri kabar maganar kada kayiwa Muddibo wani abu ni dama babban burina ka gane gaskiya ka amince da dukkanin gaskiyata."


Ido ya zuba min kafin ya shiga girgiza kansa yace."Sumayya ba zan ta'ba yafewa kaina ba mutukar na bar jininki ya zuba a banza ni d'an halak ne kuma nasan abinda ya dace ."

Shuru nayi ina tunanin abinda zai faru a gaba bana so garin d'aukar fansa wata masifar ta faru a tsakaninsu nafiso kawai ya bar maganar kada yace zai dauki mataki kan abinda akayi min.

Hannuna ya saki ya mike kallo na bishi dashi, ya nufi toilet, ajiyar zuciya na sauke a hankali na rintse idona ina addua cikin zuciyata.

Motsin fitowarsa tasa na bude idona ina kallonsa naga ya shimfida dadduma, da alama sallah zaiyi idanuwa na mayar na rufe ina tunanin iyayena yanzu ko wane irin hali suke ciki? nasan dai duk inda suke suna cikin tashin hankali da damuwa mai tsanani! hawaye suka zubo min a kumatu hannu nasa da sauri na goge ina kokarin danne kukan dake kokarin kufce min.

b'angaran Magajin Sarki kuwa nafila yayi raka biyu ya daga hannu sama ya roki Allah sosai akan abubuwan dake faruwa da rayuwarsa da makusantan sa yanzu abun ya wuce kansa har yazo kan masu kula dashi, tunda an kasa samun galaba a kansa to bari a sabauta hadiman sa, gaskiya magana dole ya dauki mataki akan al'amarin dan yana ji yana gani jinin yarinyar dake tsaye a kan rayuwarsa ya tafi a banza ba dole ya nunawa Muddibo kuskuransa, ya jima hannu a sama yana rokon Allah kafin ya shafa adduar a fuskarsa ya mike a nutse ya nufo gadon da nake kwance.

Cikin bacci na jishi a jikina, nayi saurin bude idona ina kallonsa yana kokarin kwanciya kokarin mikewa nayi yayi saurin rike hannuna! Girgiza min kai yayi a hankali yace."Ki kwanta mana." Murya na rawa nace"To ka tashi daga kusa dani.'' a hankali yace."Dan gurin dana kwanta bai isa ya tsare miki gurinki ba kiyi hakuri ki kwanta babu abinda zai faru sai alkairi."
A sanyaye na dinga kallonsa ina mamakin karfin halinsa Tamkar wata matar auransa haka yake Mu'amula dani.

"Gaskiya ni bazan kwanta gado daya dakai ba saboda haka bari kawai na sauka kasa.'' Yunkurin sauka nake ya rike kafaduna! cikin kulawa yace." Saboda na kula da motsin ki yasa zan kwanta kusa dake amma tunda bakya so shikkenan bari na sauka." kallo na bishi dashi lokacin daya sauka daga gadon ya koma kan doguwar kujera ya kwanta, tausayi ya bani ganin yanda yayi sanyi yana min magana cikin kwantar da murya na amince da cewa abinda ya faru ya girgizashi mutuka yanzu kuma na gane cewa ina da muhimanci a rayuwarsa tunda gashinan a zahiri ya nuna tashin hankalinsa..........Na jima ina tunane tunane kafin bacci ya d'aukeni! bacci mai cike da munanan mafarkai marasa dadi da ma'ana.

Kiran sunana da ake yasa na bude idona da sauri ina kallonsa yana tsaye a kaina, hannu na dora saman kaina ina jin wani irin ciwo a gurin, a nutse yasa hannu ya cire hannuna, "Sannu." kaina na d'aga ya cigaba da cewa"Kinga gurin yayi fushi ko."!? kaina na girgiza a hankali na fara kokarin mikewa ya kama hannuna, kallonsa nayi ya girgiza min kai da fadin"Kada kice komai taimaka miki zanyi kiyi alwala ko." Shuru nai masa, ya fara kokarin dora hannuna a kafadarsa, yana so ya rike kuguna. da sauri nace"Dan Allah ka barni zan iya komai da kaina. Bai saurare ni ba, ya ratsa hannusa a k'uguna, ya sani a jikinsa sosai muka nufi toilet, kallona yayi yace."Babu inda ke miki ciwo ko."? ganin yanda ya damu yasa nace"Eh babu kaina ne ke ciwo." Cikin rarrashi yace."Bari kiyi sallah sai muje gida kiyi break kisha magani insha Allahu zaki samu sauki."

Kaina na dauke jin wani irin abu dangane dashi, ya miko min brush da fad'in" Maza ki wanke bakin ki idan kuma ba zaki iya ba nayi miki ko."? saurin kar'ba nayi na nufi inda famfo yake, a nutse na wanke bakina cikin dubara nai alwalar, ya karaso gurin hannuna ya rike muka fita daga toilet din.
Farin hijabi irin na ma'aikatansa ya samin a wuyana ya gyara min dadduma na tayar da sallah.


Zama yayi kan kujera da wayarsa number Acp ya kira, suka gaisa cikin mutumci yayi masa bayanin dukkanin abinda ke faruwa, Acp yace."Tabbas biri yayi kama da mutum ranka ya dade a binkicenmu na baya sai da naso na fuskanci wani habu daga gurinsa to alhamdulillahi dama barinmu mu kama wanda yake da hannu acikin al'amarin sabida haka ka kwantar da hankalinka insha Allahu yau din nan zamu dam'keshi dole ne yayi mana bayanin yanda al'amuran suke faruwa." Yace."Okey to babu damuwa amma bana so ku shiga masarautar da niyyar kamashi kuje gurin aikinsa ku tozartashi acan sannan ku daureshi ku tafi dashi, bayan kun dam'keshi ka kira ni a waya inaso dik wani bayani da zaiyi ya kasance ina gurin." Acp yace."Babu damuwa insha Allah zan kira ka idan komai ya kammala." Sallama sukayi ya kashe wayar, ido muka had'a! naga fuskarsa ta rikice da zallar 'bacin rai! a gaskiya ban ta'ba tsammanin ina da kima a gurinsa ba.
A marairaice nace"Don Allah ka bar maganar nan wallahi idan nice na yafe."
Wani irin kallo yayi min kafin yace."Kada ki sake wannan maganar idan kina so mu zauna lafiya dake kiyi shuru da bakin ki Muddibo kashe ki yayi niyyar yayi kina tsammanin idan kin bar duniya zanyi rayuwa mai dadi? dole ne nabi kadin jinin daya zubar miki."

Kallonsa na dinga yi ina mamakin maganarsa nace"Mutuwa dole ce a gurin ko wane musulmi koda Muddibo ya kasheni nayi shahada kuma na rataya a wuyansa sabida haka dan Allah ka daina wannan maganar.

Ya jima yana kallona kafin yace."Ke! Sumayya bari nayi miki maganar k'arshe daga yau na 'yan taki kin zama mai 'yanci kuma insha Allahu a cikin satin nan za'a daura min aure dake! inaso ki zauna a k'arkashina cikin tsaro! dan na fahimci cewa ma'kiya zasu huce fushin su a kanki to zan aureki ki zauna a karkashina mu cigaba da rayuwa cikin inuwa daya.

Cikin tsabar kad'uwa da firgici nake kallonsa, ya daga min hannu tare da fadin"Bana bukatar naji komai daga bakin ki na gama yanke hukunci." Mikewa yayi tare da fad'in "Tashi muje gida." Na mike jikina a mace! gaba yayi nabi bayansa ina mamaki abinda yake shirin faruwa da rayuwata, Yarima zai aure ni sabida ya ceci rayuwata! ko kuma dai zai aureni ne saboda ya biya bukatarsa a kaina kamar yanda ya kud'urta a can baya, wannan tunane tunane ne ya dameni a fakaice na dinga kallonsa ina so na karanci abinda ke cikin zuciyarsa.


*Na kudi ne..*
Kada ki karanta mun littafi idan baki biya ba, idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.. 0542382124.....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta whsap da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
86
Duk yanda naso na karancin abinda ke cikin zuciyarsa kasawa nayi dan gabad'aya tunda muka shiga mota ya sanja fuskarsa ta rikid'e sosai tamkar wanda bai ta'ba dariya ba, na dinga satar kallonsa ina mamakin sauyawarsa, har muka shiga masarautar wata magana ta fatar baki bata had'ani dashi ba......"Mika'il Ka wuce damu can sashen Mahaifiyata." Da sauri na kalleshi, hankalinsa nakan direba yana bashi umarnin inda zai ajiyemu, Mika'i da sauri ya juya mota ya hau hanyar da zata sadamu da sashen mahaifiyar tashi......Alhamdullilahi naji yace kafin yasa hannu ya bude kofar motar, yana fitowa nima na fito kaf ma'aikatan dake gurin suka bar abinda sukeyi suka zo suna mika gaisuwarsu gurinsa, nayi mamaki sosai da ganin ya tsaya yana amsa musu, gaba yayi da sauri nabi bayansa, jama'ar gurin suka bi bayanmu da kallo domin dayawa daga cikinsu sun dauka ba zata dawo da rai da kafafunta ba saboda yanda aka fita da ita jina-jina da jini.


Tana zaune kan kilishi da carbi a hannunta muka shiga falo tare da sallama a bakin mu. zamanta ta gyara ta amsa sallamar tare da tsira mana ido fuskarta kadai ta isa ta nuna mana cewar taji dadin ganinmu, cikin sanyi jiki nake tafiya kaina a kasa, dan shi har ya karasa kusa da ita ya zauna suna gaisawa, gurfana nayi a gabanta kawai naji ta janyoni ta rungume kam a jikinta sai saukar hawayenta naji a bayana, kawai naji nima zuciyata ta karye hawaye ya dinga kokarin kwace min.

Cikin rarrashi yace."Mamma dan Allah ki daina kuka ai gatanan da ranta bata mutu ba kamar yanda Muddobu yayi niyyar kasheta." buka Da sauri ta kalleshi tana mamakin furucinsa. kansa ya daga mata yana so ya tabbatar mata da gaskiyar maganarsa,


A sanyaye ta dago ni tana kallon fuskata, cikin alhini ta dora hannunta saman raunin dake goshi na murya na rawa tace"Sannu kinji ko."? kaina na daga mata cikin kokarin danne damuwata nace"Mamma ki kwantar da hankalin ki insha Allahu babu wani abu da zai sake faruwa dani dukkanin mai nufin mu da sharri zai koma kansa."


Ajiyar zuciya ta sauke tace"Sumayya jiya da kyar na iya bacci saboda wannan tashin hankalin daya faru, shin wai su waye sukayi kokarin halakar dake ne."? Shuru nayi tare da sunkuyar da kaina kasa


Ta daga kai tana kallonsa domin karin bayani, yace."Mamma kamar yanda na fada miki da farko hakane Muddobo shi kadai ya nemi ya halakar da ita kawai saboda taki bin umarninsa.

Cike da mamaki mai tsanani tace"Ni kuwa wannan al'amarin ya bani mamaki mutuka sumayya me muddibo yake so kiyi masa kika gaza har ya kai matakin daukar dutsen wuta ya buga miki.


Murya na rawa na shiga fada mata dukkanin abinda ya faru......Mamma kuka take sosai tana girgiza kanta, gabad'ayan mu hankalinmu ya tashi muka dinga rarrashinta, da kyar tayi shuru ta rike hannuna kam! "Sumayya ke 'yar halak ce kuma kin cancanci komai a gurina hakika kina d'aya daga cikin mutane da ba zan ta'ba mantawa dasu ba a tarihin rayuwata, kina da gaskiya da amana kin rike amanar dana baki duk rintsi kina kokarin kare lafiyar gudan jinina ni kuwa me zanyi miki a duniya wanda zai birgeki." ta karasa maganar tana rintse hannuna da nata.....mirmushi nayi a sanyaye nace"Ranki ya dade wallahi banyi wannan aikin domin ki biyani ba, duk abinda nakeyi akan Yarima inayi ne saboda Allah da manzon sa, Mamma wallahi bana bukatar komai a gurinki..........Mirmushi tayi tana kallona tace"Sumayya babu macan data dace da Babana sai ke ina rokon alfarma a gurinki dan Allah ki aureshi domin ki cigaba da kula dashi." Kaina na sunkuyar gabana na faduwa naji yace."Mamma ki kwantar da hankalinki dama nima hukuncin dana yanke kenan zan aureta saboda kyawun halinta da kuma tsayayyarta akaina sannan kuma zan aureta ne domin ganin ta k'ubuta daga gurin masu farautar ta, tunda duk iya kokari sunyi domun suga bayana Allah be nufa ba wannan dalilin yasa suka dawo kanta tunda itace garkuwata to idan suka kasheta suna ganin bukatarsu zata biya a kaina." ajiyar zuciya ya sauke kafin ya cigaba da cewa" Mamma na riga na yanke hukunci akan Muddibo sai dai duk abinda zai faru ya faru na shedawa Acp dukkanin abinda ke faruwa kuma ya tabbatar min da cewa zasuje su kamashi a gurin aikinsa, dole sai tabbatar mana da gaskiyar lamari."



Fulani shuru tayi tana nisawa kafin tace"Babana ba zan hanaka ka dauki mataki akan wannan lamari ba, idan ya kasance da saka hannu Muddibo cikin faruwar wannan al'amari

Please Login or Register in order to submit comment