Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abincin da sauri na kar'ba hannu yasa zai kar'ba na janye! tare da fad'in "Baka ci a nutse bari kawai na baka da kaina." cinyarsa ya nuna min wai na zauna! cikin jin nauyi na dauki plate din abincin na zauna a cinyarsa ya rikeni sosai na shiga bashi a baki yana ci yana yi min wani irin kallo wanda na kasa fassarashi.


Daga k'arshe ma plate din abincin ya kar'ba ya ajiye kan center teble matseni yayi tsam! a jikinsa! kusan a tare muka sauke ajiyar zuciya, yasa hannu ya dauke dankwalin kaina hannusa guda ya turmusa cikin gashin kaina yana ya mutsawa, tsigar jikina ta mike wani irin sanyi ya dinga ratsa jikina! zafafan kesses yake sakar min wanda suka hautsina min lissafi da k'yar na iya ture kansa dake manne da kirjina murya na rawa nace"Ka daure ka cinye abincin ka." Kansa ya girgiza min da fad'in ''Na'koshi ki tashi muje Daki." Kallon 'kwayoyin idanunsa ya tabbatar min da abinda yake nufi.........Kokarin sauka nayi daga jikinsa ya ri'ke kuguna had'e da fad'in "Ina fata dai baki manta da al'kawarinmu ba." Kallonsa nayi ya daga min gira da fadin" kin manta ko."? Girgiza kaina nayi nace"Ban manta ba." Yace."Okey to tashi muje." gabana na faduwa na sauka daga jikinsa, yana mi'kewa nayi saurin kauda kaina dan ganin yanda girmansa ya bayyana. Hannuna ya ri'ke muka nufi dakin, ba tare da yaja wani dogon lokaci ba ya cire kayansa, nace"Wanka za kayi ne."?

Wani kallo yayi min da fadin"Ke bana son rainin hankali wane irin wanka bayan kin san abinda ke damuna." dauke kaina nai daga kansa....Ya mike daga shi sai gajeran wando ya karaso inda nake tsaye jana yayi ya kaini har bakin gadon na dinga no'kewa ina fargabar abinda zai faru dan har yanzu ina jin zafi a gabana.

Wasa yake dani sosai wanda ya sanya gabadaya sha'awata ta tashi na daina no'kewa gabadaya na sakar masa jikina ya dinga abinda yaga dama dashi.......Adduar saduwa da iyali naji yana karantowa rintse idona nayi ina addua cikin raina, cikin nutsuwa ya dinga shigata har yaje inda yake so, kafin ya fara wani abu sai da ya dan jima tukkuna ya fara a hankali a hankali hakan yasa banji zafi ba sosai! na saki jikina ina d'an jin dad'i sama-sama! ina jinsa shi yana ta sakin nishi! hade da 'kara 'karfi da kuzari! kawai sai na tsinci kaina da tura masa jikina dan motsawar da nake yana sani nishad'antuwa! haka muka kasance da juna cikin wani irin yanayi mai dadi da shau'ki! gabad'aya fita mukai daga cikin hayyacin mu domin a lokacin daf muke da biyawa junanmu bukata! babu zato babu tsammani naji yay gaggawar zare jikinsa daga jikina yayi ruf da ciki akaina hannuwansa duka yasa kan breast d'ina yana luguda yanayi yana wani irin gurnani! rasa gane yanayin da nake ciki nayi kukan ne yake kokarin kufce min saboda takaicin abinda yayi min a lokacin nake jin zan samu gamsuwa yay gaggawar cire jikinsa kome hakan yake nufi oho!!! jikina ne yayi sanyi gabana ya dinga wani irin tsiko yana zubar da ruwan dake 'kara tayar min da sha'awa! Mi'kewarsa yasa na kalleshi sai naga yana kokarin sa gajeran wandonsa kafin ma nayi wani yunk'uri ya sauka daga gadon, bin sa nayi da kallo bak'in cikin duniya kamar ya kasheni! kokarin mi'kewa zaune nayi hannuna ya sauka kan uban sperm dinshi da ya zubar a kan bedshirt d'in da sauri na dauke hannuna daga kai.......... wato wannan shine matakin daya d'auka a kaina tunda dai na'ki na amince da tsarin iyali to bari ya dinga zubar da kwayoyin haihuwarsa akan bedshirt idan yaso sai subi rariya........ anya kuwa wannan dubara ce? ko kuma dai akwai Lauje cikin nad'i.?
*Team d'in Sumayya Anya kuwa zamu yarda da wannan al'amari🤕 Kuna inaaa!! ku fito muyi zanga-zanga akan munahiki😂😂😂*





*Na kudi ne.....!*
Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake.....Vip group #600 normal gruop#300 account... 0542382124....Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
101
A ranar yini nayi akwance da damuwa gami da tunanin mafita, sai da naji kiran sallahr la'asar tukkuna na tashi naje nai wanka na kimtsa jikina kan dadduma na hau na gabatar da sallah, bayan na idar na jima hannuna a sama ina addua kafin na shafa a fuskata, daddumar na ajiye inda aka tanada, falo na fito domin samawa kaina abinda zanci, ina fitowa muka had'a ido da ita, Tambaya ce a zaune ita kad'ai yanayin fuskarta yasa na gane cewa lallai babu lafiya, wannan shine zuwanta na biyu tunda tazo da farko taga daki bata sake zuwa ba tsayin wata biyar kenan babana kuwa bai ta'ba zuwa ba sai dai ni duk sati ina zuwa na gaishe su.

Cikin kulawa nace"Tambaya yaushe kika shigo."? Tana kallona tace"Na d'an jima lokacin dana shigo kina bacci sai hadimai dake aikace-aikace daya daga cikinsu take sheda min bacci kike shine nace Kada ta tasheki zan zauna ki tashi tukkun."

A sanyaye nace"Wallahi yau yinin bacci nayi tun bayan Fitar Yarima na kwanta sai yanzu Allah ya tasheni." Cikin kulawa tace"Ai gwara da kikayi bacci zakiji dadi.'' murmushi nayi da fadin"Ina baba ina fatan yana nan lafiya." ? girgiza kanta tayi tace"Da sauki dai za'ace jikinsa ne ya tashi kwana biyu baya bacci da daddare shine nace bari nazo na fada miki ko da wani taimako da mijinki zai masa.

Hankalina ne ya tashi jin cewar babana bashi da lafiya nace" Tambaya babana baida lafiya amma kuma baki fad'a min na dubashi ba."


Murmushi mai ciwo tayi tana girgiza kai tace"Sumayya kina cikin damuwa yaushe zan zo na 'kara miki wata."


Da sauri na kalleta ina mamakin maganarta nace"Tambaya waye yace miki ina da damuwa."? girgiza kai tayi tace"Sumayya ba sai an fad'a min ba ni nagani da idona dik sanda kika je gurina domin gaisheni cikin damuwa nake ganinki ni na haifeki dole na fahimci halin da kike ciki."


Hawaye ne suka kwaranyo min a kumatu! dawowa kusa dani tayi ta rungumeni tana shafa bayana tace'Kiyi shuru ki daina kuka ki fada min matsalar da kike ciki a gidan auranki ni mahaifiyarki ce zan baki shawarwari masu amfani."


Zuciyata ce ta karye hawaye suka dinga zubo a kumatuna nace"Tambaya ciki ne dan kimanin watanni uku amma kuma wanda yayi cikin yace babu ruwansa dashi."


Cikin tsantsar tashin hankali ta dago ni tana kallon fuskata tace"Sumayya yanzu a haka ciki gareki ? kuma akan wane dalili Yayi wannan mugun furucin akan ki."


Cikin sar'kewar murya nace"Saboda kawai bashi da ra'ayin haihuwa." girgiza kanta tayi tace."Kodai bashi da ra'ayin haihuwa dake sabida kina baiwa wacce take 'karkashinsa."

Kallonta nayi, tace."Kwarai kuwa Sumayya ni a ganina wannan dalilin ne yasa yake gudun hada jini dake." girgiza kaina nayi nace"Ba haka bane Tambaya shi gabadaya haihuwarce baya so saboda wasu dalilai nasa Ai kinga Lawisa jininsu d'aya to itama baya bukatar haihuwa da ita kamar yanda baya bukatar ya haihu dani."



Tambaya jikinta ne yayi sanyi ta kalleni a sanyaye tace."Lallai dole ki shiga cikin halin damuwa Sumayya to amma mahaifiyarsa tasan abinda yake faruwa kuwa."?


Girgiza kaina nayi nace"Bata sani ba.'' Tace."Lallai kuwa yana da kyau ta sani domin wannan maganar bai kamata kiyi shuru ba dole ta sani tayi masa fad'a ai wannan ba d'abi'a bace kana musulmi ka dinga gudun haihuwa akan wane dalili ? Kije ki fad'a mata kuma ki daina kuka da damuwa kada wani ciwon ya sameki."


Nace" Mutukar bai sanja ra'ayi ba to zan sameta na fada mata duk abinda yake faruwa." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Yanzu cikin watansa nawa."? "Ina tunanin zaiyi wata uku." girgiza kanta tayi tace" Ubangiji Allah ya sauke ki lafiya Sumayya nima banki goyon bayan kibi ra'ayinsa ba duk rintsi kada ki bari ya zubar miki da ciki tinda likita ne zai iya kawo miki magani zubar da ciki kada kisha."

Shuru nai ina kallonta da mamakin nisan tunaninta gabadaya banyi tunanin hakaba eh lallai dole nayi takatsantsan dashi dan tabbas zai iya bani wata 'kwayar nasha cikin ya zube bukatarsa ta biya.


Sai kusan biyar da rabi Tambaya ta mike da niyyar tafiya, har harabar waje na rakata kana na bata sa'kon gaisuwata gurin babana kafin nazo dubashi...........Cikin damuwa mai tsanani na koma ciki ina tunanin abinda zai faru a gaba.

Sanin da nayi cewa ba'a gurina yake ba yasa ina idar da sallahr isha'i nayi shirin kwanciya, waya ta na ajiye a kusa dani wai ko zai kira ni, sai na kunna tv na kwanta ina kallo kafin bacci ya daukeni..............Jin alarm na agogon waya ta ya nuna k'arfe goma yasa na cire raina da shigowarsa wayar na kashe kafin na kashe tv din na ja bargo na rufe jikina ina addua a cikin zuciyata, can cikin baccin daya soma daukana naji sautin muryarsa a kaina, a firgice na bude idona ina kallonsa yana tsaye 'ki 'kaqam! mi'kewa zaune nayi ina kallonsa yasa hannu ya kunna bedlamp dakin yayi haske dauke kaina nayi babu walwala nace"Sannu da zuwa."

Ba tare da ya amsa ba ya mi'ko min abunda ke hannunsa " 'Kar'bi wannan maganin kisha na 'karfin jiki ne.'' hannunsa nabi da kallo kwayoyin magani ne a ciki wata 'yar farar leda!

Hannu nasa na kar'ba had'e da fadin"Nagode." fuskarsa ya saki ya zauna kusa dani tare da miqa min goran ruwan dake hannunsa.

Kar'ba kawai nayi na ajiye kan drowar. Yace."Kisha maganin mana."

Murmushi takaici nayi nace"Yanzu don Allah dan Annabi ba kaji kunya ba."? kallona ya shigayi na cigaba da cewa''Nasan fa ko wane irin magani ne kana so ka zubar min da ciki a fakaice mai yasa kake adawa da ikon ubangiji ne? tunda kaga Allah yayi maka haka to alkairi ne kayi addua akan Allah yasa dan za'a haifa maka ya zama alkairi a tare dakai da al'ummar musulmi.

Shuru yayi yana kallon kasan kafet da alama maganata ta ratsa shi dan gani nayi duk jikinsa yayi sanyi, naji dadin hakan kawai sai na cigaba dayi masa nasiha ina nuna masa illar abinda yake yi.


Kallona yayi da jan ido yace."Bani magani na tunda ba zaki sha ban kuma ce kiyi min wa'azi ba."

Ledar maganin na mi'ka masa ya kar'ba tare da kama hanyar fita ba tare da ya sake cewa wani abuba.


Girgiza kaina nayi na koma na kwanta ina addua a zuciyata akan Allah yasa ya saduda ya gane gaskiya ya hakura da hukuncin ubangiji.


Washe gari da safe daya shigo nake sheda masa rashin lafiyar mahaifina tare da neman izinin zuwa dubashi! ba tare da ya dauki maganata da muhimanci ba yace.'" Zaki iya zuwa ki dubashi amma ni kam banda lokacin amma ana iya kaishi asibiti kamar kowa."

Jikina ne yayi sanyi na bishi da ido har ya fita daga dakin, girgiza kaina nayi ina jin takaicin abinda yake nasan duk wulakancin da yake min sabida na'ki nabi umarninsa ne.


Yanayin yanda na samu babana a rikice yasa duk hankalina ya tashi, banyi zuciya ba na sake kiran wayarsa na sheda masa cewa yana cikin matsala dan akwance yake sabida galabaita......Cikin tsawa yace." To yanzu ya kike so ayi ko kina so na katse abinda nake nazo na dubashi? nace "Kisa a kawoshi asibiti."!! kashe wayarsa yay ba tare daya bari nace wani abuba.

Daure zuciyata nayi na cire duk wata damuwa a cikin raina na shedawa Tambaya yanda mukayi dashi, tace" To shikkenan sai a kaishi Asibitin. nace"Zan koma gurina yanzu zan turo direba da mutum biyu domin su kamashi." tace."To ubangiji Allah yayi miki albarka.'' na amsa da ameeen lokacin da nake kokarin fita.


To hankalina bai kwantaba sai dana ga dawowarsu lafiya ikon Allah babana da kafafunsa ya dawo Tambaya ke sheda min cewa 'karin ruwa akayi masa shine dalilin daya sa yaji kwarin jikinsa, ledar dake cike da magani ta nuna min.'' na zauna ina nuna mata yanda zata dinga bashi maganin akan 'ka'ida, ban tafi ba sai dana tabbatar da cewa yaci abinci yasha magani sannan nayi musu sallama na tafi, yanzu naji sassauci ta wannan bangaran.


Da har nayi nufin shiga gurina sai na fasa bangaran Mamma na nufa mun kwana biyu bamu gaisa da juna ba.


Tana zaune gurin da take hutawa Jakadiya ce a gefanta suna hira irin wacce suka saba, a nutse na karasa inda suke na zauna gabanta ina gaisheta, murmushin da takeyi yasa ni tunani wani abu. gaisuwata ta amsa tare da fad'in "Ya jikin naki.''?

" Da sauki" nace ina jin nauyin had'a ido da ita, bayan tashin jakadiya daga gurin ta gyara zamanta cikin nutsuwa tace"Sumayya tun kwanaki nake miki kallon mai juna biyu, sai yau dana turke babana da tambaya yake cewa dani baki da ciki, ni wallahi da naga kina laulayi yau da lafiya gobe babu na dauka ko na kusa samun jika ne".

Cikin kunya da jin nauyi nace" Eh hakane Mamma bani da ciki muna dai Addua Allah ya kawo masu albarka." da sauri ta amsa da ''ameeen 'yar albarka Ubangiji Allah ya amsa adduarki." shuru nayi ina murmushin ya'ke! tace"Yanzu babana da sassafe yake fita gashi baya dawowa da wuri ni kaina sai ya kwana biyu bai shigo mun gaisa ba, sai dai kullum muna waya dashi mussaman da safe yakan kirani yace nasa akai masa abinci ofis."

Nace"Eh hakane kam aiki ya hanashi sakewa da kowa abinci ma sai da kyar yake ci! Mamma kada kiga laifinmu wallahi muna iyakacin bakin kokarinmu gurin kula daci da shansa kawai dai yafi bukatar naki shiyasa muka rabu dashi.

Murmushi tayi tace"Haba Sumayya ai ni zanyi shedarki akan babana kin kula dashi babu aure a tsakaninku ballanatana yanzu da aure ya shiga tsakaninku na riga nasan halinsa da 'kiwar cin abinci shiyasa a duk sanda ya bukaci abinci ta gurina nake sawa a kai masa amma dai duk da haka zan zauna dashi nai masa fad'a ya dinga zama yana cin abinci tare daku."

Nace"To shikkenan Mamma mungode kwarai da gaske Allah ya 'kara girma." Ta amsa da "ameeen suma ameeen." Sallama nayi mata tace" Ya muna hira kuma zaki tafi." Murmushi nayi nace" Mamma naga magariba ta kusa ne." tace"Eh hakane to babu damuwa Sumayya Allah yayi miki albarka sai na sake ganinki ." nace "To Mammah a tashi lafiya nagode kwarai da karamci." Murmushi tayi tare da daga min hannunta, cikin nutsuwa nasa takalmana na fita daga falon

A daran ranar bai shigo ba shigo ba sai da safe ya shigo, kamar koda yaushe fuskarsa babu sassauci! muka gaisa nace"Nagode sosai da hidimarka akan mahaifina wallahi naji dadin ganin ya dawo lafiya da k'afafunsa." hararata yayi yace."Bana bukatar godiyarki ba sabida ki gode min na kula da lafiyarsa ba ina fata kin gane."

Murmushi nayi kawai na sunkuyar da kaina, yace."Ni zan fita." da sauri nace"To Allah ya taimaka." ba tare daya amsa ba ya kama hanya ya fita daga dakin, kwanciya nayi ina dan jin sassauci a zuciyata yau naji dadi sosai mun rabu cikin arziki.........Cikin baccin daya soma daukana naji mugun bugu! a furgice na bude idona ina kallon bakin kofa........... Yunkurin saukowa nake bugun kofar na sake tsananta, gabana na faduwa nace"Waye."?


"Ubanki Lawi ne."!!!! Jin muryar Lauratu yasa naji yawun bakina ya dauke Ubana take zagi akan wane dalili? fuskata a murtuke na bude kofar a shirye nake dana kare martabar iyayena........Ko kafin nayi wani yunkurin ta afko dakin! da sauri na bita da kallon mamaki! nace"Baiwar Allah waike dabba ce ne? haka kawai da sassafe zaki zo kina buga min kofa ko kuma kina bina bashi ne."?

Yanda take kallona yasa na fahimci cewa tana mamakin lafazai na a kanta, hanya na nuna mata da fad'in " Kizo ki fice min daga daki tun muna sheda juna dake."


Murmushi tayi tana durfafo inda nake na tsorata da yanayin kallon da take min amma dai na dake! sabida inaso na nuna mata tsageranci na, cikin zafin nama naga ta watso min abu a jikina! a gaggauce na matsa gefe guda kawai naga wani irin ruwa yana kumfa a 'kasan gurin ties din ya tsage! cike da d'umbin mamaki! nake kallonta tana huci!!! Ta bud'e kofar dakin ta futa a fusace! cikin karkarwar jiki na nemi guri na zauna ina jan kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! shin matar nan wane irin mugun abu tazo tayi min? " asid ne tayi nufin watsa miki a jiki domin ta 'kona ki." zuciyata ce ke fada min wannan magana, nai gaggawar kallon gurin ina mamakin yanda yayi 'baki ties din yayi duhu duk ya tsage! al'amarin ya shiga bani tsoro tare da mamaki! mai tsananin gaske..



*Na kudi ne!*
Koda zaki ganshi a group na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal group #300....account.. 0542382124....Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
102
Na jima a zaune a dakin ina jimanta al'amarin kafin na mike jiki a mace na fita falo, nan na samesu a zaune ganin fitowata yasa duk suka mike tsaye, sunayi min barka da fitowa, zama nayi kan kujera babu walwala a fuskata nace "Ku zauna inaso nayi magana daku.'' zama sukayi tare da mayar da hankalinsu kaina, nace" Daga yau sai yau kada ku sake barin matar data fita yanzu ta sake shigowa kunji abinda nace ko." Gabad'aya suke ce "Eh ranki ya dade insha Allahu zamu kiyaye." Nace"Mariya ki shiga ki gyara min dakina." da sauri ta mike ta nufi dakin su kuma suka cigaba da aikace aikacen da suke..........

Da wuri ya dawo gida nai mamakin hakan amma ban nuna a fuskata ba barka da zuwa nai masa ya amsa a sake kamar bashi ba, ruwan wanka na hada masa na fito na tarar dashi yana kokarin cire kayan jikinsa, ido muka hada murmushi yayi min na bishi da kallo ina mamakin sanjawarsa jikin mirror na tsaya Nace."Na hada maka ruwan wankan.'' "Nagode." yafada a lokacin da yake kokarin ajiye agogonsa kan mirror wani irin kallo yayi min yace'"Ba zaki taya ni wankan ba."? Murmushi nai nace"Da alama yau kana cikin nishadi .'' yace."Saboda me kikace haka."? nace"Saboda ba haka kake mu'amula dani ba." Shuru yayi still da murmushi a fuskarsa ya nufi toilet din, girgiza kaina nayi na bude wardrobe na dauko masa jallabiya da gajeran wando na zauna gefan gado ina jiran fitowarsa


Ido muka hada a lokacin da ya fito daga toilet din da sauri na kauda kaina tsigar jikina duk ta mi'ke ni kaina nasan ina bukatarsa cikin zuciyata nace" Allah yasa dai yau muyi abin arziki da juna.

Zama yayi kusa dani yana goge jikinsa da towel nace"Ga kaya na dauko maka." "Nagode." yace na mike a nutse na dauko man da yake shafawa, a nutse na tsuguna kasan kafet na fara shafa masa a kafafunsa.

"Sumayya." cikin wani irin voice yayi maganar, kallonsa nayi naga idonsa yayi ja. amsawa nayi tare da cigaba da shafa masa man.

Yace."Ya jikin naki."? ba tare dana kalleshi ba nace da sauki.'' Yace." Allah ya rabaku lafiya." da sauri na kalleshi ina mamakin adduar da yayi. girgirsa ya daga min yana murmushi.

Ajiyar zuciya na sauke nace"Yanzu ka gane kenan." hannu na ya rike yace.''To ya zanyi tunda kinfi karfina." girgiza kaina nayi nace"Kada kayi sa'bo ba laifina bane Allah ne ya nuna maka ikonsa."


Yace."Na sani Sumayya na hakura na bar masa ikonsa." murmushi nayi nace"Nagode kwarai insha Allahu za kayi alfahari da dan da za'a haifar maka."


Yace." To shikkenan yanzu me zaki bani." nace"Zan cika maka ciki da abincina mai dadi da gamsarwa.''' da murmushi a fuskarsa yace."Bayan naci na koshi me zan samu." ?


Shuru nayi yace."Yau da soyayya nazo gurinki." kallonsa nayi ya kanne min ido......murmushi kawai nai ina mamakin shu'umancinsa dama ai ruwa baya tsami banza.

Hannuwana ya ri'ke yana murzawa yace."Baby kinyi shuru ko bazan samu ba." ? nace"Zaka samu mana." yace."To nagode muje ki bani abinci naji karfin jikina." mikewa nayi ya rike hannuna muka fita falo.


Da kyar ya iya cinye abincin dana zuba mishi nace"Wai dan Allah me yasa baka san cin abinci."? yace."Haka kawai tun ina yaro haka nake nafi mayar da hankali kan biscuits da sauransu kayan zaqi." nace"Shiyasa mana gakanan kullum jiya i yau ka'ki kumari." dariya yasa yace."Kina so nayi qiba kenan."? kai na daga ina murmushi yace."Idan na zama 'kato zan dinga turmusheki fa." dariya nayi nace"ai yanzu ma turmushenin kake.''

Yace."Ai Banda nauyi kinfi ni nauyi baby." girgiza kaina nai nace" Ban yarda ba." 'yar dariya yayi yace."Sumayya bana san 'kiba shiyasa bana mayar da hankali gurin cin abinda zai janyo min ita, amma kuma ina sha'awar mace mai 'kiba da kumari irin ki.'' dan 'bata rai nayi nace"Wato kana k'arewa matan mutane kallo kenan."? girgiza kansa yayi yace."babu ruwana da matan kowa sai nawa na fada miki abinda ke raina ne."

Shuru nai ina kallonsa ya kashe min ido da fad'in muje ciki ko." dauke kaina nayi, ya mike tare da kama hannuna na mi'ke kai tsaye bedroom din muka nufa sai shashshafa jikina yake gabadaya ya gama rikita min jiki.


A daran ranar ya nuna kulawa mutuka dan ya saki jikinsa sosai ya gamsar dani tarin sha'awar dake damuna, a tare mukayi wanka na dinga addua a zuciyata akan Allah ya d'orar da zaman lafiya a tsakaninmu..........

Kwana biyu zamana dashi yayi kyau muna mu'amular arziki kuma idan na bashi abinci ko baya so sai ya zauna yaci duk dan ya faranta min rai har zuwa yayi ya duba babana na dinga murna ina sake godewa Allah daya kawo mana zaman lafiya da junanmu.


Satin mu uku da shiryawa ranar lahadi da safe na tashi da wani irin ciwon mara, na fito daga toilet na sameshi yana bacci, cikin faduwar gaba na zauna kusa dashi ina tashinsa, ya bude idonsa da fadin"Menene baby please ki bari na huta.'' nace" Ka tashi bani da lafiya.'' idonsa ya bud'e! yana kallona kafin yace." me yake damunki."? murya na rawa nace"cikina ne ke ciwo."? jim! yayi kafin ya cusa hannunsa cikin rigata 'kasan marata yasa hannunsa yana d'an dannawa! nai saurin dauke hannunsa ina ya mutse fuska! yace."baby bashi da lafiya." gabana ya fadi! hawaye na soma zuba nace"Dan Allah ka tashi ka bani magani." shuru yayi min yana kallona..... Cikin damuwa nace" ka

Please Login or Register in order to submit comment