Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta samu labarin abinda kukeyi ba zakuji dad'i ba.

A sanyaye ya sosa kansa cikin jin kunya yace."Sumayya dan Allah kiyi hakuri wallahi ni ban fiya haikewa 'yan matan masarautar nan ba su Dantala ne masuyi kema yanzu hankalina ne ya tashi sosai shiyasa na gaza hakuri na kai hannuna mazaunanki amma kiyi hakuri dan Allah kada naji maganar a bakin kowa.
Cikin takaici na girgiza kaina tare da juyawa na cigaba da tafiya raina a masifar 'kuntacce.

To koda Usuman ya duba babana nan ya gano cewa hawan jini ne ke damunsa hankalinmu ya tashi nida tambaya muka dinga kuka dan mun riga mun san ciwon hawan jini babban ciwo ne gani muke kamar mun kusa muyi bankwana dashi shiyasa gabadaya hankalinmu ya tashi....Usuman ganin duk muna hawaye yasa ya rarrashe mu tare da bamu shawarwarin yanda zamu kula dashi da lafiyarsa yace "Insha Allahu mutukar aka bi dokar da ake bukata masu dauke lalurar suka bi to zai samu lafiya, Ya miqe tare da fad'in " Zaije yanzu ya kawo masa magungunan da zasu taimaka masa...godiya mukayi masa muna zubar da hawayen tausayi......
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_



*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)

7&8
Tamkar mai tausayin taka k'asa haka yake cire qafa yana tafiya kanshi a 'kasa hannuwansa a goye a baya, Shatima da Moddibo suna gefe da gefansa sai hira sukeyi masa yana dai jinsu da kunne amma ya gagara cewa uffan sai dai idan sun fadi maganar da ta bashi dariya yayi murmushi had'e da girgiza kansa, Yarima Ali mugun miskili ne wanda magana ke masa wuya shiyasa mafi akasari mutane ke ganin kamar dan wulakanci ne 'Dabi'arsa ce ta rashin son magana da hayaniya gami da rashin fara'a 'yan uwansa da iyayensa sun san wannan halin nasa tun yana yaro dashi ya taso, tun kafin su qarasa bakin kofar masu tsaron gurin suka zube gwiwowinsu a kasa sunkuyar da kansu sukayi hade da d'unkule hannuwansu alamun gaisuwa.
Shatima da Moddibo ne kawai suka d'aga musu hannu shi kuwa gefan da suke ma bai kallaba ballantana yasan sunayi.......Shatima ne yasa hannu ya bude narkekiyar kofar da zata sada su da falon Fulani wato mahaifiyarsa, A nutse yasa kafarsa cikin falon tare da sauke ajiyar zuciya, lumshe idonsa yayi yana jin wani irin sanyi na ziyartar zuciyarsa yau dai Allah ya dawo dashi gida gaban iyayensa hakika babu wanda ya kaishi farin cikin wannan rana......Bude lumsassun idanunsa yayi ya sauke su a kanta tana gishingide kan kilishi jakadiyarta na gefanta a zaune tana mata firfita da wani irin mafice, Mama fulani kyataccan murmushi ne a fuskarta ta zuba masa ido tana jin wani irin farin ciki a cikin zuciyarta.

Da sassarfa ya k'arasa kusa da ita yayi zaman raquma a gabanta tare da sunkuyar da kansa yace."Mammah hakik'a yau ni dake ban san wanda yafi wani farin ciki ba nasan zuciyarki tana cike da farin cikin dawowata gida wannan dalilin ne ya sanya na kasa shiga sashena nace lallai sai nazo nayi tozali dake uwa tagari nayi farin ciki dana dawo gida na sameku cikin koshin lafiya keda maimartaba da duk wani makusancina."

Ajiyar zuciya ta sauke ta gyara zamanta hannu ta dora a saman kansa a nutse tace"Allah yayi maka albarka babana nayi mutukar farin cikin dawowarka masarauta lafiya tabbas farin cikin da nake ciki a yau ba zai yafi gaban a kwatanta shi zuciyata tas take da ganinka cikin koshin lafiya babana ka kara girma kayi lafiya ka kara nutsuwa ka cika mutum ta kowane 'bangare babu shakka dole nagodewa ubangiji a bisa wannan karamaci da yayi mana ina rokon Allah ya raya min kai ya albarkaci rayuwarka da zuriar da zaka samu."

Hannunta dake saman kansa ya r'iko yasa a bakinsa ya sumbuta lumshe idonsa yay yana murmushi yace."Mammah nagode sosai da adduarki akoda yaushe ina alfaharin kasantuwarki a matsayin mahaifiyata."

Murmushi tayi tare da girgiza kanta ta mayar da hankalinta kansu Shatima dake zaune a gefe da gefansa, murmushi ta sakeyi tana kokarin magana suka fara gaisheta, hannunta ta d'ora a saman kansu tace"Ubangiji Allah yayi muku albarka ya had'e kanku kuyi zumunci dan Allah tabbas nasan kuma yau kuna cikin farin cikin dawowar d'an uwanku lafiya." Shatima yace.''Hakane Mammah hakika muna cikin farin ciki mara mislatuwa muna yiwa Allah godiya daya dawo mana dashi gida lafiya.

Har yanzu da murmushi a fuskarta tace"Yana da kyau ku rakashi ko wane 'bangare na gidan nan ya gaisa da iyayensa kamar yanda yazo ya gaisa dani."
Moddibo yace."Insha Allahu Mammah." Kallonsa tayi har yanzu yana durkushe a gabanta tace"Babana zakuje sauran sashen iyayenka ku gaisa kafin ka shiga gurinka ka huta nasa hadimai sun shirya maka komai da komai." Hannunta ya sumbata cike da bin umarni yace."Mammah abinda kikace shi za'ayi insha Allah."! Miqewa yayi a nutse ya kalli 'yan uwan nasa da fad'in " ku Tashi muje." Shatima da Moddibo suka miqe kai a kasa suka ce "Mammah a tashi lafiya." Hannu ta d'aga musu fuskarta yalwace da fara'a idonta a tsaye a kansu har sai da suka fita daga falon ta girgixa kanta gami da sunkuyar da kanta kasa addua take a cikin zuciyarta kan Allah ya cigaba da had'a kawunansu suyi zumunci tsakani da Allah.

*Tushen Labari*
Maimartaba Sarki Adamu Abdullahi dattijon mutum ne wanda ya iya mulki gami da jagoranci akan komai maimartaba Adamu Abdullah mutum ne mai tsananin tausayi da jin'kai, baya ta'ba yarda talaka ya kaskanta kuma bai yarda da cuta gami da zalinci ba, al'ummar garin suna mutukar jin dadin mulkinsa gami da yanda yake gudanar da hukunci akan wanda yayi zalinci, Sarki Adamu yana da 'Ya'ya amma dukkaninsu matane d'aya ne Namiji a cikinsu, sai dai 'yan uwansa suna da yawan 'ya'ya maza shi kadai Allah yayiwa albarkar 'ya'ya mata sai ya bashi guda d'aya namiji wanda yake mutukar alfahari dashi kasancewarsa mai tsananin biyayya a gareshi.....Mahaifin Waziri da galadima ya rasu dama a hannunsa suka taso tare da 'ya'yansa tare kuma duk suka gudanar da harkokin karatunsu.........Sulaimanu Dan uwan Sarki Adamu ne ciki daya suka fito shine ya kasance mafi kusa dashi a fada sarki Adamo baya zartar da kowane irin hukunci sai yayi shawara da d'an uwansa wato Waziri Sulaimanu, duk da wannan karamcin da maimartaba keyi masa hakan bai sa ya janye muguwar kiyayyar da yake masa ba da shida zuriarsa kullum burin Waziri Sulaimanu yaga bayan d'an uwansa dan ya tsani ya wayi gari ya ganshi kan karagar mulki.......Shi a yanzu baya sha'awar mulkin tunda shekaru sunja masa yafi sha'awar d'ansa Ciroma ya hau kan kujarar badan komai ba sai dan kada bayan babu ransu a duniya mulki ya cigaba da tabbata a hannun zuriar dan uwan nasa wato Sarki Adamu, shiyasa kullum cikin damuwa yake gami da tunanin ya za'ayi ya ruguza karagar mulkin d'an uwan nasa, Kullum cikin shirya manakisa suke shida d'ansa Ciroma maimartaba sarki Adamu Allah na kareshi daga sharrinsu, Waziri Salmanu ganin ya kwanta ciwo sai jikinsa yay sanyi yana ganin kwanansa ya kare bukatarsa bata biya a kan dan uwansa ba, tabbas jikinsa na bashi mutuwa zaiyi sai kawai ya kira d'ansa ya zaunar dashi suka yanke shawarar karshe a tsakaninsu.......Ciroma mutum ne mara tsoron Allah da tunanin makomarsa, Kai tsaye ya shiga biye biyen malaman tsubbu bai bari ba har sai da bukatarsa ta biya ganin ya durkusar da maimartaba, mugwayen aljannu sun shafe jinsa da ganinsa kana sun kumbura masa jiki yana kwance sai sai komai ayi masa.....Wannan al'amari yayi wa Waziri Sulaimanu dadi mutuka yana kwance rai a hannun Allah amma 'kara tsarawa d'an nasa sharri yake yi.
Hankalin iyalan Mairataba ya tashi mutuka gaya jama'ar gari suka shiga tsananin tashin hankali da damuwar rashin lafiyar data samu shugaba nagari malamai suka dinga bada taimakonsu iyakacin bakin kokarinsu.......Waziri Sulaimanu ya tara su kaf a guri daya yace"Tunda al'amarin ya kasance a haka to shi a matsayinsa na mai zartar da hukunci da yawun d'an uwansa wato maimartaba Sarki Adamu ya wakilta AbdulJabbar wato Ciroma ya zauna kan karagar mulki kafin aga abinda Allah zai zartar.....Da yawa daga cikinsu babu wanda yay na'am da wannan hukuncin to amma saboda gudun tashin hankali da gutsiri tsoma yasa sukayi fatan alkairi ga hukuncin da ya yanke........ba'a wani ja dogon lokaci ba Ciroma ya soma zama a fada ya cigaba da gudanar da mulki cikin rashin iyawa gami da tsantsar mugunta da zalinci.........A take jama'ar gari suka gane inda ya dosa gabad'aya yafi bada muhimanci akan harkar zalinci ko sharia aka kawo gabansa baya iya yanke hukuncin da sharia ta tanadar shi a ganinsa duk abinda yake daidai ne, Jama'a suka dinga k'orafi gami da surutai har labari ya isa kunan gomnati, a lokacin ta shigo cikin al'amarin bata kuma ja wani dogon lokaci ba ta sauke Ciroma daga kan kujerar mulkin, sannan kafin gomnati ta d'ora wani a matsayin sabon sarki sai da ta duba cancanta tukkuna ta za'bi Abdul-aziz ya maye gurbin mahaifinsa tunda shi cuta ta kwantar dashi.......Komai na saurata gomnati ta damqawa Abdul-aziz jama'ar gari suka dinga farin cikin samun sa a matsayin shugaba.......Wannan al'amari yayi wa Waziri Sulaimanu da d'ansa ciwo dan Ciroma kulle kansa yayi a daki ya dinga bankar giya yana tam'bele shi kadai sai zage zage yake yana surutai...........Waziri Sulaimanu kuwa sai muce tsabar bacin rai ne yasa ya had'iyi zuciya ya mutu sai shiga akayi aka ga gawarsa.....Hankalin iyalansa yayi tsananin tashi suka dinga kuka suna tofin alatsine ga zuriar Adamu suna ganin kamar sune sukayi sanadiyar mutuwar mahaifinsu.......Tun daga mutuwar Waziri Sulaimanu gaba mai tsanani ta shiga tsakanin zuria guda biyu har yanzu kuma itace akeyi 'ya'ya da jikoki sai dai kowa na kokarin 'boye bakin cikinsa akan dan uwansa amma daidai da kwayar zarra babu mai kaunar d'an uwansa..........bayan rasuwar Waziri Sulaimanu da sati uku Ciroma yabi dare da rana yaje ya sanyawa Sarki Adamu fillo ya toshe masa hanci murus! ya kashe shi har lahira ya fito daga dakin ba tare da kowa ya ganshi ba.....Shima iyalinsa shiga sukayi suka ga gawarsa al'amarin da yayi masifar tashin hankalinsu, Mutuwar Sarki Adamu ta girgiza zukatan al'ummar gari dayawa yawansu suka dinga kokawa suna fad'ar kyawawan halayensa............
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_





*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah)
11&12
Tun bayan fitar su Satima daga 'bangaransa yake zaune shi kadai a guri guda ya gaza ta'buka komai kallon kasan d'akin kawai yake yana mamakin abinda ke faruwa a masarautar a lokacin da ya tafi karatu yana da kuruciya shiyasa baya saurin gane wasu abubuwan amma yanzu shigarsa sauran 'bangarorin gidan domin gaisawa dasu ya fahimci cewar har yanzu bata sauya zani ba a tsakanin iyalan mutane uku da suke da muhimmacin a masarauta ba'a ga maciji kowanne da akwai mugun abu a zuciyarsa dangane da d'an uwansa, Lokacin da suka shiga bangaran mai babban daki gabad'aya sun hallara a falo ita da 'ya'yanta sun kewaye ta babu wanda yasan abinda suke qullawa sai Allah.......Ganin shigowarsu ne yasa suka daidata nutsuwarsu suna masa barka da zuwa dukkaninsu sai ya'ke sukeyi da kokarin nuna masa kulawa, shi ba yaro bane ballantana ya kasa gane yanayin fuskokinsu dan wasu daga cikinsu sai satar kallonsa suke ta'kasan ido, dalilin daya sa kenan ya kasa zama ya miqe da niyyar tafiya........Uwargida na fara'a kamar gaske tace"Magajin Sarki ka tsaya kaci abincin ma tun safe 'Yan uwanka suka baro gidajan mazajensu suka yini suna shirya maka abun tar'ba."
Ba tare da ya kalleta ba yace."Nagode Gwaggo ina ganin za'a iya kai min abincin sashena idan na samu nutsuwa sai na zauna naci." Ta washe bakinta cike da jin dadi tace"To shikkenan yanzu zansa a kai maka kamar yanda ka bukata."
A nutse ya juya domin yiwa 'yan uwan nasa godiya sai kawai yaga sunyi masa caaa! da ido da sauri ya sunkuyar da kansa yana mamakin kallon da suke masa tamkar basu taba ganinsa ba, babu cikakkiyar walwala a maganarsa yace." My Aunt's ina godiya da hidima." Da farin ciki a fuskokinsu suka shiga amsawa, rufaffun takalmasa yasa ya fita daga falon, a tsaye a samu su Shatima na jiransa ya fito, kai tsaye suka wuce side din Baba Waziri nan ya samu cikakkiyar karba da kulawa gurin matayensa kamar yanda yake tsammani cike da jin kaunarsu yay musu sallama, Bangaran Ciroma da Galadima kuwa bai samu wata cikakkiyar kulawa ba dan kafatanin su adawa suke dashi Shatima da Moddibo ne kawai suke d'an nuna masa kauna da kulawa suma d'in Allah ne kad'ai yasan abinda ke zuciyarsu.......Wannan dalilin ne yasa tunda ya zauna yake tunanin al'amarin a rayuwarsa ya tsani rabuwar kai da lalacewar zumunci! ya fahimci suna masa hassada sosai saboda mahaifinsa ne ke kan mulki dukkaninsu suna zargin kamar shine zai maye gurbin mahaifinsa bayan Allah ya dauki ransa wanda shi kuma basu san mulki da wani abinda ya shafeshi baya daga cikin tsarin rayuwarsa, a wannan zamanin jan ragamar al'umma na da wahala mutuka shiyasa gabadaya baya da ra'ayi maye gurbin mahaifinsa.
Ya jima zaune a gefen katafaran gadonsa daya sha shimfid'u na alfarma irin na saurata kafin ya miqe a nutse ya nufi toilet din wanda shi kansa abin kallo ne duk abinda mutum ke bukata a kwai a cikin toilet d'in, tsaf yayi wanka ya fito daure da towel a k'ugunsa, a bakin k'ofa ya samu wani bawa hannunsa ringume da kayan sawa irin na sarauta.
Gefan gado ya samu ya zauna ba tare da yace komai ba, bawan ya karaso tare da durkusawa a gabanshi yace."Ranka ya dade ni sunana Haruna ni zan dinga yi maka hidima da duk abinda kake bukata na shigo naji kana wanka sai na dau'ko maka tufafin da suka dace.''

A nutse ya d'ago kansa yana kallon kayan dake hannun bawan, manyan kaya ne irin na saurata har da nad'i da katuwar alkyabba sam ba zai iya sanya kayan nauyi a jikinsa ba.

Girgiza masa kansa yayi a nutse yace."Mayar da wa'innan kayan ka dauko min masu sauki." Da saurin ya miqe da kayan a hannunsa ya bud'e shirgegiyar wardorobe din dake kafe a bangon dakin ya ajiye kayan tare da nemo masa irin kayan da yake bukata......Farin yadi filtex mai taushin gaske ya dauko mashi ya jiye kusa dashi kana ya sake komawa wardorbe din ya dauko wani dan madaidaicin akwati shima yazo ya ajiye masa a kusa dashi........Wata iriyar hula naga ya dauko mai tafe da takalminta yazo ya tsuguna tare da cire ledar data lullube hular da takalmin ya d'ora kan kayan ya miqe tsaye da sauri tare da matsawa gefe guda kansa a kasa yace."Ranka ya dad'e na dauko maka dukkanin abin bukata ka duba ka gani idan da akwai wani abinda kake bukata.

Gefan da kayan suke a ajiye ya duba minti biyu yana kallon gurin kafin yace."Jeka nagode." Da sauri ya sunkuyar da kansa kasa gami da fadin"Godiya nake Magajin sarki." yana gama maganarsa ya bude kofar dakin ya fita da saurin gaske........A nutse ya miqe ya nufi gaban mirror din dake cike da kayan shafe shafe da turaruka na mussaman irin na masu sarauta, Cream kawai ya shafa a jikinsa ya shafawa jikinsa turare mai kamshi, kana ya bar gurin, tsaf ya shirya jikinsa cikin farin yadin wanda akayi masa d'inki mai yankakken hannu irin na zaman gida gaban rigar da bayanta anyi aiki da farin zare wanda yake nuni da tambarin masarautar, a nutse ya bude akwatin nan naga tarin agoguna da manya manyan zubonan azurfa kala kala sai sheqi sukeyi, agogo mai sarqa yasa a hannunshi na dama kana ya zura wasu zubonan azurfa a tsayunsa guda biyu na hagu da dama, zubonan suyi masa kyau sosai da sosai. ya mayar da a kwatin ya rufe ya dauki hular yana gyarata hula ce aka d'inkata da wani irin yadi mafi akasari ma masu saurata suke amfani da ita tsayin hular ne ya bashi dariya ya dinga duba hular yana tunanin ajiyeta ya bar kansa a haka sai dai yayi dubarar lankafe saman ta ya rage mata tsayi yasa a kansa kana ya zura takalman dake gabanshi masu kalar hular .....Gaban mirror ya tsaya yana sake duba kansa, murmushi ya dinga yi yana shafa siririn sajen fuskarsa lallai malam bahaushe yayi gaskiya da yake fad'in kowa ya bar gida to gida ya barshi, yaushe rabonsa da sanya manyan kaya a jikinsa, sai yaga shi kansa ya k'arayiwa kansa kyau da kwarjini wannan zungureriyar hular da yake wa dariya yaga tayi masa kyau sosai ta sake fito masa da kewayayyar fuskarsa mai dauke da k'ayataccen sajensa, ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya bar gurin mirror kai tsaye hanyar fita daga dakin ya nufa...........Yana fitowa Haruna dake tsaye kamar gunki a kofar dakin yayi kasa da kansa tare da fadin"Barka da fitowa." Ba tare da yace masa komai ba ya wuce cikin falon.....Nan ya ganta a hakimce a kan kujera k'afarta d'aya kan 'daya tana sakar masa kyakkyawan murmushi...........Idonsa a tsaye a kanta ya samu guri ya zauna cikin d'aya daga cikin k'ayattatun kujerun dake kewaye da falon Wani irin zama yayi irin na masu mulki yasa mata idonsa yana kallo fuskarsa babu d'igon annuri.
Gimbiya Lawisa cikin iyayi da iyawa ta ma'kale murya tare da fadin "Barka da fitowa magajin sarki inayi maka barka da dawowa masarauta lafiya."
falon shuru yayi bayan gama maganarta tana jiran amsarsa taji shuru bece komai ba, dago kai tayi tana kallonsa taga yana ta kallon jikinta.......Yarima Ali na da muguwar d'abi'ar san mata dan ko acan amurukan ma shagalinsa ya sha da matan turawa da bakaken fata amma duk kulafucinsa bai ta'ba zina ba sai dai romancing nan yake biyawa kansa bukata, yana da bala'in san mata masu kyau da k'irar jiki, Gimbiya Lawisa nada kyau da lafiyayyan jiki shiyasa ya gaza dauke idonsa daga kanta sha'awarta ce ta d'arsu a zuciyarsa. Ganin tana kallonsa tana murmushi yasa yayi gyaran murya da kyar yace."Daga wane 'bangare kike.''? 'Yar dariya tayi tana kallonsa tace"Yanzu dan Allah baka gane ni ba ? nice fa Lawisa ta gurin Baba Ciroma 'kanwar Moddibo."'
Sajensa ya shafa har yanzu babu fara'a a fuskarsa yace."Ya za'ayi na gane ki bayan rabona daku sama da shekara goma lokacin dana bar gida ina tsammanin baki kai shekaru bakwai a duniya ba."
Tace"Eh hakane kam shekaruna takwas a lokacin daka tafi karatu amma kuma ni kaga ban mance da kai ba."! Shuru yay yana kallonta, Ta cigaba da cewa"Wannan dalilin ne yasa ma na shirya gagarimar walima domin taya ka murnar dawowa gida lafiya.'' Murmushi yayi yana kallonta yace."Nagode 'Kanwata inaso naga ana nuna kulawa akaina nayi farin ciki sosai da wannan karamcin yaushe ne kika tsayar da taron.

Cikin farin ciki da jin dadi tace"Naji dadi sosai daka kar'bi magana ta da mahimanci nagode sosai sannan kuma ranar jumaa ne ranar dana tsayar domin taron walimar." Da ragowar murmushi a fuskarsa yace."To shikkenan Allah ya kaimu ranar lafiya."
Falon yayi shuru Lawisa sai sa'ke-sa'ke take a cikin ranta tana tunanin ko kawai ta fad'a masa tana sonsa tunda taga nan da nan ya kar'bi maganar da ta kawo masa da muhimanci.....tana kokarin tayi magana......Aunty Safiyya d'aya daga cikin yayyunsa ta shigo falon bayanta wasu bayi ne mata guda biyu suna dauke da tire din abinci kai tsaye can gurin daining suka..........Aunty Safiyya ganin Lawisa a zaune tana murmushi yasa tayi saurin kallonta ta kalli 'kanin nata sai kawai taji farin cikin ganinsu a tare lallai babu shakka Lawisa zata taimaka musu gurin ganin bukatarsu ta biya a kansa.....Cike da farin ciki gami da nuna jin dad'i tace"A'a k'anina soyayya akeyi ne.'' Kansa ya sunkuyar qasa bece uffan ba.
Ita kuwa Lawisa sai murmushi takeyi na jin dadi tana kallon aunty Saffiyan tana sunkuyar da kanta.
Kusa dashi taje ta zauna kamar gaske ta dafa kafad'arsa da fadin'' A gaskiya nayi farin cikin ganin ku a tare dama babban burinmu a yanzu kayi aure ka sake zama babban mutum to alhamdullilahi tunda ma 'yar gida za'ayi towo na mai na ne abun yayi dad'i nasan kuma iyayenmu zasuyi farin ciki mutuka, kuma inaso na tabbatar maka da cewar kayi sa'ar matar aure domin dai Lawisa babu abinda ta nema ta rasa na bangaran kyawun hali ga uwa uba kyawun sura."

Ya d'ago kanshi a nutse yana kallonta "Aunty Safiyya waye yace miki soyayya muke? fitowa ta kenan daga daki na sameta a zaune dan sai da ta gabatar min da kanta na gane cewar famliy nace, tazo tana sheda min walimar da ta shirya domin murnar dawowata gida wannan shine dalilin daya saka kika gan mu a tare."
*BINTA UMAR ABBALE*

Shearing 👏🏻👏🏻
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_



*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
9&10
Sarki Abdul-aziz yayi gadon halin mahaifinsa marigayi Maimartaba sarki Adamu gurin kyawawan halaye sosai al'ummar gari ke jin dadin mulkinsa gabadaya 'yan uwansa sunyi masa mubaya ma'ana sun bashi hadin kai sosai amma banda Ciroma muguwar hassada yake masa da kasantuwarsa a kan karagar mulki Ciroma babu irin qulunboton da ba yayi akan ya ruguza mulkin sarki Abdul-aziz Allah bai bashi nasara ba daga karshe sai ya hakura da biye biyen bokayen ya dawo yana shirya mana'kisa ta karkashin qasa....Sarki Abdul-aziz na da mata biyu Gimbiya Huwaila itace uwar gida ana kiranta da mai babban da'ki haihuwar su bakwai tare amma duk mata ne.....Gimbiya Hawwa 'yar sarkin Agadaz itace matarsa ta biyu ana kiranta da Fulani sai da suka shekara shida da aure ta samu ciki maimartaba ya tsananta addua akan cikin yana addua akan Allah ya azurtashi da samun d'a namiji ya zama magajinsa...........Allah maji rokon bawansa sai ya amsa masa adduarsa a daidai lokacin da mutane ke tsammanin Fulani zata haifi mace sai Allah ya nuna musu ikonsa Aliyu ya diro duniya cikin koshin lafiya da kuzari.....Haihuwa wannan yaro tayi masifar tashin hankalin Ciroma ya rasa inda zai saka kansa yaji dadi, shi duk a tunaninsa Abdul-aziz ba zai ta'ba haihuwar da namiji ba saboda yana ganin duk 'ya'yansa mata ne kamar dai yanda mahaifinsa ya dinga haifar 'ya'ya mata kafin ya rasu.......Mai d'akinsa rasa gane kansa tayi a lokacin dan kulle kansa yake a daki yayi ta surkulle lallai sai yaga karshen jinjirin daka a haifa, wanda tunda ya dira a duniya mahaifiyarsa ta d,daura masa wata 'yar sar'ka a wuyansa mai dauke da ayatulkursiyu a jiki, wannan dalilin yasa duk tsaface tsafacen da yake yi baya tasiri.

'Bangaran Mai babban daki kuwa itama ita da yaranta rasa nutsuwa sukayi dan gabad'ayansu basu tsammanin Fulani zata haife cikin jikinta lafiya ba saboda irin fadi tashin da sukeyi a cewar 'ya'yan wai su ba zasu had'a uba da kowa ba shiyasa tun sanda

Please Login or Register in order to submit comment