Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sannan ki kula da duk wani abu naci da zasu kawo masa insha Allah duk sharrinsu sai ya koma kansu, ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai faru sai ikon Allah."

Ajiyar zuciya na sauke ina kallonta hakika naji sanyi a zuciyata sakamakon kwantar min da hankali da tayi nace"Insha Allahu zan kula kuma ba zan fada Mamma Fulani maganar ba, zan cigaba da kula dashi ina addua kema a matsayinki na mahaifiyata ina rokon ki ki taya ni addua Allah ya kareni daga fad'awa cikin mugun hali."

Tambaya tace"Kada ki damu Sumayya kullum cikin yi miki addua muke insha Allahu kuma adduarmu ba zata fad'i kasa ba.

Nace"Nagode sosai ina fatan kin bude akwatin kin duba kyautukan dake ciki. Da murmushi a fuskarta tace"Ban bude ba kada ki manta da zaki fita cewa kikayi sai kin dawo sai mu bude."

Mikewa nayi ina yar dariya nace"Da kin sani kin bude kin rigani gani ai kina da iko akan duk abinda ya dangance ni." Tambaya mirmushi tayi ba tace komai ba tabi ta da kallon kauna da tausayi.


Cikin nutsuwa na bude akwati nasa hannu ina fito da kayan ciki. Manya manyan lifayu ne guda uku sunyi kyau sosai sun kuma birgeni mutuka sai na dinga hango kaina a ciki nasan zasuyi min kyau kasancewa ta doguwa....sauran kayan na cigaba da dubawa, d'inkakkun atampa guda biyu supar da ingila anyi musu dinkin mutanan Nijar rigunan har gwiwa anyi musu ado da bakin leshi mai tsada... mayafai da takalma biyu sai turare biyu sai set din mayukan shafawa, Tambaya bakinta kasa rufuwa yayi ta kasa daina duba kayan sai farin ciki take tana godiya, ina mirmushi na dauki 'yar karamar akwatin da zoben gold din ke ciki na bude a nutse na fito da zoben ina duba shi sai kyalkyali yake yanda nake jin nauyinsa a hannuna nasan zaiyi kudi sosai Tambaya tace"Kai amma wannnan zoben yana da kyau sosai duba sai kyalli yake."

Nace"Tambaya gold ne Mamma ta bani wai nasa a hannuna nayi ado dashi." Tambaya ta kar'bi zoben tana dubawa, kawai sai hawaye ya shiga zobowa a fuskarta, da sauri na kalleta ina mamakin kukan da take.

Girgixa kanta tayi tace"Sumayya dole nayi kuka nayi mamaki! yanzu kece zaki saka zoben gold a hannunki tinda nake a masarautar nan ban ta'ba ganin baiwar da tayi ado da gold ba sai *murjani* amma cikin ikon Allah ke anyi miki kyautar zoben gold mai dauke da tambarin masarauta babu shakka Sumayya kin kafa tarihi a cikin bayi.

Mirmushi nayi na girgiza kaina ina kara duba zoben ni kaina ina mamakin al'amarin dan sai da ta fada ma sannan na duba zoben sosai naga tambarin masarautar jiki, ajiyar zuciya nayi na zura zoben a ya tsana na tsakiya, sosai yay min kyau na mika mata hannuna, rikewa tayi ta goge fuskarta da fad'in "Yanda kika sa shi bana fatan duk rintsi ki cireshi inaso ya dawwama a hannunki har ranar mutuwarki."

Hannu nasa na goge mata fuska da fad'in "Ki daina hawaye rabona ne ya rantse har Mamma tayi min wannan kyautar abinda kawai nake bukata a gurin ki shine addua ki cigaba dayi min akan Allah ya cigaba da bani ikon rik'e amanarta.

Hannuna dake fuskata ta rike ta sumbata cikin kauna tace" Sumayya insha Allahu kina tare da nasara a rayuwarki ke kadai muka haifa ke muke gani muji dadi in Allah ya yarda adduarmu sai tayi tasiri a kanki." Murmushi nayi cikin jin dadi mayar da kayan cikin akwati hannu tasa tana taya ni.

Babana ma da shigo yaga abin arzikin dana samu yay ta murna yana farin ciki, yace idan anyi sallar isha'i sai na jagorance su suje suyi godiya, haka kuwa akayi muna idar da sallar muka tafi.....

Tare muka sameta da yaron nata yana kishingide a gefanta ita kuma tana zaune tana fuskantarsa da alama magana mai muhimanci sukeyi.....a nutse muka gaisa dasu, na kalleta da murmushi a tare dani nace"Ranki shi dade mahaifana sunyi farin ciki sosai da kyautar bajintar da kikayi min dalilin daya sa ma suke ce lallai sai na kawo su sunyi miki godiya bisa alkairin da kikayi min.


A nutse ta juya tana kallonsu fuskarta a sake tace"Haba Tambaya ai yarinyarku ta cancanci abinda yafi haka menena na zuwa godiya, ni wallahi Sumayya ta gama min komai data tsaya take kula da Babana babu abinda ba zan iya yi mata ba, saboda haka kada ku damu kanku akan duk wata kyauta da zanyiwa 'yarku domin ta cancani abinda yafi haka.

Cike da farin ciki sukayi kasa da kansu suna sake jaddada godiyarsu babana yace."Ranki ya dade kasa hakuri nayi nace lallai ta kawo mu mu mika godiyarmu a gurinki babu abinda zamu ce miki sai dai fatan gamawa da duniya lafiya, muna rokon ubangiji Allah ya tsare gabanki da bayanki Yarima Ali Allah ya kareshi daga sharrin abin'ki.'' Mamma Fulani cikin kulawa take amsawa, kafin ta bamu umarnin tafiya, kallon gefan da yake nayi, tun lokacin da muka shiga ya sunkuyar da kansa gashi har mun 'kare abinda ya kaimu mun mike bai dago kansa ba, hakika wannan 'bakin halin nasa na 'bata min rai! Babana ya durkusa kusa dashi da fadin"Ranka ya dade a tashi lafiya." Dukkaninmu bamuyi zaton zai amsa ba ballantana ya dago kansa, dalilin daya sa ma kenan lokacin daya dago nayi saurin sunkuyar da kaina ina mamaki! "A sauka lafiya nagode." Abinda yace kenan ya mayar da kansa kasa, Sai da mahaifana sukayi gaba sosai kana nabi bayansu, gaskiya naji dadi sosai dana ganshi rad'au dashi! sai na saki raina ina addua akan Allah ya kiyaye gaba.

****
Bayan sati biyu al'amura na tafiya sannu a hankali, yanzu ya daina ta'ba min jiki sai dai kullum cikin yi min masifa yake abu kadan idan na kuskure sai yayi min wulakancin da zanji tamkar na dora hannuwana a ka, haka dai nake ta daurewa ina kulawa dashi tare da saka idona akan dukkanin abinda zai cutarshi.....Moddibo yay tafiya shiyasa na dan samu nutsuwa, sai dai Gimbiya Lawisa dake yawan aikowa kirana idan naje zata bani lemo ko farfesu da girke girke tace lallai na bashi yaci jiki na rawa nake kar'ba kafin na fita sai na tabbatar mata da cewar zan cika aikinta, ina fitowa nake samun inda babu idanun mutane na haka rami na zuba a ciki.....haka mukeyi da ita kullum kuwa cikin kallon shashasha nake mata cikin zuciyata ina fadin dama ta daina wahalar da kanta domin na lura koda da asiri a kansa ba zai tank'waru! kamar yanda take so ba, kanyi dariya da mamaki a duk lokacin da zata kawo masa ziyara kullum basa abin arziki ko sun fara hira cikin mutunci ta koma fad'a ya ci mata mutuci tas amma saboda bata da zuciya bata sati zata sake zuwa nayi ta mamakin al'amarin tunda ni dai tunda nake dashi ban ta'ba gani yaje gurinta domin suyi hira ba, a zahirin gaskiya Son da take masa bai kai wanda yake mata ba kamar dai yanda take fad'a kullum shine har yanzu ba ta gane inda ya dosa ba, dariya na kanyi a duk lokacin da tayi wannan maganar a zahiri yana nuna mata bata gabansa amma sai kace dabba ta kasa ganewa.

Ina tsaka da aiki ta aiko kirana, nace aje ace mata gani nan zuwa." da sauri na gama had'a fruit salad samun sa nayi a kishingid'e a gurin da yake hutawa, aikin da ya saba yake yi latsa waya, tire din hannuna na ajiye kusa dashi a nutse nace"Ranka ya dade ga fruit salad din na had'a."

Wannan karon be k'yale ni ba, naga ya ajiye wayar tare da mi'kewa zaune, gani nayi ya zuba min ido yanayi min kallon da ya jima beyi min irinsa ba, sai jikina yay sanyi na tabbata akwai matsala tunda ya tsareni da ido.


"Meye tsakanin ki da Haruna ne? naga yana yawan bin ki kicin idan kina aiki.'' Shuru nayi ina nazarin abinda zance masa.

"Bakya ji ne."? a dakile yay maganar yana sake tsareni da ido.

Ajiyar zuciya na sauke na dago a nutse nace" Akwai kyakykyawar fahintar juna a tsakanina da Haruna bayan wannan babu wani abunda yake tsakanina dashi.

Cikin tsawa yace."Ke kada ki rainawa mutane hankali mana! wace irin fahimtar juna ce wannan? ace kullum yana binki a dik inda kike kada ku sake ku aikata min fasiqanci a guri wallahi tallahi kika sake na kama ku sai na d'auki babban mataki a kanku."


Na dinga kallonsa zuciya na tafarfasa tsabar bacin rai naji yawun bakina ya bushe guy nan bai ta'ba 'bata min rai irin yau ba amma bari nayi maganinsa.

Babu sukuni nace"Haruna kamaman namiji ne hakanan Sumayya kamammiyar macece, Haruna da Sumayya suna san junansu shiyasa suke nesa da junansu saboda suna so suyi aure mai tsabta, ranka ya d'ade shi fasiqi ya futa daban! ana gane fasiqi a fuska da ayyukansa ba duka mutane suka taru suka zama d'ay......Wawan! duka ya kaiwa bakina nayi saurin kaucewa ina kallonsa, idanunsa naga sunyi jawur! gabana ya dinga bugawa! "Me kike nufi da wannan maganar da kike."?
Cikin dauriya nace" Bana nufin komai ranka ya dad'e inaso na nuna maka cewar maganar da kayi a kan mu bata dace ba zargi haram....."Rufe min baki munufaka."!! katseni yay da wannan magana. shuru nayi ina kallonsa, ya jima yana kallon k'asan kilishin da yake zaune, ya dago ido jawur yace."Tashi ki fice min a guri bana bukatar kallon wannan bakar fuskar taki."

"Ranka ya dad'e kayi hak..! hannu ya daga min alamun baya so na karasa, shiru nayi na yunkura na mike.." Dauke tsiyarki banza 'kazama kawai."! banji ciwon zagin da yayi min ba saboda na riga na saba, tire din dake gabansa nake kallo a sanyaye nace"Kaine fa kace na had'a maka fruit sal.....Kafin na rufe bakina ya dago tire din ya watso min shi a jiki....gabadaya gaban rigarta da zanina ya 'baci 'kasan gurin da gefan kilishin ya lalace... wayoyinsa ya kwasa yana watsa min kallon banza ya bar gurin....ban dauke idona daga kansa ba har sai da na daina ganinshi....hawayen takaici ne suka shiga zubo min a fuska durkushewa nayi a gurin na dinga kukan da yake nema ya tarwatsa min zuciyata.



*Na kudi ne..*
Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina so ki biya kudin ki ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal #300...0542382124..binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number.
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*GAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
55&56
Samun sa nayi a tsaye a tsakiyar falon yana zagaye koda na shiga gefe guda na samu na tsuguna kaina na sunkuyar k'asa ina addua kada Allah yasa ya tozartani a gabanta dan na fahimci take takensa. bece min komai ba ya zauna kan kujera tare da d'ora kafa daya kan daya zaman yayi kama dana kasaita da nuna isa, ta kasan idona nake kallonsa yana ta girgiza kafa yana latsa waya, haka ta shigo ta same mu, kujera ta nema ta zauna, falon yayi shuru na tsayin minti goma a sace na kallesu shi yana can aikin latsa waya ita kuma alamun tsoro da fargaba na hango a cikin idonta.
kaina na mayar kasa ina jin faduwar gaba, ni da ita duk abu daya ne yake damun mu.

"Lawisa me Sumayya tayi miki da zaki sa Buba ya doke ta ."? A sanyaye tace" Laifi tayi min wanda ya fusata ni shine na yanke mata wannan hukuncin.''

"Ba kwana ki nayi miki magana akan hakan ba."? Yafada yana tsareta da ido, cikin dauriya tace" Naso nayi mata hukunci da kaina tayi min gardama shiyasa na kira buba ya koya mata hankali tunda dai ita bata da mutunci.
Saurin kallonta nayi muka hada ido ta watso min harara, kaina na sunkuyar ina jiran naji abinda zaice.

"Me tayi miki abinda nake son ji kenan."? yafada hankalinsa akan wayarsa.....ajiyar zuciya ta sauke tace" Yau tsayin wata kenan ina aikota ta kawo maka sa'ko ashe zuwa take ta zubar a wani guri daya daga cikin bayina suka sheda min koda na tambayeta ba tayi gardama ba ta tabbatar min da gaskiya ne al'amarin ya 'bata min rai sosai shiyasa na yanke mata wannan hukuncin."

Kallona ya shigayi yana gyada kansa yace."Wato ke ba zaki daina saka kanki a cikin abinda be shafe ki ba ko? shuru nayi yace."Me kike nufi akan abinda kike aikatawa ke kowa baki yarda dashi ba 'yan uwana zarginsu kike yi ke yafi kamata nayi zargi tunda kece bare amma na amince nake tarayya dake ban nuna miki komai ba to ki tashi ki fita ki bani guri bana bukatar sake ganinki a gurina dan na gaji da abinda kike min." kallonsa nake inaso nayi magana ya daga min hannu fuska a murtuke yace "bana bukatar sake ganinki a sashena 'yan uwana nawa ne idan kashe ni sukayi babu abinda ya shafe ki saboda haka tashi fice min daga falo."!
Cikin tsawa da kyara ya kare maganar.

Ji nayi gwiwa ta tayi sanyi ruwan hawaye ya taru a kwarmin idona ni kam wannan wulakanci ina zan kai shi, a sanyaye na mike na nufi kofa zuciyata na wani irin zafi......ina fita hawaye ya wanke min fuska, haruna ya tare ni guri muka samu muka zauna sai da nacu kukana na koshi tukkuna na fada masa yanda mukayi.

Yace." Ki daina kuka kada ki janyowa kanki ciwon kai ni wallahi naji dadi ma da haka ta faru saboda haka yanzu abinda za'ayi shine kije can sashen Fulani ina nufin mahaifiyarsa sai ki sheda mata abinda ke faruwa kin san hausawa nacewa ta inda aka hau tanan ake sauka.

Hanci na shaqa na goge fuskata tare da mikewa tsaye nace" dama dole naje na sanar mata dan saboda kada wani abu ya faru daga baya ta zarge ni da wani abu.

Mikewa yay yace."Muje na raka ki ki fada mata." Tare muka tafi muna sake tattaunar maganar.


Ta jima kafin ta dago kanta ganin b'acin rai a fuskarta yasa na sunkuyar da kaina kasa, tace"Sumayya duk naji maganarki raina kuma ya 'baci da irin wulakancin da babana yake miki yanzu ina laifin mai kula da kai abinda babana yayi miki ya bata min rai sosai kiyi hakuri Sumayya kada kiyi fushi kinji ko zaki cigaba da hidima dashi wallahi da ke kadai naji na aminta, ita kanta yarinyar da zai aura bata kwanta min a rai ba dan dai babu yanda zanyi ne tunda iyaye sun shiga cikin lamarin, zan sameshi zanyi masa fada sosai dole ya mutun taki ko dabbah ai tasan mai kyautata mata bare mutum saboda haka kije yanzu zan kirashi a waya zan zauna dashi zamuyi magana kuma zan nuna masa kuransa.

Daurewa nayi ina kokarin danne damuwata nace"Insha Allahu zanbi umarninki zan cigaba da dawainiya da Yarima kamar yanda kike so." Albarka ta dinga sa min kafin ta bani umarnin tafiya sallama nayi mata na fito
Haruna na tsaye yana jira na ina fitowa na fada masa duk yanda mukayi jikinsa ne naga yayi sanyi yace."Shikkenan Sumayya sai ki sake kiyayewa sannan ki daina yawan saka idonki akan 'yan uwansa tunda baya so ki rabu dashi idan da rabon yasha wuya ne shikkenan."

Shuru nayi kawai ina sauraransa bana jin zan iya zuba ido wani ya cutar dashi amana na daukarwa mahaifiyarsa zanyi iyakacin bakin k'okarina sai dai idan abin yafi karfina


A waya ta kira shi ta rufeshi da fad'a ta inda ta shiga bata nan take fita ba sosai ta nuna masa bacin ranta akan abinda yake yi mamaki ne ya rufeshi ashe yarinyar nan zuwa tayi ta had'ashi da mahaifiyarsa ransa idan yay dubu ya 'baci! tunda yake da mahaifiyarsa wani abu na sa'bani bai ta'ba shiga tsakaninsu ba sai ta dalilin yarinyar.....Girgiza kansa yayi ya shiga bata hakuri tace"Haba babana ai dole raina ya 'baci akan abinda kakeyi yarinyar nan kullum na dawainiya da kai amma kullum cikin cizguna mata kakeyi su 'yan uwan naka da kake fifitasu a kanta ba kaunarka sukeyi ba har yanzu ka kasa ganewa cewar kullum farautarka suke to mutukar kana kaunar farin cikina ka mutunta Sumayya bana san cin zarafin da kake mata ka sanja hali."

Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma naji na d'auki laifina insha Allah zan gyara na daina bana san kina fushi da 'bacin rai akan abinda bai kai ya kawo ba."

"Babana idan ka naso na daina bacin rai sai ka daina abubuwan da kake na rashin kyautawa tukkuna." Hannuwanta ya ri'ke yace."Insha Allahu na daina yarinyar ta dawo ta cigaba da aikinta shikkenan ko."? Ajiyar zuciya ta sauke tace"Shikkenan magana ai ta wuce na bata hakuri sosai anjima da daddare zata shigo ta baka abinci kaima sai ka nemi afuwarta dan Allah yana san haka.

Da mamaki a fuskarsa yake kallonta har abadah baya tsammanin zai iya bawa yarinyar hakuri akan wani laifi da yayi mata kawai dai ya amsa mata ne domin ta kwantar da hankalinta ta kuma daina 'bacin rai akan al'amarin.

To koda na koma gurin mu ban yarda na fadawa iyayena abinda ya faru ba kawai nace musu nayi mata wani aiki ne...Tambaya tace"Muna nan muna tattaunawa akan maganarki da Haruna dan gidan Labaran bayan fitarki yazo gurin babanki suka tattauna ashe dama soyayya ce a tsakaninku mu bamu sani ba."
Kunyace ta rufe ni nayi yar dariya ina kokarin shiga daki nace "Tambaya kenan." Babana dake zaune kan darduma yana murmushin farin ciki yace."Sumayya a gaskiya nayi farin ciki da wannan al'amari sosai na yaba da tarbiyar Haruna yana da nutsuwa da kintsi nayi imanin zai rike min ke da mutunci wannan dalilin yasa na amince da maganar amma na cewa mahaifin nasa sai na zauna dake kin sake tabbatar min da bakin ki.

Shuru nayi ina wasa da hannuwana, yace."Sumayya babu kunya a tsakanina dake ni mahaifin ki ki fada min shin kina son Haruna ko aa."

Murmushi nayi nace"Eh baba ina sonsa ina rokon Allah yasa shi din alkairi ne a tare dani." cike da farin ciki ya amsa da ameeen Sumayya ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkairi Allah yasa damu za'ayi."

Mikewa nayi ina jin kunya da nauyi na shiga daki, kayana na tube nayi shirin wanka.......Bayan nayi wanka naci abinci gurin karatu na nufa karfe biyar da rabi mun taso Lahira na bawa jakata nace ta kai min gurin mu kai tsaye sashen Yarima na nufa

A falo na same shi yana kallace-kallace a tv gaishe shi nayi ya'ki amsawa mikewa nayi na nufi kicin na shiga aikina............Tsaf na shirya mai abinci na jera komai kan tire mai fadi ina kokarin dauka ya fad'o kicin din.

Gabana ne ya fadi da sauri na risina ina gaishe shi, sama-sama ya amsa yace."Yawwa kin gama abincin ko."? kaina na daga masa gabana na bugawa.

Wata yar takarda ya ciro daga aljihunsa ya kwance cikin bada umarnin yace."Bude abincin.'' a sanyaye na bude fulas din, maganan ya zazzage a cikin miya yace ."Sa cokali ki juya sosai." da sauri nayi yanda yace."maza dauki muje." da sauri na rufe fulas din na dauki tire din hanya ya nuna min da hannunsa, na fito falon ina diri-diri!! cikin tsawa! yace."Wuce muje sama ki kai masa abincin yana can mutukar naji maganar nan ta fito sai na kashe ki."

Da sauri na shiga hawa benan har ina had'awa da biyu, shawarwari nake da zuciyata shawarar karshe na yanke da zuciyata, da gangan na gurde kafata na fadi a gurin sosai na bugu da karfen benan tire din abincin da abubuwan dake kai suka watse a gurin fallatsin miya har jikin rigarsa.

Cikin zafi nama ya mi'kar dani tsaye! wuyana ya matse yana tsuma yace."Kina sane kika zubar da abincin nan ko."? idanuwana sun gwalalo waje sabida wahalar sha'ka na girgiza kaina, alamun A'a, hannu ya fitar ya tsinka min mari wanda sai da hancina ya fashe na dinga jin dummm! a kunnena! dishi dishi nake kallonsa yana wani irin huci!! ya sake fitar da hannu zai mare ni, Yarima ya bude ya kofar dakinsa

Ganinta sha'ke a hannun Muddibo yasa da sauri ya k'arasa gurin kokarin cire hannunsa yake daga wuyana yana sake matse ni.....cikin b'acin rai yace."Muddibo wai me tayi maka ne ka matse mata wuya haka."? Yana huci yace."Ka duba jikina da kyau ka gani yarinyar bata san ta ratse a wani a gurin na wuce ba ta hada kafada da kafada dani har sai da ta samu nasarar 'bata min jiki da miya."

Kallon jikinsa yayi yaga duk jar miya a jikin rigarsa hakuri ya shiga bashi yana kokarin cire hannunsa dake d'amke da wuyana, da kyar Muddibo ya cika ni na zube a gurin ina tari makogwarona ya bushe sosai sai zare ido nakeyi ina kallonsu suka sauka k'asa a tare, sunkuyar da kaina nayi ina kiran sunan Allah a cikin zuciyata.



*Na kudi ne*
Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya ga yanda abin yake...Vip group #600 normal gruop#300 account....0542382124...Binta umar gtbank.....idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊?)
57&58
Sai da na samu nutsuwa tukkuna na mike jikina a mace na sauka 'kasa sunkuyar da kaina nayi ban yarda na kalli inda suke ba na wuce kicin tamkar kazar 'kwai ya fashewa a ciki. gabadaya jikina ya mutu ina tunanin da Muddibo ya samu nasara kashe ni yayi niyyar yi, tsintsiya da abin kwasar shara na dauko ina fitowa muka hada ido dashi, ganin fuskarsa nayi tamkar hadarin dake daf da zubar da ruwan sama da sauri na janye idona cikin zuciyata nace''duk wani abu da nake akanka inayi ne domin mahaifiyarka daba dan daraja da mutuncinta ba wallahi da bazan zauna ina wahalar da kaina ba......gurin na gyara tsaf nayi mopping dinshi ina kokarin sauka kasan sai gashi, ratsewa nayi na bashi hanya yazo daidai dani yana hararata da fadin"Na dauka nima kafad'a da kafad'ar zakiyi dani."

Sunkuyar da kaina kasa nayi ina Allah-Allah ya wuce dan bana bukatar tashin hankali

"Kizo ina san ganinki." Da sauri na dago kaina naga ya wuce ni yana kokarin bude dakinsa, sai da ya shiga tukkuna na ajiye mopper hannuna bayansa nabi ina adduar rinjaye.

Samun sa nayi kan sofa yayi zaman kasaita na tsuguna dan nesa dashi babu walwala a fuskata nace"Gani." sai daya mula tukkuna yace."Ashe haushi kika ji dan na kore ki daga sashena shine kikaje kika hadani da mahaifiyata ko."?

Babu fara'a a tare dani nace"Banji haushi ba wallahi sai ma farin ciki da nayi naje na fad'awa mahaifiyarka ne domin yana da kyau ta san cewar ka kore ni tunda itace ta turo ni nayi maka hidima ni ban fada mata domin na shiga tsakaninku ba."

Tsaki yaja yana min kallon kaskanci yace.''Ke dai kika sani munafuka kawai tunda kin nace sai kinyi min aiki sai kizo na saki aikin kuma wallahi kikayi min gardama ranki sai ya 'baci.''

"Ranka ya dade ko wane irin aiki ka sanya ni zanyi maka mutukar bai sha'ba sharia ba."

Shuru yayi min yana duban k'asa nasan idan ya tsirawa kasa ido yana daukar lokaci yasa nima na dauke kaina ina jiran ya gama.

sai da ya dauki mintina goma tukkuna yace."Shiga toilet ki hada kananun kayana ki wanke." ba tare da nace komai ba na mike na nufi toilet din.....Bin bayanta yayi da kallo har sai da ta shige ya dauke idonsa shi dai ya rasa yanda zaiyi da rayuwarsa sha'awarta kullum karuwa take yayi yayi ya cireta daga ranshi abin ya fassakara ya rasa wace irin masifa ce Allah ya dora masa.


Duk kananun kayansa dake toilet din sai da na wanke tas na shanya inda aka tanada toilet din na gyara yayi tsaf tsaf dashi na fito na same shi zaune a inda yake ya kurawa tv ido.....nishin dake tashi a cikin tv yasa nai saurin kallon gurin mace da namiji ne suke sex sai nishi suke namijin yana kan macan

Please Login or Register in order to submit comment