Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

'yan uwansa suka shiga tsaftace dakin, ni kuma na kama hanya na fita daga dakin ganin ko kallon inda nake beyi ba.

Alwala nayi nai sallah na fito na sake zama ina saka wasikar jaki, muryar babana naji yana sallama da sauri na daga kaina sai na gansu shida Tambaya, wani irin farin ciki ne ya ziyarci zuciyata dama kwana biyu dauriya kawai nake da tunaninsu nake kwana nake tashi, da sauri na mike naje na taresu ina dariya nace"Baba sannunku da zuwa naji dadin zuwanku." Tambaya tace"Muna ta sa ranar zuwa Allah bai nufa ba sai yau." Cikin kulawa babana yace."Ai izini na nema gurin Fulani amaryar Maimartaba shine tasa aka kawo mu."

Nace."Aikuwa naji dadi sosai da zuwanku kuzo muje nayi muku jagora." Hannunsa na rike muka nufi dakin..............Yana zaune a inda yake da alama ma baiyi sallah ba cikin zuciyata nace"Saboda rashin kula da addininsa komai aka nufe shi dashi na sharri yana iya kamashi, a zahiri kuwa cewa nayi "Ranka ya dad'e fatan ka wuni lafiya ga Iyayena sunzo domin su dubaka." Dago kansa yayi yana kallonsu, su kuma sun sunkuyar da kansu kasa cikin ladabi da tausasa harshe suke gaisheshi, sai naga shima ya sassauta muryarsa ya amsa cikin kulawa yana nuna musu gurin zama da hannunsa.

Yanda ya tar'bi iyayena da sakakkiyar fuska yasa naji dadi a raina, nace"Baba ku zauna ga guri nan." Zama sukayi kan kujera suna murmushi yanda na lura suma sunji dadin tar'bar da suka samu.

Shuru dakin yay na minti biyu nida iyayena tunani muke shi kuma hankalinsa gabadaya yana kan wayarsa, da alama yana duba abu mai muhimanci a wayar......Muryar babana naji yace."Kar'bi wannan Sumayya ki bashi kayan dubiya ne babu yawa, ranka ya d'ade gashinan babu yawa.'' Da sauri na kar'bi ledar da yake mi'ka min, na isa inda yake na bashi
A nutse yace."Ajiye kan drowar nagode sosai." Ajiyewa nayi da sauri na matsa daga gurin.....d'akin ne ya sake dau'kar shuru na tsayin minti goma kafin babana yace."Ranka ya dade zamu tafi Ubangiji Allah ya kare ya kiyaye gaba munayi maka fatan alkairi har karshen rayuwarka.

Wayar dake hannunsa ya ajiye kan drowar cikin kulawa ya amsa da fadin"Ameen suma ameen nagode kwarai ku sauka lafiya." Babana da Tambaya suka kama hanyar futa suna jin dadi a cikin zuciyarsu bayansu nabi nima raina tas naji dadi sosai da bai wulakanta min iyayena ba.

Har bakin mota na rakasu suka shiga direba yaja suka tafi cike da kauna da kewarsu na koma cikin asibitin... dakin na koma still yana zaune a inda yake ya d'auki wayar yana dubawa, agogo na duba naga biyar shaura, jikina na bani baiyi sallah ba cikin rawar baki nace"Ranka ya dade biyar saura lokacin sallah ya wuce."
Kallona yayi cikin mamaki yace."Waye yace miki banyi sallah ba? lallai yarinyar nan kin raina ni da yawa ni kike tunawa lokacin sallah."? Da sauri nace"Aa ba nufina na 'bata maka rai ba ranka ya dad'e nasan sharrin abar dake hannunka waya tana hana ibadah akan lokaci shiyasa nayi maka wannan maganar." Tsaki! mai karfi yaja ya d'auke kansa daga kaina, juyawa nayi zan fita daga dakin yace."Ke! zo ki d'auke tsiyarku bana bukata."

Da sauri na Juyo ina kallonsa dan ban fahimci maganarsa ba, ledar kayan dubiyar da babana ya kawo masa ya jefo min ta sauka daidai kafafuna. "D'auka ki fita dashi d'aga d'akin nan."! yafada yana min wani irin kallo.

A hankali na sunkuya ina kallon kayan dubiyar manya manyan mangwaro ne masu kyau da nuna duk wanda ya gansu sai yayi sha'awa saboda kyawunsu, cikin ledar na mayar da mangwaron k'walla na taruwa a idona na mi'ke tsaye da ledar a hannuna, cikin rawar murya nace" Me yasa lokacin da'aka baka ka kar'ba harda godiya wannan abin da kayi d'abiar munafukan mutane ne." Uffan bece min ba dan idan da sabo ya saba da tsayayyata bana jin tsoron fad'a masa gaskiya komai d'acinta sai dai ya gaji da marina ko dukuna........."Allah ya shiryeka shirin addinin musulnci." Abinda na fad'a kenan a k'untace na kama hanya zan fita daga dakin naji yace."Da yake Ubanki ne ya kawo min kayan dubiyar ai baki tsaya kin duba kin binkicika ba kai tsaye kika ajiye min sabida kina ganin shi ba zai iya cutar dani ba ko."?

Kallonsa nayi raina bak'ik'irin nace"Babana ba zai cutar da kai ba kuma baza'a hada baki dashi a cuceka ba, inaso na tabbatar maka da cewa akan gaskiya mahaifina na iya rasa rayuwarsa mutum ne shi mai tsoron Allah da gudun duniya idan ma kana zarginsa akan wani abu to ka daina domin kuwa kana daukar hakkinsa.


"Dallah malama fita ki bani guri kin tsaya kaina kina tsara magana ni bana shedar mahaifinki dan ban yarda dashi ba ke bari kiji ke kanki ban yarda dake ba ballanatana Ubanki duk wannan tsayayyar da kike a kaina kallon ki kawai nake."

Cikin sigar k'unsa ba'kin ciki nace"Na lura tunda na hanaka kaina kake zagina kana cin mutuncina to bari kaji wallahi mai kusantar wannan jikin nawa sai salihin namiji nagartacce mai addini maganar rashin yarda daka keyi ka yarda dani ko kada ka yarda dani bai dameni ba domin Allah nake kula da kai kuma nasan yafi kowa sanin zuciyata insha Allahu burinka ba zai cika a kaina ba."! ina kare maganar na bude kofar dakin a zafafe! na fita tare da buga masa kofar da karfin gaske.


Ya jima maganganun yarinyar na yi masa amsa kuwwa a kunne tunda yake ba'a ta'ba mayar masa da raddi masu zafi irin na yarinyar ba, tana samun dama a kansa sosai tana farfada masa ba'ka'ken maganganu iya son ranta yasan kuma ba komai ne ya janyo haka ba illah zulamarsa daya nuna a fili amma yana da kyau rana guda ya nuna mata cewa bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane.

Tunda mukayi haka dashi naji gabadaya zaman asibitin ya fita daga raina addua na dinga yi akan Allah yasa a sallameshi domin mu koma gida na gaji da zama a asibitin na kuma gaji da irin wulakanci da iskancin da yake min, sati biyu da nayi a asibitin nayi asarar karatuna nasan an wuce ni sosai dole idan na koma na nemi wata ta koya min hakan ya sake sakani cikin damuwa kullum fuskata a had'e babu walwala, Dr Rabo shine yake nema ya shige min hanci kusan kullum da daddare sai yayi kirana ofis dinsa idan naje kawai nsai kura min ido yayi ta kallona idan na tambayi ba'asi sai yay murmushi yace."Kawai ya kirani ne domin mu gaisa ya kuma kalleni yaji dadi. cike da takaici nake tambayarsa meye amfanin kallon nawa, kai tsaye sai yace." Shi kadai yasan amfanin hakan, rai a 'bace nake fita daga ofis din.......Ana ya gobe za'a sallameshi dana shiga dakin na sameshi kan kujera daga shi sai gajeran wando farar fatar jikinsa sai daukar ido take kirjinsa cike yake da gashi hakanan saman kafafunsa gashine a kwance bakikirin, ban iya kallonsa a hakaba ba na kautar da kaina da fad'in "Ranka ya dad'e Haruna yace." Kana nema na."? Banza yay dani bai kalli inda nake tsaye ba ballantana ya amsa min. daure zuciyata nayi na sake yi masa magana, ya kalleni a watse yace."Meye tsakaninki da wannan likitan mai ciki kamar rumbu." Dr Rabo gajere ne mai tumbi shiyasa ya kirasa da wannan sunan.

Murmushi nayi dan na sake 'kuntata masa nace"Ranka ya dade kana yawan kushe hallitar Allah kaima fa kana da mukusa a jikinka kasan d'an adam tara yake be cika goma ba."

Rai a 'bace! yace."Ba wannan na tambayeki ba na tambayaki abinda yake tsakanin ki da Dr Rabo." Ajiyar zuciya na sauke nace"Sirri ne a tsakani na dashi bana bukatar kowa ya sanshi.

Naga ya zuba min da'kwa-da'kwan idanunsa yana hararata yace."Wane sirri zaki 'boye bayan abu gashinan a zahiri na sani jama'a sun sani duk daran duniya kina shiga ofis dinsa yana lalata dake shine zaki ce sirri."!!

Gabana ya dinga fad'uwa! wannan wane irin d'an sharri ne? 'kazafi zaiyi mana kenan, tsabar firgici da tashin hankali na gagara cewa komai....Yace."Ko nayi k'arya ne."! Hawaye ne suka zubo min na kalleshi muryata na rawa nace" Allah ya sakamin k'azafin da kayi min insha Allahu sai mun tsaya gaban ubangiji akan wannan magana da ka fad'a.'" Hanyar fita na nufa ina kuka wiwi!! jikinsa ne yay sanyi ganin irin uban kukan data fita tanayi! tsaki yaja ya mik'e ko banza ya samu sassauci a cikin zuciyarsa yarinyar ta jima tana 'kuntata masa yau ya rage kuncin dake damunsa, tuntuni ya gane Dr Rabo sonta yake shiyasa gabadaya ya gaza nutsuwa yana fargaba kada yaje wani abu ya shiga a tsakaninsu mugun kishin Dr yake ya'ki nunawa ne saboda wata manufa tashi, da yarinyar ta amince ta zama mai d'eba masa kewa to da tuni ya 'yanta ta ita da iyayenta su tashi daga sunan bayi su koma mutane masu 'yanci, yana jin tsoron Dr Rabo ya yaudareta ta bashi kanta shiyasa gabadaya shima yaji zaman asibitin ya isheshi.

'Daki na shiga na zauna na dinga rizgar kukan dana dade ina tarawa, a duniya ba'a ta'ba yi min abinda ya sani cikin kunci da bakin ciki ba irin k'azafin da guy nan yayi min wato tunda na'ki yarda dashi da bukatarsa shine ya yanke shawarar 'bullowa ta wannan hanyar na tsani zina da masu aikatata sai gashi yau banji ba ban gani ba anyi min 'kazafi da ita, kuka sosai nake ina rirrike kaina.

Muryar Haruna naji a kaina a firgice na dago ina kallonsa hannu nasa na goge hawayen fuskata nace"Haruna yaushe ka shigo ko motsin bude kofa banji ba.

A sanyaye yace."Ya za'ayi dama kiji motsin bude kofa kina irin wannan kukan." Cikin ya'ke nace"Haruna waye yace da kai kuka nake wani abu ne ya shige min ido shine ruwan hawaye yake futa.

Murmushi yay yace."Ni ba yaro bane ballantana ki yaudareni da wannan maganar akan idona kika fito daga dakin da Yarima Ali yake kina kuka dan Allah yau dai kiyi min bayanin abinda ke tsakaninki dashi dan sau tari ina yawan ganinki kina fitowa daga dakin cikin bacin rai."

Kasa cewa komai nayi ina mamaki maganarsa ashe Haruna yana hankalce da abinda ke faruwa tsakanina da Yarima! a gaskiya nayi mamaki, dan kada ya zargi wani abu mai muni a tsakanina dashi yasa na yanke shawarar fad'a masa haka." Wallahi Haruna na gaji da zaman asibitin nan na gaji da wulakancin da muke fuskanta daga gurinsa nifa sai nake ganin kamar ni kadai ya tsana kullum cikin zagin iyayena yake yana buga min tsawa duk abinda zanyi masa bana gwaninta, wannan dalilin yasa kullum kake ganina ina fitowa daga dakin raina a bace."


Haruna yace."Hakuri zakiyi da yanda kika tsinci rayuwarki a ciki sumayya ki cigaba dayin aikin ki koda kuwa zai ce ki kwanta a kasa ya bi ta kanki baki da za'bi dole kibi umarninsa kasancewarki baiwar dake karkashinsa dole ki d'auki hakurin dukkanin abinda zaki gani, shawarar da zan baki shine ki tsananta addua akan Allah ya baki miji a kurkusa idan kinyi aure shikkenan kin huta da wannan aikin. amma mutukar ba kiyi aure ba to babu shakka zaki cigaba dayi masa hidima har karshen rayuwarki."

Maganganun Haruna sun kashe min jiki sosai na soma hango 'kamshin gaskiya a cikin maganarsa babu shakka idan nayi aure na huta da fargaba da tashin hankali ko banza nasan zan samu sassauci a wani 'bangare.

A sanyaye nace"Haruna nagode sosai na kuma ji dadi da wannan shawarar taka insha Allahu zan duba wanda ya dace dani na aura." Murmushi yayi yace."To babu damuwa Sumayya nima ina cikin layin masu so dan a gaskiya kina burgeni mutuka Sumayya kina da nutsuwa da kamun kai babu namijin da ba zaiyi sha'awar ki zama uwar 'ya'yansa ba."

Kallonsa nake ina mamakin furucinsa, yay murmushi yana shafa sumarsa yace."Ni zan tafi domin na barki kiyi tunani sai anjima." hanyar fita ya kama nabi shi da kallon mamaki har ya fita daga dakin......
*BINTA UMAR ABBALE*




*Na kudi ne..!*
Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake.....Vip gruop#600 normal group #300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084563262*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
53&54
Wai shin da wane ma'auni zan auna irin wulakancin da guy nan yake min? me nayi masa kullum yake wulakanta ni yake cin zarafina yana tozartani! a ganina ban cancanci haka daga gurinsa ba, ina ruwansa da alaqata da Haruna da har zai dauki zafi! ya kiramu fasikai wannan kalma daya kiran mu da ita tafi damuna akan watsa min fruit salad din da yayi.
Hannu nasa na share hawayen daya kasa daina zuba, na mike jikina a sanyaye na shiga gyara gurin ina jin wani irin zafi a zuciyata tsaf na gyara gurin na nufi kofa da niyar fita, kicibus mukayi da Haruna kallona ya shiga yi yana nazari, nayi saurin sunkuyar da kaina ina kokarin magana yace."Sumayya me ya 'bata miki jikinki."? Ji nayi zuciyata ta karye hawaye suka zubo min, murya na rawa nace"Haruna muje kada ya sauko ya same mu a tsaye."

A sanyaye ya bude min kofa na fita ya biyo bayana, sai da mukayi nisa sosai na sheda masa abinda ya faru Haruna shuru yay yana girgiza kansa yace."Sumayya ni dai banga abinda mukayi wanda ya kaucewa sharia ba amma zan kiyaye shige miki idan kina gurin kada wata maganar ta sake biyo baya.

Nace"Nima haka na gani amma wannan shawarar daka yanke itace tafi amfani idan kana so muyi hira ka bari idan na gama abinda nakeyi na fito sai muyi hirar." Yace."Babu damuwa anjima zan sanar da mahaifina maganar auramu sai ya samu baba Lawi su tattauna." Murmushi nayi nace"To shikkenan hakan yayi.'

Haruna har sashenmu ya rakani na sanjo kaya na fito ya rakani sashen Ciroma domin amsa kiran da Gimbiya Lawisa keyi min.


Samun ta nayi a hakimce bayin ta sun kewaye ta sai fadanci sukeyi durkusawa nayi ina gaisheta, a wulakance ta amsa, ta dubesu tare da basu umarnin tashi. da sauri suka bar gurin.

Minti biyar a tsakani naji muryarta." Sai yanzu ki kaga damar zuwa."? cikin nutsuwa nace"Afuwa ranki ya dade aiki nake a lokacin da kika aika kirana ki gafarce ni."

Shuru tayi tana watsa min kallon banza tace"Sumayya anya kuwa kina aikata aikin da nake sanya ki kuwa nifa bana ganin canjin komai a gurin Yarima kullum iskanci yake min ya'ki ya dinga nuna min so da kulawa.

Nace"Haba ranki ya dade ba zan ci amanarki ba ina aikata aikin ki akan tsari kin san komai sai a hankali insha Allah zaki shawo kansa zai soki ya kaunaceki tamkar ransa.

Murmushi tayi tace"Sumayya shiyasa nake sonki domin kina kwantar min da hankalina amma al'amarin Yarima Ali ya soma bani tsoro wallahi.'"

Murmushi nayi nace"Ranki ya dade ki yawaita addua kina rokon Allah ya janyo miki hankalinsa kanki gefe guda kuma kina 'yan daburu irin namu na mata.

Gyara zamanta tayi tace"Sumayya duk dabaru na sun kare wallahi kullum na kai masa ziyara da fada muke rabuwa gabadaya ma ni gani nake kamar tunaninsa na wani guri bana gabansa.

Shuru nayi ina nazarin abinda zance mata naji tace"Ko kina ganin na bashi kaina ne."? na kalleta da sauri inayi mata kallon mara hankali .....Tace"To Sumayya duk wasu dabaru nayi ya'ki karkato da hankalinsa kaina.


Nace"Ranki ya dade idan kika bashi kanki ya sanki a matsayin mace ai kin cutar da kanki ko kunyi aure ba zakiyi daraja ba kuma wulakancin da zaiyi miki sai yafi nada, kada kiyi wannan gangancin ki cigaba da dayin 'yan dabaru insha Allah za'a dace."

Ajiyar zuciya mai zafi ta sauke tace"Shikkenan Sumayya zan cigaba da bin shawararki." Nace"Yawwa ranki ya dade......Akushin dake gabanta tace"Ki dauka wannan ki kai masa farfesun kifi ne nayi masa ki tabbatar yasha farfesun dan na zuba sinadarai a ciki kuma ina saka ran zanci galaba."

Nace"Angama ranki ya dade yanzu kuwa zanje na aikata aikin ki." Akushin na dauka na rike hannu biyu nai mata sallama na bar gurun......Lantana dake la'be tana ganin fitowar Sumayya a hankali tabi bayanta

Ina isa inda nake zubar da kayan asirin na waiwaya ko'ina sai dana na tabbatar da babu kowa a gurin na watsar da farfesun da sauri na rufe akushin na bar gurin ina jin takaicin abinda ke faruwa.

Ko zaman minti goma banyi ba sakon kiran Lawisa ya iskeni, Cike da mamaki nake kallon 'Yar aiken, inaso nayi magana Babana ya katseni da fadin na tashi naje....jikina ya bani akwai wani abu mikewa nayi nasa takalmana nabi bayan 'Yar aiken.

Tsaye muka sameta tana kaiwa da kawowa a gurin, fuskarta kawai ta isa ta nuna min akwai matsala "Ranki ya dade gan......Kafin na karasa ta wanka min mari! tana huci tace" Sumayya ashe dama munafurta kikeyi ? ashe duk abinda nake baki zuwa kike kina zubarwa.''

Gabana ya yanke ya fadi baki na rawa nace"Ranki ya dade waye ya fada miki haka? wallahi karya ne ina bin umarninki.'' Wani marin ta sake kawo min nayi saurin kaucewa ina binsu Lantana da kallo sai 'kus-'kus sukeyi tabbas a cikinsu wata ta kawo gulmar.

"Bazan yarda da rantsuwarki ba Sumayya sai kin tabbatar min da gaskiyar magana daga bakin ki kana kuma ki nuna min inda kike zubar min da kaya.''

Shuru nayi zufa na keto min.

" Ke nake saurare 'yar iska munafuka kawai."

Naji ciwon zagin da tayi min amma sabida nasan nice bani da gaskiya yasa na cije nace"Ranki ya dade dik wacce ta kawo miki gulma gaskiya ne duk wani kayan asiri da zaki bani nasawa Yarima abinci da ruwan sha zubarwa nake a wani kebantacen guri idan baki manta ba ko dazu sai dana sake tunasar dake cewa asiri ba zai janyo miki kauna da so ba nace miki ki dage da addua sannan kuma ki canza salo, wannan dalilin yasa nake zubarwa saboda ba zan jefa kaina a halaka ba."

Huci! ta dinga yi tana kallona tace"Shin kin san irin mak'udan kudin da ake fitarwa kafin a 'karbo maganin nan kuwa."? shuru nayi mata tace"Lallai Sumayya baki da mutunci kuma wallahi sai na dauki tsatstsauran mataki a kanki ki shige muje ki nuna min inda kike watsar min da kaya."

Nace"Ranki ya dade ki gafarce ni banyi hakan dan na bata miki rai ba ina guje miki fushin Alla....Hannu tasa ta gwabe min baki! rufe min baki munafuka kawai wallahi sai naci mutuncinki a gidan nan." shuru nayi ina kallonta tasa takalmanta tayi gaba suka rufa mata baya, sai da sukayi nisa kana nabi bayansu..

a gurin na same su Lantana tana nuna mata ramin da nake zubawa. juyowa tayi tana kallona na sunkuyar da kaina kasa, rai a bace ta juya suka rufa mata baya.....wata rumfar bukka na samesu sai zurga zurga take tana magana dasu.

Ina karasowa gurin tace nasa gwiwata a kasa, nayi yanda tace kallonsu tayi tace su biyo layi kowacce ta mare ni hagu da dama.

Mikewa nayi ina kallonta nace"Ranki ya dade ke nayi wa laifi dan haka ke zaki hukunta ni basu ba.''


"Sumayya so nake ki 'kask'anta yanda kika sa raina baci kema naki sai ya 'baci."!

" Ranki ya dade ki gafarce ni ba zan zauna wanda muke matsayi daya dasu su mare ni ba gaskiyar magana kenan."

Tana huci! tace"Ni kikewa gardama ko."? kasa nai da kaina babu yanda xa'ayi na zauna su Lantana su mareni duk abinda za tayi sai da tayi.


"Lantana je ki kirawo min Buba kice yazo da bulalarsa." Lantana da sauri ta tafi....hannu ta goya a baya ta shiga zagaye gurin
cikin zuciyata nace wahalalliyar banza da wofi kawai.

Buba da Haruna na tare suna hira Lantana ta isa gurin ta shedawa buba kiran da ake masa, Buba yace kije ganinan zuwa...

Haruna jikinsa ne yay sanyi yace"Buba dan Allah kada ka doki Sumayya akan gaskiyarta."Buba yace."Idan tana tsaye a gurin dole nabi umarninta idan ta bar gurun zan kyaleta amma dai duk da haka zan dinga dubarar dukan kasa a madadin ita nake duka."

Yana kare maganarsa yay saurin barin gurin, Haruna jikinsa dik yayi sanyi kwata kwata baya so a ta'ba lafiyar Masoyiyarsa. yana kokarin mikewa Buba ya karaso gurin hannunsa nannade da murtukekiyar bulala mai baki biyu, ko sauraransa beyi ba yay gaba.
Haruna da sauri ya nufi sashen Yarima domin ya sheda masa abinda ke faruwa.


Sai da gabana ya fadi ganin katuwar bulalar dake hannun Buba, gumi ya dinga tsiyaya a jikina dana sani na yarda su Lantana sun mareni da tuni an wuce gurin.

"Ranki ya dade gani." Buba ya fada yana me kaskantar da kansa....

jajayen idanunta ta watsa masa tace"Buba so nake ka zane jikin Sumayya har sai rigarta ta yage wallahi idan ka sassauta mata sai ka fuskanci hukunci daga gurina."

Murmishi yayi irin na mugunta yace."Angama ranki ya dade." Bulalar ya daga da karfi gaske ya labta min a gadon bayana, kara na saki na rintse idona ina jin radadin zafi a inda ya doke ni....Gimbiya Lawisa murmushi tayi suma su Lantana suka soma dariya, ido jawur nake kallonsu....Buba na dariyar shakiyanci ya sake daga bulalar zai labta min "Kai kar ka daketa." da sauri na bude idona! yana tsaye a gurin haruna na gefansa gani nayi kowa ya shiga hankalinsa har ita Lawisan ta sunkuyar da kanta.

Hannu nasa na sharce gumin goshina ina godewa Allah da zuwansa gurin........'"Kai buba me tayi maka kake mata irin wannan dukan."? yana watsa masa harara yake maganar. Buba yace"Ranka ya dade umarnim gimbiya lawisa ne amma ni Sumayya ba tayi min komai ba."

Yace."To duk ku bar gurin nan." Buba dasu Lantana suka bar gurin...yunkurawa nayi zan tafi yace."Ke! ku sameni a gurina domin naji ta bakin kowa dan na fahimci akwai rashin jituwa a tsakaninku.'' gurin ya bari haruna yabi bayansa.
Kawai sai na tsinci kaina da watsa mata kallon banza a fusace na bar gurin....Gimbiya lawisa a sanyaye ta nufi sashen Yarima saboda tana tsoron abinda zai biyo baya tana tsoron ya tozarta irin na kwanakin baya


*Na kudi ne...*
Allah ya isa kika karanta baki biya ba idan kina so ki biya ga yanda abin yake......Vip group #600 normal #300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa Dashan Allah✊?)
51&52
Shara na samu Tambaya nayo shigowata yasa ta dakata ta tsaya tana kallona. kasa cewa nayi da ita komai nayi saurin shigewa daki, Tambaya kasa nutsuwa tayi ta ajiye tsintsiyar hannunta a sanyaye tabi bayanta, samuna tayi a zaune na zabga tagumi, shigowarta tasa nayi gaggawar cire tagumin ina kallonta xama tayi gefena a nutse tace"Sumayya lafiya na ganki kin shigo jikin ki a sanyaye ina fatan ba wata matsala bace."? shuru nayi ina kallon kasan gurin, shawarwari nake da zuciyata yana da kyau na sanar da mahaifiyata abubuwan da suke faruwa saboda ina jin tsoron wani mummunan abu ya faru nasan nida iyayena zamu shiga uku, ni sam ban san me yasa baya so mahaifiyarsa tasan abinda yake faruwa ba, kuma idan akace za'a cigaba da tafiya a haka to babu shakka ni dashi rayuwarmu na cikin matsala domun 'yan uwansa basa kaunarsa zasuyi amfani da yardar da yake musu su cutar dashi babban burinsu suga baya motsi a duniya inda shi kuma ya kasa ganewa kullum gani yake ba zasu ta'ba cutar dashi ba.....A sanyaye na warware mata abunda ke faruwa babu abinda na rage mata, yanda na lura itama jikinta yayi sanyi amma domin ta kwantar min da hankali yasa ta dafa kafad'ata tace"Sumayya ki nutsu kinji ko ki daina sa wasiwahsi a cikin zuciyarki insha Allah ba zasuyi tasiri a kansa ba duk sharrin da suke shiryawa zai koma kansu, kamar yanda yace baya bukatar mahaifiyarsa tasan abinda ke faruwa to kiyi shuru kada ki sheda mata, shawarar da zan baki shine ki tsananta gurin kula da shige da ficen masu shiga sashensa,

Please Login or Register in order to submit comment