Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

suna zaginki dauke kaina kurrum nayi na rabu dasu sukayi su gama." Girgiza kaina nayi cikin 'kunar zuciya nace"Tambaya kada ki damu Allah yana tare da masu gaskiya kedai ki tsananta addua a gurin Allah ya bayyana gaskiyar lamari." Tace!"Addua kullum cikin yin ta nake Insha Allahu Allah sai ya kare ki daga sharrin masu shari.'' Ameen nace na dauki buta domin daura alwalar sallar magariba....




*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi baki biya ba keda kika futar da book din keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
77
Sosai ya rike 'kuguna ya matseni a jikinsa yana sauke wani irin numfashi yun'kurin k'wace jikina nayi ya sake matseni a raunane yace."Ba zan sake ki ba sai kin yafe min." Hawaye suka sake xubo min nace"Me kayi min kake neman yafiya a gurina ni ai baiwa ce zan iya kwanciya kabi ta kaina kaga dan ka 'kona ni ai ba wani abu bane."

Saukar hannushi naji a kirjina yana shafawa, "am sorry my love." a hard'e ya fadi maganar, yanda yake shafa fatar gurin yasa tsigar jikina duk ta tashi, gabadaya naji gwiwata tayi sanyi, a raunane nace"Sake ni na yafe maka." K'in saki na yayi ya cigaba da shafar gurin 'kunar yana sauke min hucin numfashinsa a wuyana, jikina yay la'asar ikon Ubangiji Allah ya had'ani da nataccen mutum........"Ki bari na duba miki." Da sauri nace."Nifa ban 'kone ba ka sake ni na tafi na yafe maka."

Da sauri ya juyo dani kafad'una ya rike ya kurawa fuskata ido kafin naga ya sauke idonsa inda k'unun ya zubawa ido ." ina kallonsa yasa bakinsa yana hura gurin, nayi saurin ture kansa gabana na bugawa, a buge ya dago yana kallona da jajayen idanunsa, dauke kaina nayi daga kallon fuskarsa dan gabadaya ni yanzu al'amarin sa tsoro yake bani.


Hannu yasa ya juyo da fuskata yana wani marairaice fuska yasa harshe yana lashe bushashshen hawayen daya bushe a fuskata......mirya na rawa nace"Dan darajar Allah ka bari babu kyau fa abinda da kakeyi ka sakeni na tafi wallahi na yafe maka."

Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke naga ya daidaita nutsuwarsa hannuna ya rike ya fara tafiya.

Turjewa nayi cikin faduwar gaba nace"Ina zaka kaini." ?

"Zan duba miki 'kunar ne." Girgixa kaina nayi nace"Ka barta kawai in Allah ya yarda ba zata tashi ba.'' Ido ya tsira a gurin kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kalleni, dauke kaina nayi saboda bana son kallon kwayoyin idanunsa, "Sumayya.'' kallonsa nayi saboda yanda naji ya ambaci sunan nawa ya cigaba da cewa" Maimartaba ya umarce ni akan lallai na janye maganar aurena dake."

Ajiyar zuciya na sauke lokaci guda naji wani irin farin ciki ya mamaye zuciyata.

Girgiza kansa yayi yace.''Nasan jin wannan maganar yasa ki farin ciki ko.''' shuru nayi ina kallonsa! girgiza kansa yayi yana wani murmushi yace."Ni yaro ne mai biyayya gami da bin umarnin iyayena saboda haka zanyi kokari ganin nabi umarnin mahaifina ammafa ki sani duk hanyar da nasan zanbi na hanaku rayuwar jin dadi dake da masoyin naki na sani mafita a nan shine ki mallaka min abinda nake 'kulafuci idan na samu ko sau daya ne to zan barki ki zauna lafiya da mijinki.''

Yanda yake maganar ya nuna min da cewa tabbas zai iya aikata komai akaina da Haruna, jikina ne yayi sanyi na dinga jin tsoron sharrinsa kasa magana kawai nayi na zuba masa jajayen idanuna.

"Baki ce komai ba." Yafada yana sake nani'kar Jikina.''
''Yallabai bani da abinda zance maka saboda na fahimci kayi nisa kuma baka tsoron Allah akan biyan bukatarka babu komai duk abinda zakayi mana kaje kayi Allah yana kallonka.''

"Okey! wannan maganar taki ta nuna min cewa ba zaki bani abinda nake bukata ba."

Kai tsaye nace"Wai shin sau nawa zan fada maka wannan maganar ne? na fada maka cewa ba zan ta'ba amincewa da kai akan sa'bon Allah ba ranka ya dad'e ba zan baka kaina ba koda kuwa zaka sa min bakin bindiga a mak'ogwaro na wallahi akan na baka kaina sai dai ka kashe ni."!!!
Ya dinga kallona fuskarsa tana rikicewa da wani 'bacin rai gabad'aya kammaninsa sun sauya! nima idanuna nasa masa ina tabbatar masa da gaskiyar maganata........Motsin bude kofa ne yasa gabad'aya muka kalli bakin kofar, gimbiya Lawisa ce ta shigo cikin shiga ta alfarma da alama kwalliyar ta mussaman ce, ganinmu daf da juna yasa nan take yanayin fuskarta ya sanja da zallan 'bacin rai.


Matsawa nayi daga jikinsa na sunkuyar da kaina gabana na wani irin fad'uwa, Gimbiya Lawisa ta karaso kusa damu shashshekar kukanta naji tana magana........ da sauri na dago kaina ina kallonta ina kuma mamakin abinda take fada, tana wani irin kuka ta cigaba da cewa"Yanzu meye a jikin wannan mummunar yarinyar da har kake rungumeta a jikinka ashe dama ba aikin abinci kawai take maka ba tana biya maka bukatarka idan ta tas........Wani gigitacan mari ya kwada mata ido jajawur yace."Kada ki sake jifan mu da wata mummanar kalma kawai saboda kin shigo kin tarar damu daf da juna sai ki fassara da wata manufa ta daban! wallahi idan kikayi wasa akan wannan dalilin sai na janye maganar auranki dama ba sonki nake ba takura min akeyi.'

Lawisa gumi ya dinga yanko mata kai amma Yarima baida kirki a gaban baiwa ya kwada mata mari yana fadin ba sonta yake ba.sunkuyar da kanta tayi takaicin duniya ya isheta wai shin ya za tayi ta janyo hankalinsa a kanta, tsaki yaja mai karfi ya wuce ya bar mu a tsaye a gurin..
Ganin ya futa yasa nima nayi yunkurin barin gurin, da sauri ta tari gabana na kalleta ta kalleni cikin tashin hankali tace''Sumayya ki fada min abinda ke tsakaninki da Magajin sarki." Cikin jarumta nace"Ke me kika gani a tsakaninmu."? a fusace tace"Wace irin magana kikeyi wannan ki bani amsar tambayata." nace"To babu wani abu dake tsakanina dashi."

"Babu abunda ke tsakaninki dashi na ganku dab da juna." Cikin k'osawa nace"Duba kirjina ki gani'' ta dinga wulkita idanunta tana dubawa. nace"Me kika gani."? ''Naga kamar kin kone." Kai tsaye nace"Shi ya 'kona ni da kunun gyada mai zafi haka kawai banyi masa komai ba, idan kina so ki tabbatar ga sheda nan." na nuna mata kayan dake watse a gurun, a sanyaye ta kalleni tace"To me yasa na ganku dab da juna?" kaina na dafe cikin damuwa nace"Nadama yayi da abinda yayi min shine yake min tofi a gurin 'kunar."

Ajiyar zuciya ta sauke tace"Allah ya taimake ki kin fada min gaskiya kuma naga sheda a zahiri wallahi da baki fada min gaskiya ba da sai na dauki mataki mai tsauri a kanki''' cikin takaici nace ranki ya dade na baki shawara."? tace"Ina jinki." nace "Ki rage son Yarima domin idan kika bari ya gane zaki sha wahala tunda gashi a gabana yana fadar shi takurashi akayi akan ya aureki.'"
Bina tayi da kallo ta kasa cewa komai, ganin haka yasa na sunkuya na kwashe kayan dake watse a gurin, kicin na kai na fito na sameta a tsaye a inda take, goge gurin daya 'baci nayi tas na mayar da Mopar na fito na sameta a tsaye sai kace gunki sai tunani take tsaki naja a zuciyata na kama hanyar futa ina fadin shashasha mara tunani.


Ban shiga gurin mu ba sai da na samu Haruna na fad'a masa labari mai dadi.

Haruna ya dinga murna yana godewa Allah, a gurin yayi sujjadar godiya ga Ubangiji ya mike yana mana kyakkyawar addua.


Jigum-jigum! na samu iyayena a tsakar gida, gwiwata tayi sanyi d'an farin cikin dana shiga dashi ya dauke, guri na samu na zauna ina tambayarsu..

A sanyaye Tambaya tace"Maimartaba ya aiko mahaifinki yaje koda yaje fada sai yace masa maganar auranki da Haruna tana nan dan haka suje su cigaba da shiri shi bai bada goyan baya Yarima ya aureki ba. Sumayya lokacin da naji wannan maganar sai da na kusa kuka gaskiya naso ki auri magajin sarki."

Murmushi nayi nace"Tambaya ki daina damuwa dan Allah tunda kikaga Allah yayi haka to shine alkairi." babana yace."Nima abinda nake ta so ta gane kenan amma taki fahimta sai damuwa take."

Nace"Hakane baba duk yanda Allah ya tsara haka zamuyi hakuri mu kar'ba nima naso na auri Yarima saboda ganin yanda kuka nuna farin cikin ku amma tunda kukaga Allah ya zartar da wannan hukunci to shine alkairi ni daku sai mu barwa Allah ikonsa'' na fadi hakane domin na kwantar musu da hankali amma ko daya bana fatan auran Yarima saboda nasan da aniyar da zai aureni nafi sha'awar auran Haruna saboda nasan shine daidai dani kuma yana min kaunar da Yarima ba yayi min irinta.


*****
Bayan sati biyu al'amura suka cigaba da gudana yanda ya kamata, maganar aurena da Yarima ta rushe tsakanina kuma da Haruna a kullum 'kauna da sha'kuwa na kara 'karuwa a tsakaninmu yanzu mun kwantar da hankalin mu mun daina fargabar abinda zai faru tunda Maimartaba ya shiga cikin al'amarin mun san dole duk wanda yake adawa da auranmu ya hakura, ta 'bangaran Yarima kuwa kullum babu yabo babu fallasa a tsakaninmu ya zuba mana ido dan tun ranar daya 'kona ni wata magana mai tsayi bata sake shiga tsakaninmu ba, kullum ina shiga nayi aikace aikace na baya ce min kanzil sai magana ta kama sannan zai kulani naji dadi sosai daya janye jikinsa dani ina adduar Allah yasa ya hak'ura ya rabu dani nayi rayuwata hankali kwance..................Cikin shiri ya sauko ya same ni ina goge-goge yace."Sumayya bana tsammanin zan zauna nayi breakfast." kallonsa nayi yana gyara necktie d'in wuyansa nace"Ranka ya dad'e yana da kyau dai ka zauna ka karya kafin ka futa idan ka zauna a ofis baka da lokaci saboda jama'a." Girgiza kansa yayi yana gyara gilishin idonsa yace." Ba zan iya tsayawa ba amma ki bawa Haruna ko Hamza kayan breakfast din ya kawo min ofis." Nace"To shikkenan ranka ya dade Allah ya bada sa'a." Amsawa yayi tare da kama hanyar fita, har ya kai bakin kofa ya tsaya na kalleshi saboda nasan da abinda ya tsayar dashi, yace."Na bar bedroom dina a bude ki gyara min har toilet." nace"To insha Allahu zan gyara."
Fita yayi ni kuma da sauri na hau saman domin gyara masa dakin kamar yanda ya 'bukata.


Koda ya shigo falon yaji shuru kai tsaye kicin ya nufa nan yaga komai a shirye akan tire ajiyar zuciya ya sauke, yaji dadi sosai da samun komai a kammale, hannu yasa ya dauko wani abu a cikin aljihunsa, ya kwance abun dake cikin wata bak'ar takarda, bud'e fulas din yay nan yaga miyar taushe wacce taji gyada da watadaccan nama, sai kamshi take, gabadaya ya zazzage abinda yake cikin takardar a cikin miyar yasa spoon ya juya sosai maganin ya 'bace a cikin miyar, rufewa yayi da sauri ya fita daga kicin din yana addua Allah yasa bukatarsu ta biya.



Tsaf na gyara masa dakin nasa turaran wuta mai kamshi kana na sauko kasa, kicin din na nufa a gurguje na had'a komai a cikin wani kwando na mussaman


Hannuna rike da kwandon dake dauke da abincin na fito na samu Haruna shi kadai a zaune , ina mirmushi nace"Sahibi kana zaune kai kadai ina Hamza ya tafi ya barka cikin kadaici." kallon kauna yayi min yace."Hamza yaje gurun iyayensa domun su gaisa nima abinda ya hanani tafiya ina jira ki fito nayi tozali dake.

Murmushi nayi cikin kauna nace"Haruna kenan to gani na fito ina fata kaji dadi daka ganni." Yace."Naji dadi sosai Sumayya jiya kwana nayi ina mummunan mafarki sai nake ganin kamar na kusa rabuwa dake Sumayya mafarkin jiya ya bani tsoro wallahi."

Ji nayi gwiwata tayi sanyi nace"Haruna dan Allah ka daina irin wannan maganar bana so insha Allahu babu abunda zai rabamu nasan har yanzu kana fargaba akan lamarina da Yarima to ka kwantar da hankalinka tunda Maimartaba yace dole ya hakura ai magana ta kare."

Murmushi yayi yace."To shikkenan Sumayya insha Allahu na daina damuwa sannan kuma ina rokon Allah ya cika mana burinmu." Cikin jin dadi na amsa da ameen ya rabbi."

Nace"Magajin sarki yau ya futa da sauri da alama akwai abinda yasa ya kasa tsayawa ya karya kummalo shine yace idan na kammala komai kai ko Hamza wani ya kai masa ofis."
Yace."To babu damuwa ai tunda Hamza baya nan bari na kar'ba kawai na kai masa."
'Dan 'bata fuska nayi nace" bana so kasha wuya naso Hamza yana nan da shine zai kai masa.
Dariya yayi ya mike tsaye yace." Sumayya kenan kamar yanda bakya so na wahala nima haka wallahi dani mai iko ne da duk wannan wahalar bakiyi ba." murmushi na dinga saki ina kallonsa, ya kar'bi kwandon abincin daga hannuna, tare muka jera har gurin da motoci suke, nayi wa daya daga cikin direbobin bayani a take ya mi'ke had'e da bud'ewa Haruna mota ya shiga, shima ya zauna a mazauninsa, hannu na daga masa da murmushi a fuskata nace"Sai ka dawo." shima da kyakykyawan murmushi a fuskarsa yake daga min hannu, na dinga mamakin yanda fuskarsa ke fitar da annuri murmushin da yake min yayi yawa dan har direba yaja motar bai dauke idonsa daga kaina ba, a sanyaye na nufi gurinmu gabana na faduwa kadan kadan...


Koda ya isa ofis ruwan coffee kawai yasha yaji ya gamsar dashi, kawai sai ya cigaba da aikin dake gabansa, yayin da marasa lafiya keta shige da fice a asibitin...............Haruna a nutse ya fito daga motar bayan direba yayi parking a gurin da aka tanada, kai tsaye cikin asibitin ya nufa, da yake yasan ofis din nasa kai tsaye kofar ya nufa, masu gadin kofar suka dakatar dashi. sai da daya ya shiga ya sheda masa tukkuna ya fito ya bashi umarnin shiga.

Kanshi a kasa yana rubuce rubuce jikin wata takarda ya amsa sallamar Haruna, haruna yaja gefe ya tsaya hannunsa rike da kwandon abincin, sai bayan kusan minti goma ya dago kansa, Haruna da sauri ya mika gaisuwarsa, babu yabo babu fallasa ya amsa, Haruna yace.''Ranka ya dade Sumayya ta aikoni da kayan karin kummalon ka." Yayi shuru yana kallon takardar dake gabansa, dagowa yay a nutse yace."Haruna kaje da abincin nan ba zan iya cin komai ba yanzu idan kuma kana bukata kaje ka samu wasu su taya ka ci''
A sanyaye yace."To godiya muke ranka ya dad'e Allah ya taimaka maka a cikin dukkunanin al'amuranka." Ya amsa da amin ya Allah. hanya ya nuna masa da hannu da fadin"Kana iya tafiya." Haruna da sauri ya bude kofa ya fita bayan yayi masa fatan tashi lafiya.


Haruna yana fita direba ya samu yace ya fito su samu wani guri suci abincin dan wanda aka kawowa baya bukata, Direba da sauri ya kulle mota suka samu wani 'ke'bantaccan guri a cikin asibitin suka zauna a nutse suka fito da kayan abincin.........Funkaso ne shar dashi yana ta kamshi, suka bud'e fulas din miya yawun bakinsu duk ya tsinke, cikin plate suka zuba funkason da yawa suka lafta miya da uban nama, suka shiga ci suna hira, bayan sun gama ci da minti biyar gabad'ayansu suka fice daga hayyacinsu suka dinga mur'kususu a gurin suna matagugu! da ri'ke cikinsu!! salati suka shigayi idanuwansu suka kafe suna kallon sararin samaniyya, babu shakka gubar da'aka zuba cikin abincin mai karfi ce dan anan take Haruna ya fadi a gurin rai yayi halinsa, minti goma a tsakani direban shima ya fad'i yana kiran sunan Allah....





*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi baki biya ba, keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300....account... 0542382124..Binta umar gtbabk...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKAWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
75&76
Koda na fito samun Haruna nayi shi kadai a zaune ya zabga uban tagumi! kai tsaye inda yake na nufa a sanyaye na zauna a gefansa kallonsa nayi a nutse na kira sunansa Ya dago yana kallona da jajayen idanunsa, tausayi ya bani saboda nasan irin kaunar da yake min, nace"Haruna kada ka tayar da hankalinka akan wannan maganar Yarima bai isa ya raba tsakaninmu ba.'"

Cike da mamaki yake kallona kafin yace."Sumayya kin san bani da kwanjin da zanyi gogayya da Yarima a gurun neman auranki dole na hakura dake na bar masa."

Nace"Haba Haruna kada ka bani kunya mana me yasa zaka karaya da wuri ashe dama duk so da kaunar da kake min suna ya tara ba zaka iya tsayawa a fafata da kai ba."

Girgiza kansa yayi yace."Sumayya kenan ba zaki gane abinda nake nufi ba, ki sani ni bawa ne wanda yake karkashin masarauta dole ne nabi umarni koda kuwa hakan na barazana da rayuwata tilas na janye maganar auranki kamar yanda ya bukata cewa na sanar da mahaifina halin da ake ciki to dole na fada masa ya samu mahaifinki ya sheda masa halin da ake ciki."

A sanyaye nace"Amma ban ta'ba tsammanin haka daga gurunka ba wallahi na raina kaunar da kake min daga magana guda har ka karaya ka janye na yarda kaima ba sona kake ba sha'awata kake.'' rai a bace na mike zan bar gurin da sauri yace."Sumayya duk me ya janyo wannan maganar dan Allah ki tsaya ki saurare ni wallahi karfina akafi akan soyayyarki amma ina me tabbatar miki da cewa da wani ne ba Yarima ba to da sai inda karfina ya 'kare.''
Saboda yanda nake jin zafi a zuciyata yasa ko tsayawa banyi ba bare na saurari maganarsa, gurinmu na shiga raina a 'bace."

Kai tsaye k'uryar daki na shiga na kwanta hawaye ba zuba a kuncina Yarima zai gwada iko da mulki ya aureni domin ya biya bukatarsa daga baya ya sake ni anya kuwa zan iya amincewa da wannan al'amarin.

"Sumayya." Muryar Tambaya naji tana kirana, da sauri na goge fuskata na amsa da "Na'am." Tace."Yawwa ashe kin shigo kinga ni ina zaune zaman jiran shigowarki bacci ya dauke ni babanki ma bai shigo ba ko."?

Nace"Eh bai shigo ba ai lokacin dana shigo kina bacci shiyasa." Tace"Eh yanzu ma motsinki naji na farka akwai kwad'on zogale a kicin na ajiye miki." Nace"To kafin na kwanta zan dauka naci.''
Shuru tayi ba sake magana ba da alama bacci ne a kanta, sai da aka jima tukkuna na mike a hankali na fita na dauko kwadon zogalen a tsakar gidan na zauna nasa kwanon zogalen a gabana na garara ci gabad'aya hankalina ya dauke gurin tunani naji muryar Babana a kaina....da sauri na dago kaina ina kokarin kawar da damuwa ta nace"Baba ka shigo." a sanyaye yace."Eh tun dazu nake tsaye a kanki ina magana baki ji ba." Shuru nayi ba wai dan bani da abin fada ba."

Yace.''Ki dauko kwanon abincin ki shigo ciki akwai maganar da zamuyi.'' naji gabana ya fadi jin abinda yace binsa nayi da kallo har ya shiga dakin.......Mikewa nayi ba tare dana dauki kwanon zogalen ba nabi bayansa dakin.

Zaune na same shi a kan shimfid'arsa kallon guda nayi masa na gane yana cikin damuwa, a sanyaye na zauna ina fuskantarsa

Kallona yayi a nutse yace."Sumayya wani babban al'amari ne yake so ya faru dake damu baki daya." Nayi shuru ina sauraransa nasan dai mahaifin haruna ya sameshi da maganar data dame ni.

Ya cigaba da cewa"Yanzu kafin na shigo mahaifin Haruna yaron nan da aka tsayar da maganar auranku yazo min da wata magana wacce ta sani farin ciki ta kuma sani fargaba." shuru yay yana kallona na lura kamar yana jin nauyin fada min maganar nace"Baba na riga nasan maganar dakake so ka fad'a min." kallona yayi yana so yayi magana Tambaya ta mike zaune da alamun bacci a tare da ita tace"Allah yasa dai lafiya naji sai magana kuke 'kasa-'kasa ga alhini a tare daku.''

A sanyaye yace."Tambaya yanzun nan mahaifin Haruna yake sheda min cewar yaronsa ya janye maganar auransa da Sumayya saboda ba zai iya had'a takara da magajin Sarki ba."

Tambaya cike da tsoro tace."Malam kayi min bayani yanda zan fahimta bangane ba zai iya had'a takara da magajin sarki ba, me ya sako Yarima cikin al'amarin auran Haruna da Sumayya."


Murmushi yayi yace."Tambaya Magajin Sarki da kansa ya umarci Haruna ya janye maganar auransa da Sumayya saboda yana so ya aureta."

Tambaya gud'a ta ragwad'a cike da farin ciki da annushuwa tace"Malam da gaske kake wannan magana ko mafarki nake yi." Murmushi yayi yace."Ba mafarki kikeyi ba gaskiya ne wannan maganar." Tambaya kamo ni tayi ta rungume a jikinta ta dinga rangwad'a min gud'a akaina tana zabga min addua." har sai da babana ya dakatar da ita sannan ta sake ni kana ganinta kasan tana cikin walwala da farin ciki.

Ni kam kallonsu kawai nake ina mamakin murnar da sukeyi tabbas da sun san da munufar da Yarima zai aureni da basuyi murna ba, ganin yanda suke ta farin ciki yasa na danne damuwata kawai na dinga binsu da kallo.....Babana sunkuyar da kansa yayi yana girgiza kansa, Tambaya tace."Malam ya kuma naga ka shiga halin damuwa." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Tambaya ina tunanin abinda zai biyo baya idan Allah ya kaddara al'amarin babu shakka mutane zasu nuna mana bakin ciki ina tsoran kada wani ya cutar damu ta dalilin wannan al'amarin." A sanyaye tace."Malam ka kwantar da hankalinka babu abinda zai same mu da izinin ubangiji duk wanda ya nufe mu da sharri sai ya koma kansa da yardar Allah kuma wannan aure sai anyi shi tunda maganar ta fito daga bakin Yarima ai magana ta kare sai da muyi kyakkyawar addua."" Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleni a nutse yace."Sumayya kinyi shuru baki ce komai ba ina fata kinyi na'am da wannan al'amari."

A sanyaye nace" A gaskiya Baba ni wannan al'amari sam be kwanta min a rai ba wannan dalilin ne yasa kukaji nayi shuru da bakina." Tambaya hannuna ta rike a sanyaye tace"Haba Sumayya kiyi wa kanki kyakkyawan addua mana ki roki Allah yasa haka shine alkairi a rayuwarki mu dai mun amince da wannan sauyin da Allah yayi miki a matsayinmu na iyayenki muna miki fatan alkairi kuma muna umartarki da ki kar'bi al'amarin da zuciya daya insha Allahu Allah zai sa albarka a ciki." ajiyar zuciya na sauke a sanyaye nace Allah yasa albarka a cikin al'amarin." Gabadaya suka amsa da "ameeen ya Allah."


Washe gari da safe sukuku! na tashi inata tunanin yanda al'amura zasu kasance a gaba iyayena sun kar'bi al'amarin hannu biyu sai murna da farin ciki suke wannan dalilin yasa gabadaya gwiwata tayi sanyi kawai na zubawa sarautar Allah ido ina tunanin yanda al'amura zasu kasance............Sallama mukaji daga waje, da sauri babana yasa takalminsa ya fita, minti biyar ya dawo yana murmushi yace."Tambaya al'amarin nan fa da gaske ne dan yanzu Magajin sarki ya aiko naje na sameshi a gurinsa.

Cikin murna tace"To shikkenan Ubangiji Allah yasa muji alkairi." Yana kokarin fita ya amsa da ameeen ya Allah."


Cikin hijabi na fito daga daki kafadata rataye da jakar

Please Login or Register in order to submit comment