Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta daga kafafunta sama shi kuma sai bugunta yake tana nishi hade da sambatu.

Da sauri na dauke kaina ina fadin"Subahanallahi! kallonsa nayi naga idanuwansa sunyi jajawur! ya k'ura min ido yasa lips dinsa na kasa a baki yana tsotsa, tsorata nayi da yanayin sa nayi gaggawar kama hanya domin fita daga dakin wata zuciyar tace "Ki tsaya ki tunasar dashi abinda yake aikatawa bai dace ba.

Juyowa nayi still idonsa na tsaye a kaina, nace" Ranka ya dade kaji tsoron Allah kaji tsoron ranar haduwarka dashi, wallahi wannan abinda kakeyi sam bai dace da kai ba, yanzu meye amfanin ganin tsaraici Allah ya la'anci mutanan dake ganin tsaraicin wani wannan dan abun daka raina yana iya janyo maka fushin Ubangiji ranka ya dade a daidai wannan lokaci ya kamata ace kana massalaci kana salati kafin a kira sallar amma ka zauna kana kallon shed'anu kafurai wa'inda Allah ya la'ance su fisibilillahi meye fa'idar abinda kake aikatawa."
Har na kare maganata idanuwansa na tsaye a kaina. ganin bece min komai ba yasa na girgiza kaina na kama hanya zan fita.

A sanyaye naji ya kira ni "Sumayya." juyowa nayi a karo na biyu ina kallonsa, nadama nagani a fuskarsa, yace."Zo nan muyi magana." Zuwa nayi na durkusa gefansa ina addua Allah yasa ya dauki nasiha ta.


"Zoki zauna nan muyi magana." kusa dashi ya nuna min wai naje na zauna, gaskiya ba zanje ba dan ina tsoron abinda zai biyo baya.

"Ranka ya dade ba sai nazo kusa da kai ba zan fahimci abinda xaka fada kunnuwana naji duk abinda zakace." romot ya dauka ya kashe tv kana ya juyo yana kallona, ni kallon da yake min shine yake d'aga min hankali dan a tsorace nake a dakin.


Sai da ya gama kallona tukkuna yace."Naji nasihar ki nima kuma nasan abinda nake yi bashi da kyau na rasa yanda zanyi ne Sumayya a duk lokacin da kika gifta ta gabana sai naji sha'awarki a yanzu bani da muradin ko wace mace sai ke na roke ki ki bani kanki na rana guda na biya bukatata."

Ji nayi gumi na tsatstsafowa daga jikina kallonsa kurrum nake ina mamakin maganarsa, kallon da yake min shine ya tabbatar min da gaskiyar maganarsa duk ya koma kalar tausayi sai marairaice fuska yake yana kankantar da idanuwansa.......sunkuyar da kaina kasa nayi ina tunanin abinda zance masa, motsinsa naji a kusa dani da sauri na dago kaina ido muka hada yana gurfane a gabana ya wani zuba min idanuwansa kamar zai cinye ni.

Cikin wani irin yanayi na fargaba da tashin hankali nace"Ranka ya dad'e nasha fada maka baza ka samu abunda kake so ba, ni bana daya daga cikin irin matan dake sarayar da kima da mutucinsu inaso jikina da komai nawa ya zama mallakin mijina na sinna dan girman Allah da darajar Annabi kada ka sake yi min irin wannan maganar wallahi tallahi bazan ta'ba amincewa bukatarka ba kayi hakuri da maganata ranka ya dade kayi na farko kayi na biyu idan ka kuskura kayi na uku zan samu mahaifiyarka na fada mata abinda ke faruwa ka rabu dani da wannan maganar." Ido jawur nakare maganata inaso na tabbatar masa da cewa daf nake dana tona masa asiri.

a maimakon ya saduda sai ya sake kusanto ni ya matseni jikin kujera yana min wani shu'umin kallo gabadaya ya fita daga cikin hayyacinsa dan da alama ma bai ji barazana ta ba.

tureshi nayi ina kokarin mikewa ya rike hannuwana tsam na dinga kokarin kwacewa karfin ba daya bane hawayen fargaba ne suka soma zubo min.

Kirjina ya ban'kare min ya tsirawa nonuwana ido ajiyar zuciya ya sauke ya d'ora fuskarsa a kan kirjina yana wani irin abu, wani irin abu naji ya tokare min a wuya, hannuwa nayi yun'kurin kwacewa ya rike sosai ya cigaba da goga fuskarsa a kirjina sai nishi yake fitarwa.

Ya kai minti biyar yana iskancin da yake so kafin ya dago kansa, yawun bakina na tofa masa a fuska ina masa kallon banza nace"Yanzu me kaji da akayi hakan wato kai kai baka jin nasiha ko? kasan gaskiya kasan abinda kake aikatawa haramun ne shine ka ban'kare min kirji kana iskancin da kake so Allah ya isa."

Ajiyar zuciya ya sauke yace."Sumayya idan baki rufe bakin ki ba wallahi zanyi miki abinda yafi haka! har ni kike tofawa yawu saboda kawai ina bukatarki to idan baki fadawa mahaifiyata ba bakya kaunar Allah da annabi."

"Kaga yallabai sakar min hannu tunda kayi abinda kake so." a zafafe nayi maganar.....hannuwana ya sake d'amkewa yace."Wannan tsiwar taki ita zata janyo miki komai nifa ba cewa nayi sai na shiga ramin ki ba ki bani wannan kawai ya isa ya gamsar dani." Yana maganar yana kallon kirjina.

Shuru nayi zuciyata sai tunzurani take...."Sumayya ki taimaika min dan Allah ki bari na samu satisfaction dake ba zan rabaki da budurcin ki ba."

Hawayen da nake makalewa suka zubo a kumatuna ni yau na rasa wane irin mutum Allah ya had'ani dashi wannan wane irin naci ne? hawayen fuskata ya shiga lashewa yana tsotsar kumatuna, na dinga jin tsigar jikina na tashi bakina yake so ya kama na kautar da fuskarta, hannu yasa ya juyo da ita, muka dinga kallon juna, ''Kin amince ko."? cikin mayaudariyar mirya yayi maganar." Girgiza kaina nayi nace"Ban amince ba." mirya na rawa yace."To yanzu ya kike so ayi ni dai ba zan bari ki fita ba sai bukatata ta biya." shuru nayi ina shawarwari da zuciyata nace"Ranka ya dad'e sha'awata kake ba sona kake ba ko."? Eh ina sha'awarki Sumayya ki bani jikinki na biya bukatata." na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa..."Na amince zan baka jikina ka biya bukatarka amma ta hanyar aure." da sauri ya kalleni, kaina na daga masa nace"Ka aure ni na amince idan bukatarka ta biya a kaina ka sake ni ina ganin haka shine mafita.

Ina sane nayi masa wannan maganar saboda nasan abin ba zai yuwu ba.

"Ke a ganinki ni na dace da zama mijinki.''? cikin izgilanci yay maganar. Nace" Be dace ba amma ai kaji abinda nace ko nace idan bukatarka ta biya sai ka sake ni nidai ba zan baka kaina ba sai da aure.

Tsaki yaja da fadin''Ke bana san ki 'bata min rai ki sanja wata shawarar wannan ba tayi ba ni ba sa'an auranki bane kin gane ko.''? nace"To shikkenan sai ka danne sha'awarka a kaina tunda ka ki'yin yanda nace." Bina yay da kallo yace."ba zan aureki ba saboda baki dace dani ba ta kowane fanni kawai ki gindaya kudin da kike bukata sai na biya mutukar zaki mallaka min albarkatun jikinki.

Cikin zafin zuciya na ture shi na mike tsaye "Bana bukatar komai a gurinka na yanke shawara idan ba tayi maka ba sai kayi hakuri ." Kafata ya janyo da karfi na fada kansa matse ni yay a jikinsa daidai kunnena yace."Bafa fin karfina kikayi ba wallahi yanzu zanyi miki rashin mutunci ." Imani na cire na dasa masa hakora na a wuyansa, da sauri ya sake ni yana yamutsa fuska, da sauri na dauki dankwalina na daura na fita daga dakin, duk rintsi na daina shiga dakinsa sai dai duk abinda zaiyi min yayi.

Sai da muka dauki tsayin sati biyu bama magana da juna kullum idan na shiga sashen aikin gabana nake nayi tafiyata shima nasa bangaran fushi yake dani sosai dan har na gama aikina baya kallon inda nake kullum fuskarsa a murtuke, sai dai duk sanda Gimbiya Lawisa ta kawo masa ziyara ina shan dariya dan kafin su rabu sai sunyi fada yafi a 'kirga sam bata da zuciya sai tayi ta bashi hakuri alhalin duk rabin laifin nasa ne amma sai ta dauka ta dorawa kanta cikin zuciyata nace aiki ya same ki.


Hidima ce ta tashi a gidan sarautar sai shirye shirye ake ana gyara gurin da za gudanar da gagarimar Walimar da maimartaba ya shirya domin murna bud'e katafaran asibitin daya ginawa yaron nashi, hankalin Uwargida da 'yayanta ya tashi suka dinga sintiri a gidan suna 'kulle-'kullen yanda zasu tarwatsa taron jama'ar da maimartaba ya gayyato domin su tayashi farin ciki......Muddibo ya zama tamkar mahaukaci sai shige da fice yake gurin malamai burinsa kawai bukatarsa ta biya

Gama aikina kenan na fito da niyyar tafiya aunty Safiyya ta shigo, har 'kasa na durkusa na gaisheta, ta amsa a lokacin da take kokarin zama kan kujera, mikewa nai tsaye tace"Yarima na sama."? da sauri nace"E ranki ya dad'e." Tace."Je kice masa nazo yazo mu gaisa." Da sauri na amsa da to.

Aunty Safiyya na ganin 'bacewar Sumayya da sauri ta mi'ke ta isa bakin benan ta shiga barbad'a wani abu tana yi tana kiran sunansa, sai da tayi sau bakwai tukkuna ta koma ta zauna.


Bubbuga kofar dakin nayi gabana na fad'uwa! ciki ciki naji maganarsa, nace"Ranka ya dade aunty Safiyya ce tazo tana falo tana jiranka."

"Gani nan." abinda ya fada kenan. nayi saurin barin gurin, samun ta nayi tana duba wayarta nace"Ranki ya dade gashi nan zuwa." Tace."Okey kawo min ruwa." da sauri na nufi kicin domin cika umarninta.

Hannuna ri'ke da tire me dauke da goran ruwa da kwalin lemo na fito daga kicin din daidai lokacin da yake kokarin saukowa hawa biyu ya taka amma sauran be iya ba takawa ba kansa ya dinga juyawa yana ganin dishi dishi kafin nayi aune kawai na hango shi yana gangarowa! salati na kurma tire din hannuna ya fadi a guje na nufe shi ina kiran sunansa, duk tsayin benan da yawan steps haka ya dinga gangarowa yana buge kansa, zuwa nayi domin tareshi kafin nayi wani yunk'uri ya tunkud'e ni na fad'i a gurin tare muka dinga gangarowa har sai da muka dire kasa, na mike zumbur! ina nishi da salati! aunt Safiyya ta karaso gurin sai salati take tare muka isa inda yake kwance tamkar wanda ya mutu haka yay numfashinsa sai fita yake da sauri, wasu hawayen fargaba da tashin hankali ne suka shiga zubo min....."Ke! maza jeki dauko ruwa suma yayi." miryar ta ta dawo dani da sauri na bar gurin.....Tun daga nesa na hange ta tana danna kirjinsa tare da kara kunnanta a kirjinsa.. murya na rawa nace"Aunty ga ruwan! kar'ba tayi ta bude ta shiga shafa masa a fuska, shuru be farfado ba, jikina na rawa nace"Ranki ya dade ko naje na fadawa Mamma." Girgixa kanta tayi tace"Zo ki cigaba da shafa masa ruwan bari naje na sanar da maimartaba." Da sauri na zauna inda ta tashi na cigaba da shafa masa ruwan a fuskarsa kuka kawai nake ina tofa masa addua, kansa na tallafo na rungume a kirjina goran ruwan na ajiya na cigaba da tofa masa duk adduar da tazo bakina gabadaya na kasa tsayar da hawayen dake zuba.
Zazzafar ajiyar Zuciya ya sauke naji yayi motsi, da sauri na kalli fuskarsa naga ya bude idonsa Allah na godewa kana na kira sunansa, "Ranka ya dade sannu me yake damunka."
jikinsa ya cire anawa ya tsira min ido minti biyu kafin yace."Me ya faru jikina ciwo yake min.'' naji wani irin rauni gami da tsabar tausayinsa.
" Gangarowa kayi daga sama." nafada ina goge hawayen dake zubo min.'' juyawa naga yayi yana kallon tsayin benan.'" Ya juyo nai saurin kauda kaina...."Ina aunty Safiyyan." ?
"Taje kiran Maimartaba." mikewa yay yace."Zoki hada min ruwan zafi na gasa jikina kamar anyi min dukan tsiya haka nake ji.'' Na mike da sauri na rike hannunsa, kallona yayi nace."Kada ka sake hawa benan ka zauna a falo."

"Sabida me."? ya fada cikin sigar tuhuma! cikin fargabar masifar sa nace ni dai nace kada ka hau." Kasa yayi da kansa yana nazari kafin ya cire hannunsa yaje ya zauna a kan kujera, da sauri na nufi kicin......kanwa na jika a madaidaicin bokiti na fito benan na nufa da addua a bakina na shiga bin Steps d'in one by one ina yayyafa ruwan kanwar ina addua a bakina, sai da ruwan kanwar ya bushe na same shi a zaune a inda yake nace"Kana iya hawa." mikewa yayi ba tare da yace komai ba ya nufi saman nace"Ranka ya dade ka hau kana karanta ayatulkursiyu." bece min komai ba ya fara hawa steps din. ajiyar zuciya na sauke bayan hawansa Allah nagodewa kana nabi bayansa domin hada masa ruwan wankan daya b'ukata..




*Na kudi ne..!*
Kika karanta baki biya ba Allah ya isa, idan kina so ki biya kudinki ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
59&60
Tsaye na sameshi a bakin toilet din kallona yake har na karaso kusa dashi ina kokarin shige shi na shiga toilet din ya tare hanya, kallonsa nayi gabana na fad'uwa yace."Ki fada min gaskiyar abinda ya faru dani." Nace"Ranka ya dade abinda na sani shi na fada maka gangarowa kayi daka sama." Okey to meye amfanin abinda kika yayyafa a jikin steps. " yafada yana tsare ni da ido, duk sai naji gwiwata tayi sanyi ina jin tsoron kada ya zargeni da wani abun nace''Ruwan kanwa ne na yayyafa." "Kina nufin me kenan."? haushi ya bani nace" Dan Allah ka bar maganar tunda dai Allah ya kare shikkenan."

Shuru yayi yana kallona sauri nayi na shiga toilet din bayana ya biyo koda na ganshi a tsaye yana kallona sai na sake tamke fuska na hada masa komai na wankan da sauri na fita.

Wanka yake yana tunanin al'amarin jikinsa ya soma sanyi ya kuma soma gazgata abubuwan dake faruwa 'yan uwanshi na kokarin suga bayanshi ya rasa me yasa suka damu dashi da duk abunda ya Shafeshi sarauta suke so shi kuma baya so sune suke wahalar da kansu a banza.



Na jima zaune a falon ina jiran dawowar aunty Safiyyar shuru har kusan mintina talatin bata dawo ba cikin zuciyata nace dama karya take babu wanda zata kira, ajiyar zuciya na sauke ina mamakin al'amarin babu shakka wani mugun abun ta shigo dashi gashi nan yaso yayi tasiri a tare dashi mikewa nayi da fadin''Insha Allahu haka zaku gaji ku bari, gurin mu na nufa ina cike da mamakin al'amarin.


Aunty Safiyya tare da mahaifiyarta suna zaune suna sake tattauna maganar , tace"Nasan da wuya ya tashi dan lokacin dana fito daga sashen numfashinsa ya dauke jikinsa ya saki." Uwargida tace"Koda Allah yasa zai tashi to fatanmu ya tashi da nakasa so nake wani sashe na jikinsa ya lalace kafa ko hannu." Aunt Safiyya ajiyar zuciya ta sauke tace''Bari na koma sashen nasa domin ganin abinda ke faruwa.

Lokacin da ta shiga falon shuru taje ta tsaya a inda ya fadi tana mamakin ina yake, motsin saukowarsa taji tayi saurin daga kanta ganinsa tayi yana saukowa cikin kwalliya kamshin turaransa har inda take.

Gabanta ya dinga faduwa tana kallonsa yana saukowa sai murmushi yake mata, gwiwa a sanyaye tace"Kanina.'' yace."Na'am aunt Safiyya zauna mana kin tsaya." kujera ta nema ta zauna tana kallonsa ya zauna a kujerar dake fuskantarta, gaisheta yayi ta amsa jikinta sanyi kalau tace" Amma nayi mamakin ganin ka a haka dazu fa yanke jiki kayi ka fado daga sama, na fita a gigice domin naiman taimako abin mamaki kuma yanzu na ganka radau.

Yace."Nima a jikina naji abinda ya faru sai bayan na dawo daidai nake tambayar hadimata take sheda min abinda ya faru." Girgiza kanta ta shigayi kafin tace"Allah ya kiyaye gaba."

"Ameeen yace yana nazarinta ya soma hango rashin gaskiya a tattare da ita....gyaran murya yayi tayi saurin kallonsa yace." Aunt Safiyya na rasa abinda nayi wa mutane suke son suga bayana." Taji gabanta ya fadi jin abinda yace tace"Yarima ai dole mutane su nuna ganin kyashin su a kanka kai dai ka dage da addua.''


Murmushi yayi yace."Addua kullum cikin yinta nakeyi kuma a matsayinku na 'yan uwana ku tayani." tace"Kada ka damu dan uwana." Shuru falon yayi yace."Kin same aunt." girgiza kanta tayi yace."Na soma zargin wannan hadimar tawa domin dazu na ganta tana yayyafa wani abu akan stpes." yana maganar yana kallon reaction dinta

ta dinga kallonsa bakinta na rawa tace"To me take yayyafa wa ? kaji shegiya ko ta hada baki da wani a cikin gidan nan dan cutar da kai."?

Yace."Nima abinda nake zargi kenan." mikewa tayi zumbur ta nufin benan ta hau duddubawa! nan ta gane *kanwa* yarinyar ta zuba dan duk ga alamunta nan, lallai yarinyar nan bata da mutunci ta karya musu aiki, a sanyaye ta juyo suka hada ido dashi nan ya sake tabbatar da zarginsa gaskiya al'amarin ya bashi mamaki mutuka.

Zama tayi tana xage zage da fadin"Lallai sai ta tura an kira mata yarinyar ta turketa domin ta fada mata wanda ya turo ta ta zuba masa magani.

Yace."Aunt Safiyya ki barta kawai ni zan koya mata hankali daga yau ta bar aiki a sashena, tace."Eh dama hukuncin da zaka yanke mata kenan ni da kaina zan duba wacca ta cancanta ta kula da kai anjima zamu tare

Yace."To shikkenan godiya nake." Hira sukayi sama sama tayi masa sallama ta tafi, tana fita ya shiga mamakinta gabadaya yanayin data nuna ya tabbatar masa da rashin gaskiyarta, yana sane ya juya maganar kan Sumayya ya nuna ita yake zargi domin kawai yaga yanda zata nuna.


Shatima ne yay sallama ya shigo ya samu guri ya zauna yana kallonsa yace."Na ganka kamar kana da damuwa ina fatan ba aunty Safiyya bace dan naga fitar ta rai a bace.

Shuru yayi na minti uku kafin yace."Shatima al'amarin gidan nan yana bani mamaki mutuka ashe har yanzu ba zamu daina cin dunduniyar junanmu ba! ashe ba zamu kaunaci junanmu ba shin wai me muka mai da mulki ne? kowa babu alkairi a zuciyarsa kullum kudirinsa ya za'ayi ya cutar da jininsa ni aunty Safiyya ta shigowa guri da surkulle bansan me take nufi dani ba."

Shatima yace."Kayi min bayani yanda zan fahimta wane irin surkulle aunty Safiyyan ta shigo maka dashi."?


ajiyar zuciya ya sauke yace."Ina kwance a daki yarinyar nan Sumayya ta shiga take sheda min zuwanta lafiya lau na fito a dakina ina fara saukowa na fita daga hayyacina a yanzu zancan da nake maka jikina ciwo yake min.


Shatima mirmushin takaici yayi yace."Yarima kenan wato kai ka dauka zaka zauna lafiya a masarauta ko? to bari kaji na fada maka abinda ka tafi ka bari yana nan sai ma abinda ya k'aru Uwargida da 'ya'yanta suna nan suna shirya mugun abu Baba Ciroma da iyalinsa suma suna nan akan bakansu.....Baba Galadima shine mahaifina shima bazan rufe maka ba baya kaunarka dan saboda suna ganin kai zaka gaji sarauta dukkaninsu sunfi so saurauta ta dawo hannunsu saboda haka sai ka kula da kyau ni dai bana cikin tsarinsu dan mulki sam be dame ni ba shiyasa idan naga Muddibo na hauka yake bani mamaki Wallahi ni nafi bukatar kasuwanci na yafi min komai.

Yarima ajiyar zuciya ya sauke yace." Shatima su suka damu da mulki kasan Allah mulki baya gabana nafi bukatar na tsaya akan aikina na taimakon marasa lafiya nayi mamaki sosai da jin wannan magana, Muddibo duk yanda muke dashi ashe adawa yake dani."

Shatima yace."Ban fada maka wannan magana ba dan ka 'kullace su inaso dai ka kula sosai ka daina sakewa da duk mutanan dana lissafo maka wallahi basa kaunarka Waziri da iyalinsa ne kawai ke kaunar cigabanka." Yarima Ali shiru yayi yana mamakin al'amarin Shatima yace."Shiyasa fa sam banyi na'am da auranka da Lawisa ba nasan zasu Iya Shiryo wata ma'karkashiyar ta 'bangaranta."
Da sauri yace."Ni dama sam yarinyar ba tayi min ba wallahi tunda abun ya zama haka zan samu maimartaba akan maganar.
Shatima ya girgiza masa kai da fadin"Kada ka yanke wannan hukuncin tunda dai an riga an tsayar da magana sai kayi hakuri kasan ko kaje ka cewa maimartaba ka janye ba zai yarda ba sai anyi."
Shuru yayi yana tunanin maganar.




Washe gari da sassafe na tashi nayi mana Wanki nayi wanka na fito ina tsaka da shiryawa Tambaya ta shigo dakin ta same ni, tunda na ganta a sanyaye nasha jinin jikina tace"Sumayya jikina yayi sanyi jin Uwargida ta aiko kiran ki.

Gabana ya fadi jin abinda tace nace''Yaushe ta aiko." Tace"Yanzu yanzu. cikin tararrabi da faduwar gaba nace"Ki kwantar da hankali babu wani abu tunda dai nasan banyi mata komai ba ko naje ba zata tuhume ni ba."

Tace" To Allah yasa kiyi sauri kisa kayan ki kije. dankwalina na daura nace bari naje daga can zan wuce sashen Yarima tace."To Allah yasa muji Alkairi.


Koda na shiga falon sai da nasha jinin jikina ganinsu duk sun kewayeta fuskokinsu babu fara'a zubewa nayi ina gaishesu babu wacce ta amsa a cikinsu na sunkuyar da kaina cike da ladabi nace"Ranki ya dade gani."

Zama ta gyara tana kallona tace"Wama sunanki." da sauri nace"Sunana Sumayya Lawi." Tace"Ubanki wace irin bauta yake a cikin gidan nan."? nace"Yana bautawa Dawakai ne." Ta ya mutsa fuska tana wasa min kallon banza tace"Kece kika wargaza mana aikinmu na jiya ko."? mirya na rawa nace"Ranki ya dad'e wane irin aiki."? Wani bahagon mari aunty Safiyya ta kwada min tana huci! tace"Kada ki raina mana hankali dan ubanki tambaya ma kike."?

Ido jawur nace"Tuba nake ranki ya dade." Uwargida tace"Kalle ni da kyau."! na dago kaina ina kallonta, tace."Kinyi na farko kuma kinyi na karshe wallahi tallahi duk sanda mukaje muka gudanar da aikinmu kika karya sai na saubata miki rayuwarki sai kin rasa ruwan kur'ba a masarautar nan ki tsaya a matsayin ki na baiwa babu ruwanki da Yarima duk wani abu da zamuje sashen mu gudanar ido ne naki."

Nace"Ranki ya dade ku gafarce ni wallahi ban san wane aiki na lalata muku ba." Gabadaya zuba min ido sukayi, aunty Safiyya tace"Wato ba zaki daina wannan maganar ba ko. " shuru nayi tace"kinji abinda aka ce ko baki ji ba."? da sauri nace"Naji ranki ya dade....tace"Na tura hadima daga nan bangaran zata dinga saka mana ido akanki babu ruwanki akan dukkanin abinda zata gudanar aiki muka sata kiyi aikin ki tayi nata." nace insha Allah zan kiyaye." Aunty Bishira tace"Sumayya idan kika sake 'bata mana aiki a karo na biyu sai kin zubar sa hawaye wallahi tallahi mummunan mataki zamu dauka a kanki." Nace."Ranki ya dade zan kiyaye insha Allah."

"Tashi kije." uwargida ce tayi maganar, sunkuyawa nayi da fadin"Na barku lafiya." babu wacce ta kulani da sauri na fito gabana na bugawa, kai tsaye sashensa na nufa ina shiga na tarar da sabuwar hadimar da suka turo tana goge goge, harararta nayi na wuce, samansa na hau na tsaya bakin kofa ina bugawa
"Waye"? da sauri nace" Nice." "Kije babu abunda nake bukata an riga an gabatar min da komai." abinda yace min kenan ba tare da ya bude kofar ba, tsaye nayi ina mamakin maganarsa, an riga an gabatar masa da komai hakan na nuna min cewar dasa hannunsa gurin zuwan sabuwar Hadimar, na kai minti biyar a tsaye ina sa'kawa da kwancewa kafin na sauka kasa na sameta tana ta aiki.....hararar ta na sakeyi ina jin wani irin mugun haushinta, hanya na kama zan fita tace"Ke Sumayya wai me nayi miki ne tunda kika shigo kike hararata."
Juyowa nayi kamar zanyi magana sai kuma na fasa tsaki mai karfi naja na fice na barta taba bina da kallo

Koda na koma sashen mu kasa nutsuwa nayi na dinga tunane tunane marasa kyau ina idar da sallar magariba na koma sashen, babu kowa a falon shuru sai kamshi yake tsayawa nayi zuciyata sai sa'ke-sa'ke take min kai tsaya benan na nufa, hannu nasa na buga shuru beyi magana ba na sake bugawa gabana na faduwa gani nake Suwaiba na cikin dakin, can naji muryarsa a shaqe yana fadin"Waye."? da sauri nace"Nice ranka ya dade ka bude na gyara maka dakin." Still muryarsa a hard'e yace."Kije bana bukata." Gabana ne ya dinga faduwa kawai naji kwalla tana

Please Login or Register in order to submit comment